Kai kawai ya iya ɗaga masa, ta juya ta koma cikin ɗakin. Zaunawa ta yi tana sauke ajiyar zuciya, sai kuma ta kafe wayar da ido kamar mai shakkun kunnawa.
Can dai ta kunna wayar zuciyarta cike da fargaba, da tunani kala-kala. Gabanta ya soma faɗuwa lokacin da saƙwanni suka riƙa shigo mata bayan ta kunna wayar. Sai dai mafi yawanci su duka na Mtn ne, sai saƙo ɗaya mai ɗauke da number Yasmeen. Saƙon ta fara buɗewa, tana tunanin wane irin saƙo ne Yasmin ta aiko nata.
_Salam Namra na haihu na samu baby girl, na kira wayarki ban samu ba_
Murmushi ta yi tare da hawaye a lokaci ɗaya.
“Allah ya raya miki babyn ki, ya baki lafiyar shayarwa”
Shine furucin da tayi a fili, ta rumgume wayar ta lumshe ido.
‘Ya kamata na koma gida, ko me me zai faru ya faru a can, na yi kuskure tun farko da ban sauka gidan mu’
Tunanin da take a ranta kenan, kamin ta buɗe ido, ta fara kallon ɗakin.
“Gobe... Gobe ya kamata na je gida, an cire duk wani fargaba da yake rai na, zan cire tsoro zan gwada ƙarɓar sunana ko Alƙah zai za na dace, ba zaka taɓa winning ko losing ba matuƙar baka taɓa gwadawa ba, i hate to try”
A fili ta yi furucin zuciyarta cike da yaƙinin lallai zata iya, kuma ta shirya fuskantar ko wane irin hukunci na Abbah.
“Taya zai yafe min idan ban je ba? Taya zan shirya da Anty idan ban je ba? I have to do this, Allah ka taimake ni”
Komawa ta yi ta kwanta, zuciyarta cike da saƙe-saƙe kala-kala.
ABDOOL POV.
“Lafiya ƙalau aka ɗaura aure”
“Mashallah Allah ya nuna mana na ka, ya maka albarka”
“Amin Mai Martaba”
“Ka yi kyau sosai, ka fito kamar wani babban sarki”
Kallon Mamaki Abdool yayi kamar ance masa Mai Martaba yana tsaye gabansa.
“Waya faɗa maka?”
“Babu ruwanka, ai har hoton ka an turo min alkyabar ta karɓe ka sosai”
Dariya yayi cike da mamaki, dan shi dai be san ya ɗora hoton daya saka alkyaba ba a media balle yace ko wani ne ya tura masa.
“Mai martaba kasan ance informer hukunsu ɗaya da da mai fashi da makami ko”
“To ayi haƙuri Major ayi haƙuri muma muna kan aikin mu ne”
Ƙyalƙyalewa yayi da dariya daga shi har Mai Martaba, daga bisani Mai martaba ya ɗora da.
“Ƙarfe nawa zaka ta so?”
Shiru yayi kamar mai tunani, haka kawai ya samu kansa da rashin jindaɗin tafiyar.
“Zan turo maka dogarawan ka sai a bar min Sadauki, zamu kwana biyu kamin mu dawo”
“Why?”
“Just kawai ina son ganin kaduna ne, kasan rabo na sa kaduna since... I can't even remember”
Ya ɗan sosa kansa yana kallon titi da mutake ta kai kawo suna sha'aninsu.
“Fine as you wish, amman aikin ka fa”
“Mun samu hutu ai ko ka manta?”
“Haka ne, to ba matsala amman dai karka ɗauki lokaci i have surprise for you”
“Thank you super Dad”
Daga haka ya kashe wayar ya kalli Sadauki dake front seat ya ce.
“Mai Martaba ya ce sauran za su iya kama hanya yanzu kai kawai zaka tsaya sai jibi za mu koma”
“An gama Yarima, Allah ya ƙara maka lafiya”
Be amsa ba sai kawai ya maida hankalinsa kan titi. Can kuma ya kalli agogo hannunsa.
“Yaushe zamu isa Kaduna?”
“Allah ya taimaki Yarima, nan da minti goma sha biyar zamu isa”
Daga nan be sake cewa komai ba har suka isa masaukinsa. Su suka buɗe masa mota ya fito suka rufa masa baya suna masa kirari, iya ƙofar falon suka tsaya. Sai ya juyo ya kalli Sadauki ya ce.
“A ba ko wannensu 30k kai kuma ka shirya anjima zamu je mu duba marar lafiyar nan”
Sai da ya shige sannan suka janyo ƙofar suka rufe masa. Alkyabar jikinsa ya fara cirewa sannan ya buɗe maɓallan rigarsa, ya kishingida saman kujera, ya lumshe ido.
Tun da ya shiga ciki be fito ba sai da aka yi kiran sallah magariba daman basu baro zariya ba sai da aka yi la'asar.
Tare da Sadauki suka yi sallah a masallacin da ke kusa da gidan, sannan suka nufo gida. A hanyar su ta dawowa ne Abdool yake masa jan kunne.
“Bana son abunda kake min, karka sake ɗauko min takalmi ka aje min, kuma daga yau kar na sake jin wani kirari nawa a bakin ka, ka kira ni da Abdool kawai ko Yarima amman ba sai ka min kirare ba”
“Allah ya taimake ka za a daina”
Ya faɗa cikin girmamawa.
“Zaka iya tuna inda muka je gidan mai Napep ɗin nan da muka kaɗe?”
