gani ma ai kasan haɗi ne, daɓ ga fatar fuskar ta banbanta dana jikin hoton, kuma miyasa ba a kawo lokacin da bana nan ba, sai da ina nan? za a iya haɗa irin wannan hoton a computer? But i can't believe is taya suka samu hoton ki?”
“Wallahi ban sani ba”
“Baki sani ba kamar ya? What kind of nonsense is this? Aljani za a turo ya ɗauki hoton ki ko me?”
Durƙushewa tayi ƙasa tana kuka.
“Wallahi ban sani ba Hilal na rantse da Allah ban aikata ba”
“Naji baki aikata ba, faɗa min ta ina suka aka samu hoton ki?”
Ya faɗa a tsawace irin zuciyarsa ta fara kawowa ɗin nan.
“Wallahi ban sani ba, ni ban turawa kowa hotona ba”
Ɗuƙawa yayi a hasale ya kwashe hotunan ya nufi ɗakinsa da su. Wani irin zugi zuciyarsa ke masa, baƙin kishi ya taso masa.
Haka ya tiƙa duba hotunan kamar wanda zai haddace su, shi dai what he believe Kalsoom ba zata aikata haka ba, sai dai kuma kansa ya ɗaure har yana jin tunaninsa na ƙoƙarin canjawa.
Bedside drawer sa ya buɗe ya zuba hotunan ya rufe, sannan Shirya cikin ƙananan kaya ya feshe jikinsa da turare ya ɗauki atms ɗinsa ya saka a aljihu da wasu ƴan canja, sannan ya ɗauki wayarsa da keys, ya fice daga ɗakin fuska babu annuri.
Sheshekar kukanta ya ɗago da hankalinsa i zuwa gareta, ashe duk tsawon lokacin tana a gurin tana aikin kuka, jikinsa ya mutu yaji ba daɗi ganin kamar shine silar hawayenta. Ƙarasawa yayi kusa da ita ya ɗafa ta
“Kalsoom Calm down, nima fa wayayyen mutum ne nasan za a iya haɗa wannan, amman kin ƙi ki bawa zuciyata damar yarda da hakan”
Ɗagowa tayi ta kalleshi tana kuka fuskarta da majina nashe-nashe.
“Wallahi ban sani ba, ni ban turawa kowa hoto na ba”
“Kina da grp ɗin da kika chat da maza ko?”
Ta ɗanyi shiru tana tunani.
“Grp ɗaya ne, shima kuma na koyon sana'ah ne, kuma ban taɓa magana a grp ɗin ba Wallahi, Instagram ɗina da Facebook tun da nayi aure ban sake hawan ko ɗaya ba Wallahi”
“Good indeed, kina instagram ba? Kina facebook?”
“Amman tun da nayi aure ban sake shiga ba”
Zaunawa yayi kusa da ita yana cire password ɗin wayarsa.
“Ba ni handle ɗin ki”
“Kalsoom_Miss-Arewa”
Instagram ya shiga yayi searching sunanta, sai ga account ɗinta. Yadda ya riƙa ganin hotunan ta sai wani baƙin kishi ya motsa masa.
“Duba nan, yanzu miye amfanin waɗannan hotunan? Kina tallar kan ki kamar ba mace ba, miye abun burgewa a sakin jiki wasu mazan na kallo, ke a ɗaukar ki duk wayewa ce ko? Dole ne sai kin sa hotunan ki a instagram ko facebook?”
“Wallahi ni ba da wata manufar na yi ba”
“Nasan ba wata manufar kika yi ba, su yanzu waɗanda suke da wata manufar ai sun ɗauka sun yi yadda suke so da shi. Duk abunda addini yake hana ƙu baku ganewa, duk abunda kika ga musulunci yace a bar shi barin shi yafi alheri amman baku ganewa, dubi wannan abun wani gurin ma ai rabin jikin ki a waje, ba editing kaɗai ba har asiri sai a ɗauki hoton ki ta nan aje a miki”
Yaja tsaki yana mai miƙewa tsaye.
“Kamin na dawo ki tabbatar kin goge duka hotunan ki da suke facebook da Instagram, ban hana ki yin chat ba amman ban yafe ki yi da wani namiji ba da aurena, duk mazan nan nan friends ɗin ki yi unfriend ɗin su, kuma Wallahi kar na sake ganin hoton ki a social network”
“Wallahi ni daga yau ma na daina chat ɗin gaba ɗaya, amman ka yarda da ni dan Allah”
“Idan ban yarda da ke ba, zan zauna ina magana da ke haka? Very soon an gano wanda yayi wannan abun, akwai mai son shiga tsakanin mu ne”
Gabansa ta dawo ta risina ta riƙe ƙafafunsa.
