kunna wayarta, saƙon da ya shigo mata be bata mamaki ba saboda momi ta faɗa mata komai tun kamin Asim yayi mata wannan saƙon.
_Apple ɗin da kika ci Mahaifiyarki ce ta ba ni tace na kaiwa tsohuwar mamata, bayan kuma ta san na mutuwa ne, mahaifiyata ta ci ta mutu dan haka na yi ɗaukar fansa da ke_
_Ba ka yi kuskure ba Asim, Mahaifiyarta ta cancanci fiye da abunda ka yi mata, ni kuma na yi kuskuren yarda da kai, amman har gobe ina son ka_
Shine amsar da ta mayar masa, ta share hawayenta ta kwanta saman gado tana kallon window. Yayinda Hajiya Sadiya take tsaye a falo tana ta buge-bugen waya akan a taimaka mata kar ƴarta ta mutu, idan ta kira wannan tana kuka ta kira wannan duk ta bi ta haukace sai kuka take kamar zata tashi gidan. jin kamar ƴarta na tari yasa ta bar falon a guje ta nufi ɗakin tana kiran sunanta, amman ina Nably ta yi nisa har bata iya magana, duk ta ɓata gadon da aman jini kamar wacce ta amaye hanjin cikinta. Hannayenta biyu tasa tallafo kanta tana shafata.
“Nabila karki ta fi ki bar ni ke kaɗai kika rage min, na shiga uku na saka kai na a halaka, wannan baƙar ƙungiya bata min rana ba”
Kallonta kawai Nabila ke yi a wahalce tana numfashi da ker, hawaye na bin fuskarta har ta amsa kiran mahallicinta.
Wani uban ihu Hajiya Sadiya ta saki ta fita a ɗakin a guje, tana kaiwa harabar gidan ta zame ta faɗi ƙasa ba sumammiya.
UZAIR POV.
Wasa-wasa yau kusan talatin da ɗaya ana abu ɗaya babu sauƙi, sau biyu ana fita da shu waje amman babu abunda yake canjawa kuma ko ina aka je abu ɗaya ake faɗa cewar ba zai sake tafiya ba.
Tun ranar da ya aika Tahir be gane kan maganarshi ba, sai yawo yake ta masa da hankali, kullum da kalar abinda zai faɗa masa, kuma duk tsowon lokaci Yasmin bata taɓa taka asibitin da sunan ta zo ganin Uzair ba, abunda ya bawa kowa mamaki ciki har da Abbah. Ranar wata Lahadi duka ƴan'uwa suka saka ta gaba ana mata faɗa da tambayar dalilin ƙin zuwa ganin mijinta, amman ta kasa furta musu komai sai kuka take, a dole tasa suka ƙyaleta suka saka mata ido.
Ana sauran kwana biyu Abbah ya sake fitar da shi india, Tahir ya zo dubasa daman duk bayan kwana biyu yake zuwa ya gansa.
Yau ya fi bashi tausayi fiye da ko yaushe, ya rame sosai kamar ba abokinsa ba, wai yau Uzair ne kwance a nan baya iya komai, lallai duniya abun tsoro ce. Hawayen da ya gani a idon Uzair ya tashi hankalinsa sosai hakan yasa yau ya yanke shawara faɗa masa gaskiya, da kuma ba shi shawarar abunda yake tunanin zai zame masa mafita.
Ajiyar zuciya Tahir ya sauke yana kallon Uzair ya ce.
“Na yi ta maka wasa da hankali akan maganar Malamin nan, magana ta gaskiya Uzair mutumen baya raye, lokacin da naje gidansa na samu ranar ake sadakan bakwai nasa, na ɓoye maka ne saboda karka tashi hankalinka”
Wasu zafafan hawaye ne suka zubowa Uzair, ya haɗe yawun bakinsa cike da tausayin kansa ya ce.
“Tawa ta ƙare kenan! Haka ƙarshe na zai zo ni kuma? Ina ma ace mutuwa na yi na huta...”
Tahir ya dafa ƙafaɗarsa ya matsa kaɗan.
“ina tunanin abunda ya fi, ka samu Namra da iyayenta ka yi musu bayanin komai, kuma na nemu yafiyarsu, wata ƙila abunda ka aikata ne haƙƙi yake biye da kai, idan kuma har ba haka bane, to Amira ce ta yi maka asiri, idan zaka fallasa komai ka fallasa tare da Amira idan tana gurin, hakan zaisa guiwarta ta yi sanyi ta je ta kare abunda ta yi maka”
“Zan aikata Tahir indai har wannan zai sa na samu lafiyata, amman ya za'ayi Amira ta zo nan? Da wane ido zan kalli Abbah na ce ina son magana da Namra?”
“Zan kawo maka Amira, Namra kuma ka faɗawa Abbah kana son ganinta tare da Abbah”
Ya jinjina kai, shi dai ya shirya yin komai akan lafiyarsa, dan bai jin zai jure zama a irin wannan rayuwar. Bayan Tahir ya fita Mahaifiyarsa ta dawo ɗakin daman yanzu ita ce take jinyarsa ita da wani ƙanensa da kuma ƙanwarsa.
“Umma ina son ganin Abbah da Namra”
Ta kalleshi cike da mamaki.
“Ta maka me? Yarinyar da tun da ka kamu da rashin lafiyarnan bata taɓa cewa tana gaisheka ba balle ta zo duba ka ita zaka nemi gani yanzu?”
