tsaye ta san inda suka dosa, daman ita ta san ciki ne da ita, to Kalsoom fa ita ma cikin ne.
A take yawun bakinta suka tsinke, cikinta ya ɗauki kuka, ba ƙaranin ƙoƙari rayi ba wajen ƙawata fuskarta da murmushi, dan ta nunawa Hilal ta jidaɗin.
“Mashallah Kalsoom ita ma tana da ciki? What a blessed”
“Tana ma har ya riga na ki, bata da matsala sosai ne shiyasa ba za a gane tana da cikin ba”
Amsarsa ta tabbatar mata da zarginta, daman dalilin tambayar kenan. Wata duniyar take ƙoƙarin kai shi dan ta nuna masa farincikinta, ta kuma ɓoye masa baƙincikin da ke son bayyana a fuskarta.
Zuwana Kalsoom yasa ya daina takura akansa a kanta, duk magiyar da yake mata yake nuna mata maitarsa yanzu ya daina tun da ya samu wani halalin nasa, sai dai daren yau da raya masa shi fiye da yadda yake zato, a yau tayi masa abunda ta shekara goma bata masa ba, ta sakar masa jikinta sosai, har sai da shi kansa ya gaji dan kansa ya bar.
Tare suka yi wanka, suka ci abinci da kuma dan abun taɓawa daya siyo musu ɗazu, a lokacin ƙarfe biyun dare yayi. Suna gamawa ta kwanta dan ba gado haƙƙinsa, shi kam be kwanta ba sai yayi nafisa raka'ah biyu, raka'ar farko ya karanta fatiha da ayatul kursiyu sai ya dora kulhuwallahu sama, a raka a ta biyu kuma ya karanta fatiha da amanar rasulu ya ɗora kulhuwallahu sama, sannan ya zauna yayi zaman tahiya kamin ya sallame a cikin tahiyar ya faɗawa Allah buƙatarsa, sannan ya sallame.
Sai da yayi salatin annabi da godiya ga Allah da istigifari ƙafa ɗari ɗari sannan ya sake ɗaga hannu yayi kirari ga ubangijinsa ya nemi yafiyarsa, sannan ya sake koro da buƙatarsa.
A cikin ɗauko abun ɗibar jini ya ɗibi jininta dan yasan da safe ba zai samu damar ɗiba zata ce masa aiki.
Washe garin da zai kai yaransa makaranta suma ya ɗibi nasu, Kalsoom kam sai daf da zai fita sannan ya ɗibi nata sai raki take masa tana masa shagwaɓa, wai da zafi ita zai ƙarar mata da jini, haka ta riƙa narke masa a jiki har yayi lattin zuwa aiki.
NAMRA POV.
Kwata-kwata bachi ƙaura yayi mata daga ido, bata ma jin alamunsa balle har tasa rai zai so mata, abu ɗaya zuwa biyu yayi mata tsaye a rai, maganganun da Asim yayi shi da mahaifiyarsa, wata zuciyar na shawarta akan ta bayayyana masa ta kuma tambaye shi abunda yake ƙoƙarin ɓoye mata, yayinda ɗayar kuma take ce mata ta haƙura taga iya gudun zuwansa dan tabbatar da zarginta.
Babu amfani da raya dare da tunani bayan Ubangijinta yana kallonta, kuma yana shirye ya amsa buƙatunta, tayi haramar ƙorar sheiɗan sannan ta samu kuzarin fita tayi alwalah, sannan ta dawo ɗakin tayi nafila ta ɗora sa salatin Annabi.
Firgigit Mardiya ta farka daga dogon bachin da take a farkigice har tana ihu. Namra ma dake kusa da ita sai da ta ji tsoro kowa dake cikin ɗakin ya matsa, Mahaifiyarta ta tashi tana kallonta.
Gabanta ta fara kallo kamin ta kalli bayanta, sai kuma ta bi ko'ina na ɗakin da kallo, ajiyar zuciya ta sauke yafi ashirin, sannan ta haɗe yawun bachin da suka cika mata baki, ba dan tasan tayi ba.
“Ke lafiyarki?”
Ashe dai duniya take, jin muryar mahaifiyarta ya ƙara tabbatar mata da a farke take.
“Wallahi wani mumunan mafarki na yi, wai wuta tana bina”
“Subhanallahi, ke kuwa ai addu'ah zaki yi”
Namra ta faɗa, tana rufe ƙur'anen dake hannunta, sannan ta nufi gurin bachinta tayi addu'ah bachi ta kwanta ba dan tana jin bachin ba, sai dan tana buƙatar jinginar da jikinta da tabar suka saba mata shimfiɗa da ita.
Washe gari...
Da sassafe ta siye tea da buroɗi ta nufi asibiti, dan bata son su Mama su kama hanya bata isa ba, tun da babu wanda zai kula da Asim sai ita. Duk yadda take ganin ta doka sammako sai taga har sun fi ta, dan tana shiga ɗakin taga alamar sun kama hanya.
Bata yarda ta nunawa Asim komai ba, ta gaisheshi sannan ta masa ya jiki ta soma zuba masa tea ɗin.
“Jiya kika tafi baki faɗa ba”
“Eh pad ɗina ne ya lalace shine naje gida na canja, su Mama sun kama hanya ko?”
Ajiyar zuciya ya sauke, yanzu kam hankalinsa ya kwanta, daman can yana tunanin ko ta ji maganar sune yasa taje ba tare data faɗa musu ba, ashe shi da Mama ba su canka dai-dai.