“Na gode Allah ya saka mana”
Ɗagota yayi ya rumgume. Zuciyarsa cike da kishin hotunan can daya kalla, duk da yasan cewar ba haɗi ne amman yana kishin hakan.
*🌺🌺🌺 ZAGON ƘASA 🌺🌺🌺*
Website
www.khadeejacandy.com.ng
*PAGE - 30*
NOT EDITED ⚠️
Ƴan ƙuɗin da suka mata saura a jakarta, da kuma dubu ashirin ɗin nan Hajiyar gidan ta bata, su ne take ta maneji ta su tana siyen abinci.
A kullum gidan su Mardiya take kwana, wani lokacin har zanenta take ɗaurawa, kamin ta ɗinka kala biyar a cikin kuɗin. Tayi ta zuba ido tana jiran kuɗin Anty Amarya har ta gaji, tun tana sa ran zata ta kira wayar har ta gaji da jiran ta fara tunanin wata mafitar.
Da ta fito daga gida kai tsaye ta nufi gidansu Hajiya Saratu, har ta isa zuciyarta na nuna mata illar abunda zata yi, ko ba komai zai nisanta ta da Ubangijinta, sannan duk wanda yasan abunda ta aikata mutuncinta zai zube a idonsa, ashe Allah zai jarrabeta da wani matsi har kuma ta nemi tsaɓa masa, idan har ta yi haka bata kasance cikin nagartaccin bayi ba.
Juyar da fuskarta tayi gefen ti-ti tana kallon motocin dake kai da kawo, hawaye na silalawo daga idonta, wani bangare na zuciyar yana ƙoƙarin rinjayarta akan idan har ba ita ba, bata da wata mafita, babu kuma wanda zai taimake ta sai ita. Haka ko wane bawa zuciyarsa take nasalta masa alheri da sheri duk ɓangaren daya rinjaye ka shi zaka aikata.
Hannu ta kai ta share hawayenta, tana mai jin ƙyamar abun a ranta, yanzu idan taje garin aikata ta mutu fa? Me zata cewa Allah? Haƙiƙa an jarrabi wasu gabaninta da suka yi haƙuri kuma sai Allah yayi musu mafita, kuma bayan ita za a jarrabi wasu a bayanta, haka Ubangiji yake jarraba bayinsa dan ya auna imaninsu da kuma yarda da ƙaddara.
“Haƙiƙa za mu jarrabe ku da wani abu na tsoro da yunwa da tawayar dukiyoyi da rayuka, da ƴaƴan itatuwa , ka yi albishir ga masu haƙuri (Wajen jure waɗannan jarabce-jarabcen) Waɗanda idan masifa ta same su sai su ce INNALILLAHI WA'INNA ILAIHI RAJI'UN ma'ana :- mu ga Allah muka fito kuma a gare shi za a maiyardar mu. Wanɗannan gafara da kyakkayawan yabo daga Ubangijinsu sun tabbata gare su, da rahama kuma waɗannan sune shiryayyu.” (Baƙara: 155-157)
Tuna waɗannan ayoyin ya ankarar da ita abubuwan data manta, ji tayi kamar an tsikareta, gashin jikinta ya tashi, a nan ta soma tambayar kanta, dan me zata yarda zuciyarta ta rinjayeta ta tsaɓi Ubangijinta? Ta fita daga waɗancan bayin da Allah ke yabo? Ashe Ubangijinta be mata dukan gata ba? Ashe daman Imaninta ƙanƙane ne?
Ta furta a fili, har sai da mai Napep ɗin ya kalleta.
“Hajiya lafiya dai?”
“Lafiya ƙalau dan Allah juya da ni ka kai ni babbar Asibiti”
“To amman fa wasu kuɗin zaki sake biya”
“Na ji mu tafi”
“Tau Hajiya lafiya kike kuka?”
Sai a lokacin ta tuna da hawayen dake fuskarta, sa sauri ta share hawayen ba tare data ce masa komai ba har suka isa asibitin, sannan ta fita ta ciro kuɗinsa ta ba shi.
Ko da ta shiga cikin ɗakin Asim na zaune, kamsa ya kumbura sosai har idonsa ɗaya ya liƙe, hankalinta ya tashi dan yanzu wannan kumburin ya fi na jiya.
Kusa da shi ta zauna zuciyarta cike da tausayinsa, har idaniyarta na ƙoƙarin zubar masa da ƙwalla.
“Asim kaga har yanzu Anty bata kira ba, kuma bata aiko ba, ni kuma bana da wata mafitar, ga kuɗi da ake bina ma ban san yadda zan yi ba, wannan kumburin naka yana tsorata ni”
Ya matse ƙallah data cika masa ido.
“Namra ko gida za mu koma ne?”