“Allah ya taimake ka, zan gane”
“To za mu koma mu duba shi, akwai canji a hannunka ko? Zamu siya musu fruits”
“An gama Yarima”
“Zan shiga na canja sai muje”
“A canja da kyau ɗan Sarki, Allah yaja zamanin ka”
Kallo ɗaya Abdool yayi masa ya kauda ido yana girgiza kai.
******************
Bayan salla magariba Uwani ta shigo ɗakin ta kunna mata kendir, ta aje mata maltina da Madara da kuma tea mai kauri, tare da biredi.
“Kuma ɗawainiya da ni na gode sosai”
Mirmushi Uwani ta yi
“Ba komai ai yi ma kai ne. Ki ci dai ki samu karfin jiki”
“Ni kaina ina son na samu ƙarfin jikin ko zan samu damar komawa gurin iyayena”
“Tafiya za ki yi?”
“Gobe na ke so idan Allah ya yarje min”
“Amman ina laifin ko nan da sati idan kin ƙara jin sauƙi?”
“Wata ƙila idan suka ga na samu sauƙi su ƙi karɓa na, amman ganina a hakan zai sa su tausaya min”
“Amman dai da kin yi haƙuri har ki ji sauƙi”
“Ina son tafiyar ne”
“To bari na faɗawa Neina”
Ta juya cikin rashin jidaɗi dan yanzu sun ɗan fara sabawa da Namra, zancen tafiyarta be mata daɗi ba.
“Neina wai kin ji Namra zata tafi”
Abunda ta fito tana faɗa kenan, ganin Yarima yasa ta yi saurin sadda kanta ƙasa jikinta ya shiga rawa.
“Barka da dare”
“Barka...”
Ya amsa kaɗan-kaɗan yana tsaye kan Lamido, dan ya kasa zama tun da ya shigo gidan yanzu ma ya samu kansa da ƙyamar gidan. Farar shadda dake jikinsa sai ƙara haska shi take. Uwani ta yi mamakin ganin sa ba dogorai, sai dai haka be hana ta gane shi ba.
Unƙurawa Lamido yayi ya tashi zaune daga kwance da yake, dan zuwan Abdool be sashi ya ɗago ba duk da cika masa ido da yayi, da kuma kwarjinin da ya yi masa, yana jin rashin sakewa da Abdool wata ƙila saboda ba matsayin ɗaya ba, ko kuma dan kaɗewar da yayi masa ne ya hana shi ganin farinsa sai haushinsa yake ji. A ƙoƙarinsa na avoiding ɗin Yarima ya kalli Uwani da Neina ya ce.
“Wani abu aka mata ne?”
“A'a wallahi sai dai ko ta gaji da zama ne, ko tana son ta koma Katsina ne”
Cewar Neina. Sai Uwani ta amsa da
“A'a wai ta ce tana son ta koma gida ne, ko zasu tausaya mata su karɓe ta, kuma wai gobe zata je, kamar wace ake kora”
“Amman Namra bata da tunani, taya zata koma gurin iyayenta cikin wannan hali?”
“Wlh kuwa, ni ma na ce ta yi haƙuri dai har gaba...”
Tsawa Sadauki ya katsawa Uwani, wanda shi kansa Lamido sai da ya zabura balle kuma Neina da daman jikinta rawa yake, ganin ɗan sarki tsaye a gidansu.
“Ke ƴar talakawa ba a wata magana a gaban Ɗan Sarki, kama kan ki ki iya bakin ki...”
Sosai Uwani ta shiga natsuwarta tsabar tsoro ma har ji tayi kamar ta amayar da hanjin cikinta. Abdool kuma wa watsa ma Sadauki Harara, dan sosai yake jin daɗin maganar da suke, sarau zuciyarsa ta raya masa da Namra ake, duk da bashi da tabbacin hakan.
Tsawar da Sadauki yayi ma Uwani ne yasa Namra ta san da akwai baƙo a gidan dan ta ji muryar da ba ta ɗan gidan ba. Hakan yasa ta aje maltinar dake hannunta, ta gyara tsawyuwar Hijabin dake jikinta ta leƙo ƙofar ɗakin.
Bata gane ko waye ba, bata kuma ta mu da ta sani ɗin ba, sai kawai ta juya ta koma ɗakin. Shi kam Abdool sarai ya gane ta, dan ya daɗe da haddace fuskarta, duk da duhun magariba ya fara saukowa hakan be hana shi gane ta ba.
Ya daidaita tsayuwar hannayensa da ke cikin aljihu, ya juya ba tare daya ce da su komai ba, sai sadauki ne yake musu Allah ya ƙara lafiya, duk suka amsa da Ameen ban da Lamido.
Be yarda yayi ma Abdool kallon banza ba, ko wata yassar magana sai da ya juya baya ya fice.
“Wani zai nunawa isa, girman kan tsiya”
“Aa Lamido karka jawa kanka, dan Allah ka iya bakin ka”
Neina ta faɗa zuciyarta cike da tsoro. Wani wawan tsaki Lamido yaja ya wuyar da fuskarsa zuwa ɗakin da Namra take ciki.
**************
Tafiya yake guda guda yana tsotsar bakinsa kamar mai shan minti. Jinginawa yayi da motar da suka zo, yana kallon Sadauki yana tsaya gefensa cike da ladabi.
“A bincika min baƙuwar fuskar da take gidan nan, wacce ta zo daga Katsina i can't recall her name amman ai ka ji yarinyar da suke magana akai ko?”
“Za a bincika, Allah yaja zamanin ka, ya ƙara maka lafiya”
Wannan karon Abdool da kansa yayi driver zuwa suka ɗauki hanyar masaukinsa, sai tariyar maganar su Uwani yake, yana analyzing.
ASIM POV.
