“Ina son ka yafe mata abunda ta yi maka, ko da ba zaka zauna da ita ba, ni zan zauna da ita a matsayin ƴata, daman ni gida na gidan ƴaƴa ne, amman idan ka yafe mata kuma ka saka mata albarka zata ga haske a rayuwarta”
Abbah ya sauke ajiyar zuciya.
“Allah ya taimake ka, ba wai bana son Namra ba ne, kawai ta aikata min abunda ban taɓa mafarkin zata aikata min ba ne, ta zaɓi wani sama da ni, ta bar karatun ta da danginta saboda shi...”
“Wallahi ta yi nadama yanzu, abunda kawai Mai Martaba yake so ka yafe mata mu zamu zauna da ita”
Abdool ya faɗa yana mai saukowa ƙasa ya zauna kusa da Abbah. Anty Amarya ta ɗago ta kalli Abdool.
“Idan har ya yafe mata, ni na fi kowa cancantar na zauna da ƴa ta”
Abbah ya data kai ya kalli Anty Amarya sannan ya kalli Mai Martaba.
“Mamana ta shiga rigarka ta samu alfarmarka, duk da yake ina jiran zuwan wannan ranar da Mamana zata gane kuskure da kuma gangancin abunda ta aikata, na sani wata zata dawo a gareni ko da kuwa mijinta be wulaƙanta ba, nasani wata rana zata gane muhimmancin iyaye, da kuma irin gudumawar da suke badawa a rayuwa, ko da babu saki na sani akwai ciwo, ba fata nake mata ba, amman nasan wata rana zai iya kamata ba duk miji bane yake zama da mace mai wani ciwo, sam bana son na mutu na bar Mamana a cikin halin da ta zaɓi kasancewa a ciki, na sani wata rana zata ratu ba ni, sai dai bana son ta rayu a cikin halin ina fushi da ita, dan nasan ba zata ga dai-dai, ina son Mamana sosai, kuma na yafe mata duniya da lahira”
Mai Martaba yayi murmushin ƙasaita irin nasu na manya.
“Lallai kana son ƙulla abota da ni”
Abdool ma yayi dariya mai cike da farinciki da har suka bayyana haƙoransa da kuma dimples ɗinsa ya ce
“Ni da Mai Martaba muna godiya”
Anty Amarya ta share hawayen idonta tana murmushi.
“Dan Allah idan tana cikin gidan nan ku faɗa mata Mahaifinta ya yafe mata, ta fito mu ganta”
“Bata tare da mu, tana can a Kaduna a wani gida rakuɓe, bata san Mai Martaba ya aika maka ba, ni ne kawai na ga tana cikin matsala kuma na san irin matsalar da rashin zama kusa da iyaye yake haifarwa”
“Allah ya maka albarka Allah ya raya maka iyalanka, ya cika maka burinka, ya taimake ka akan dukan lamurranka, na gode sosai yadda ki yi wannan jihadin Allah ya baka abunda kake so”
Ya amsa da “Amin” Yana wani sunsun da kai, shi ala dole ga surukin da ba san da shi ba 😂.
Mai Martaba ya miƙawa Abbah hannu yana murmushi.
“Yanzu kam zamu yi gaisuwar mutunci da kai, kaga har ƙoƙarin raba uwa da ƴa kake.”
Mai Martaba ya faɗa yana miƙewa tsaye. Da sauri Abbah ya miƙe tsaye, da hannunsa biyu ya riƙa hannun Mai Martaba yana dariya.
“Tuba na ke ranka ya daɗe, Allah yaja kwanan ka”
Juyawa Mai Martaba ya juya Abdool ya miƙe tsaye da sauri ya take masa baya. Har turakarsa Abdool ya rakashi farincike shinfiɗe a fuskarsa, Mai Martaba na shiga Babban falonsa Abdool ya riƙa alƙyabarsa ya cire masa ya jingine, sannan Mai Martaba ya cire rawaninsa da kansa ya aje a gefe, da sauri Abdool ya ɗauki rawanin ya aje a muhalinsa. Sannan ya zo ya zauna ƙasan carpet ya dafa ƙafafun Mai Martaba yana dariya.
“Na gode sosai da karamcin da Mai Martaba yayi min, ba zan taɓa manta wannan ba, Allah ya ja zamanin ka”
Murmushi yayi sai da aka ɗauki daƙiƙu sannan Mai Martaba ya amsa da
“Amin. Nan da minti talatin zamu je ɗan dime ƙaddamar da zakka, idan da hali sai ka shirya muje”
“...A...”
Sai kuma yayi shiru. Kallonsa kawai Mai Martaba yayi hakan ya cilastashi ƙarasa maganar.
“Da naso naje ne can Kaduna na kai su inda take”
Mai Martaba ya sake kallon ɗansa, irin kallon nan na akwai wani abu a ƙasa.
“Babana be kamata kana saka kanka a cikin irin wannan rayuwarba, karka manta kai ɗan sarki ne, kuma nan gaba kaɗan kai Sarki ne, sannan kai mutun ne mai babban muƙami a nigeria, be kamata ana ganin fuskarka a ko'ina ba, wani gurin kamata yayi ka aika, ko kasa ayi. Shi babban mutum ba ko ina ake son yana kasancewa ba, musamman ƴaƴan sarakuna, yana janyo raini, wani gurin ma yakan zubar da mutumcin mutum, amman kai sai naga kamar baka damu da hakan ba”
Yayi ƙasa da kansa, dan yasan Mai Martaba ya faɗi gaskiya, sai dai shi kan har ga Allah yana son ya zama na farko da zai fara yi ma Namra wannan albishir ɗin ko ba komai zai ƙara kwarjini a idonta.