“Idan mun koma za su ce mun kwaso ciwo mun dawo”
“Likita yace idan ba allura nan aka min ba yana da wahala naji sauƙi da wuri”
Hannayenta tasa ta rumgume shi tana kuka. Shi kuma a take yaji sha'awarta ta saukar masa, ya kai hannu yana ɗan shafa ta. Data anƙaro da abunda yake nufi da ita sai tayi saurin ɗagowa daga jikinsa.
“Ina Mama?”
“Tana waje”
Ya sake miƙa hannu yana shafa fuskarta, yana ƙoƙarin ɗaga hijabinta ya zura ɗayan hannunsa ciki.
“Asim asibiti muke fa, kuma dubi halin da kake ciki”
Yawun bakinsa ya haɗe, ba tare daya daina abunda yake mata ba. Ana taɓa ƙofar ɗakin tayi saurin tashi tsaye, shi kuma ya bita da kallo idonsa har sun fara canja kala.
“Mama ina wuni?”
“Lafiya ƙalau ya rana?”
“Alhamdulillah”
Ta ɗan kalleshi cike da kunya, dan gani take kamar Mama ta lura da abunda suke.
“Bari naje gurin Hajara”
Bata jira abunda zai ce ba ta fice. Sai Mama ta zauna a kujerar dake kusa da Asim tana faɗin
“Lamarin nan naka fa ƙaruwa kawai yake yi”
“Tau Mama nayi maganar kuɗin adashen nan kin kawo wasu hujjoji na daban, ko mutuwa na yi ai ke kika rasa ni tun da su ƴar su wani zata aura”
“Shawara da nake kenan a zuciyana, zan je nayi mata bayani sai na karɓo kuɗin daman dubu ɗari uku ne, idan Allah yasa ka samu sauƙi sai a shiga wani kuma”
“Haka yafi, tun da kin ga har yanzu basu saje kira ba ma balle su aiko. Yaushe zaki je?”
“Gobe nake son naje, nima kuɗin da suke hannun na duk sun tafi gurin siyen abinci, ga tufafin nan ƙala ɗaya kullum ƙara naje ya ɗauko wasu tun da waɗanda muka zo da su sun ƙone, da Hajara zan koma in yaso sai na dawo ni kaɗai, daman Haruna ya matsa da maganar yaushe zata dawo”
“Ni Wallahi inda da hali ma da kin tafi yanzu, sai ki dawo gobe da wuri, dan ni kaɗai na san halin da nake ciki, kuma kin ga yanzu aka yi ƙarfe ɗaya, nasan zuwa yamma kin isa”
Ta ɗan yi shiru tana nazari.
“Rana be yi ba?”
“Be yi ba Wallahi, tun da kin ga ma Namra ta zo sai ta zauna nan har ki dawo”
“Tau bari na gani, ai duk na natse ma da wannan kumburin na ka”
Ta tashi ta fita cikin yanayin damuwa. Wayar Asim dake hannun Hajara Namra ta karɓa, ta saka number Babban Yayansu ɗan Hajiya Barau, sai ta matsa can nesa da Hajara ta kira shi.
KALSOOM POV.
Ba itace da girkin ba, amman sanin halin Rashida yasa bata tsaya jiranta ba ta shiga kitchen ta ɗora musu breakfast, daman wani lokacin ita take shirya musu tun da Rashida aiki take zuwa.
Sai da ta shirya komai, na karyawa sannan ta ɗauko kulolin su ta zuba musu abincin su, sannan ta kira su ɗaya bayan ɗaya ta miƙa musu kulolin.
“Ku je gurin mota zan tashi Daddyn ku yanzu”
Ta nufi ɗakinsa, tana buɗe maɓallan rigar bachin ta. A tsakiyar gado yake kwance yana lulluɓe irin yana jin tsayi ɗin nan.
Air conditioner ta fara kashewa sannan ta nufi window ta buɗe su duka ta ɗage labulayen sannan ta nufo inda yake kwance ta yaye bedsheet ɗin tana taɓa masa kunne.
“Likita tashi safiya yayi fa”
Hannu ya kai ya janyo ta saman gadon ya rumgume ta
“Ban gaji da bachi ba”
“Yara suna gurin mota suna jiran ka”
“Ya salam”
Ya ƙara rumgume ta tsamtsam ƙirjinsa, kamar ba zai tashi ba, sai faman lumshe ido yake alamar bachi na masa daɗi.
“Doc. Doc. Doc”
Shiru be motsa bama balle ya amsa ta, hannu ta kai ta murɗa masa kunne, har sai da tayi ƙara ya kama hannunta ya ciza sannan ya tashi, yana jan kitson ta.
“I hate dis Morning”
“Really”
Ta tsire baki tana koyonsa.