Ledodin dake hannunsa ya dire mata yana sauke gajiya tare da miƙa mata ragowar canji.
“Yayi Kyau Asim kana ƙoƙari sosai. Ya kamata ka hutu kam nima zan je gida na da yake can cikin gari dan yata zata zo, kuma bata san ina wannan sana'ar ba, dole acan nake sauka idan zata zo, dan haka zaka yi hutun kwana biyu sai kaje gurin matar ka ku yi murnar mota ka ɗauke ta kuje gari ku shana”
Ya ɗan yi murmushi tare da sosa kansa, shi kansa ya jidaɗin wannan hutun da zata ba shi dan zai bashi dama ya je gurin baƙuwarsa, kuma daman can yana son ɗaukar Mardiya su fita gari.
“Ai bana da mata Hajiya bana da mata yanzu, ina dai kam nema”
Ta masa kallon rashin fahimta.
“ Kamar ya ba nasan kana da mata ba ada?”
“Eh mun ɗan samu matsala ne, har mun rabu ai”
“Subhanalillahi, kai kam Asim me ya kai ka?mata mai haƙuri da juriya haka? Me ta maka”
“Wlh Hajiya ta cika kwaɗayi ne, ga complain akan aiki nan, shiyasa kawai naga rabuwar ta fi, yanzu dai wata na ke so idan Allah ya yarda”
Idan ran Hajiya Sadiya yayi dubu ya ɓace a yanzu dam bata jidaɗin maganar nan ta Asim ba
“Amman Wallahi sam ba ka yi tunani ba, taya zaka sakin matar da ta rufa maka Asiri har haka, ka gaggauta mayarda matar ka matuƙar tana son mu shirya da kai, ni bana son ana ciwa mace mutuci”
“Wallahi Hajiya bana jin daɗin zama da ita ne, duk ita ce silar halin rayuwar dana shiga, sam arziki na da nata be haɗu ba, daman can ban yi istiƙara ba na aure ta, yanzu muna rabuwa komai nawa ya dawo daidai, arziki sai shigowa yake”
“Na dai faɗa maka, rufin asirin ka ka maida auren ka a yanzu duk inda matar ka take ka yi gaggawar mayar da ita shine kwanciyar hankalin ka, kaje ka yi tunani, ni sam bana son ana wulaƙanta mace akan aure, to kacewa iyayenta me? Sam dam baka da tunani Asim, idan ma akan aikin ka ai da ka yi sahawara da ni dole za mu samu mafita yadda za'ayi”
Miƙewa ta yi tsaye cike da ɓacin rai ta nƴfi ɗakinta. Shi kam Asim da kallo ya bi ta yana mamakin yadda ta haƙiƙan akan Namra kamar wata ƴar'uwata, tunani yake yi da ace ya fada nata gaskiyar rabuwarsu da Namra akan ciki ne wata ƙila ma ranta ya fi haka ɓaci.
[7/18, 8:12 PM] Khadeeja Candy♥: *68 NOT EDITED*
Ta ina zai fara neman ta? Taya ma zai je neman yarinyar da yake ganin rabuwa da ita kamar ya huta da ƙaya ne?
“Zata dawo, na san bata je gidan su ai da yanxu an kira ni, amman na san zata dawo gare ni dole, amman neman ta yanzu a gare ni ai aiki ne sabo, kuma zata jidaɗi sosai idan har na neme ta”
Abunda yake faɗa kenan yana tuƙa motarsa a hankali. Wayarsa ce ta yi ringing, da sauri ya ɗauka ganin mai kiran har da murmushi a fuskarsa.
“Hello Babe”
“Hey how are you?”
“Fine i'm just thinking of you”
“Kar ka damu ai gobe za mu haɗu, zaka gan ni a fuska nima na gan ka a fuska”
“I can't wait, me kike so a shirya miki?”
“Na yi waya da Mom nawa zata shirya min komai”
“Ya yi kyau lallai Mom tana ji da ƴar nan ta ta”
“Ai dole ta ji da ni, ni kaɗai gare ta, ko ƙawaye na ma Mom son su take balle kuma ni”
“Wow kai lallai ko zata so miji ki ma sosai”
“Sosai ma”
“Gaskiya na yi sa'ah”
“Sa'ah?”
“Eh mana, ai kin san dole Mom ta so ni sosai, to da ni mijin Nably ne right?”
“Uhnn. Yeah”
“Ko dai ban kwanta miki ba ne?”
“Idan baka kwanta min ba, ai ba zan tsaya ina baka lokaci na ba, ni fa ban ma yarda da rayuwar social media ba amman kai lokaci ɗaya ka shiga rai na sosai wallahi”
“Haka nake so kin san ni da gaske na ke yi wallahi auren ki zan yi matuƙar kika amince min”
“Wannan maganar ya kamata sai idan mun haɗu tukuna mu yi ta”
“To na bari gimbiyata”
“Zan duba abu sai na kira ka”
“Okay i love you”
“Thank you”
Daga haka ta katse kiran. Shi kuma ya mannawa wayar kiss zuciyarsa cike da farinciki dan har ga Allah yana ƙaunar Nabila, kuma ita yake fata ta maza matarsa ta biyu.
Wani tsiririn tsaki ya ja lokacin daya isa bakin gate ɗin gidansa, cox he hate one thing buɗe gate, gani yake a yanzu ya kamata ace buɗe masa ake, shi gaba ɗaya gidan ma ya ishe shi, plan ɗinsa a yanzu na samun sabon gida ne mai rai da lafiya, gidan da duk wanda ya kallesa sai yayi magana ba wannan ƙonanne ba.