“Amman Mai Martaba ina son na kasance nina zan yi ma yarinyar nan Albishir, idan mun kama hanyar Kaduna yanzu kasan kamin yamma mun isa”
Mai Martaba ya shafa fuskarsa.
“Idan har ganinta kake son yi, zaka iya aikawa a taho da ita”
“She's so stubborn ba lallai bane ta zo, kuma abun zai fi burgewa idan iyayenta da kan su sukaje suka ɗauko ta”
Kallon tsab Mai Martaba yayi ma Abdool sai ya ɗauke kansa, tare da ɗaga masa hannu, alamar go ahead.
*** **** ****
Fitar da Mai Martaba da Abdool suka yi ne, yaba Anty Amarya damar data kai ta ƙare ma Faɗar kallo. Manyan hotuna da ta gani na Abdool ɗaya a cikin kayan sarauta ɗaya kuma a cikin kakin soja, yanzu kan sarai ta tuna waye Abdool. Mutumen da ya taɓa taimaka mata lokacin da motarsu ta lalace ana ruwan sama.
“Gaskiya yana da kirki, matar ka da ƴaƴanka sun yi dacen uba na gari”
Ta faɗa idonta kan hoton Abdool. Abbah dai be ce komai ba, sai fama idonsa abinci yake yana shaƙar daddaɗan ƙamshin dake tashi faɗar.
Fitowar Abdool ne yasa duk suka maida dubansu gurinsa. Wata shigar ce a jikinsa bata ɗazun ba, wannan ma ta fitar da kyausa, da kuma annurin fuskarsa. Zuwa yayi ya risina gabansu, ya yi ƙasa da muryarsa sosai.
“Idan kun shirya zamu je Kaduna yanzu sai na nuna muku inda Namra take”
“Abunda muke jira kenan”
Anty Amarya ta yi saurin amsawa.
“Mai Martaba yana shiri ne, idan ya fita muma zamu kama hanya”
Ya faɗa yana kallon fuskar Abbah dan yaji me zai ce. Murmushi kawai Abbah yayi ya ɗaga masa kai, yana masa kallon mutum mai hankali da natsuwa.
NAMRA POV.
Murmushi kawai take, sai ɗaga kai tana maidawa, duk firar da ake, bata saka baki saboda itama nata ya isheta, su kansu suna firar ne ɗan kawai su rage mata kewa. Amman ta ƙi ta sake, sai dai a kan yi murmushi ko ɗaga kai, gudun kar suce ta ƙyale su, tun da Abdool ya takalo mata maganar gida sai ta koma wata irin, tunanin rayuwar jindaɗin da take ciki ta baya ta riƙa dawo mata, da kuma tunanin halin da Asim ya jefata, ga halin ko in kula da ya nuna mata, da kuma ƙin son haɗa jini da ita, ace duk tsawon wannan lokacin be neme ta, da gaske baya da buƙatar ta kenan? A ɗayan ɓangare kuma tana tunanin yadda zata shirya da iyayenta har ta koma ta zauna a tare da su wanda take ganin abu ne mai matuƙar wahala yin haka.
Duk dariya suka sa lokacin da Lamido yake bada wani labari na ban dariya, ita kam Namra sai ta saka kuka tana mai ɗaga murya dan damuwarta tasa ta manta da agaban jama'ah take, babu wanda hankalinsa ya fi tashi kamar Lamido, dan ya tsani ganin Namra cikin damuwa balle kuma zubar hawayenta. Sai da taga hankalin kowa ya dawo kanta sannan ta sassauta kukan da take ta tashi da gudu ta shige ɗaki. Ajiyar zuciya Lamido ya sauke cike da rashin daɗin rai ya ce
“Yarinyar tana cikin damuwa, ni ko bana son ganin ta cikin wannan halin, dan zai ƙara mata damuwar ne kawai, babu abunda yake raina a yanzu kamar na maza sanadiyar farincikinta, zan yi iya yadda zan iya na ganin na cire ta cikin wannan halin inshallah”
Neina ta miƙe ƙafafunta tana kallon ɗanta cike da son sa da kuma tausayinsa ta ce
“Cire yarinyar nan a damuwa abu ne mai wahala Lamido, ga dukan alamu ƴar babban mutunce, shiga irin lamarin gidan su sai yi wahala gareka tun da kai ba ɗan kowa ba ne”
Ɗauke kansa ya yi ya maida gurin ƙofar da Namra take. Sai da Neina ta tashi sannan ya miƙe tsaye yana ɗan ɗingishi ya nufi ɗakin. Zaune ya same ta kusa da ƙofa tana raira kukanta mai ban tausayi da taɓa zuciya.
“Namra kukan nan da zai miki magani da tuni yayi miki, kina ƙara saka kan ki ne cikin damuwa ne kawai”
Ɗago kai ta yi ta kalleshi.
“Idan ban yi kuka ba mi zanyi? Kana tsammanin mace data shiga cikin halin da nake ciki zata yi abota da dariya ko farinciki? Ba zaka gane abunda nake ji ba”
“Nasan kin shiga rayuwa kala-kala amman kuka ba zai miki magani ba, ki taimaka min ki tausaya min ki daina wannan kukan Namra, saboda gani nake kamar nine silar zubar hawayenki, ina damuwa sosai”
Hannayenta biyu tasa ta share hawayenta, sannan ta miƙe tsaye ta nufi gurin katifa ta zauna, ta yo ƙoƙarin tsayardar kukanta ne kawai dan ta lura da damuwar da Lamido yake idan tana kukan, balle kuma har ya kai ga yi mata magana, ita kanta tasan ba kowa ne zai juri zama da ita ta dinga masa kuka kamar ƙaramar yarinya.