“I hate dis Morning”
Ya zare ido, lokacin da idonsa suka kai kan ƙirjinta.
“Wow”
Ya kai hannu zai taɓa ta, ta fisgi kanta cikin zafin nama, ta sauka saman gado ta fice daga ɗakin tana masa dariya.
Tashi yayi ya shiga bathroom ya wanke bakinsa da fuskarsa sannan ya fito ya kai yaran makaranta. Ko da ya dawo babu kowa falo, sai kawai ya nufi ɗakin Rashida dan yaga motarta waje alamar yau bata fita da wuri ba kenan.
Tana ganin ya shigo ta juya kwancinta ta bashi baya. Hakan be da me shi sai ma dariya da yayi ya ƙarasa kusa da ita ya juyo da ita, hawayen daya gani a idonta ya tashi hankalinsa.
“Lafiya Pyar?”
“Bana jindaɗi ne”
“Me ke damun ki”
“Nima ban sani ba”
“Amman miyasa baki faɗa min ba?”
“Taya zan faɗa maka bayan ta shiga haƙƙina taje ta tashe ka, kuma ta san yau ba girkin ta bane”
“Ta riga ta saba ne, saboda kina fita sa sassafe ba tare da kin damu da tashi na ba, balle haɗa mana abun karyawa”
“Ni gaskiya ta daina shiga min haƙƙi bana so”
“Shikenan zan mata magana, amman yanzu faɗa min me kike ji yana damun ki”
“Fever, sneeze, headache and nauseous”
“Zan diɓi jininki da fitsari idan zan fita, yanzu tashi mu karya sai ki sha magana”
Ta ƙara manne masa a jiki.
“A'a ni bana so cin komai”
“Tea fa?”
“Sai dai idan kai zaka haɗa min da kan ka”
“Yes ni zan haɗa miki ai”
Ya faɗa yana murmushi, sannan ya tashi ya fice. Ajiyar zuciya Rashida ta sauke, ranta yana mata ba daɗi, idan har zarginta ya tabbata gasjiyar tana da ciki, tana cikin matsala dan bata iya tantance na waye ne,
‘Taya wani zai gane idan ba ni ma faɗa ba?’
Tambayar da tazo mata kenan a zuciyarta, sai kawai ta tashi ta shiga banɗaki.
Hilal sai da ya shiga ɗakinsa ya ɗauko maganinka sannan ya nufo ɗakin Kalsoom, a lokacin tana zaune gaban madubi tana shiryawa dan fitowarta daga wanka kenan.
Daga bakin ƙofa ya tsaya yana kallonta yace
“Wifey Yau madam babu lafiya, ba zata fito ba tea kawai zata sha, ni ma kuma bana jin cin komai”
Kai ta ɗaga masa tayi murmushin da be kai zuci ba. Har ya wuce, sai kuma ya dawo ya tsaya bakin ƙofar ya miƙa mata hannu.
“Taso na haɗa miki breakfast”
Ba musu ta taso ta miƙa masa hannun ba dan ranta na mata daɗi ba. A kujerar data saba zama ya zaunar da ita, ya ɗauki kofi biyu ya haɗa tea, ya aje mata ɗaya gabanta ya zuba mata ƙwai da sauran abubuwan da suke gurin, sannan yaƴi mata kiss ya ɗauki tea ɗin ya nufi ɗakin Rashida.
Da kallo ta bishi, zuciyarta na sosuwa da lamarinsa, tabbas yana son matarsa fiye da yadda yake son kansa, yanzu ya kasa karyawa saboda bata da lafiya, ta lura da yadda yanayinsa ya canja a take, taya zata shiga rayuwar irin waɗannan ma'auratan sannan tace zata samu farinciki?
Hannu ta kai ta shafa cikinta, hawaye masu zafi suka silalo daga idonta.
Sai da ya bata tea ɗin tasha sannan ya bata magani, sai ya sake fita yaje ya ɗauko wasu robobi guda biyu ya miƙa mata babbar.
“Kiyi fitsari a wannan”
Hannunsa sanye da safa, ya ɗibi jininta ya zuba a ƙaramin robar sannan ya manna mata kaɗa ya lunda mata, ya kwance robar daya ɗaure mata hannun da shi, kwashe kayan yayi ya fice. Bayan kamar thirty minutes ya dawo ɗakin da shirinsa na zuwa office.
Robar fitsarin ya ta bashi, ya karɓa yayi mata kiss, sannan ya fice. Ɗakin Kalsoom ya shiga, tana jin motsinta ta lafe kamar tana bachi, itama kiss ɗin yayi mata sannan ya fice.
Rashida na jin tashin motarsa ta janyo wayarta ta danna number Asmee, ringing huɗu tayi sannan ta ɗauka.