Sai da ya fito ya buɗewa kansa gate ya shiga da Motar sannan ya dawo ya rufe gate ɗin. Kusa da BQ ya faka motarsa, ya faka motarsa ya buɗe ya fito, daga shigarsa cikin ɗakunan da suke BQ ɗin sai ya fara ya ƙuna fuska, like yana ƙyama, gurin duk ya yi datti kamar be taɓa zama a gurin ba. Da shigarsa ɗakin first thing da ya fara yi ɗauko murhun gawaye da ragowar gawai ɗin da Namra ta bari, ya zuba masa kanazir ɗin da Namra take kunna wuta da shi ya saka kofinta na roba na ƙyasta ashana, nan ta ke wutar ta kama, kamar an saka mata hetur.
Ƙamin tukunyarta ya ɗauka ya ɗauraye ya zuba mata ruwa, ya ɗora saman wutar sannan ya shiga ciki ya ɗauki tsintsina ya share ɗakin tsab kamar mace, ya ruba zuwa yayi mopping, sannan ya cire tufafin jikinsa ya ɗaura tawul, ya zo ya zube ruwan a roba ya sirka da ruwan sanyi, ya kai ɗaki.
Sai da ya tura kofar ɗakin, sannan ya cire tawul ɗin jikinsa ya zauna cikin robar, kamar wani ƙaramin yaro. Ƙasansa yake gasawa, dan har yanzu zafi yake masa duk da ya sha magani, kuma yana kan sha, amman gurin na masa zafi musamman idan zai duƙa ko kuma zai yi bayan gida.
Sai dai Hajiya ta faɗa masa dan yana sabon shiga ne da ya saba komai ba zai ji ba.
Ya samu kusan minti talatin a cikin ruwa, sannan ya tashi ya ɗaura tawul ɗin ya ɗauki ruwan ya zubar a can waje. Be da mu da ƙorar da tufafinsa na ɗazu suka yi ba, ya ɗauke su a haka ya saka, ya kwanta saman katifa, yana danna wayarsa.
Number Mama ya saka, duk da yana da ita a contact ɗinsa be tsaya nema ba sai kawai ya saka ya danna mata kira.
Ta daɗe tana ringing kamin ta ɗauka tana masa complain
“Ai na ɗauka na manta da ni, ka sake wata uwar”
“Hahha Mama kenan ni na isa duk duniyar nan ai bana da uwa kamar ki”
“Amman Ibrahim ace ko ɗan kiran nan na waya babu, babu aike, babu komai, daga na yi jinyarka ka warke shikenan Namratu ta karɓe min kai?”
“Wallahi Mama kina nan cikin rai na, kawai dai akwai irin da na ke ne, akwai kuɗin da nake jira ina son da na zo zan siya miki gida na nema miki mai aiki, na saka miki komai ba za ki nema ba”
“Ibrahim da gaske?”
“Wallahi Mama”
“Wane irin kuɗi ne wannan? Karka ka jefa kan ka a halaka, garin neman gira a rasa ido, zamani ya lalace tsafi ya yi yawa”
Dariya ya yi dan yasan abunda Mama take tsoro, kamar kar ace tsafi ne a bada ita.
“Ba tsafi na ke ba, kuma ko tsafi na ke ai ba zan bada ke ba, wannan matar data ɗauke ni aiki ce take ba ni kuɗi kuma kullum idan na mata ciniki a shagonta riba uku ake kasawa ita da biyu ni da ɗaya”
“Wane irin sana'ah ne haka?”
“Wayoyi ne mu ke sidawa, da zinari”
“Hahaha Mashallah, ka ga abun Allah ko? Sannu-sannu sai ka fi haka ma, ai ina nan ina maka addu'ah indai kuɗi ne suna nan zuwa”
“A cigaba da yi mana addu'ar nan ai ita cw ke bin mu. Nan da wata ɗaya zan zo gurin ki”
“To Allah ya yarda, ya dafa maka, ɗan Albarka, irin alheri”
Dariya ya yi kana ya ɗora da.
“Zan aiko miki kuɗi ta hanyar Yusufa, zai kawo miki dubu dari da hansi ki riƙe kamin na zo”
“Kai Alhamdulillah Ibrahim Allah ya biya ka yau ɗa na ne yake ba ni wannan kuɗi Allahu akbar...”
Sai kawai ta sa kuka. Shi kuma ya kashe wayar yana dariya, da ganin kuɗin a gare shi yanzu ai ba wani abun ba ne, he past that level, manyan su ma yake hange, he's feeling so high.
KALSOOM POV.
Life goes on yadda take tsammanin rayuwa ba haka ta zo mata ba,tana iya ƙoƙarinta wajen ganin ta kwamtar da hankalinta, 5ana koyar yadda zata yi rayuwa babu abokin rayuwarta, but she can't duk abunda take tunanin sauƙi ne a gareta, sai
Showing 177001 words to 180000 words out of 280121 words
“Zauna a ɗakin kawai, make yourself comfortable”
Kai kawai ya iya ɗaga masa, ta juya ta koma cikin ɗakin. Zaunawa ta yi tana sauke ajiyar zuciya, sai kuma ta kafe wayar da ido kamar mai shakkun kunnawa.
Can dai ta kunna wayar zuciyarta cike da fargaba, da tunani kala-kala. Gabanta ya soma faɗuwa lokacin da saƙwanni suka riƙa shigo mata bayan ta kunna wayar. Sai dai mafi yawanci su duka na Mtn ne, sai saƙo ɗaya mai ɗauke da number Yasmeen. Saƙon ta fara buɗewa, tana tunanin wane irin saƙo ne Yasmin ta aiko nata.