Ajiyar zuciya Lamido ya sauke ya shafa fuskarsa sannan ya juya ya fice. Ba tayi minti talatin da zaman ba, taji yaro ya doko sallama wai Abdallah daga Katsina yana sallama da Namra. Wani baƙin haushi ta ji ya turniƙe ta, yau kuma da wacce ya zo? Me yake nema a gareta ne? Ba zai barta da damuwarta ba! Tana jin motsin shigowar Neina ta yi saurin kwantawa saman katifar ta lafe sosai kamar ta yi bachi.
“Na san ba bachi kike ba Namra, kuma kon ji lokacin da aka ce ana sallama da ke a waje, ki rufa mana asiri ki tashi kije”
Neina ta faɗa zuciyarta Fal da tsoro, dan ita tun da taji ance ɗan sarki ne, duk fargaba da tsoro suka kama ta, kullum zulluminta ɗaya kar yasa ayi musu wani abu.
Sosai Namra ta so tayi pretending like tayi bachi amman jin yadda muryar Neina take mata magana kamar mai magiya, yasa ta motsa har ta buɗe ido ta kalle
“Neina ban san me mutumen yake nufi da ni ba, me zai zo yayi min a yanzu?”
“Kije dai Allah, ko ma minene zaki ji, kin rufa mana asiri Namra, kin ga mu talakawa ne bayin Allah, karki ja mana abun ba zamu iya ɗauka ba”
“Bana nufin janyo muku komai Neina, amman kamar ba ki fahimci abunda nake nufi ba”
“Na fahimta, kawai ki tashi ki tafi, idan kuma har baki jin tafiyar, ni zan iya bashi izinin ya shigo nan yayi magana da ke, wata ƙila ma carpet ɗinsa da daya manta shekaranjiya ya zo karɓa”
Kamin ta Namra ƙara yin magana. Lamido ya ɗaga labulen ɗakin ya kunno kai yana faɗin.
“Neina kina tsoron masu milki da yawa”
“Dole na tsoraci masu milki Lamido, kafi kowa sanin sune sanadin shigar mu wannan halin”
Tana kaiwa nan ta juya ta fice. Shi ma Lamido juyawa yayi ya fice cikin rashin daɗin rai, yakan samu kansa a cikin rashin jindaɗi a duk lokacin da Yarima ya tsaya ƙofar gidansu da sunan kiran Namra.
Namra bata motsa daga inda take ba, sai ga Neina ta dawo ɗakin riƙe da carpet ɗin ta miƙa mata.
“Tashi kije ki kai masa, ko ba komai wulaƙanta ɗan Adam babu kyau, balle babban mutun kamarsa”
Wannan karon Namra bata yi mata musu, ta tashi ta karɓi carpet ɗin ta miƙe tsaye, already tana da hijab ɗinta sanye, sai kawai ta bi bayan Neina suka fice tare, takalminta ta zura, ta nufi ƙofar fita.
As usual gurin daya saba tsayuwa ya tsaya, tana tunkara inda yake tsaye gabanta ya soma faɗuwa, ta rasa dalilin daya saka yake mata kwarjini, tana isa kusa da shi ta miƙa masa carpet ɗin ta ce
“Ga carpet ɗin ka dan nasan ita ka dawo ƙarɓa”
Be ɗago ya kalleta ba, balle ta gane maganarta ta ratsa kunnensa, sai sha'aninsa yake da wayarsa, kamar be san da tsayuwarta a gurin ba.
Tayi tsayuwar minti ɗaya a gurin zuwa biyu, kamin ya ɗago ya kalleta ta cika sosai da taji kamar ta jefa masa wata baƙar magana amman bakinta be bata haɗin kai ba, gashi sai jin take kamar ta jefa masa carpet ɗin, sai dai kwajininsa ya hana hannunta kuzari, ballema ta yi ƙoƙarin yin hakan.
Babu enough hasken da zai iya haske fusakarta sosai, amman hakan be hana shi karantar tana ciki fushi ba, ko ba komai yasan ya ɓata mata lokaci, kuma ya shiga huruminta na ƙinjin gargaɗin da tayi masa akan kar ƙafarsa ta sake tako ƙofar gidansu.
“Ƙomai naki kyau yake min Namra, fushinki da faɗanki da tsawarki duka burgeni suke, abu ɗaƴa ya rage min yanzu na gani naki, shine dariyarki”
Ya faɗa yayinda ya ke cigaba da dannar wayarsa, amman hankalinsa da idonsa suna kan Namra. Wannan karon tayi nasarar yaudarar kanta, har ta samu haɗin kan idanuwanta, ta jefe Abdool da wani shegen kallo.
“Carpet ɗin ka kawai na fito kawo maka, ban fito dan ka yaba fushi ko faɗa na ba, kuma bana tunanin an halicceka dan ka ga dariyata kawai, saboda haka karka ɓatawa kanka lokaci, ka karɓi Carpet ɗin ka”
“Miya hana ki bar carpet ɗin a inda na barta tun ranar? Wane salo ne yasa kika ɗauke ta? Yanzun da nazo na aika nace a bani carpet ne? Wato ba zaki iya ganin abun Abdool ki ƙyale ba ko?”
Wannan karon da murmushi a fuskarsa, ya soka mata wannan maganar, ya gyara tsayuwarsa yana kallon taurarin da suka yi sama ado.