“Asmee an tashi lafiya?”
“Lafiya ƙalau ya gidan?”
Ya amsa mata muryarta da alamar damuwa.
“Asmee yau ba zan samu fita ba, bana jindaɗi, sai dai kr kije idan da hali”
“Me ke damun ki?”
“Abubuwa da yawa ga jikin duk ya min nauyi”
“Ko dai ciki ne?”
“Haka nake tunani nima”
“Allah ya raba lafiya”
Jin ta faɗa ba da wani jindaɗi ba yasa Rashida Tambaya.
“Ya naji muryar ki ba daɗi?”
“Ba komai, nima bana jindaɗin ne, amman zan daure a haka naje”
“Yauwa na gode sosai, kin ce dai yana aiki sosai ko?”
“Sosai Wallahi kamar yan kan wuƙa, duk yadda mu kayi zan faɗa miki”
“Okay na gode”
Rashida na kashe wayar Asmee ta fashe da kuka.
‘Allah kasa ba gaske bane Allah, idan har da gaske ne ya ci amanata, tun da yasan yana da shi kuma ya nemi ya kwana da ni, Wallahi dana sani ni dama ban je gunsa neman magani ba, mugun Malami kawai’
Abunda take ta tunani a zuciyarta kenan, a fili kam kuka kawai take, kamar ta cire idonta.
_________________________________________
Kuyi Haƙuri da wannan idan Allah ya bani iko zan kara muku wani anjima.
BEST REGARDS 💖🌺
KHADEEJA CANDY 😘
*🌺🌺🌺 ZAGON ƘASA 🌺🌺🌺*
Website
www.khadeejacandy.com.ng
Godiya marar iyaka gareki Daughter, na gode na gode I really did not expect this awesome surprise from your side
Allah ya kara arziki 😘
*PAGE - 31*
NOT EDITED ⚠️
Ƴan seconds ya rage wayar ta fara ringing sai kawai ta kashe, tana tunanin yadda za fallasawa kanta asiri idan har ta yarda ta faɗa masa danuwarta, ba duka ɗan'uwane yake taimako dan Allah ba, ballanta shi data san dole ne ya faɗawa Hajiya Barau, ita kuma fitar da maganar zata yi, sai a fara cewa tana roƙon dangi.
Juyowa tayi ta nufo gurin da Hajara take zaune, ita ma ta zauna tana miƙa mata wayar.
“Har kin kira?”
“A'a ban kira ba na fasa ne”
Ta faɗa tana murmushi, isowar Mama yasa ta sadda kanta ƙasa tana watsa da yatsun hannunta.
“Wai gida za mu koma yanzu”
Daga Hajara har Namra kallonta suka yi
“Gida kuma? Ina ba dai sokoto ba ko?”
Namra ta tambaya cike da mamaki.
“Can fa, wai so nake muje yanzu kamin yamma mun isa sai da gobe kuma mu juyo”
“Amman zuwa lafiya ne?”
Mama ta ɗan yi shiru kamar mai tunanin abunda zata ce mata.
“A'a wai kuɗi zan je na ranto idan har Allah yasa an samu sai a siye maganin da likita ya rubuta ta, tun da naga alamun sauƙi a jikinsa amman kumburin nan na kansa yana bani tsoro. Kuma ina son naje na ɗauko wasu tufafin gashi mai son Hajara shi ma ya damu yaushe za mu dawo”
Namra ta sauke ajiyar zuciya cike da tausayawa, ji take kamar ace tana da mafitar su ta ɗauka ta bada, ba sai taje neman rance ba.
“Amman Mama da zaki yi haƙuri har gobe, saboda yanzu rana yayi sosai, kuma zaku iya zuwa ku tarar da jira a tasha, ƙara ki haƙura har da safe sai ki tafi, amman tafiyar dare ba kyau,
Showing 63001 words to 66000 words out of 280121 words
“Wallahi ban sani ba”
“Baki sani ba kamar ya? What kind of nonsense is this? Aljani za a turo ya ɗauki hoton ki ko me?”
Durƙushewa tayi ƙasa tana kuka.
“Wallahi ban sani ba Hilal na rantse da Allah ban aikata ba”
“Naji baki aikata ba, faɗa min ta ina suka aka samu hoton ki?”
Ya faɗa a tsawace irin zuciyarsa ta fara kawowa ɗin nan.
“Wallahi ban sani ba, ni ban turawa kowa hotona ba”
Ɗuƙawa yayi a hasale ya kwashe hotunan ya nufi ɗakinsa da su. Wani irin zugi zuciyarsa ke masa, baƙin kishi ya taso masa.
Haka ya tiƙa duba hotunan kamar wanda zai haddace su, shi dai what he believe Kalsoom ba zata aikata haka ba, sai dai kuma kansa ya ɗaure har yana jin tunaninsa na ƙoƙarin canjawa.