_Salam Namra na haihu na samu baby girl, na kira wayarki ban samu ba_
Murmushi ta yi tare da hawaye a lokaci ɗaya.
“Allah ya raya miki babyn ki, ya baki lafiyar shayarwa”
Shine furucin da tayi a fili, ta rumgume wayar ta lumshe ido.
‘Ya kamata na koma gida, ko me me zai faru ya faru a can, na yi kuskure tun farko da ban sauka gidan mu’
Tunanin da take a ranta kenan, kamin ta buɗe ido, ta fara kallon ɗakin.
“Gobe... Gobe ya kamata na je gida, an cire duk wani fargaba da yake rai na, zan cire tsoro zan gwada ƙarɓar sunana ko Alƙah zai za na dace, ba zaka taɓa winning ko losing ba matuƙar baka taɓa gwadawa ba, i hate to try”
A fili ta yi furucin zuciyarta cike da yaƙinin lallai zata iya, kuma ta shirya fuskantar ko wane irin hukunci na Abbah.
“Taya zai yafe min idan ban je ba? Taya zan shirya da Anty idan ban je ba? I have to do this, Allah ka taimake ni”
Komawa ta yi ta kwanta, zuciyarta cike da saƙe-saƙe kala-kala.
ABDOOL POV.
“Lafiya ƙalau aka ɗaura aure”
“Mashallah Allah ya nuna mana na ka, ya maka albarka”
“Amin Mai Martaba”
“Ka yi kyau sosai, ka fito kamar wani babban sarki”
Kallon Mamaki Abdool yayi kamar ance masa Mai Martaba yana tsaye gabansa.
“Waya faɗa maka?”
“Babu ruwanka, ai har hoton ka an turo min alkyabar ta karɓe ka sosai”
Dariya yayi cike da mamaki, dan shi dai be san ya ɗora hoton daya saka alkyaba ba a media balle yace ko wani ne ya tura masa.
“Mai martaba kasan ance informer hukunsu ɗaya da da mai fashi da makami ko”
“To ayi haƙuri Major ayi haƙuri muma muna kan aikin mu ne”
Ƙyalƙyalewa yayi da dariya daga shi har Mai Martaba, daga bisani Mai martaba ya ɗora da.
“Ƙarfe nawa zaka ta so?”
Shiru yayi kamar mai tunani, haka kawai ya samu kansa da rashin jindaɗin tafiyar.
“Zan turo maka dogarawan ka sai a bar min Sadauki, zamu kwana biyu kamin mu dawo”
“Why?”
“Just kawai ina son ganin kaduna ne, kasan rabo na sa kaduna since... I can't even remember”
Ya ɗan sosa kansa yana kallon titi da mutake ta kai kawo suna sha'aninsu.
“Fine as you wish, amman aikin ka fa”
“Mun samu hutu ai ko ka manta?”
“Haka ne, to ba matsala amman dai karka ɗauki lokaci i have surprise for you”
“Thank you super Dad”
Daga haka ya kashe wayar ya kalli Sadauki dake front seat ya ce.
“Mai Martaba ya ce sauran za su iya kama hanya yanzu kai kawai zaka tsaya sai jibi za mu koma”
“An gama Yarima, Allah ya ƙara maka lafiya”
Be amsa ba sai kawai ya maida hankalinsa kan titi. Can kuma ya kalli agogo hannunsa.
“Yaushe zamu isa Kaduna?”
“Allah ya taimaki Yarima, nan da minti goma sha biyar zamu isa”
Daga nan be sake cewa komai ba har suka isa masaukinsa. Su suka buɗe masa mota ya fito suka rufa masa baya suna masa kirari, iya ƙofar falon suka tsaya. Sai ya juyo ya kalli Sadauki ya ce.
“A ba ko wannensu 30k kai kuma ka shirya anjima zamu je mu duba marar lafiyar nan”
“An gama Yarima, takawarka lafiya ɗan sarki jikan sarki, an gama ɗan adalin Sarki”
Sai da ya shige sannan suka janyo ƙofar suka rufe masa. Alkyabar jikinsa ya fara cirewa sannan ya buɗe maɓallan rigarsa, ya kishingida saman kujera, ya lumshe ido.
Tun da ya shiga ciki be fito ba sai da aka yi kiran sallah magariba daman basu baro zariya ba sai da aka yi la'asar.
Tare da Sadauki suka yi sallah a masallacin da ke kusa da gidan, sannan suka nufo gida. A hanyar su ta dawowa ne Abdool yake masa jan kunne.
“Bana son abunda kake min, karka sake ɗauko min takalmi ka aje min, kuma daga yau kar na sake jin wani kirari nawa a bakin ka, ka kira ni da Abdool kawai ko Yarima amman ba sai ka min kirare ba”
“Allah ya taimake ka za a daina”
Ya faɗa cikin girmamawa.
“Zaka iya tuna inda muka je gidan mai Napep ɗin nan da muka kaɗe?”
“Allah ya taimake ka, zan gane”
“To za mu koma mu duba shi, akwai canji a hannunka ko? Zamu siya musu fruits”
“An gama Yarima”
“Zan shiga na canja sai muje”
“A canja da kyau ɗan Sarki, Allah yaja zamanin ka”
Kallo ɗaya Abdool yayi masa ya kauda ido yana girgiza kai.
******************
Bayan salla magariba Uwani ta shigo ɗakin ta kunna mata kendir, ta aje mata maltina da Madara da kuma tea mai kauri, tare da biredi.
“Kuma ɗawainiya da ni na gode sosai”
Mirmushi Uwani ta yi
“Ba komai ai yi ma kai ne. Ki ci dai ki samu karfin jiki”
“Ni kaina ina son na samu ƙarfin jikin ko zan samu damar komawa gurin iyayena”
“Tafiya za ki yi?”