“Eh tace da wuri zata je yadda zata tararda matar da za a ranto kuɗin gareta”
“Allah yasa a dace”
Ta faɗa tana miƙa masa tea, kallon da tayi masa da kuma maganarsa sun zari zuciyarta, miyasa Asim yake ɓoye mata? Wani tunanin ne ya zo mata sai ta kawar da fuskarta gefe.
_______________________________
BEST REGARDS 💖🌺
KHADEEJA CANDY😘
*🌺🌺🌺 ZAGON ƘASA 🌺🌺🌺*
Website
www.khadeejacandy.com.ng
*PAGE - 33*
NOT EDITED ⚠️
Washe garin ranar da Mama ta tafi ta dawo, guraren uku da rabi na rana. Ita kaɗai ta dawo ba tare da Hajara ba, Namra bata nuna mata komai ba ta tarbeta da far'ah tana mata sannu da zuwa.
Tana son tayi labari Namra ta tsare su taƙi ta tashi, shi kansa Asim yana son magana da ita amman ba dama, tun da Namra tana gurin.
Kamar ta san Namra bata tanadar mata komai, tun a hanya ta tayi gurin biredin ta da lemu, sai ta ta ci ta ƙoshi, sannan ta tashi ta fita.
Da kanta taje ta biya kuɗin maganin dan kar taba Namra.
Ta dawo daga biyan maganin ne, Namra ta tashi tayi musu sallama ta baro asibitin.
Har ta iso gida kuka take, tana tunanin yadda Asim yake ɓoye mata lamarin, dan ta lura da yadda suke kallon kallo da Mama, hakan ya soma tabbatar mata da abunda Anty Amarya ke faɗa mata.
“Idan har ta tabbata Asim na son yaudarata....”
Sai kuma tayi shiru ta share hawayenta, ta miƙawa mai Napep kuɗinsa ta shige gida.
*** ***
“Thank you”
Ta faɗa tana murmushi tare da kallon mutumen daya tashi daga saman kujerar ta ya nufi ƙofar fita. Sai da ya fice sannan ta kalli wayarta dake ringing, sannan ta kai hannu ta ɗauka zuciyarta na raya mata irin labarin da Asmee zata bata.
“Ƴar gari kamar kin san yanzu nake tunanin ki nace ko kin samu zuwan kuwa?”
Kuka ta fara ji kamin Asmee ta ɗora mata da zancen dalilin kiran nata.
“Rashida ina ciki matsala”
“Lafiya miya faru?”
“Wani malami ne da muke zuwa gurinsa, yana ba mu taimako, shine yanzu ake ce mana malamin yana da ciwon nan na zamani, shine tun ranar na kasa sukuni ban ma sama naje gurin matsalar ki ba”
“Innalillahi wa'inna ilaihi raji'un, Asmee garin yaya? Ya taɓa sex dake ne? Ko me?”
Kuka tayi sosai har ka kasa magana.
“Ki faɗa min mana ki daina kuka”
“Ya taɓa lokacin da je neman wani taimako sai yace min sai na kawo sperm ɗin wani wanda ba mijina ba, da jinin al'ada da shi za a haɗa, ni kuma na ce masa ban san inda zan samo ba, shine....”
Ta ƙarasa da kuka
“Ke yanzu kin je an gwada jinin ki ance kina ɗauke da ciwon ne? Stop crying and tell me Asmee”
“Ban je ba, tsoro nake ji ban san wanda zan faɗawa ba sai, dan bani da ƙawa irin ki, na rasa yadda zan yi tsoron gwajin na ke, aiki ma na daina zuwa yanzu”
“Innalillahi Ya salam Ya salam”
Ta soma zagaye office ɗin tana dafe kai, da wayar a kunnenta.
“Ki kwantar da hankalin ki kinji karki faɗawa kowa, kuma karki yi abunda zai sa mijin ki ko wani ya zargi wani abu, i will call you back”
Tayi saurin kashe wayar tana tuna jininta da Hilal ya ɗiba, idai har Asmee ta kamu da cutar to itama zata iya kamuwa da ita tun da har suna using mutum ɗaya.
Faɗuwa tayi zaune zumi na keto mata ta ko'ina, hannu ta kai tana shafa kanta, tana girgiza shi kamar wani ne a gabanta.
“Ko shiyasa ya sake ɗibar jinina? Amman kuma ai da ba zai kusance ni ba, amman yanzu idan ya auna dole ya gano idan akwai shi”
A fili take furucin zuciyarta a karaye, jikinta har tsimi yake, yanzu kam hannaye biyu tasa ta dafe kanta tana tunanoma kanta mafita.
“Dole ne na dakatar dashi daga yin gwajin, kuma dole ne nima naje na bincika kai na, indai har da gaske ne Asmee kin cuce ni”
Da sauri ta tashi ta kaɗe jikinta ta fiddo hoda a jakarta ta gyara fuskarta sannan ta ɗauki jakar ta fita. Sai da ta biya ta faɗa musu fitar gaggauwa ta kamata, sannan ta fito harabar bankin ta shiga motar, ta ɗauki hanyar Asibiti.
Akwai ƴar tazara tsakaninta da asibitin, amman yadda ta sakarwa motar wuta yasa ta isa cikin ƙanƙanen lokaci. A harabar asibitin tayi parking, ta fito ta duba gurin da aka tanadarwa manyan likitoci dan faka motocinsu.
Motar Doc Hilal ce ta uku a gurin, that's means yana cikin asibitin, safa da marwa ta fara yi tana tunanin ta inda zata fara. Lab ne ya faɗo mata a rai. Da fargaba ta kutsa kai cikin asibitin ta ɗauki hanyar da zata hada ta da lab ɗin, ƙasa-ƙasa take kallon mutane, tana fargabar haɗuwa da Hilal, dan ko ganinta yayi bata san me zata ce masa ba.