“Ai mu ƴaƴan Sarakuna bama shimfiɗa kuma bama ɗaukewa, wacan karon ma ba na shimfiɗawa kai na bane a karon kai na, nasan wata rana zan rubuta a diary, bayan Mai Martaba da Ummina, na taɓa shimfiɗawa Namra carpet har ma na zauna da ni da ita”
“Amman kai ka baka da aikin yi Wallahi, Allah yayi min tsare da mugun ƙudirinka, baka cikin hayyacinka ne? Miyasa zaka zo kana min wasu kalamai kamar wanda be san halin da nake ciki ba?”
“Ina ma ina da mugun ƙudiri a kanki! Da kin ga yanzu sace ci kawai zan yi na gudu naje nayi rayuwarda da nake so da ke, ni kaina ina mamakin halin dana shiga saboda ke, ban san miyasa ƙwaƙwalwata take ƙoƙarin zautuwa da lamarin ki ba”
Kai ta girgiza ta jefar da carpet ɗin a ƙasa.
“Wallahi baka da tausayi baka da tunani kwata-kwata a zuciyarka, taya zaka kalleni ka yi irin wannan maganar, you're fake Prince ba asalin Yariman ƙwarai bane kai, wata ƙila sarautar ta ku ta ƙauye ce, dan yariman ƙwarai ba zai tsaya mace kamar ni tana faɗa masa magana ba”
Lumshe ido yayi yana murmushi, tare da tsutsar baki kamar mai shan Sweet Candy. Ko da ya buɗe idonsa har ta ɓace daga gurin kamar walkiya.
Murmushin da ke fuskarsa ya faɗaɗa, kamin ya shiga muhalin massages ya aika saƙo. Cikin mintunan da basu fi goma ba, sai ga wata mota ta faka a gurin ɗauke da Anty Amarya da Abbah.
“Ga gidan can”
Ya faɗa yana nuna musu da kai, sannan ya buɗe motarsa ya shiga. Su kuma suka doshi ƙofar gidan, Abbah ne ya tsaya daga waje, Anty Amarya ta kunna kai ciki, zuciyarta sai bugawa take fat fat fat...
HILAL POV.
Ba a'ayi wasu events ban da walima, daman can shi baya ra'ayi sai kuma aka ci sa'ah amaryar tasa uztaziyace ita bata da son duniya. Ranar jumma'ah akayi walimar bayana an saka amarya lalle kamar yadda al'ada ta gada. Sai aka ɗaura aure ranar asabar, an yi taro sosai musamman ta ɓangaren Teema tun da ita aurenta ne na fari, kuma ita ta farko mace da mahaifinta zai fara yi ma aure. Yadda Hilal yaƙe yaƙar baki yana amsa gaisuwar mutane da ala sa albarka sai ka ɗauka auren so da ƙauna ne suka yi shi da Teema, tun da sha biyu aka ɗaura aure aka yi liyafar cin abinci bayan a sauko daga sallar azahar. Shi kam be samu dawowa gidansa ba sai da yamma ta yi lis.
Yadda ya tararda Kalsoom be yi zaton zai same ta haka ba, ta bala'in ruɗashi, kyau tayi har na fitar hankali, bakar shaddace jikinta an mata riga da saket, ɗinkin ya matse ta ya fitarda surar jikinta sosai, ta kashe ɗaure ɗankwalinta ya kalli kudu masu gabas, ga wata uwar kwalliyar kanti da aka mata a fuska, yadda take motsa bakinta ma abun kallo ne.
“Ango ka sha mai”
Ta faɗa tana wani fari da ido. Shi dai mutuwar tsaye yayi a ƙofar falon yana kallonta, sallama ma sai ta gagari bakinsa, ji yayi kamar ya je ya rumgumeta sai dai ƙanenta da kuma Amiyarta Salma dake falon sun han shi rawar gaban hantsi.
Yana amsa gaisuwar da suke masa ya nufi ɗakinsa, zuciyarsa cike da ƙaunar matarsa, dan yaji daɗin halin daya same ta ta bashi ƙwarin guiwa sosai, shi da ya zo da zimmar ya lallaɓata kar ta saka ranta a damuwa, sai gashi yaga kamar ma ta fi shi farinciki.
Babbar rigarsa ya fara cirewa sannan ya zauna saman gado, sai gata ta shigo hannunta riƙe da copin madara ta yanka masa ayaba ciki ta saka sugar kaɗan. Saman ƙafafunsa ta zauna ta riƙa aika masa madarar a baki, shi ko sai wani lumshe ido yake yana buɗewa kamar wani tsohon ɗan iska, kamin yasa hannayensa ya zagaye kunkurunta.
“Wannan ado haka ai sai ki haukata, so kike amaryar nan ta rasa gane kai na ko?”
Murmushi ta yi ta aje kofin a ƙasa tasa hannayenta
Showing 198001 words to 201000 words out of 280121 words
“Kasan abunda nake so da kai?”
Abbah ya girgiza kai tareda ɗaga hannu sama.
“A'a Allah ya taimake ka”
“Ina son ka yafe mata abunda ta yi maka, ko da ba zaka zauna da ita ba, ni zan zauna da ita a matsayin ƴata, daman ni gida na gidan ƴaƴa ne, amman idan ka yafe mata kuma ka saka mata albarka zata ga haske a rayuwarta”
Abbah ya sauke ajiyar zuciya.
“Allah ya taimake ka, ba wai bana son Namra ba ne, kawai ta aikata min abunda ban taɓa mafarkin zata aikata min ba ne, ta zaɓi wani sama da ni, ta bar karatun ta da danginta saboda shi...”