Bedside drawer sa ya buɗe ya zuba hotunan ya rufe, sannan Shirya cikin ƙananan kaya ya feshe jikinsa da turare ya ɗauki atms ɗinsa ya saka a aljihu da wasu ƴan canja, sannan ya ɗauki wayarsa da keys, ya fice daga ɗakin fuska babu annuri.
Sheshekar kukanta ya ɗago da hankalinsa i zuwa gareta, ashe duk tsawon lokacin tana a gurin tana aikin kuka, jikinsa ya mutu yaji ba daɗi ganin kamar shine silar hawayenta. Ƙarasawa yayi kusa da ita ya ɗafa ta
“Kalsoom Calm down, nima fa wayayyen mutum ne nasan za a iya haɗa wannan, amman kin ƙi ki bawa zuciyata damar yarda da hakan”
Ɗagowa tayi ta kalleshi tana kuka fuskarta da majina nashe-nashe.
“Wallahi ban sani ba, ni ban turawa kowa hoto na ba”
“Kina da grp ɗin da kika chat da maza ko?”
Ta ɗanyi shiru tana tunani.
“Grp ɗaya ne, shima kuma na koyon sana'ah ne, kuma ban taɓa magana a grp ɗin ba Wallahi, Instagram ɗina da Facebook tun da nayi aure ban sake hawan ko ɗaya ba Wallahi”
“Good indeed, kina instagram ba? Kina facebook?”
“Amman tun da nayi aure ban sake shiga ba”
Zaunawa yayi kusa da ita yana cire password ɗin wayarsa.
“Ba ni handle ɗin ki”
“Kalsoom_Miss-Arewa”
Instagram ya shiga yayi searching sunanta, sai ga account ɗinta. Yadda ya riƙa ganin hotunan ta sai wani baƙin kishi ya motsa masa.
“Duba nan, yanzu miye amfanin waɗannan hotunan? Kina tallar kan ki kamar ba mace ba, miye abun burgewa a sakin jiki wasu mazan na kallo, ke a ɗaukar ki duk wayewa ce ko? Dole ne sai kin sa hotunan ki a instagram ko facebook?”
“Wallahi ni ba da wata manufar na yi ba”
“Nasan ba wata manufar kika yi ba, su yanzu waɗanda suke da wata manufar ai sun ɗauka sun yi yadda suke so da shi. Duk abunda addini yake hana ƙu baku ganewa, duk abunda kika ga musulunci yace a bar shi barin shi yafi alheri amman baku ganewa, dubi wannan abun wani gurin ma ai rabin jikin ki a waje, ba editing kaɗai ba har asiri sai a ɗauki hoton ki ta nan aje a miki”
Yaja tsaki yana mai miƙewa tsaye.
“Kamin na dawo ki tabbatar kin goge duka hotunan ki da suke facebook da Instagram, ban hana ki yin chat ba amman ban yafe ki yi da wani namiji ba da aurena, duk mazan nan nan friends ɗin ki yi unfriend ɗin su, kuma Wallahi kar na sake ganin hoton ki a social network”
“Wallahi ni daga yau ma na daina chat ɗin gaba ɗaya, amman ka yarda da ni dan Allah”
“Idan ban yarda da ke ba, zan zauna ina magana da ke haka? Very soon an gano wanda yayi wannan abun, akwai mai son shiga tsakanin mu ne”
Gabansa ta dawo ta risina ta riƙe ƙafafunsa.
“Na gode Allah ya saka mana”
Ɗagota yayi ya rumgume. Zuciyarsa cike da kishin hotunan can daya kalla, duk da yasan cewar ba haɗi ne amman yana kishin hakan.
*🌺🌺🌺 ZAGON ƘASA 🌺🌺🌺*
Website
www.khadeejacandy.com.ng
*PAGE - 30*
NOT EDITED ⚠️
Ƴan ƙuɗin da suka mata saura a jakarta, da kuma dubu ashirin ɗin nan Hajiyar gidan ta bata, su ne take ta maneji ta su tana siyen abinci.
A kullum gidan su Mardiya take kwana, wani lokacin har zanenta take ɗaurawa, kamin ta ɗinka kala biyar a cikin kuɗin. Tayi ta zuba ido tana jiran kuɗin Anty Amarya har ta gaji, tun tana sa ran zata ta kira wayar har ta gaji da jiran ta fara tunanin wata mafitar.
Da ta fito daga gida kai tsaye ta nufi gidansu Hajiya Saratu, har ta isa zuciyarta na nuna mata illar abunda zata yi, ko ba komai zai nisanta ta da Ubangijinta, sannan duk wanda yasan abunda ta aikata mutuncinta zai zube a idonsa, ashe Allah zai jarrabeta da wani matsi har kuma ta nemi tsaɓa masa, idan har ta yi haka bata kasance cikin nagartaccin bayi ba.