“Gobe na ke so idan Allah ya yarje min”
“Amman ina laifin ko nan da sati idan kin ƙara jin sauƙi?”
“Wata ƙila idan suka ga na samu sauƙi su ƙi karɓa na, amman ganina a hakan zai sa su tausaya min”
“Amman dai da kin yi haƙuri har ki ji sauƙi”
“Ina son tafiyar ne”
“To bari na faɗawa Neina”
Ta juya cikin rashin jidaɗi dan yanzu sun ɗan fara sabawa da Namra, zancen tafiyarta be mata daɗi ba.
“Neina wai kin ji Namra zata tafi”
Abunda ta fito tana faɗa kenan, ganin Yarima yasa ta yi saurin sadda kanta ƙasa jikinta ya shiga rawa.
“Barka da dare”
“Barka...”
Ya amsa kaɗan-kaɗan yana tsaye kan Lamido, dan ya kasa zama tun da ya shigo gidan yanzu ma ya samu kansa da ƙyamar gidan. Farar shadda dake jikinsa sai ƙara haska shi take. Uwani ta yi mamakin ganin sa ba dogorai, sai dai haka be hana ta gane shi ba.
Unƙurawa Lamido yayi ya tashi zaune daga kwance da yake, dan zuwan Abdool be sashi ya ɗago ba duk da cika masa ido da yayi, da kuma kwarjinin da ya yi masa, yana jin rashin sakewa da Abdool wata ƙila saboda ba matsayin ɗaya ba, ko kuma dan kaɗewar da yayi masa ne ya hana shi ganin farinsa sai haushinsa yake ji. A ƙoƙarinsa na avoiding ɗin Yarima ya kalli Uwani da Neina ya ce.
“Wani abu aka mata ne?”
“A'a wallahi sai dai ko ta gaji da zama ne, ko tana son ta koma Katsina ne”
Cewar Neina. Sai Uwani ta amsa da
“A'a wai ta ce tana son ta koma gida ne, ko zasu tausaya mata su karɓe ta, kuma wai gobe zata je, kamar wace ake kora”
“Amman Namra bata da tunani, taya zata koma gurin iyayenta cikin wannan hali?”
“Wlh kuwa, ni ma na ce ta yi haƙuri dai har gaba...”
Tsawa Sadauki ya katsawa Uwani, wanda shi kansa Lamido sai da ya zabura balle kuma Neina da daman jikinta rawa yake, ganin ɗan sarki tsaye a gidansu.
“Ke ƴar talakawa ba a wata magana a gaban Ɗan Sarki, kama kan ki ki iya bakin ki...”
Sosai Uwani ta shiga natsuwarta tsabar tsoro ma har ji tayi kamar ta amayar da hanjin cikinta. Abdool kuma wa watsa ma Sadauki Harara, dan sosai yake jin daɗin maganar da suke, sarau zuciyarsa ta raya masa da Namra ake, duk da bashi da tabbacin hakan.
Tsawar da Sadauki yayi ma Uwani ne yasa Namra ta san da akwai baƙo a gidan dan ta ji muryar da ba ta ɗan gidan ba. Hakan yasa ta aje maltinar dake hannunta, ta gyara tsawyuwar Hijabin dake jikinta ta leƙo ƙofar ɗakin.
Bata gane ko waye ba, bata kuma ta mu da ta sani ɗin ba, sai kawai ta juya ta koma ɗakin. Shi kam Abdool sarai ya gane ta, dan ya daɗe da haddace fuskarta, duk da duhun magariba ya fara saukowa hakan be hana shi gane ta ba.
Ya daidaita tsayuwar hannayensa da ke cikin aljihu, ya juya ba tare daya ce da su komai ba, sai sadauki ne yake musu Allah ya ƙara lafiya, duk suka amsa da Ameen ban da Lamido.
Be yarda yayi ma Abdool kallon banza ba, ko wata yassar magana sai da ya juya baya ya fice.
“Wani zai nunawa isa, girman kan tsiya”
“Aa Lamido karka jawa kanka, dan Allah ka iya bakin ka”
Neina ta faɗa zuciyarta cike da tsoro. Wani wawan tsaki Lamido yaja ya wuyar da fuskarsa zuwa ɗakin da Namra take ciki.
**************
Tafiya yake guda guda yana tsotsar bakinsa kamar mai shan minti. Jinginawa yayi da motar da suka zo, yana kallon Sadauki yana tsaya gefensa cike da ladabi.
“A bincika min baƙuwar fuskar da take gidan nan, wacce ta zo daga Katsina i can't recall her name amman ai ka ji yarinyar da suke magana akai ko?”
“Za a bincika, Allah yaja zamanin ka, ya ƙara maka lafiya”
Wannan karon Abdool da kansa yayi driver zuwa suka ɗauki hanyar masaukinsa, sai tariyar maganar su Uwani yake, yana analyzing.
ASIM POV.
Ledodin dake hannunsa ya dire mata yana sauke gajiya tare da miƙa mata ragowar canji.
“Yayi Kyau Asim kana ƙoƙari sosai. Ya kamata ka hutu kam nima zan je gida na da yake can cikin gari dan yata zata zo, kuma bata san ina wannan sana'ar ba, dole acan nake sauka idan zata zo, dan haka zaka yi hutun kwana biyu sai kaje gurin matar ka ku yi murnar mota ka ɗauke ta kuje gari ku shana”
Ya ɗan yi murmushi tare da sosa kansa, shi kansa ya jidaɗin wannan hutun da zata ba shi dan zai bashi dama ya je gurin baƙuwarsa, kuma daman can yana son ɗaukar Mardiya su fita gari.