“Wallahi ta yi nadama yanzu, abunda kawai Mai Martaba yake so ka yafe mata mu zamu zauna da ita”
Abdool ya faɗa yana mai saukowa ƙasa ya zauna kusa da Abbah. Anty Amarya ta ɗago ta kalli Abdool.
“Idan har ya yafe mata, ni na fi kowa cancantar na zauna da ƴa ta”
Abbah ya data kai ya kalli Anty Amarya sannan ya kalli Mai Martaba.
“Mamana ta shiga rigarka ta samu alfarmarka, duk da yake ina jiran zuwan wannan ranar da Mamana zata gane kuskure da kuma gangancin abunda ta aikata, na sani wata zata dawo a gareni ko da kuwa mijinta be wulaƙanta ba, nasani wata rana zata gane muhimmancin iyaye, da kuma irin gudumawar da suke badawa a rayuwa, ko da babu saki na sani akwai ciwo, ba fata nake mata ba, amman nasan wata rana zai iya kamata ba duk miji bane yake zama da mace mai wani ciwo, sam bana son na mutu na bar Mamana a cikin halin da ta zaɓi kasancewa a ciki, na sani wata rana zata ratu ba ni, sai dai bana son ta rayu a cikin halin ina fushi da ita, dan nasan ba zata ga dai-dai, ina son Mamana sosai, kuma na yafe mata duniya da lahira”
Mai Martaba yayi murmushin ƙasaita irin nasu na manya.
“Lallai kana son ƙulla abota da ni”
Abdool ma yayi dariya mai cike da farinciki da har suka bayyana haƙoransa da kuma dimples ɗinsa ya ce
“Ni da Mai Martaba muna godiya”
Anty Amarya ta share hawayen idonta tana murmushi.
“Dan Allah idan tana cikin gidan nan ku faɗa mata Mahaifinta ya yafe mata, ta fito mu ganta”
“Bata tare da mu, tana can a Kaduna a wani gida rakuɓe, bata san Mai Martaba ya aika maka ba, ni ne kawai na ga tana cikin matsala kuma na san irin matsalar da rashin zama kusa da iyaye yake haifarwa”
“Allah ya maka albarka Allah ya raya maka iyalanka, ya cika maka burinka, ya taimake ka akan dukan lamurranka, na gode sosai yadda ki yi wannan jihadin Allah ya baka abunda kake so”
Ya amsa da “Amin” Yana wani sunsun da kai, shi ala dole ga surukin da ba san da shi ba 😂.
Mai Martaba ya miƙawa Abbah hannu yana murmushi.
“Yanzu kam zamu yi gaisuwar mutunci da kai, kaga har ƙoƙarin raba uwa da ƴa kake.”
Mai Martaba ya faɗa yana miƙewa tsaye. Da sauri Abbah ya miƙe tsaye, da hannunsa biyu ya riƙa hannun Mai Martaba yana dariya.
“Tuba na ke ranka ya daɗe, Allah yaja kwanan ka”
Juyawa Mai Martaba ya juya Abdool ya miƙe tsaye da sauri ya take masa baya. Har turakarsa Abdool ya rakashi farincike shinfiɗe a fuskarsa, Mai Martaba na shiga Babban falonsa Abdool ya riƙa alƙyabarsa ya cire masa ya jingine, sannan Mai Martaba ya cire rawaninsa da kansa ya aje a gefe, da sauri Abdool ya ɗauki rawanin ya aje a muhalinsa. Sannan ya zo ya zauna ƙasan carpet ya dafa ƙafafun Mai Martaba yana dariya.
“Na gode sosai da karamcin da Mai Martaba yayi min, ba zan taɓa manta wannan ba, Allah ya ja zamanin ka”
Murmushi yayi sai da aka ɗauki daƙiƙu sannan Mai Martaba ya amsa da
“Amin. Nan da minti talatin zamu je ɗan dime ƙaddamar da zakka, idan da hali sai ka shirya muje”
“...A...”
Sai kuma yayi shiru. Kallonsa kawai Mai Martaba yayi hakan ya cilastashi ƙarasa maganar.
“Da naso naje ne can Kaduna na kai su inda take”
Mai Martaba ya sake kallon ɗansa, irin kallon nan na akwai wani abu a ƙasa.
“Babana be kamata kana saka kanka a cikin irin wannan rayuwarba, karka manta kai ɗan sarki ne, kuma nan gaba kaɗan kai Sarki ne, sannan kai mutun ne mai babban muƙami a nigeria, be kamata ana ganin fuskarka a ko'ina ba, wani gurin kamata yayi ka aika, ko kasa ayi. Shi babban mutum ba ko ina ake son yana kasancewa ba, musamman ƴaƴan sarakuna, yana janyo raini, wani gurin ma yakan zubar da mutumcin mutum, amman kai sai naga kamar baka damu da hakan ba”
Yayi ƙasa da kansa, dan yasan Mai Martaba ya faɗi gaskiya, sai dai shi kan har ga Allah yana son ya zama na farko da zai fara yi ma Namra wannan albishir ɗin ko ba komai zai ƙara kwarjini a idonta.
“Amman Mai Martaba ina son na kasance nina zan yi ma yarinyar nan Albishir, idan mun kama hanyar Kaduna yanzu kasan kamin yamma mun isa”
Mai Martaba ya shafa fuskarsa.
“Idan har ganinta kake son yi, zaka iya aikawa a taho da ita”
“She's so stubborn ba lallai bane ta zo, kuma abun zai fi burgewa idan iyayenta da kan su sukaje suka ɗauko ta”
Kallon tsab Mai Martaba yayi ma Abdool sai ya ɗauke kansa, tare da ɗaga masa hannu, alamar go ahead.