“Zan yi wata magana da ita mai muhimmanci, dan Allah ki taimaka min itace kawai mafitar wannan ciwon da nake yi, da ta zo zan samu sauƙi”
“Ban gane ba? Kamar ya itace mafitar ciwonka? Kana magana kamar wanda baya cikin hayyacinsa, Uzairu cuta fa ba mutuwa ba ce”
“Ki taimaka min ki kawo min ita mu yi magana zan faɗa muku komai,ciki har da dalilin daya sa Yasmin ta ƙi ta tako asibitin nan”
Da farko Umma ta ɗauka zafi ciwo ne yasa shi wannan maganar, daga baya kuma sai ta fahimci yana cikin hankalin kansa, sai dai maganganun da yake sun ɗaure mata kai.
Tahir na barin gidan ya nufi gidansu Amira, kamin ya isa sai da ya kira yayanta ya faɗa masa shi baya gida amman Amira tana gida. Harabar gidan ya shiga da motarsa, sannan mai gadin ya shiga ciki yace ana sallama da Amira, bayan ƴan mintuna ya dawo yace wai ance wanene?
“Kace Tahir ne abokin Big Bro”
Sai mai gadin ya koma, ya dawo ya ce wai ance ya shigo ciki. Ba musu ya doshi babbar ƙofar Falon. Da sallama ya shiga Ammy ta amsa masa tare da Amira sannan ya zauna, suka gaisa ya faɗa musu abunda yake tafe da shi. Ba Amira ba har Ammy ta yi mamakin jin Uzair na son ganinta to me zai ce mata? Bayan duk abunda yayi mata, daman tun da suka samu labarin bashi da lafiya Ammy da Abban Amira suke cewa wai amanar Amira ce ta kama shi.
“Yana nemana kamar ya ? Me zai ce mun?”
“Nima ban sani ba, amman yace maganar tana da muhimmanci, sosai”
Ammy ta ce
“To ba zata ita kaɗai ba, tare zamu je, kuma sai Abbah ta ya dawo duk abunda ya ce shi zamu yi”
Tahir ya miƙe tsaye yana faɗin
“Kamin na zo nan sai da na yi magana da Big bro, idan har wani abu ne mai cutar da ke ba zai bari na shigo nan na faɗa miki ba”
“Koma dai minene sai mahaifinta ya dawo”
“To hakan yayi, ni zan wuce”
“A gaida gida”
Ammy ta faɗa sannan ta bishi da kallo har ya fice. Gaɓa ɗaya jikin Amira yayi sanyi, zuciyarta sai yaye-yaye take mata, ta rasa dalilin da zai sa Uzair ya so ganinta, to ko yana zargin tana da hannu a ciwonsa ne? Ko kuma wani abun ne kuma ya faru? Maganar Abbah ce ta dawo da ita daga duniyar tunanin da ta tafi.
“Bari na kira Abbah ki na faɗa masa”
Kai kawai ta iya ɗagawa ta cigaba da tunanin da take.
NAMRA POV.
Bayan an gama bikin Maryam da Hindatu, Abbah ya shiga fafutukar nemawa Namra Admissions a wata makarantar koyarda ilmin computer. Kasancewar duka jami'o'i a yanzu sun gama ɗaukar ɗalibai, gashi kuma bata da komai a yanzu saboda ƙonewar da takardunta suka yi a motarta lokacin da Asim ya taɓa haɗari, ba ƙaramin kuɗi Abbah ya kashe ba wajen fito mata da tsofin takardun da suke makarantar primary da kuma Secondary school. Jami'ah kuma sai next year zata fara, tun da ta riga ta lalata karatunta tun a wacan lokacin.
Sai dai wannan karon kan Alhamdulillah komai ya zo da sauƙi, kasancewar Abbah ya saki ƙuɗi cikin ƙanƙanen lokaci aka yi komai. Aiko murna gurin Anty Amaeya da Namra ba a magana kamar su haɗe Abbah, dan jindaɗi.
Monday mai zuwa Namra zata fara zuwa makaranta, ranar Assabar da Safe Abbah ya kawo mata sabon direba da zai riƙa kai ta makaranta, Namra ta yi murna sosai dan bata tsammaci haka daga gurin Abbah ba.
“Abbah ka yi min abubuwan da ban yi tsammani ba, ka nuna min sosai, Allah ya ba ni ikon saka maka”
Duk suka amsa da Amin har Anty Amarya dake ƙara jin son Abbah har cikin ɓargon ranta. Namra ta ɗauki ɗankwalin abayarta ta yafa ta fita dan ganin sabon direban nata. Tsaye tayi cak a baki ƙofa tana furta
“Lamido”
“Yes Ma'am”
Ya amsa a natse, yayi fari yayi kyau sosai ƙananna kayan da ke jikinsa sun ƙarɓe sa sosai. Ta nunashi da yatsa sai ta kasa magana. Murmushi yayi ya gabatar da kansa.
“My Name is Aliyu Adamu Lamido your new driver”
“How.... How....”
Maganar ta laƙe ta ƙi fitowa sai ta sake nuna shi da yatsa.
“You...”
Murmushi ya sake yi yana kallon yadda ta canja ta yi kyau kamar ba ita ba, baƙin nan nata sai sheƙi yake ga dogon hancin nan da farraren idonta da suka ƙara fitowa.
‘Black beauty akwai kyau’
A zuciyarsa yayi maganar a fili kuma murmushi yake mata mai ɗaukar hankali. Juyawa ta yi ta koma cikin falon, cike da ruɗani ta kalli Abbah ta ce.