Juyar da fuskarta tayi gefen ti-ti tana kallon motocin dake kai da kawo, hawaye na silalawo daga idonta, wani bangare na zuciyar yana ƙoƙarin rinjayarta akan idan har ba ita ba, bata da wata mafita, babu kuma wanda zai taimake ta sai ita. Haka ko wane bawa zuciyarsa take nasalta masa alheri da sheri duk ɓangaren daya rinjaye ka shi zaka aikata.
Hannu ta kai ta share hawayenta, tana mai jin ƙyamar abun a ranta, yanzu idan taje garin aikata ta mutu fa? Me zata cewa Allah? Haƙiƙa an jarrabi wasu gabaninta da suka yi haƙuri kuma sai Allah yayi musu mafita, kuma bayan ita za a jarrabi wasu a bayanta, haka Ubangiji yake jarraba bayinsa dan ya auna imaninsu da kuma yarda da ƙaddara.
“Haƙiƙa za mu jarrabe ku da wani abu na tsoro da yunwa da tawayar dukiyoyi da rayuka, da ƴaƴan itatuwa , ka yi albishir ga masu haƙuri (Wajen jure waɗannan jarabce-jarabcen) Waɗanda idan masifa ta same su sai su ce INNALILLAHI WA'INNA ILAIHI RAJI'UN ma'ana :- mu ga Allah muka fito kuma a gare shi za a maiyardar mu. Wanɗannan gafara da kyakkayawan yabo daga Ubangijinsu sun tabbata gare su, da rahama kuma waɗannan sune shiryayyu.” (Baƙara: 155-157)
Tuna waɗannan ayoyin ya ankarar da ita abubuwan data manta, ji tayi kamar an tsikareta, gashin jikinta ya tashi, a nan ta soma tambayar kanta, dan me zata yarda zuciyarta ta rinjayeta ta tsaɓi Ubangijinta? Ta fita daga waɗancan bayin da Allah ke yabo? Ashe Ubangijinta be mata dukan gata ba? Ashe daman Imaninta ƙanƙane ne?
“Innalillahi wa'inna ilaihi raji'un
Innalillahi wa'inna ilaihi raji'un
Innalillahi wa'inna ilaihi raji'un”
Ta furta a fili, har sai da mai Napep ɗin ya kalleta.
“Hajiya lafiya dai?”
“Lafiya ƙalau dan Allah juya da ni ka kai ni babbar Asibiti”
“To amman fa wasu kuɗin zaki sake biya”
“Na ji mu tafi”
“Tau Hajiya lafiya kike kuka?”
Sai a lokacin ta tuna da hawayen dake fuskarta, sa sauri ta share hawayen ba tare data ce masa komai ba har suka isa asibitin, sannan ta fita ta ciro kuɗinsa ta ba shi.
Ko da ta shiga cikin ɗakin Asim na zaune, kamsa ya kumbura sosai har idonsa ɗaya ya liƙe, hankalinta ya tashi dan yanzu wannan kumburin ya fi na jiya.
Kusa da shi ta zauna zuciyarta cike da tausayinsa, har idaniyarta na ƙoƙarin zubar masa da ƙwalla.
“Asim kaga har yanzu Anty bata kira ba, kuma bata aiko ba, ni kuma bana da wata mafitar, ga kuɗi da ake bina ma ban san yadda zan yi ba, wannan kumburin naka yana tsorata ni”
Ya matse ƙallah data cika masa ido.
“Namra ko gida za mu koma ne?”
“Idan mun koma za su ce mun kwaso ciwo mun dawo”
“Likita yace idan ba allura nan aka min ba yana da wahala naji sauƙi da wuri”
Hannayenta tasa ta rumgume shi tana kuka. Shi kuma a take yaji sha'awarta ta saukar masa, ya kai hannu yana ɗan shafa ta. Data anƙaro da abunda yake nufi da ita sai tayi saurin ɗagowa daga jikinsa.
“Ina Mama?”
“Tana waje”
Ya sake miƙa hannu yana shafa fuskarta, yana ƙoƙarin ɗaga hijabinta ya zura ɗayan hannunsa ciki.
“Asim asibiti muke fa, kuma dubi halin da kake ciki”
Yawun bakinsa ya haɗe, ba tare daya daina abunda yake mata ba. Ana taɓa ƙofar ɗakin tayi saurin tashi tsaye, shi kuma ya bita da kallo idonsa har sun fara canja kala.
“Mama ina wuni?”
“Lafiya ƙalau ya rana?”