*** **** ****
Fitar da Mai Martaba da Abdool suka yi ne, yaba Anty Amarya damar data kai ta ƙare ma Faɗar kallo. Manyan hotuna da ta gani na Abdool ɗaya a cikin kayan sarauta ɗaya kuma a cikin kakin soja, yanzu kan sarai ta tuna waye Abdool. Mutumen da ya taɓa taimaka mata lokacin da motarsu ta lalace ana ruwan sama.
“Gaskiya yana da kirki, matar ka da ƴaƴanka sun yi dacen uba na gari”
Ta faɗa idonta kan hoton Abdool. Abbah dai be ce komai ba, sai fama idonsa abinci yake yana shaƙar daddaɗan ƙamshin dake tashi faɗar.
Fitowar Abdool ne yasa duk suka maida dubansu gurinsa. Wata shigar ce a jikinsa bata ɗazun ba, wannan ma ta fitar da kyausa, da kuma annurin fuskarsa. Zuwa yayi ya risina gabansu, ya yi ƙasa da muryarsa sosai.
“Idan kun shirya zamu je Kaduna yanzu sai na nuna muku inda Namra take”
“Abunda muke jira kenan”
Anty Amarya ta yi saurin amsawa.
“Mai Martaba yana shiri ne, idan ya fita muma zamu kama hanya”
Ya faɗa yana kallon fuskar Abbah dan yaji me zai ce. Murmushi kawai Abbah yayi ya ɗaga masa kai, yana masa kallon mutum mai hankali da natsuwa.
NAMRA POV.
Murmushi kawai take, sai ɗaga kai tana maidawa, duk firar da ake, bata saka baki saboda itama nata ya isheta, su kansu suna firar ne ɗan kawai su rage mata kewa. Amman ta ƙi ta sake, sai dai a kan yi murmushi ko ɗaga kai, gudun kar suce ta ƙyale su, tun da Abdool ya takalo mata maganar gida sai ta koma wata irin, tunanin rayuwar jindaɗin da take ciki ta baya ta riƙa dawo mata, da kuma tunanin halin da Asim ya jefata, ga halin ko in kula da ya nuna mata, da kuma ƙin son haɗa jini da ita, ace duk tsawon wannan lokacin be neme ta, da gaske baya da buƙatar ta kenan? A ɗayan ɓangare kuma tana tunanin yadda zata shirya da iyayenta har ta koma ta zauna a tare da su wanda take ganin abu ne mai matuƙar wahala yin haka.
Duk dariya suka sa lokacin da Lamido yake bada wani labari na ban dariya, ita kam Namra sai ta saka kuka tana mai ɗaga murya dan damuwarta tasa ta manta da agaban jama'ah take, babu wanda hankalinsa ya fi tashi kamar Lamido, dan ya tsani ganin Namra cikin damuwa balle kuma zubar hawayenta. Sai da taga hankalin kowa ya dawo kanta sannan ta sassauta kukan da take ta tashi da gudu ta shige ɗaki. Ajiyar zuciya Lamido ya sauke cike da rashin daɗin rai ya ce
“Yarinyar tana cikin damuwa, ni ko bana son ganin ta cikin wannan halin, dan zai ƙara mata damuwar ne kawai, babu abunda yake raina a yanzu kamar na maza sanadiyar farincikinta, zan yi iya yadda zan iya na ganin na cire ta cikin wannan halin inshallah”
Neina ta miƙe ƙafafunta tana kallon ɗanta cike da son sa da kuma tausayinsa ta ce
“Cire yarinyar nan a damuwa abu ne mai wahala Lamido, ga dukan alamu ƴar babban mutunce, shiga irin lamarin gidan su sai yi wahala gareka tun da kai ba ɗan kowa ba ne”
Ɗauke kansa ya yi ya maida gurin ƙofar da Namra take. Sai da Neina ta tashi sannan ya miƙe tsaye yana ɗan ɗingishi ya nufi ɗakin. Zaune ya same ta kusa da ƙofa tana raira kukanta mai ban tausayi da taɓa zuciya.
“Namra kukan nan da zai miki magani da tuni yayi miki, kina ƙara saka kan ki ne cikin damuwa ne kawai”
Ɗago kai ta yi ta kalleshi.
“Idan ban yi kuka ba mi zanyi? Kana tsammanin mace data shiga cikin halin da nake ciki zata yi abota da dariya ko farinciki? Ba zaka gane abunda nake ji ba”
“Nasan kin shiga rayuwa kala-kala amman kuka ba zai miki magani ba, ki taimaka min ki tausaya min ki daina wannan kukan Namra, saboda gani nake kamar nine silar zubar hawayenki, ina damuwa sosai”
Hannayenta biyu tasa ta share hawayenta, sannan ta miƙe tsaye ta nufi gurin katifa ta zauna, ta yo ƙoƙarin tsayardar kukanta ne kawai dan ta lura da damuwar da Lamido yake idan tana kukan, balle kuma har ya kai ga yi mata magana, ita kanta tasan ba kowa ne zai juri zama da ita ta dinga masa kuka kamar ƙaramar yarinya.
Ajiyar zuciya Lamido ya sauke ya shafa fuskarsa sannan ya juya ya fice. Ba tayi minti talatin da zaman ba, taji yaro ya doko sallama wai Abdallah daga Katsina yana sallama da Namra. Wani baƙin haushi ta ji ya turniƙe ta, yau kuma da wacce ya zo? Me yake nema a gareta ne? Ba zai barta da damuwarta ba! Tana jin motsin shigowar Neina ta yi saurin kwantawa saman katifar ta lafe sosai kamar ta yi bachi.