“Abbah da gaske shine sabon direba na?”
“Eh ko be miki ba ne?”
“Me direban yayi”
Anty Amarya ta tambaya. Zaunawa Namra ta yi tana faɗin.
“Anty Lamido ne fa”
“Wane Lamido kin san shi ne?”
“A gidansu na sauka Kaduna, shi ya ɗinga ɗawainiya da ni har kuka zo kuka ɗauke ni, Lamido na gidansu Neina fa”
“Au shine? Ya akayi ya zo nan ne?”
“Nima ban sani ba, abun ya ɗaure min kai ne, Abbah ina ka haɗu da shi?”
“A can ƙamfani ya same ni, wai yana son a ɗauke shi direba idan zai samu, kuma baya son na kamfani na gida yake so, kin san daman ni kuma ina neman direban da zai riƙa kai ki scul yana maido ki, shiyasa na ɗauke shi”
Namra ta girgiza kai.
“Abbah why not ka ɗauke shi aiki a kamfanin ka, yayi degree fa, aikin ne be samu ba”
“Ko zan ɗauke shi ba yanzu ba, sai naga gudun ruwansa, idan dai be miki ba za a iya canja miki wani”
“Oh no yayi min, ba matsala Allah ya saka maka da alheri”
“Amin, yanzu sai ki tashi muje Asibiti, Uzair ya ce min yana son ganinki”
“Ni?”
Ta nuna kanta, ba ita kaɗai ba, har Anty Amarya mamaki ta yi.
“Ya za'ayi Uzair ya cw yana son ganin Namra? Kin yi wata magana da shi ne?”
“Anty ya za'ayi na yi magana da shi, tun da na bar garin nan har na dawo wata kalma bata taɓa shiga tsakani na da shi ba”
“Ɗazu dai Mahaifiyarsa ta kira ni tace min dan Allah na zo da ke, Uzair yace zai yi wata magana da ke mai muhimmanci”
“Ni gaskiya ba zani ba”
“Sai fa kin je, indai har zan baki umarni ki bi, bawan Allah nan ban san abunda ya tare miki ba, daga kawai yace yana son ki, kuma na ga yanzu ko lafiyar jikinsa bata ishe shi ba, ya aikamata ki je ki masa sannu”
“Zan je kawai bisa Umarnin ka”
“To tashi ki saka Hijabin ki”
Ba musu ta tashi ta nufi ɗakinta dan ɗauko Hijabin.
“Wai ko na taso muje har da ni ne?”
Anty Amarya ta faɗa tana kallon Abbah, dan taji me zaice, dan tana cike da son sanin dalilin kiran Namra da Uzair yayi bata son a bata labari.
“Tashi muje komai dai son gulmarki sai kin ba su ɗaki sun yi magana”
Abbah ya faɗa da fuskar zolaya. Anty Amarya ta tashi tana dariya ta nufi ɗakinta.
Cikin ƙanƙanen lokaci suka isa asibitin, gaban Namra sai fat fat fat yake, duk da bata san ta yi wani laifi ba, tana jin tsoron kiran da Uzair yake mata. Bama kamar lokacin da suka shiga ɗakin ta yi ido huɗu da Amira, kallon kallon Akuya kallon Kura suka riƙa yi ita da Amira, ko wannen kuma.ya kasa cewa ɗan'uwansa uffan. Daga su har Ammy da Anty Amarya, Ammy sai faman hararar Anty Amarya take da Namra, Abbah ne kawai ya gaisa da Abban Amira, sannan Big Bro ya gaishe shi, ya kuma gaishe da Anty Amarya sai kuma ya kalli Namra fuskarsa da murmushi ya ce.
“Namra ba gaisuwa, kin san ni fa yayanki ne”
“Ina wuni”
Ta gaisheshi ba tare da tayi murmushi ba, ita hankalinta gaba ɗaya ya tattara ya koma kan Uzair yanayin yadda ta ganshi ya bata mamaki, daman hausawa suka ce abunda duk ya baka tsoro wata rana sai ya baka tausayi, gaba ɗaya ya tafi da imaninta, ya rame sosai, ga ledar fitsari an saka masa ta ƙasanshi, saboda rashin tashin da yake. A ɗayan ɓangaren kuma tana mamakin ganin Amira a ɗaki tare da iyayenta da kuma abokinsa Tahir.
“Ka tara mutane a nan kuma baka ce komai ba”
Umma ta faɗa cikin rashin daɗin rai, dan bata so ya kira Amira ba, duk da bata san dalilinsa na kiranta ba.
Ya ɗauki dogon lokaci kamin hawayen da suke masa zuba su tsagaita masa har yaja dogon numfashi ya sauke, sannan ya soma magana.