Ta tararda mutane da ɗan yawa a gurin da aka tana da dan karɓar results ɗin jini da fitsari, hakan yasa ta zagaya ta shiga ciki tun da ita ba baƙuwar asibitin ba ce.
Biyu daga cikin mutanen da suke gurin sun gane, tun da sun san matar Doc ce, cikin mutunci da far'ar ta gaisa da su tana yi tana kallo ƙofa.
“Habib na ce kun gama gwajin jinin da Doc ya kawo? Za a tafi dashi wani garin ne”
Wanda ta kira da Habib ɗin ya amsa da.
“Eh tun ranar muka shi ba ai”
“Ba yau ya kawo ba?”
“A'a ina jin tun monday ne, Monday or Tuesday? Abbas kai ka bashi ko?”
Wanda aka kira da Abbas ɗin be ma kula.da zancen su ba sai rubuce-rubucen sa yake, Habib ɗin ya kalleta.
“Ina jin Monday ne, an dai kwana biyu yanzu”
Gabanta ya faɗi sosai.
“O'o nasan ya jefar da results ɗin wani wajen shiyasa ya ƙi ya faɗa min, amman yau be kawo maka wani ba?”
“Gaskiya be kawo ba, dan mu muka yi duty safe yanzu zamu tashi”
Nauyi zuciyarta sosai tayi mata har sai da ta tsayi ya gagareta, ta zauna a kujerar dake gurin.
“Amman dan Allah ya za'ayi na samu results ɗin wacan gwajin? Tun da ya ɓatar nasan ba zaku rasa a littafin ku”
“Wallahi da an fito da results ɗin an rubuta a littafi ansa a paper na results ɗin ake kai su ɗakin ajiya, sai dai shi Doc zai iya zuwa yayi ma Doc Omar magana, sai ya bincika masa, amman nan results kawai muke badawa”
“Okay Thank you bari na koma gurin Doc ɗin nayi masa magana”
“Okay a gaida yara”
Ya faɗa yana kallon bayanta, irin ƴan iskan samarin nan ne da basa gani su kauda idonsu.
Ƙafafunta sun mata nauyi, ga idonta dake son ciki da ƙwalla tana mayarwa, akwai ƴar tazara tsakanin office ɗin da lab, hakan ya bata damar tunanin abunda zata cewa Hilal idan ya ganta, idan kuma ta koma bata shiga ba ta san zai iya samu labarin ta shigo cikin asibitin tun da akwai waɗanda suka santa, kuma zasu iya faɗa masa.
_Thank you so much my tomatir my albasa my daddawa my miyar kuka_
Yana dannawa Ƙalsoom reply ɗin ta whatsapp. Rashida ta turo ƙofar office ɗin ta shigo da murmushi a fuskarta.
Tashi yayi daga jinceren da yake saman kujera ya kalli da dariya.
“Surprise surprise surprise”
“Yes Darling, na biyo ta nan baya ne shina nace bari na biyo na ga farinciki na”
Ya ɓata rai sosai lokacin daya lura da yanayin tufafin dake jikinta. Suit ne mai wando ta riga sai ɗan ƙaramin hijabi dake kanta.
“Daman Haka kike fita daga office? Ba mun yi maganar nan dake ba dan me zaki fito baki ɗora abaya a sama ba, a cikin office ɗin ki kawai na yarda ki riƙa zama haka, kika ce kin ji ashe ni kike ma ko? Yana ɗaya daga cikin dalilin daya sa bana son aikin nan na ki, bana son wani na ganin matana abun nan yana min zafi”
Sai a lokacin ta kula da tufafin da suke jikinki, tsabar hankalinta baya jikinta bata ma san ta fito a haka ba. Hannayenta tasa ta laƙamo wuyansa.
“Im sorry Wallahi fitar gaggauwace shiyasa amman ba zan sake ba i promise”
“Yanzu haka kika shigo a asibitin nan kowa na kallon ki? Haba Rashida idan an girma a san an girma mana, kefa uwace kamata yayi idan kin ga Ezzah tayi wannan shigar kiyi mata faɗa ba wai ki yi ba”
Ta saki wutan nasa ta nufi freezer dan ita ba faɗan da yake mata bane a gabanta, abunda ya kawo ta take ƙoƙarin yi, tsayawa tayi ta duba da kyau drinks ɗin da tasan babu a freezer ɗin tace masa tana so.
“Nidai nace kayi haƙuri, kuma ina son nasha coc”
Ta faɗa tana marairaice masa, daman tasan baya shan coca-cola saboda irin abubuwan da ake faɗa akanta, kuma ta san yadda ya tsani kayan yahudawa.
Kamar zai ce mata babu, sai kuma ya ƙyaleta tun da yasan tana da ciki wani abun dole ya ɗaga mata ƙafa, sai dai be sakar mata fuska ba dan har yanzu ransa a ɓace yake, sai kawai ya juya ya fita.
Da sauri ta nufi teburinsa ta fara duba takardun da suke gurin, bata ga abunda take nema ba, hakan yasa ta nufi wata ƴar ƙaramar wardrobe dake gefen kujerar, har ta kai hannu ta buɗe sai kuma wani tunanin ya zo mata.
‘Idan na yamutsa masa takardu dole zai zargi wani abu’
Sai kawai ta fasa buɗewa ta koma ta zauna a kujerarsa ta ɗauki ƙafafunta ta ɗora saman teburin kamar babu abunda yake damunta, alhalin a can cikin zuciyarta tashin hankaline da tunani suka taru suka mata katutu.