“Ai bana da mata Hajiya bana da mata yanzu, ina dai kam nema”
Ta masa kallon rashin fahimta.
“ Kamar ya ba nasan kana da mata ba ada?”
“Eh mun ɗan samu matsala ne, har mun rabu ai”
“Subhanalillahi, kai kam Asim me ya kai ka?mata mai haƙuri da juriya haka? Me ta maka”
“Wlh Hajiya ta cika kwaɗayi ne, ga complain akan aiki nan, shiyasa kawai naga rabuwar ta fi, yanzu dai wata na ke so idan Allah ya yarda”
Idan ran Hajiya Sadiya yayi dubu ya ɓace a yanzu dam bata jidaɗin maganar nan ta Asim ba
“Amman Wallahi sam ba ka yi tunani ba, taya zaka sakin matar da ta rufa maka Asiri har haka, ka gaggauta mayarda matar ka matuƙar tana son mu shirya da kai, ni bana son ana ciwa mace mutuci”
“Wallahi Hajiya bana jin daɗin zama da ita ne, duk ita ce silar halin rayuwar dana shiga, sam arziki na da nata be haɗu ba, daman can ban yi istiƙara ba na aure ta, yanzu muna rabuwa komai nawa ya dawo daidai, arziki sai shigowa yake”
“Na dai faɗa maka, rufin asirin ka ka maida auren ka a yanzu duk inda matar ka take ka yi gaggawar mayar da ita shine kwanciyar hankalin ka, kaje ka yi tunani, ni sam bana son ana wulaƙanta mace akan aure, to kacewa iyayenta me? Sam dam baka da tunani Asim, idan ma akan aikin ka ai da ka yi sahawara da ni dole za mu samu mafita yadda za'ayi”
Miƙewa ta yi tsaye cike da ɓacin rai ta nƴfi ɗakinta. Shi kam Asim da kallo ya bi ta yana mamakin yadda ta haƙiƙan akan Namra kamar wata ƴar'uwata, tunani yake yi da ace ya fada nata gaskiyar rabuwarsu da Namra akan ciki ne wata ƙila ma ranta ya fi haka ɓaci.
[7/18, 8:12 PM] Khadeeja Candy♥: *68 NOT EDITED*
Ta ina zai fara neman ta? Taya ma zai je neman yarinyar da yake ganin rabuwa da ita kamar ya huta da ƙaya ne?
“Zata dawo, na san bata je gidan su ai da yanxu an kira ni, amman na san zata dawo gare ni dole, amman neman ta yanzu a gare ni ai aiki ne sabo, kuma zata jidaɗi sosai idan har na neme ta”
Abunda yake faɗa kenan yana tuƙa motarsa a hankali. Wayarsa ce ta yi ringing, da sauri ya ɗauka ganin mai kiran har da murmushi a fuskarsa.
“Hello Babe”
“Hey how are you?”
“Fine i'm just thinking of you”
“Kar ka damu ai gobe za mu haɗu, zaka gan ni a fuska nima na gan ka a fuska”
“I can't wait, me kike so a shirya miki?”
“Na yi waya da Mom nawa zata shirya min komai”
“Ya yi kyau lallai Mom tana ji da ƴar nan ta ta”
“Ai dole ta ji da ni, ni kaɗai gare ta, ko ƙawaye na ma Mom son su take balle kuma ni”
“Wow kai lallai ko zata so miji ki ma sosai”
“Sosai ma”
“Gaskiya na yi sa'ah”
“Sa'ah?”
“Eh mana, ai kin san dole Mom ta so ni sosai, to da ni mijin Nably ne right?”
“Uhnn. Yeah”
“Ko dai ban kwanta miki ba ne?”
“Idan baka kwanta min ba, ai ba zan tsaya ina baka lokaci na ba, ni fa ban ma yarda da rayuwar social media ba amman kai lokaci ɗaya ka shiga rai na sosai wallahi”
“Haka nake so kin san ni da gaske na ke yi wallahi auren ki zan yi matuƙar kika amince min”
“Wannan maganar ya kamata sai idan mun haɗu tukuna mu yi ta”
“To na bari gimbiyata”
“Zan duba abu sai na kira ka”
“Okay i love you”
“Thank you”
Daga haka ta katse kiran. Shi kuma ya mannawa wayar kiss zuciyarsa cike da farinciki dan har ga Allah yana ƙaunar Nabila, kuma ita yake fata ta maza matarsa ta biyu.
Wani tsiririn tsaki ya ja lokacin daya isa bakin gate ɗin gidansa, cox he hate one thing buɗe gate, gani yake a yanzu ya kamata ace buɗe masa ake, shi gaba ɗaya gidan ma ya ishe shi, plan ɗinsa a yanzu na samun sabon gida ne mai rai da lafiya, gidan da duk wanda ya kallesa sai yayi magana ba wannan ƙonanne ba.
Sai da ya fito ya buɗewa kansa gate ya shiga da Motar sannan ya dawo ya rufe gate ɗin. Kusa da BQ ya faka motarsa, ya faka motarsa ya buɗe ya fito, daga shigarsa cikin ɗakunan da suke BQ ɗin sai ya fara ya ƙuna fuska, like yana ƙyama, gurin duk ya yi datti kamar be taɓa zama a gurin ba. Da shigarsa ɗakin first thing da ya fara yi ɗauko murhun gawaye da ragowar gawai ɗin da Namra ta bari, ya zuba masa kanazir ɗin da Namra take kunna wuta da shi ya saka kofinta na roba na ƙyasta ashana, nan ta ke wutar ta kama, kamar an saka mata hetur.