“Abbah zaka iya tuna wani lokaci a baya da aka ce Namra ta gudu taje gurin Asim? Ni na ɗana mata tarko tare da aminiyarta Amira, na bata sabon number da sunan zata zo ta ga Asim a bayan gidansu su gaisa, alhalin ni ne ba Asim ba, bayan na ɗauke ta sai abokaina suka canja min shawara da sunan kar na mata komai, na maidata a can, abokina ne ya faɗawa mai gadin gidana abunda zai faɗa akan ya tsince ta a bayan gidan ana ƙoƙarin yaga mata mutunci, kuma ana kiran sunan Asim... Kasan dalilin da yasa na yi mata wannan sheri? Saboda ta tona min asiri akan abunda na ke aikatawa, wato na neman maza ƴan'uwana, ba ƙarya ta faɗa ba, ta gan ni da gaske ina aikata wannan abun, amman na ƙaryata ta ne saboda ina ganin kamar asirina zai tonu ne, a lokacin, shine dalilin da yasa na ɓullo da maganar neman aurenta, sai ita kuma ta ƙi yarda, sanadin hakan da kuma gudun karta tona min asiri abokina Najib ya kai ni gurin wani boka muka mata asiri, yace sai an kawo rigarta da ita za ayi wannan asirin, sai na samu Amira na biyata na faɗa mata haka kuma ta yarda ita taje ta aro min rigarta da sunan ita zata saka muka kai akayi mata asiri da wannan rigar, daman can bokan ya faɗa mana duk lokacin da ta saka rigar idan har asirin be kamata ba to zai dawo kan mu ne, saboda Namra tana da ƙarfin addu'ah. Da asirin be kama Namra ba sai ya kama Amira, sanadin hakan ta gudu ta bar gida, ban sake jin ɗuriyarta ba, sai a lokacin da ta aiko min da wasiƙar cewar idan har ban je na kare wannan aikin ba zata iya aikata min komai. A lokacin ne Yasmin ta gani, kuma ta gano abunda ya shiga tsakanina da Adnan, wata rana ne da rana na shigo sai na tarar bata cikin gidan, sai kawai na afkawa ɗa na, daman can nafi son yi namiji, tun daga lokacin na keɓe Adnan ina jiyarsa bata gane ba, sai daga baya, sanadin hakan tace zata kai ni kotu, ni kuma na ƙaryata gaskiyarta, Washe garin ranar ne Hajiya barau ta kira ni ta faɗa min Namra ta dawo, daman ita take labarta min halin da Namra take ciki, da kuma duk wani abu dake gudana a gidan...”
Tun da ya fara maganar be tsaya ba sai da ya kai aya. Idon Abbah sun rine sun yi ja sosai, Abbah Amira ma kansa ya ɗaga sama ya maida hannayensa baya yana jinjina lamarin. Anty Amarya da Ammy kuma suna hawaye, Amira kan kasa kuka ta yi duk ta rikice jikinta sai rawa yake gumi na keto mata ta ko'ina.
“Miye dalilinka na faɗar gaskiya Uzair miyasa ba ka yi shiru da bakin ka ba? Miyasa baka ɓoye sirrinka ba kamar yadda nima na ɓoye nawa? Ban yi niyar faɗawa kowa abunda ka aikata ba Uzair, duk da rayuwar da na shiga ta fi wacce kake ciki a yanzu, dan ni nafi ƙaunar irin ciwon nan naka na san zai sadani da lahira a nan kusa, sama da jiran gawon shanu, jiran abunda babu ranar zuwansa. Ban taɓa tunanin haka ba, na yi tunanin ka haɗa kai da Namra ne ka cutar da ni ashe ni na cutar da kai na! Yanzu na fahimci dalilin da ya sa na gudu na bar gidan mu, kuma bayan na gudu ban faɗa hannun ƙwarai ba, sai na faɗa hannun ɗan fashi, ya mayarda da ni kamar matarsa, ta sanadinsa na ceci wani mutun wanda nake wa jiran gawon shanu, a familynsu na zauna, ina ganin kamar wata sabuwar rayuwa zan shimfiɗa ashe a saman wuta na yi shinfiɗar....”
Amira ta ƙarasa tana durƙushewa a gurin cikin wani irin kuka da yake jin kamar ta haɗiye zuciya ta mutu ta huta. Lokuta da dama ta kan ji hakan idan ta tuna yadda Abdool ya juya mata baya, mutumen da ta fi ƙauna fiye da komai a rayuwarta, a yanzu haka bata da buri sai na shi, shiyasa ta kasa maida jikinta duk da tana tare da iyayenta.
Gaba ɗaya Namra ta ruɗe ta kasa gane komai, daga Uzair ɗin har Amira kallonsu take tana hawaye.
“Yasmin ta kasa samun fili a zuciyarta ta yafe min, saboda na yi mata sara ne a baƙin wuya, amman ke na san zaki iya yafe min, duk da kema na miki illah, amman ki dubi girman Allah ki yafe min ko Allah zai tashi ƙafaɗuna. Idan kuma har wani aikin ne Amira ta yi min dan Allah ki je ki warware shi, saboda na tsorata da kalamin da kika rubuta min cewar zaki ɗauki mataki. Ba zan iya jure zama cikin wannan rayuwar ba, ki taimaka min ki yafe min Namra...”
“Ba zata yafe maka ba, ashe kai ne silar komai, Namra ba zata yafe maka ba...!”
Abbah ya faɗa a tsawace, har sai da Namra ta kalleshi. Ya nufi ƙofa a hasale ya buɗe.
“Mamana wuce mu je”
Abban Amira yayi saurin riƙe Abbah.
“Haba ai babba baya haka, babba
Showing 237001 words to 240000 words out of 280121 words
_Apple ɗin da kika ci Mahaifiyarki ce ta ba ni tace na kaiwa tsohuwar mamata, bayan kuma ta san na mutuwa ne, mahaifiyata ta ci ta mutu dan haka na yi ɗaukar fansa da ke_
_Ba ka yi kuskure ba Asim, Mahaifiyarta ta cancanci fiye da abunda ka yi mata, ni kuma na yi kuskuren yarda da kai, amman har gobe ina son ka_
Shine amsar da ta mayar masa, ta share hawayenta ta kwanta saman gado tana kallon window. Yayinda Hajiya Sadiya take tsaye a falo tana ta buge-bugen waya akan a taimaka mata kar ƴarta ta mutu, idan ta kira wannan tana kuka ta kira wannan duk ta bi ta haukace sai kuka take kamar zata tashi gidan. jin kamar ƴarta na tari yasa ta bar falon a guje ta nufi ɗakin tana kiran sunanta, amman ina Nably ta yi nisa har bata iya magana, duk ta ɓata gadon da aman jini kamar wacce ta amaye hanjin cikinta. Hannayenta biyu tasa tallafo kanta tana shafata.