Yadda ya fita haka ya dawo fuska a haɗe kamar be taɓa dariya ba, ransa ya sosu sosai da ganin irin dress ɗin data shigo dashi cikin asibitin.
Miƙa mata Coc ɗin yayi ya nufi windows ɗin office ɗin ya rufe. Tashi tayi tare da Coc a hannu daman can ba shanta zata yi ba, bata ma jin zata iya saka wani abu a cikinta yanzu.
“Ni zan wuce”
Ya watsa mata wani kallo.
“Haka zaki fita?”
Ta ɗan kalli jikinta
“To ya zan yi?”
“Ban sani ba”
Ya nufi hanger ɗinsa ya ɗauko labcoat ya ɗora mata sama.
“Kuma kar ki cireta har office”
“Doc zan bi ta lab na karɓi results, nayi mafarkin na haifi ƴan'biyu”
Dariya yayi sosai, wanda be shirya yi ba
“Toh ai ba a jini ake ganin twins ba, kuma ban ma kai awon jinin ba”
“Miyasa?”
“Ba nan za min ba, Asibitin Alex zan kai, saboda asibitin su tafi ta mu kayan aiki”
“Okay”
Ta faɗa zuciyarta cike da jindaɗin jin inda zata kai jinin, wani gurin kuma ta jidaɗin da be riga ya kai ɗin ba.
“To ina ka aje shi? Karka sake ce min ya ɓata kuma”
“Ba zai ɓata ba yana nan cikin mota na”
Ya faɗa yana jan hancinta, ita kuma ta kai bakinta dai-dai nashi tayi masa kiss.
Har gurin mota ya rakata sai da ta shiga yaga tashinta sannan ya koma office ɗin.
A maimakon ta koma asibitin sai kawai ta jiya pharmacy ta siye abu sannan ta ɗauki hanyar da zata kai ta gidan Asmee.
“Naje na biya kuɗin har na magani, sun ce Nurse zata riƙa baka”
Ta faɗa tana hita da ɗan ƙaramin mafecin dake hannunta.
“Mashallah har nawa aka biya ne?”
“Dubu ɗari da goma sha ɗaya, ni ban san dalilin yasa ta kawo ka wannan asibitin ba, ace allura guda dubu tara magani ma shegen tsaɗa”
“Asibitin kuɗi ce fa, ba kiga ɗaki suka ware mana ba”
“Allah dai ya baka lafiya mu bar Asibitin nan, ni ban ma ƙi mun koma gida ba gaba ɗaya”
“Gaskiya ni ba zan koma gida yanzu ba, ana kallo kayi aure ka auri masu abu sai kuma aga yadda na dawo da ciwo, kuma a can ai sai ma mun fi jin kunya tun da ƙyale ni zasu yi, maƙiya sai su mana dariya”
“Ai ba za a maka dariya ba kam sai dai a zagi iyayenta”
“Ni dai na fi son zamana nan, a cikin kuɗin ki bani dubu ɗari na bata sai ta siye wasu abubuwan, tun da tace BQ ɗin be ƙone ba sai mu zauna a cikin”
“A'a wane irin dubu ɗari kuma? Dubu shirin ai ya isheta ta siye komai”
“Mama har katifa fa da sauran kayan aiki, ashirin ba zasu isa ba”
“Ni zan je na siyo katifar, da kai na haka kawai za a ɗauki har dubu ɗari a bata, idan an bata nawa ya rage ni bana da lalurar ne? Ban ga dalilin da zata ci amfanin ka kai baka ci nata ba, wallahi tallahi na tsani yarinyar nan saboda iyayenta, sam basu da mutunci”
Asim ya sauke jiyar zuciya.
“Ni bana ma son tunawa da su Wallahi, rai na har ɓaci yake, hmmm Allah dai ya bani lafiya, na warke na tashi garau, Wallahi sai na basu mamaki”
“Ai kana da maƙiya kam Ibrahim Allah dai ya baka lafiya”
Da Amin ya amsa yana gyara zamam ƙafarsa.
RASHIDA POV.
Cikin mintuna ta isa gidan Asmee, tana fito mota Asmee na fitowa daga falo ta tarbeta.
Tashin hankalin dake fuskar Rashida ya ɓatar da na Asmee dan yadda taga Rashida ta rikice ta damu sai ita ta sassautama kanta, a tunaninta Rashida ta damu da matsalar ta ne har haka.
Da suka shiga falo kowanne kasa magana yayi sai kallon kallo suke, Rashida na tunanin ta ina zata fara, Asmee na fargabar irin amsoshi da zata bata.
“Wai ke ya akayi kika yi wannan kuskuren, Asmee dan me zaki cuci kan ki ki cece mu?”
“Rashida na faɗa wani haɗi ne yayi min wanda dole sai
Showing 69001 words to 72000 words out of 280121 words
A take yawun bakinta suka tsinke, cikinta ya ɗauki kuka, ba ƙaranin ƙoƙari rayi ba wajen ƙawata fuskarta da murmushi, dan ta nunawa Hilal ta jidaɗin.
“Mashallah Kalsoom ita ma tana da ciki? What a blessed”
“Tana ma har ya riga na ki, bata da matsala sosai ne shiyasa ba za a gane tana da cikin ba”
Amsarsa ta tabbatar mata da zarginta, daman dalilin tambayar kenan. Wata duniyar take ƙoƙarin kai shi dan ta nuna masa farincikinta, ta kuma ɓoye masa baƙincikin da ke son bayyana a fuskarta.