“Na san ba bachi kike ba Namra, kuma kon ji lokacin da aka ce ana sallama da ke a waje, ki rufa mana asiri ki tashi kije”
Neina ta faɗa zuciyarta Fal da tsoro, dan ita tun da taji ance ɗan sarki ne, duk fargaba da tsoro suka kama ta, kullum zulluminta ɗaya kar yasa ayi musu wani abu.
Sosai Namra ta so tayi pretending like tayi bachi amman jin yadda muryar Neina take mata magana kamar mai magiya, yasa ta motsa har ta buɗe ido ta kalle
“Neina ban san me mutumen yake nufi da ni ba, me zai zo yayi min a yanzu?”
“Kije dai Allah, ko ma minene zaki ji, kin rufa mana asiri Namra, kin ga mu talakawa ne bayin Allah, karki ja mana abun ba zamu iya ɗauka ba”
“Bana nufin janyo muku komai Neina, amman kamar ba ki fahimci abunda nake nufi ba”
“Na fahimta, kawai ki tashi ki tafi, idan kuma har baki jin tafiyar, ni zan iya bashi izinin ya shigo nan yayi magana da ke, wata ƙila ma carpet ɗinsa da daya manta shekaranjiya ya zo karɓa”
Kamin ta Namra ƙara yin magana. Lamido ya ɗaga labulen ɗakin ya kunno kai yana faɗin.
“Neina kina tsoron masu milki da yawa”
“Dole na tsoraci masu milki Lamido, kafi kowa sanin sune sanadin shigar mu wannan halin”
Tana kaiwa nan ta juya ta fice. Shi ma Lamido juyawa yayi ya fice cikin rashin daɗin rai, yakan samu kansa a cikin rashin jindaɗi a duk lokacin da Yarima ya tsaya ƙofar gidansu da sunan kiran Namra.
Namra bata motsa daga inda take ba, sai ga Neina ta dawo ɗakin riƙe da carpet ɗin ta miƙa mata.
“Tashi kije ki kai masa, ko ba komai wulaƙanta ɗan Adam babu kyau, balle babban mutun kamarsa”
Wannan karon Namra bata yi mata musu, ta tashi ta karɓi carpet ɗin ta miƙe tsaye, already tana da hijab ɗinta sanye, sai kawai ta bi bayan Neina suka fice tare, takalminta ta zura, ta nufi ƙofar fita.
As usual gurin daya saba tsayuwa ya tsaya, tana tunkara inda yake tsaye gabanta ya soma faɗuwa, ta rasa dalilin daya saka yake mata kwarjini, tana isa kusa da shi ta miƙa masa carpet ɗin ta ce
“Ga carpet ɗin ka dan nasan ita ka dawo ƙarɓa”
Be ɗago ya kalleta ba, balle ta gane maganarta ta ratsa kunnensa, sai sha'aninsa yake da wayarsa, kamar be san da tsayuwarta a gurin ba.
Tayi tsayuwar minti ɗaya a gurin zuwa biyu, kamin ya ɗago ya kalleta ta cika sosai da taji kamar ta jefa masa wata baƙar magana amman bakinta be bata haɗin kai ba, gashi sai jin take kamar ta jefa masa carpet ɗin, sai dai kwajininsa ya hana hannunta kuzari, ballema ta yi ƙoƙarin yin hakan.
Babu enough hasken da zai iya haske fusakarta sosai, amman hakan be hana shi karantar tana ciki fushi ba, ko ba komai yasan ya ɓata mata lokaci, kuma ya shiga huruminta na ƙinjin gargaɗin da tayi masa akan kar ƙafarsa ta sake tako ƙofar gidansu.
“Ƙomai naki kyau yake min Namra, fushinki da faɗanki da tsawarki duka burgeni suke, abu ɗaƴa ya rage min yanzu na gani naki, shine dariyarki”
Ya faɗa yayinda ya ke cigaba da dannar wayarsa, amman hankalinsa da idonsa suna kan Namra. Wannan karon tayi nasarar yaudarar kanta, har ta samu haɗin kan idanuwanta, ta jefe Abdool da wani shegen kallo.
“Carpet ɗin ka kawai na fito kawo maka, ban fito dan ka yaba fushi ko faɗa na ba, kuma bana tunanin an halicceka dan ka ga dariyata kawai, saboda haka karka ɓatawa kanka lokaci, ka karɓi Carpet ɗin ka”
“Miya hana ki bar carpet ɗin a inda na barta tun ranar? Wane salo ne yasa kika ɗauke ta? Yanzun da nazo na aika nace a bani carpet ne? Wato ba zaki iya ganin abun Abdool ki ƙyale ba ko?”
Wannan karon da murmushi a fuskarsa, ya soka mata wannan maganar, ya gyara tsayuwarsa yana kallon taurarin da suka yi sama ado.
“Ai mu ƴaƴan Sarakuna bama shimfiɗa kuma bama ɗaukewa, wacan karon ma ba na shimfiɗawa kai na bane a karon kai na, nasan wata rana zan rubuta a diary, bayan Mai Martaba da Ummina, na taɓa shimfiɗawa Namra carpet har ma na zauna da ni da ita”
“Amman kai ka baka da aikin yi Wallahi, Allah yayi min tsare da mugun ƙudirinka, baka cikin hayyacinka ne? Miyasa zaka zo kana min wasu kalamai kamar wanda be san halin da nake ciki ba?”