“Nabila karki ta fi ki bar ni ke kaɗai kika rage min, na shiga uku na saka kai na a halaka, wannan baƙar ƙungiya bata min rana ba”
Kallonta kawai Nabila ke yi a wahalce tana numfashi da ker, hawaye na bin fuskarta har ta amsa kiran mahallicinta.
Wani uban ihu Hajiya Sadiya ta saki ta fita a ɗakin a guje, tana kaiwa harabar gidan ta zame ta faɗi ƙasa ba sumammiya.
UZAIR POV.
Wasa-wasa yau kusan talatin da ɗaya ana abu ɗaya babu sauƙi, sau biyu ana fita da shu waje amman babu abunda yake canjawa kuma ko ina aka je abu ɗaya ake faɗa cewar ba zai sake tafiya ba.
Tun ranar da ya aika Tahir be gane kan maganarshi ba, sai yawo yake ta masa da hankali, kullum da kalar abinda zai faɗa masa, kuma duk tsowon lokaci Yasmin bata taɓa taka asibitin da sunan ta zo ganin Uzair ba, abunda ya bawa kowa mamaki ciki har da Abbah. Ranar wata Lahadi duka ƴan'uwa suka saka ta gaba ana mata faɗa da tambayar dalilin ƙin zuwa ganin mijinta, amman ta kasa furta musu komai sai kuka take, a dole tasa suka ƙyaleta suka saka mata ido.
Ana sauran kwana biyu Abbah ya sake fitar da shi india, Tahir ya zo dubasa daman duk bayan kwana biyu yake zuwa ya gansa.
Yau ya fi bashi tausayi fiye da ko yaushe, ya rame sosai kamar ba abokinsa ba, wai yau Uzair ne kwance a nan baya iya komai, lallai duniya abun tsoro ce. Hawayen da ya gani a idon Uzair ya tashi hankalinsa sosai hakan yasa yau ya yanke shawara faɗa masa gaskiya, da kuma ba shi shawarar abunda yake tunanin zai zame masa mafita.
Ajiyar zuciya Tahir ya sauke yana kallon Uzair ya ce.
“Na yi ta maka wasa da hankali akan maganar Malamin nan, magana ta gaskiya Uzair mutumen baya raye, lokacin da naje gidansa na samu ranar ake sadakan bakwai nasa, na ɓoye maka ne saboda karka tashi hankalinka”
Wasu zafafan hawaye ne suka zubowa Uzair, ya haɗe yawun bakinsa cike da tausayin kansa ya ce.
“Tawa ta ƙare kenan! Haka ƙarshe na zai zo ni kuma? Ina ma ace mutuwa na yi na huta...”
Tahir ya dafa ƙafaɗarsa ya matsa kaɗan.
“ina tunanin abunda ya fi, ka samu Namra da iyayenta ka yi musu bayanin komai, kuma na nemu yafiyarsu, wata ƙila abunda ka aikata ne haƙƙi yake biye da kai, idan kuma har ba haka bane, to Amira ce ta yi maka asiri, idan zaka fallasa komai ka fallasa tare da Amira idan tana gurin, hakan zaisa guiwarta ta yi sanyi ta je ta kare abunda ta yi maka”
“Zan aikata Tahir indai har wannan zai sa na samu lafiyata, amman ya za'ayi Amira ta zo nan? Da wane ido zan kalli Abbah na ce ina son magana da Namra?”
“Zan kawo maka Amira, Namra kuma ka faɗawa Abbah kana son ganinta tare da Abbah”
Ya jinjina kai, shi dai ya shirya yin komai akan lafiyarsa, dan bai jin zai jure zama a irin wannan rayuwar. Bayan Tahir ya fita Mahaifiyarsa ta dawo ɗakin daman yanzu ita ce take jinyarsa ita da wani ƙanensa da kuma ƙanwarsa.
“Umma ina son ganin Abbah da Namra”
Ta kalleshi cike da mamaki.
“Ta maka me? Yarinyar da tun da ka kamu da rashin lafiyarnan bata taɓa cewa tana gaisheka ba balle ta zo duba ka ita zaka nemi gani yanzu?”
“Zan yi wata magana da ita mai muhimmanci, dan Allah ki taimaka min itace kawai mafitar wannan ciwon da nake yi, da ta zo zan samu sauƙi”
“Ban gane ba? Kamar ya itace mafitar ciwonka? Kana magana kamar wanda baya cikin hayyacinsa, Uzairu cuta fa ba mutuwa ba ce”
“Ki taimaka min ki kawo min ita mu yi magana zan faɗa muku komai,ciki har da dalilin daya sa Yasmin ta ƙi ta tako asibitin nan”
Da farko Umma ta ɗauka zafi ciwo ne yasa shi wannan maganar, daga baya kuma sai ta fahimci yana cikin hankalin kansa, sai dai maganganun da yake sun ɗaure mata kai.