Zuwana Kalsoom yasa ya daina takura akansa a kanta, duk magiyar da yake mata yake nuna mata maitarsa yanzu ya daina tun da ya samu wani halalin nasa, sai dai daren yau da raya masa shi fiye da yadda yake zato, a yau tayi masa abunda ta shekara goma bata masa ba, ta sakar masa jikinta sosai, har sai da shi kansa ya gaji dan kansa ya bar.
Tare suka yi wanka, suka ci abinci da kuma dan abun taɓawa daya siyo musu ɗazu, a lokacin ƙarfe biyun dare yayi. Suna gamawa ta kwanta dan ba gado haƙƙinsa, shi kam be kwanta ba sai yayi nafisa raka'ah biyu, raka'ar farko ya karanta fatiha da ayatul kursiyu sai ya dora kulhuwallahu sama, a raka a ta biyu kuma ya karanta fatiha da amanar rasulu ya ɗora kulhuwallahu sama, sannan ya zauna yayi zaman tahiya kamin ya sallame a cikin tahiyar ya faɗawa Allah buƙatarsa, sannan ya sallame.
Sai da yayi salatin annabi da godiya ga Allah da istigifari ƙafa ɗari ɗari sannan ya sake ɗaga hannu yayi kirari ga ubangijinsa ya nemi yafiyarsa, sannan ya sake koro da buƙatarsa.
A cikin ɗauko abun ɗibar jini ya ɗibi jininta dan yasan da safe ba zai samu damar ɗiba zata ce masa aiki.
Washe garin da zai kai yaransa makaranta suma ya ɗibi nasu, Kalsoom kam sai daf da zai fita sannan ya ɗibi nata sai raki take masa tana masa shagwaɓa, wai da zafi ita zai ƙarar mata da jini, haka ta riƙa narke masa a jiki har yayi lattin zuwa aiki.
NAMRA POV.
Kwata-kwata bachi ƙaura yayi mata daga ido, bata ma jin alamunsa balle har tasa rai zai so mata, abu ɗaya zuwa biyu yayi mata tsaye a rai, maganganun da Asim yayi shi da mahaifiyarsa, wata zuciyar na shawarta akan ta bayayyana masa ta kuma tambaye shi abunda yake ƙoƙarin ɓoye mata, yayinda ɗayar kuma take ce mata ta haƙura taga iya gudun zuwansa dan tabbatar da zarginta.
Babu amfani da raya dare da tunani bayan Ubangijinta yana kallonta, kuma yana shirye ya amsa buƙatunta, tayi haramar ƙorar sheiɗan sannan ta samu kuzarin fita tayi alwalah, sannan ta dawo ɗakin tayi nafila ta ɗora sa salatin Annabi.
Firgigit Mardiya ta farka daga dogon bachin da take a farkigice har tana ihu. Namra ma dake kusa da ita sai da ta ji tsoro kowa dake cikin ɗakin ya matsa, Mahaifiyarta ta tashi tana kallonta.
Gabanta ta fara kallo kamin ta kalli bayanta, sai kuma ta bi ko'ina na ɗakin da kallo, ajiyar zuciya ta sauke yafi ashirin, sannan ta haɗe yawun bachin da suka cika mata baki, ba dan tasan tayi ba.
“Ke lafiyarki?”
Ashe dai duniya take, jin muryar mahaifiyarta ya ƙara tabbatar mata da a farke take.
“Wallahi wani mumunan mafarki na yi, wai wuta tana bina”
“Subhanallahi, ke kuwa ai addu'ah zaki yi”
Namra ta faɗa, tana rufe ƙur'anen dake hannunta, sannan ta nufi gurin bachinta tayi addu'ah bachi ta kwanta ba dan tana jin bachin ba, sai dan tana buƙatar jinginar da jikinta da tabar suka saba mata shimfiɗa da ita.
Washe gari...
Da sassafe ta siye tea da buroɗi ta nufi asibiti, dan bata son su Mama su kama hanya bata isa ba, tun da babu wanda zai kula da Asim sai ita. Duk yadda take ganin ta doka sammako sai taga har sun fi ta, dan tana shiga ɗakin taga alamar sun kama hanya.
Bata yarda ta nunawa Asim komai ba, ta gaisheshi sannan ta masa ya jiki ta soma zuba masa tea ɗin.
“Jiya kika tafi baki faɗa ba”
“Eh pad ɗina ne ya lalace shine naje gida na canja, su Mama sun kama hanya ko?”
Ajiyar zuciya ya sauke, yanzu kam hankalinsa ya kwanta, daman can yana tunanin ko ta ji maganar sune yasa taje ba tare data faɗa musu ba, ashe shi da Mama ba su canka dai-dai.
“Eh tace da wuri zata je yadda zata tararda matar da za a ranto kuɗin gareta”
“Allah yasa a dace”
Ta faɗa tana miƙa masa tea, kallon da tayi masa da kuma maganarsa sun zari zuciyarta, miyasa Asim yake ɓoye mata? Wani tunanin ne ya zo mata sai ta kawar da fuskarta gefe.
_______________________________
BEST REGARDS 💖🌺
KHADEEJA CANDY😘
*🌺🌺🌺 ZAGON ƘASA 🌺🌺🌺*
Website
www.khadeejacandy.com.ng
*PAGE - 33*
NOT EDITED ⚠️
Washe garin ranar da Mama ta tafi ta dawo, guraren uku da rabi na rana. Ita kaɗai ta dawo ba tare da Hajara ba, Namra bata nuna mata komai ba ta tarbeta da far'ah tana mata sannu da zuwa.