Ƙamin tukunyarta ya ɗauka ya ɗauraye ya zuba mata ruwa, ya ɗora saman wutar sannan ya shiga ciki ya ɗauki tsintsina ya share ɗakin tsab kamar mace, ya ruba zuwa yayi mopping, sannan ya cire tufafin jikinsa ya ɗaura tawul, ya zo ya zube ruwan a roba ya sirka da ruwan sanyi, ya kai ɗaki.
Sai da ya tura kofar ɗakin, sannan ya cire tawul ɗin jikinsa ya zauna cikin robar, kamar wani ƙaramin yaro. Ƙasansa yake gasawa, dan har yanzu zafi yake masa duk da ya sha magani, kuma yana kan sha, amman gurin na masa zafi musamman idan zai duƙa ko kuma zai yi bayan gida.
Sai dai Hajiya ta faɗa masa dan yana sabon shiga ne da ya saba komai ba zai ji ba.
Ya samu kusan minti talatin a cikin ruwa, sannan ya tashi ya ɗaura tawul ɗin ya ɗauki ruwan ya zubar a can waje. Be da mu da ƙorar da tufafinsa na ɗazu suka yi ba, ya ɗauke su a haka ya saka, ya kwanta saman katifa, yana danna wayarsa.
Number Mama ya saka, duk da yana da ita a contact ɗinsa be tsaya nema ba sai kawai ya saka ya danna mata kira.
Ta daɗe tana ringing kamin ta ɗauka tana masa complain
“Ai na ɗauka na manta da ni, ka sake wata uwar”
“Hahha Mama kenan ni na isa duk duniyar nan ai bana da uwa kamar ki”
“Amman Ibrahim ace ko ɗan kiran nan na waya babu, babu aike, babu komai, daga na yi jinyarka ka warke shikenan Namratu ta karɓe min kai?”
“Wallahi Mama kina nan cikin rai na, kawai dai akwai irin da na ke ne, akwai kuɗin da nake jira ina son da na zo zan siya miki gida na nema miki mai aiki, na saka miki komai ba za ki nema ba”
“Ibrahim da gaske?”
“Wallahi Mama”
“Wane irin kuɗi ne wannan? Karka ka jefa kan ka a halaka, garin neman gira a rasa ido, zamani ya lalace tsafi ya yi yawa”
Dariya ya yi dan yasan abunda Mama take tsoro, kamar kar ace tsafi ne a bada ita.
“Ba tsafi na ke ba, kuma ko tsafi na ke ai ba zan bada ke ba, wannan matar data ɗauke ni aiki ce take ba ni kuɗi kuma kullum idan na mata ciniki a shagonta riba uku ake kasawa ita da biyu ni da ɗaya”
“Wane irin sana'ah ne haka?”
“Wayoyi ne mu ke sidawa, da zinari”
“Hahaha Mashallah, ka ga abun Allah ko? Sannu-sannu sai ka fi haka ma, ai ina nan ina maka addu'ah indai kuɗi ne suna nan zuwa”
“A cigaba da yi mana addu'ar nan ai ita cw ke bin mu. Nan da wata ɗaya zan zo gurin ki”
“To Allah ya yarda, ya dafa maka, ɗan Albarka, irin alheri”
Dariya ya yi kana ya ɗora da.
“Zan aiko miki kuɗi ta hanyar Yusufa, zai kawo miki dubu dari da hansi ki riƙe kamin na zo”
“Kai Alhamdulillah Ibrahim Allah ya biya ka yau ɗa na ne yake ba ni wannan kuɗi Allahu akbar...”
Sai kawai ta sa kuka. Shi kuma ya kashe wayar yana dariya, da ganin kuɗin a gare shi yanzu ai ba wani abun ba ne, he past that level, manyan su ma yake hange, he's feeling so high.
KALSOOM POV.
Life goes on yadda take tsammanin rayuwa ba haka ta zo mata ba,tana iya ƙoƙarinta wajen ganin ta kwamtar da hankalinta, 5ana koyar yadda zata yi rayuwa babu abokin rayuwarta, but she can't duk abunda take tunanin sauƙi ne a gareta, sai
Book Chapters
Chapter 1Chapter 2Chapter 3Chapter 4Chapter 5Chapter 6Chapter 7Chapter 8Chapter 9Chapter 10Chapter 11Chapter 12Chapter 13Chapter 14Chapter 15Chapter 16Chapter 17Chapter 18Chapter 19Chapter 20Chapter 21Chapter 22Chapter 23Chapter 24Chapter 25Chapter 26Chapter 27Chapter 28Chapter 29Chapter 30Chapter 31Chapter 32Chapter 33Chapter 34Chapter 35Chapter 36Chapter 37Chapter 38Chapter 39Chapter 40Chapter 41Chapter 42Chapter 43Chapter 44Chapter 45Chapter 46Chapter 47Chapter 48Chapter 49Chapter 50Chapter 51Chapter 52Chapter 53Chapter 54Chapter 55Chapter 56Chapter 57Chapter 58Chapter 59Chapter 60 Chapter 61Chapter 62Chapter 63Chapter 64Chapter 65Chapter 66Chapter 67Chapter 68Chapter 69Chapter 70Chapter 71Chapter 72Chapter 73Chapter 74Chapter 75Chapter 76Chapter 77Chapter 78Chapter 79Chapter 80Chapter 81Chapter 82Chapter 83Chapter 84Chapter 85Chapter 86Chapter 87Chapter 88Chapter 89Chapter 90Chapter 91Chapter 92Chapter 93Chapter 94