Tahir na barin gidan ya nufi gidansu Amira, kamin ya isa sai da ya kira yayanta ya faɗa masa shi baya gida amman Amira tana gida. Harabar gidan ya shiga da motarsa, sannan mai gadin ya shiga ciki yace ana sallama da Amira, bayan ƴan mintuna ya dawo yace wai ance wanene?
“Kace Tahir ne abokin Big Bro”
Sai mai gadin ya koma, ya dawo ya ce wai ance ya shigo ciki. Ba musu ya doshi babbar ƙofar Falon. Da sallama ya shiga Ammy ta amsa masa tare da Amira sannan ya zauna, suka gaisa ya faɗa musu abunda yake tafe da shi. Ba Amira ba har Ammy ta yi mamakin jin Uzair na son ganinta to me zai ce mata? Bayan duk abunda yayi mata, daman tun da suka samu labarin bashi da lafiya Ammy da Abban Amira suke cewa wai amanar Amira ce ta kama shi.
“Yana nemana kamar ya ? Me zai ce mun?”
“Nima ban sani ba, amman yace maganar tana da muhimmanci, sosai”
Ammy ta ce
“To ba zata ita kaɗai ba, tare zamu je, kuma sai Abbah ta ya dawo duk abunda ya ce shi zamu yi”
Tahir ya miƙe tsaye yana faɗin
“Kamin na zo nan sai da na yi magana da Big bro, idan har wani abu ne mai cutar da ke ba zai bari na shigo nan na faɗa miki ba”
“Koma dai minene sai mahaifinta ya dawo”
“To hakan yayi, ni zan wuce”
“A gaida gida”
Ammy ta faɗa sannan ta bishi da kallo har ya fice. Gaɓa ɗaya jikin Amira yayi sanyi, zuciyarta sai yaye-yaye take mata, ta rasa dalilin da zai sa Uzair ya so ganinta, to ko yana zargin tana da hannu a ciwonsa ne? Ko kuma wani abun ne kuma ya faru? Maganar Abbah ce ta dawo da ita daga duniyar tunanin da ta tafi.
“Bari na kira Abbah ki na faɗa masa”
Kai kawai ta iya ɗagawa ta cigaba da tunanin da take.
NAMRA POV.
Bayan an gama bikin Maryam da Hindatu, Abbah ya shiga fafutukar nemawa Namra Admissions a wata makarantar koyarda ilmin computer. Kasancewar duka jami'o'i a yanzu sun gama ɗaukar ɗalibai, gashi kuma bata da komai a yanzu saboda ƙonewar da takardunta suka yi a motarta lokacin da Asim ya taɓa haɗari, ba ƙaramin kuɗi Abbah ya kashe ba wajen fito mata da tsofin takardun da suke makarantar primary da kuma Secondary school. Jami'ah kuma sai next year zata fara, tun da ta riga ta lalata karatunta tun a wacan lokacin.
Sai dai wannan karon kan Alhamdulillah komai ya zo da sauƙi, kasancewar Abbah ya saki ƙuɗi cikin ƙanƙanen lokaci aka yi komai. Aiko murna gurin Anty Amaeya da Namra ba a magana kamar su haɗe Abbah, dan jindaɗi.
Monday mai zuwa Namra zata fara zuwa makaranta, ranar Assabar da Safe Abbah ya kawo mata sabon direba da zai riƙa kai ta makaranta, Namra ta yi murna sosai dan bata tsammaci haka daga gurin Abbah ba.
“Abbah ka yi min abubuwan da ban yi tsammani ba, ka nuna min sosai, Allah ya ba ni ikon saka maka”
Duk suka amsa da Amin har Anty Amarya dake ƙara jin son Abbah har cikin ɓargon ranta. Namra ta ɗauki ɗankwalin abayarta ta yafa ta fita dan ganin sabon direban nata. Tsaye tayi cak a baki ƙofa tana furta
“Lamido”
“Yes Ma'am”
Ya amsa a natse, yayi fari yayi kyau sosai ƙananna kayan da ke jikinsa sun ƙarɓe sa sosai. Ta nunashi da yatsa sai ta kasa magana. Murmushi yayi ya gabatar da kansa.
“My Name is Aliyu Adamu Lamido your new driver”
“How.... How....”
Maganar ta laƙe ta ƙi fitowa sai ta sake nuna shi da yatsa.
“You...”
Murmushi ya sake yi yana kallon yadda ta canja ta yi kyau kamar ba ita ba, baƙin nan nata sai sheƙi yake ga dogon hancin nan da farraren idonta da suka ƙara fitowa.
‘Black beauty akwai kyau’
A zuciyarsa yayi maganar a fili kuma murmushi yake mata mai ɗaukar hankali. Juyawa ta yi ta koma cikin falon, cike da ruɗani ta kalli Abbah ta ce.
“Abbah da gaske shine sabon direba na?”
“Eh ko be miki ba ne?”
“Me direban yayi”
Anty Amarya ta tambaya. Zaunawa Namra ta yi tana faɗin.
“Anty Lamido ne fa”
“Wane Lamido kin san shi ne?”
“A gidansu na sauka Kaduna, shi ya ɗinga ɗawainiya da ni har kuka zo kuka ɗauke ni, Lamido na gidansu Neina fa”
“Au shine? Ya akayi ya zo nan ne?”
“Nima ban sani ba, abun ya ɗaure min kai ne, Abbah ina ka haɗu da shi?”
“A can ƙamfani ya same ni, wai yana son a ɗauke shi direba idan zai samu, kuma baya son na kamfani na gida yake so, kin san daman ni kuma ina neman direban da zai riƙa kai ki scul yana maido ki, shiyasa na ɗauke shi”
Namra ta girgiza kai.