Tana son tayi labari Namra ta tsare su taƙi ta tashi, shi kansa Asim yana son magana da ita amman ba dama, tun da Namra tana gurin.
Kamar ta san Namra bata tanadar mata komai, tun a hanya ta tayi gurin biredin ta da lemu, sai ta ta ci ta ƙoshi, sannan ta tashi ta fita.
Da kanta taje ta biya kuɗin maganin dan kar taba Namra.
Ta dawo daga biyan maganin ne, Namra ta tashi tayi musu sallama ta baro asibitin.
Har ta iso gida kuka take, tana tunanin yadda Asim yake ɓoye mata lamarin, dan ta lura da yadda suke kallon kallo da Mama, hakan ya soma tabbatar mata da abunda Anty Amarya ke faɗa mata.
“Idan har ta tabbata Asim na son yaudarata....”
Sai kuma tayi shiru ta share hawayenta, ta miƙawa mai Napep kuɗinsa ta shige gida.
*** ***
“Thank you”
Ta faɗa tana murmushi tare da kallon mutumen daya tashi daga saman kujerar ta ya nufi ƙofar fita. Sai da ya fice sannan ta kalli wayarta dake ringing, sannan ta kai hannu ta ɗauka zuciyarta na raya mata irin labarin da Asmee zata bata.
“Ƴar gari kamar kin san yanzu nake tunanin ki nace ko kin samu zuwan kuwa?”
Kuka ta fara ji kamin Asmee ta ɗora mata da zancen dalilin kiran nata.
“Rashida ina ciki matsala”
“Lafiya miya faru?”
“Wani malami ne da muke zuwa gurinsa, yana ba mu taimako, shine yanzu ake ce mana malamin yana da ciwon nan na zamani, shine tun ranar na kasa sukuni ban ma sama naje gurin matsalar ki ba”
“Innalillahi wa'inna ilaihi raji'un, Asmee garin yaya? Ya taɓa sex dake ne? Ko me?”
Kuka tayi sosai har ka kasa magana.
“Ki faɗa min mana ki daina kuka”
“Ya taɓa lokacin da je neman wani taimako sai yace min sai na kawo sperm ɗin wani wanda ba mijina ba, da jinin al'ada da shi za a haɗa, ni kuma na ce masa ban san inda zan samo ba, shine....”
Ta ƙarasa da kuka
“Ke yanzu kin je an gwada jinin ki ance kina ɗauke da ciwon ne? Stop crying and tell me Asmee”
“Ban je ba, tsoro nake ji ban san wanda zan faɗawa ba sai, dan bani da ƙawa irin ki, na rasa yadda zan yi tsoron gwajin na ke, aiki ma na daina zuwa yanzu”
“Innalillahi Ya salam Ya salam”
Ta soma zagaye office ɗin tana dafe kai, da wayar a kunnenta.
“Ki kwantar da hankalin ki kinji karki faɗawa kowa, kuma karki yi abunda zai sa mijin ki ko wani ya zargi wani abu, i will call you back”
Tayi saurin kashe wayar tana tuna jininta da Hilal ya ɗiba, idai har Asmee ta kamu da cutar to itama zata iya kamuwa da ita tun da har suna using mutum ɗaya.
Faɗuwa tayi zaune zumi na keto mata ta ko'ina, hannu ta kai tana shafa kanta, tana girgiza shi kamar wani ne a gabanta.
“Ko shiyasa ya sake ɗibar jinina? Amman kuma ai da ba zai kusance ni ba, amman yanzu idan ya auna dole ya gano idan akwai shi”
A fili take furucin zuciyarta a karaye, jikinta har tsimi yake, yanzu kam hannaye biyu tasa ta dafe kanta tana tunanoma kanta mafita.
“Dole ne na dakatar dashi daga yin gwajin, kuma dole ne nima naje na bincika kai na, indai har da gaske ne Asmee kin cuce ni”
Da sauri ta tashi ta kaɗe jikinta ta fiddo hoda a jakarta ta gyara fuskarta sannan ta ɗauki jakar ta fita. Sai da ta biya ta faɗa musu fitar gaggauwa ta kamata, sannan ta fito harabar bankin ta shiga motar, ta ɗauki hanyar Asibiti.
Akwai ƴar tazara tsakaninta da asibitin, amman yadda ta sakarwa motar wuta yasa ta isa cikin ƙanƙanen lokaci. A harabar asibitin tayi parking, ta fito ta duba gurin da aka tanadarwa manyan likitoci dan faka motocinsu.
Motar Doc Hilal ce ta uku a gurin, that's means yana cikin asibitin, safa da marwa ta fara yi tana tunanin ta inda zata fara. Lab ne ya faɗo mata a rai. Da fargaba ta kutsa kai cikin asibitin ta ɗauki hanyar da zata hada ta da lab ɗin, ƙasa-ƙasa take kallon mutane, tana fargabar haɗuwa da Hilal, dan ko ganinta yayi bata san me zata ce masa ba.
Ta tararda mutane da ɗan yawa a gurin da aka tana da dan karɓar results ɗin jini da fitsari, hakan yasa ta zagaya ta shiga ciki tun da ita ba baƙuwar asibitin ba ce.
Biyu daga cikin mutanen da suke gurin sun gane, tun da sun san matar Doc ce, cikin mutunci da far'ar ta gaisa da su tana yi tana kallo ƙofa.
“Habib na ce kun gama gwajin jinin da Doc ya kawo? Za a tafi dashi wani garin ne”
Wanda ta kira da Habib ɗin ya amsa da.
“Eh tun ranar muka shi ba ai”
“Ba yau ya kawo ba?”
“A'a ina jin tun monday ne, Monday or Tuesday? Abbas kai ka bashi ko?”