“Ina ma ina da mugun ƙudiri a kanki! Da kin ga yanzu sace ci kawai zan yi na gudu naje nayi rayuwarda da nake so da ke, ni kaina ina mamakin halin dana shiga saboda ke, ban san miyasa ƙwaƙwalwata take ƙoƙarin zautuwa da lamarin ki ba”
Kai ta girgiza ta jefar da carpet ɗin a ƙasa.
“Wallahi baka da tausayi baka da tunani kwata-kwata a zuciyarka, taya zaka kalleni ka yi irin wannan maganar, you're fake Prince ba asalin Yariman ƙwarai bane kai, wata ƙila sarautar ta ku ta ƙauye ce, dan yariman ƙwarai ba zai tsaya mace kamar ni tana faɗa masa magana ba”
Lumshe ido yayi yana murmushi, tare da tsutsar baki kamar mai shan Sweet Candy. Ko da ya buɗe idonsa har ta ɓace daga gurin kamar walkiya.
Murmushin da ke fuskarsa ya faɗaɗa, kamin ya shiga muhalin massages ya aika saƙo. Cikin mintunan da basu fi goma ba, sai ga wata mota ta faka a gurin ɗauke da Anty Amarya da Abbah.
“Ga gidan can”
Ya faɗa yana nuna musu da kai, sannan ya buɗe motarsa ya shiga. Su kuma suka doshi ƙofar gidan, Abbah ne ya tsaya daga waje, Anty Amarya ta kunna kai ciki, zuciyarta sai bugawa take fat fat fat...
HILAL POV.
Ba a'ayi wasu events ban da walima, daman can shi baya ra'ayi sai kuma aka ci sa'ah amaryar tasa uztaziyace ita bata da son duniya. Ranar jumma'ah akayi walimar bayana an saka amarya lalle kamar yadda al'ada ta gada. Sai aka ɗaura aure ranar asabar, an yi taro sosai musamman ta ɓangaren Teema tun da ita aurenta ne na fari, kuma ita ta farko mace da mahaifinta zai fara yi ma aure. Yadda Hilal yaƙe yaƙar baki yana amsa gaisuwar mutane da ala sa albarka sai ka ɗauka auren so da ƙauna ne suka yi shi da Teema, tun da sha biyu aka ɗaura aure aka yi liyafar cin abinci bayan a sauko daga sallar azahar. Shi kam be samu dawowa gidansa ba sai da yamma ta yi lis.
Yadda ya tararda Kalsoom be yi zaton zai same ta haka ba, ta bala'in ruɗashi, kyau tayi har na fitar hankali, bakar shaddace jikinta an mata riga da saket, ɗinkin ya matse ta ya fitarda surar jikinta sosai, ta kashe ɗaure ɗankwalinta ya kalli kudu masu gabas, ga wata uwar kwalliyar kanti da aka mata a fuska, yadda take motsa bakinta ma abun kallo ne.
“Ango ka sha mai”
Ta faɗa tana wani fari da ido. Shi dai mutuwar tsaye yayi a ƙofar falon yana kallonta, sallama ma sai ta gagari bakinsa, ji yayi kamar ya je ya rumgumeta sai dai ƙanenta da kuma Amiyarta Salma dake falon sun han shi rawar gaban hantsi.
Yana amsa gaisuwar da suke masa ya nufi ɗakinsa, zuciyarsa cike da ƙaunar matarsa, dan yaji daɗin halin daya same ta ta bashi ƙwarin guiwa sosai, shi da ya zo da zimmar ya lallaɓata kar ta saka ranta a damuwa, sai gashi yaga kamar ma ta fi shi farinciki.
Babbar rigarsa ya fara cirewa sannan ya zauna saman gado, sai gata ta shigo hannunta riƙe da copin madara ta yanka masa ayaba ciki ta saka sugar kaɗan. Saman ƙafafunsa ta zauna ta riƙa aika masa madarar a baki, shi ko sai wani lumshe ido yake yana buɗewa kamar wani tsohon ɗan iska, kamin yasa hannayensa ya zagaye kunkurunta.
“Wannan ado haka ai sai ki haukata, so kike amaryar nan ta rasa gane kai na ko?”
Murmushi ta yi ta aje kofin a ƙasa tasa hannayenta
Book Chapters
Chapter 1Chapter 2Chapter 3Chapter 4Chapter 5Chapter 6Chapter 7Chapter 8Chapter 9Chapter 10Chapter 11Chapter 12Chapter 13Chapter 14Chapter 15Chapter 16Chapter 17Chapter 18Chapter 19Chapter 20Chapter 21Chapter 22Chapter 23Chapter 24Chapter 25Chapter 26Chapter 27Chapter 28Chapter 29Chapter 30Chapter 31Chapter 32Chapter 33Chapter 34Chapter 35Chapter 36Chapter 37Chapter 38Chapter 39Chapter 40Chapter 41Chapter 42Chapter 43Chapter 44Chapter 45Chapter 46Chapter 47Chapter 48Chapter 49Chapter 50Chapter 51Chapter 52Chapter 53Chapter 54Chapter 55Chapter 56Chapter 57Chapter 58Chapter 59Chapter 60Chapter 61Chapter 62Chapter 63Chapter 64Chapter 65Chapter 66Chapter 67 Chapter 68Chapter 69Chapter 70Chapter 71Chapter 72Chapter 73Chapter 74Chapter 75Chapter 76Chapter 77Chapter 78Chapter 79Chapter 80Chapter 81Chapter 82Chapter 83Chapter 84Chapter 85Chapter 86Chapter 87Chapter 88Chapter 89Chapter 90Chapter 91Chapter 92Chapter 93Chapter 94