“Abbah why not ka ɗauke shi aiki a kamfanin ka, yayi degree fa, aikin ne be samu ba”
“Ko zan ɗauke shi ba yanzu ba, sai naga gudun ruwansa, idan dai be miki ba za a iya canja miki wani”
“Oh no yayi min, ba matsala Allah ya saka maka da alheri”
“Amin, yanzu sai ki tashi muje Asibiti, Uzair ya ce min yana son ganinki”
“Ni?”
Ta nuna kanta, ba ita kaɗai ba, har Anty Amarya mamaki ta yi.
“Ya za'ayi Uzair ya cw yana son ganin Namra? Kin yi wata magana da shi ne?”
“Anty ya za'ayi na yi magana da shi, tun da na bar garin nan har na dawo wata kalma bata taɓa shiga tsakani na da shi ba”
“Ɗazu dai Mahaifiyarsa ta kira ni tace min dan Allah na zo da ke, Uzair yace zai yi wata magana da ke mai muhimmanci”
“Ni gaskiya ba zani ba”
“Sai fa kin je, indai har zan baki umarni ki bi, bawan Allah nan ban san abunda ya tare miki ba, daga kawai yace yana son ki, kuma na ga yanzu ko lafiyar jikinsa bata ishe shi ba, ya aikamata ki je ki masa sannu”
“Zan je kawai bisa Umarnin ka”
“To tashi ki saka Hijabin ki”
Ba musu ta tashi ta nufi ɗakinta dan ɗauko Hijabin.
“Wai ko na taso muje har da ni ne?”
Anty Amarya ta faɗa tana kallon Abbah, dan taji me zaice, dan tana cike da son sanin dalilin kiran Namra da Uzair yayi bata son a bata labari.
“Tashi muje komai dai son gulmarki sai kin ba su ɗaki sun yi magana”
Abbah ya faɗa da fuskar zolaya. Anty Amarya ta tashi tana dariya ta nufi ɗakinta.
Cikin ƙanƙanen lokaci suka isa asibitin, gaban Namra sai fat fat fat yake, duk da bata san ta yi wani laifi ba, tana jin tsoron kiran da Uzair yake mata. Bama kamar lokacin da suka shiga ɗakin ta yi ido huɗu da Amira, kallon kallon Akuya kallon Kura suka riƙa yi ita da Amira, ko wannen kuma.ya kasa cewa ɗan'uwansa uffan. Daga su har Ammy da Anty Amarya, Ammy sai faman hararar Anty Amarya take da Namra, Abbah ne kawai ya gaisa da Abban Amira, sannan Big Bro ya gaishe shi, ya kuma gaishe da Anty Amarya sai kuma ya kalli Namra fuskarsa da murmushi ya ce.
“Namra ba gaisuwa, kin san ni fa yayanki ne”
“Ina wuni”
Ta gaisheshi ba tare da tayi murmushi ba, ita hankalinta gaba ɗaya ya tattara ya koma kan Uzair yanayin yadda ta ganshi ya bata mamaki, daman hausawa suka ce abunda duk ya baka tsoro wata rana sai ya baka tausayi, gaba ɗaya ya tafi da imaninta, ya rame sosai, ga ledar fitsari an saka masa ta ƙasanshi, saboda rashin tashin da yake. A ɗayan ɓangaren kuma tana mamakin ganin Amira a ɗaki tare da iyayenta da kuma abokinsa Tahir.
“Ka tara mutane a nan kuma baka ce komai ba”
Umma ta faɗa cikin rashin daɗin rai, dan bata so ya kira Amira ba, duk da bata san dalilinsa na kiranta ba.
Ya ɗauki dogon lokaci kamin hawayen da suke masa zuba su tsagaita masa har yaja dogon numfashi ya sauke, sannan ya soma magana.
“Abbah zaka iya tuna wani lokaci a baya da aka ce Namra ta gudu taje gurin Asim? Ni na ɗana mata tarko tare da aminiyarta Amira, na bata sabon number da sunan zata zo ta ga Asim a bayan gidansu su gaisa, alhalin ni ne ba Asim ba, bayan na ɗauke ta sai abokaina suka canja min shawara da sunan kar na mata komai, na maidata a can, abokina ne ya faɗawa mai gadin gidana abunda zai faɗa akan ya tsince ta a bayan gidan ana ƙoƙarin yaga mata mutunci, kuma ana kiran sunan Asim... Kasan dalilin da yasa na yi mata wannan sheri? Saboda ta tona min asiri akan abunda na ke aikatawa, wato na neman maza ƴan'uwana, ba ƙarya ta faɗa ba, ta gan ni da gaske ina aikata wannan abun, amman na ƙaryata ta ne saboda ina ganin kamar asirina zai tonu ne, a lokacin, shine dalilin da yasa na ɓullo da maganar neman aurenta, sai ita kuma ta ƙi yarda, sanadin hakan da kuma gudun karta tona min asiri abokina Najib ya kai ni gurin wani boka muka mata asiri, yace sai an kawo rigarta da ita za ayi wannan asirin, sai na samu Amira na biyata na faɗa mata haka kuma ta yarda ita taje ta aro min rigarta da sunan ita zata saka muka kai akayi mata asiri da wannan rigar, daman can bokan ya faɗa mana duk lokacin da ta saka rigar idan har asirin be kamata ba to zai dawo kan mu ne, saboda Namra tana da ƙarfin addu'ah. Da asirin be kama Namra ba sai ya kama Amira, sanadin hakan ta gudu ta bar gida, ban sake jin ɗuriyarta ba, sai a lokacin da ta aiko min da wasiƙar cewar idan har ban je na kare wannan aikin ba zata iya aikata min komai. A lokacin ne Yasmin ta gani, kuma ta gano abunda ya shiga tsakanina da Adnan, wata rana ne da rana na shigo sai na tarar bata cikin gidan, sai kawai na afkawa ɗa na, daman can nafi son yi namiji, tun daga lokacin na keɓe Adnan ina jiyarsa bata gane ba, sai daga baya, sanadin hakan tace zata kai ni kotu, ni kuma na ƙaryata gaskiyarta, Washe garin ranar ne Hajiya barau ta kira ni ta faɗa min Namra ta dawo, daman ita take labarta min halin da Namra take ciki, da kuma duk wani abu dake gudana a gidan...”