Wanda aka kira da Abbas ɗin be ma kula.da zancen su ba sai rubuce-rubucen sa yake, Habib ɗin ya kalleta.
“Ina jin Monday ne, an dai kwana biyu yanzu”
Gabanta ya faɗi sosai.
“O'o nasan ya jefar da results ɗin wani wajen shiyasa ya ƙi ya faɗa min, amman yau be kawo maka wani ba?”
“Gaskiya be kawo ba, dan mu muka yi duty safe yanzu zamu tashi”
Nauyi zuciyarta sosai tayi mata har sai da ta tsayi ya gagareta, ta zauna a kujerar dake gurin.
“Amman dan Allah ya za'ayi na samu results ɗin wacan gwajin? Tun da ya ɓatar nasan ba zaku rasa a littafin ku”
“Wallahi da an fito da results ɗin an rubuta a littafi ansa a paper na results ɗin ake kai su ɗakin ajiya, sai dai shi Doc zai iya zuwa yayi ma Doc Omar magana, sai ya bincika masa, amman nan results kawai muke badawa”
“Okay Thank you bari na koma gurin Doc ɗin nayi masa magana”
“Okay a gaida yara”
Ya faɗa yana kallon bayanta, irin ƴan iskan samarin nan ne da basa gani su kauda idonsu.
Ƙafafunta sun mata nauyi, ga idonta dake son ciki da ƙwalla tana mayarwa, akwai ƴar tazara tsakanin office ɗin da lab, hakan ya bata damar tunanin abunda zata cewa Hilal idan ya ganta, idan kuma ta koma bata shiga ba ta san zai iya samu labarin ta shigo cikin asibitin tun da akwai waɗanda suka santa, kuma zasu iya faɗa masa.
_Thank you so much my tomatir my albasa my daddawa my miyar kuka_
Yana dannawa Ƙalsoom reply ɗin ta whatsapp. Rashida ta turo ƙofar office ɗin ta shigo da murmushi a fuskarta.
Tashi yayi daga jinceren da yake saman kujera ya kalli da dariya.
“Surprise surprise surprise”
“Yes Darling, na biyo ta nan baya ne shina nace bari na biyo na ga farinciki na”
Ya ɓata rai sosai lokacin daya lura da yanayin tufafin dake jikinta. Suit ne mai wando ta riga sai ɗan ƙaramin hijabi dake kanta.
“Daman Haka kike fita daga office? Ba mun yi maganar nan dake ba dan me zaki fito baki ɗora abaya a sama ba, a cikin office ɗin ki kawai na yarda ki riƙa zama haka, kika ce kin ji ashe ni kike ma ko? Yana ɗaya daga cikin dalilin daya sa bana son aikin nan na ki, bana son wani na ganin matana abun nan yana min zafi”
Sai a lokacin ta kula da tufafin da suke jikinki, tsabar hankalinta baya jikinta bata ma san ta fito a haka ba. Hannayenta tasa ta laƙamo wuyansa.
“Im sorry Wallahi fitar gaggauwace shiyasa amman ba zan sake ba i promise”
“Yanzu haka kika shigo a asibitin nan kowa na kallon ki? Haba Rashida idan an girma a san an girma mana, kefa uwace kamata yayi idan kin ga Ezzah tayi wannan shigar kiyi mata faɗa ba wai ki yi ba”
Ta saki wutan nasa ta nufi freezer dan ita ba faɗan da yake mata bane a gabanta, abunda ya kawo ta take ƙoƙarin yi, tsayawa tayi ta duba da kyau drinks ɗin da tasan babu a freezer ɗin tace masa tana so.
“Nidai nace kayi haƙuri, kuma ina son nasha coc”
Ta faɗa tana marairaice masa, daman tasan baya shan coca-cola saboda irin abubuwan da ake faɗa akanta, kuma ta san yadda ya tsani kayan yahudawa.
Kamar zai ce mata babu, sai kuma ya ƙyaleta tun da yasan tana da ciki wani abun dole ya ɗaga mata ƙafa, sai dai be sakar mata fuska ba dan har yanzu ransa a ɓace yake, sai kawai ya juya ya fita.
Da sauri ta nufi teburinsa ta fara duba takardun da suke gurin, bata ga abunda take nema ba, hakan yasa ta nufi wata ƴar ƙaramar wardrobe dake gefen kujerar, har ta kai hannu ta buɗe sai kuma wani tunanin ya zo mata.
‘Idan na yamutsa masa takardu dole zai zargi wani abu’
Sai kawai ta fasa buɗewa ta koma ta zauna a kujerarsa ta ɗauki ƙafafunta ta ɗora saman teburin kamar babu abunda yake damunta, alhalin a can cikin zuciyarta tashin hankaline da tunani suka taru suka mata katutu.
Yadda ya fita haka ya dawo fuska a haɗe kamar be taɓa dariya ba, ransa ya sosu sosai da ganin irin dress ɗin data shigo dashi cikin asibitin.
Miƙa mata Coc ɗin yayi ya nufi windows ɗin office ɗin ya rufe. Tashi tayi tare da Coc a hannu daman can ba shanta zata yi ba, bata ma jin zata iya saka wani abu a cikinta yanzu.
“Ni zan wuce”
Ya watsa mata wani kallo.
“Haka zaki fita?”
Ta ɗan kalli jikinta
“To ya zan yi?”
“Ban sani ba”
Ya nufi hanger ɗinsa ya ɗauko labcoat ya ɗora mata sama.
“Kuma kar ki cireta har office”
“Doc zan bi ta lab na karɓi results, nayi mafarkin na haifi ƴan'biyu”
Dariya yayi sosai, wanda be shirya yi ba
“Toh ai ba a jini ake ganin twins ba, kuma ban ma kai awon jinin ba”
“Miyasa?”
“Ba nan za min ba, Asibitin Alex zan kai, saboda asibitin su tafi ta mu kayan aiki”
“Okay”
Ta faɗa zuciyarta cike da jindaɗin jin inda zata kai jinin, wani gurin kuma ta jidaɗin da be riga ya kai ɗin ba.
“To ina ka aje shi? Karka sake ce min ya ɓata kuma”
“Ba zai ɓata ba yana nan cikin mota na”
Ya faɗa yana jan hancinta, ita kuma ta kai bakinta dai-dai nashi tayi masa kiss.
Har gurin mota ya rakata sai da ta shiga yaga tashinta sannan ya koma office ɗin.
A maimakon ta koma asibitin sai kawai ta jiya pharmacy ta siye abu sannan ta ɗauki hanyar da zata kai ta gidan Asmee.
__________________________________________
*🌺🌺🌺 ZAGON ƘASA 🌺🌺🌺*
Website
www.khadeejacandy.com.ng
*PAGE - 34*
NOT EDITED ⚠️
ASIM POV.
“Naje na biya kuɗin har na magani, sun ce Nurse zata riƙa baka”
Ta faɗa tana hita da ɗan ƙaramin mafecin dake hannunta.
“Mashallah har nawa aka biya ne?”
“Dubu ɗari da goma sha ɗaya, ni ban san dalilin yasa ta kawo ka wannan asibitin ba, ace allura guda dubu tara magani ma shegen tsaɗa”
“Asibitin kuɗi ce fa, ba kiga ɗaki suka ware mana ba”
“Allah dai ya baka lafiya mu bar Asibitin nan, ni ban ma ƙi mun koma gida ba gaba ɗaya”
“Gaskiya ni ba zan koma gida yanzu ba, ana kallo kayi aure ka auri masu abu sai kuma aga yadda na dawo da ciwo, kuma a can ai sai ma mun fi jin kunya tun da ƙyale ni zasu yi, maƙiya sai su mana dariya”
“Ai ba za a maka dariya ba kam sai dai a zagi iyayenta”
“Ni dai na fi son zamana nan, a cikin kuɗin ki bani dubu ɗari na bata sai ta siye wasu abubuwan, tun da tace BQ ɗin be ƙone ba sai mu zauna a cikin”
“A'a wane irin dubu ɗari kuma? Dubu shirin ai ya isheta ta siye komai”
“Mama har katifa fa da sauran kayan aiki, ashirin ba zasu isa ba”
“Ni zan je na siyo katifar, da kai na haka kawai za a ɗauki har dubu ɗari a bata, idan an bata nawa ya rage ni bana da lalurar ne? Ban ga dalilin da zata ci amfanin ka kai baka ci nata ba, wallahi tallahi na tsani yarinyar nan saboda iyayenta, sam basu da mutunci”
Asim ya sauke jiyar zuciya.
“Ni bana ma son tunawa da su Wallahi, rai na har ɓaci yake, hmmm Allah dai ya bani lafiya, na warke na tashi garau, Wallahi sai na basu mamaki”
“Ai kana da maƙiya kam Ibrahim Allah dai ya baka lafiya”
Da Amin ya amsa yana gyara zamam ƙafarsa.
RASHIDA POV.
Cikin mintuna ta isa gidan Asmee, tana fito mota Asmee na fitowa daga falo ta tarbeta.
Tashin hankalin dake fuskar Rashida ya ɓatar da na Asmee dan yadda taga Rashida ta rikice ta damu sai ita ta sassautama kanta, a tunaninta Rashida ta damu da matsalar ta ne har haka.
Da suka shiga falo kowanne kasa magana yayi sai kallon kallo suke, Rashida na tunanin ta ina zata fara, Asmee na fargabar irin amsoshi da zata bata.
“Wai ke ya akayi kika yi wannan kuskuren, Asmee dan me zaki cuci kan ki ki cece mu?”
“Rashida na faɗa wani haɗi ne yayi min wanda dole sai
Book Chapters
Chapter 1Chapter 2Chapter 3Chapter 4Chapter 5Chapter 6Chapter 7Chapter 8Chapter 9Chapter 10Chapter 11Chapter 12Chapter 13Chapter 14Chapter 15Chapter 16Chapter 17Chapter 18Chapter 19Chapter 20Chapter 21Chapter 22Chapter 23Chapter 24 Chapter 25Chapter 26Chapter 27Chapter 28Chapter 29Chapter 30Chapter 31Chapter 32Chapter 33Chapter 34Chapter 35Chapter 36Chapter 37Chapter 38Chapter 39Chapter 40Chapter 41Chapter 42Chapter 43Chapter 44Chapter 45Chapter 46Chapter 47Chapter 48Chapter 49Chapter 50Chapter 51Chapter 52Chapter 53Chapter 54Chapter 55Chapter 56Chapter 57Chapter 58Chapter 59Chapter 60Chapter 61Chapter 62Chapter 63Chapter 64Chapter 65Chapter 66Chapter 67Chapter 68Chapter 69Chapter 70Chapter 71Chapter 72Chapter 73Chapter 74Chapter 75Chapter 76Chapter 77Chapter 78Chapter 79Chapter 80Chapter 81Chapter 82Chapter 83Chapter 84Chapter 85Chapter 86Chapter 87Chapter 88Chapter 89Chapter 90Chapter 91Chapter 92Chapter 93Chapter 94