Tun da ya fara maganar be tsaya ba sai da ya kai aya. Idon Abbah sun rine sun yi ja sosai, Abbah Amira ma kansa ya ɗaga sama ya maida hannayensa baya yana jinjina lamarin. Anty Amarya da Ammy kuma suna hawaye, Amira kan kasa kuka ta yi duk ta rikice jikinta sai rawa yake gumi na keto mata ta ko'ina.
“Miye dalilinka na faɗar gaskiya Uzair miyasa ba ka yi shiru da bakin ka ba? Miyasa baka ɓoye sirrinka ba kamar yadda nima na ɓoye nawa? Ban yi niyar faɗawa kowa abunda ka aikata ba Uzair, duk da rayuwar da na shiga ta fi wacce kake ciki a yanzu, dan ni nafi ƙaunar irin ciwon nan naka na san zai sadani da lahira a nan kusa, sama da jiran gawon shanu, jiran abunda babu ranar zuwansa. Ban taɓa tunanin haka ba, na yi tunanin ka haɗa kai da Namra ne ka cutar da ni ashe ni na cutar da kai na! Yanzu na fahimci dalilin da ya sa na gudu na bar gidan mu, kuma bayan na gudu ban faɗa hannun ƙwarai ba, sai na faɗa hannun ɗan fashi, ya mayarda da ni kamar matarsa, ta sanadinsa na ceci wani mutun wanda nake wa jiran gawon shanu, a familynsu na zauna, ina ganin kamar wata sabuwar rayuwa zan shimfiɗa ashe a saman wuta na yi shinfiɗar....”
Amira ta ƙarasa tana durƙushewa a gurin cikin wani irin kuka da yake jin kamar ta haɗiye zuciya ta mutu ta huta. Lokuta da dama ta kan ji hakan idan ta tuna yadda Abdool ya juya mata baya, mutumen da ta fi ƙauna fiye da komai a rayuwarta, a yanzu haka bata da buri sai na shi, shiyasa ta kasa maida jikinta duk da tana tare da iyayenta.
Gaba ɗaya Namra ta ruɗe ta kasa gane komai, daga Uzair ɗin har Amira kallonsu take tana hawaye.
“Yasmin ta kasa samun fili a zuciyarta ta yafe min, saboda na yi mata sara ne a baƙin wuya, amman ke na san zaki iya yafe min, duk da kema na miki illah, amman ki dubi girman Allah ki yafe min ko Allah zai tashi ƙafaɗuna. Idan kuma har wani aikin ne Amira ta yi min dan Allah ki je ki warware shi, saboda na tsorata da kalamin da kika rubuta min cewar zaki ɗauki mataki. Ba zan iya jure zama cikin wannan rayuwar ba, ki taimaka min ki yafe min Namra...”
“Ba zata yafe maka ba, ashe kai ne silar komai, Namra ba zata yafe maka ba...!”
Abbah ya faɗa a tsawace, har sai da Namra ta kalleshi. Ya nufi ƙofa a hasale ya buɗe.
“Mamana wuce mu je”
Abban Amira yayi saurin riƙe Abbah.
“Haba ai babba baya haka, babba
Book Chapters
Chapter 1Chapter 2Chapter 3Chapter 4Chapter 5Chapter 6Chapter 7Chapter 8Chapter 9Chapter 10Chapter 11Chapter 12Chapter 13Chapter 14Chapter 15Chapter 16Chapter 17Chapter 18Chapter 19Chapter 20Chapter 21Chapter 22Chapter 23Chapter 24Chapter 25Chapter 26Chapter 27Chapter 28Chapter 29Chapter 30Chapter 31Chapter 32Chapter 33Chapter 34Chapter 35Chapter 36Chapter 37Chapter 38Chapter 39Chapter 40Chapter 41Chapter 42Chapter 43Chapter 44Chapter 45Chapter 46Chapter 47Chapter 48Chapter 49Chapter 50Chapter 51Chapter 52Chapter 53Chapter 54Chapter 55Chapter 56Chapter 57Chapter 58Chapter 59Chapter 60Chapter 61Chapter 62Chapter 63Chapter 64Chapter 65Chapter 66Chapter 67Chapter 68Chapter 69Chapter 70Chapter 71Chapter 72Chapter 73Chapter 74Chapter 75Chapter 76Chapter 77Chapter 78Chapter 79Chapter 80 Chapter 81Chapter 82Chapter 83Chapter 84Chapter 85Chapter 86Chapter 87Chapter 88Chapter 89Chapter 90Chapter 91Chapter 92Chapter 93Chapter 94