“Alhamdulillah”
Ta ɗan kalleshi cike da kunya, dan gani take kamar Mama ta lura da abunda suke.
“Bari naje gurin Hajara”
Bata jira abunda zai ce ba ta fice. Sai Mama ta zauna a kujerar dake kusa da Asim tana faɗin
“Lamarin nan naka fa ƙaruwa kawai yake yi”
“Tau Mama nayi maganar kuɗin adashen nan kin kawo wasu hujjoji na daban, ko mutuwa na yi ai ke kika rasa ni tun da su ƴar su wani zata aura”
“Shawara da nake kenan a zuciyana, zan je nayi mata bayani sai na karɓo kuɗin daman dubu ɗari uku ne, idan Allah yasa ka samu sauƙi sai a shiga wani kuma”
“Haka yafi, tun da kin ga har yanzu basu saje kira ba ma balle su aiko. Yaushe zaki je?”
“Gobe nake son naje, nima kuɗin da suke hannun na duk sun tafi gurin siyen abinci, ga tufafin nan ƙala ɗaya kullum ƙara naje ya ɗauko wasu tun da waɗanda muka zo da su sun ƙone, da Hajara zan koma in yaso sai na dawo ni kaɗai, daman Haruna ya matsa da maganar yaushe zata dawo”
“Ni Wallahi inda da hali ma da kin tafi yanzu, sai ki dawo gobe da wuri, dan ni kaɗai na san halin da nake ciki, kuma kin ga yanzu aka yi ƙarfe ɗaya, nasan zuwa yamma kin isa”
Ta ɗan yi shiru tana nazari.
“Rana be yi ba?”
“Be yi ba Wallahi, tun da kin ga ma Namra ta zo sai ta zauna nan har ki dawo”
“Tau bari na gani, ai duk na natse ma da wannan kumburin na ka”
Ta tashi ta fita cikin yanayin damuwa. Wayar Asim dake hannun Hajara Namra ta karɓa, ta saka number Babban Yayansu ɗan Hajiya Barau, sai ta matsa can nesa da Hajara ta kira shi.
KALSOOM POV.
Ba itace da girkin ba, amman sanin halin Rashida yasa bata tsaya jiranta ba ta shiga kitchen ta ɗora musu breakfast, daman wani lokacin ita take shirya musu tun da Rashida aiki take zuwa.
Sai da ta shirya komai, na karyawa sannan ta ɗauko kulolin su ta zuba musu abincin su, sannan ta kira su ɗaya bayan ɗaya ta miƙa musu kulolin.
“Ku je gurin mota zan tashi Daddyn ku yanzu”
Ta nufi ɗakinsa, tana buɗe maɓallan rigar bachin ta. A tsakiyar gado yake kwance yana lulluɓe irin yana jin tsayi ɗin nan.
Air conditioner ta fara kashewa sannan ta nufi window ta buɗe su duka ta ɗage labulayen sannan ta nufo inda yake kwance ta yaye bedsheet ɗin tana taɓa masa kunne.
“Likita tashi safiya yayi fa”
Hannu ya kai ya janyo ta saman gadon ya rumgume ta
“Ban gaji da bachi ba”
“Yara suna gurin mota suna jiran ka”
“Ya salam”
Ya ƙara rumgume ta tsamtsam ƙirjinsa, kamar ba zai tashi ba, sai faman lumshe ido yake alamar bachi na masa daɗi.
“Doc. Doc. Doc”
Shiru be motsa bama balle ya amsa ta, hannu ta kai ta murɗa masa kunne, har sai da tayi ƙara ya kama hannunta ya ciza sannan ya tashi, yana jan kitson ta.
“I hate dis Morning”
“Really”
Ta tsire baki tana koyonsa.
“I hate dis Morning”
Ya zare ido, lokacin da idonsa suka kai kan ƙirjinta.
“Wow”
Ya kai hannu zai taɓa ta, ta fisgi kanta cikin zafin nama, ta sauka saman gado ta fice daga ɗakin tana masa dariya.
Tashi yayi ya shiga bathroom ya wanke bakinsa da fuskarsa sannan ya fito ya kai yaran makaranta. Ko da ya dawo babu kowa falo, sai kawai ya nufi ɗakin Rashida dan yaga motarta waje alamar yau bata fita da wuri ba kenan.
Tana ganin ya shigo ta juya kwancinta ta bashi baya. Hakan be da me shi sai ma dariya da yayi ya ƙarasa kusa da ita ya juyo da ita, hawayen daya gani a idonta ya tashi hankalinsa.
“Lafiya Pyar?”
“Bana jindaɗi ne”
“Me ke damun ki”
“Nima ban sani ba”
“Amman miyasa baki faɗa min ba?”
“Taya zan faɗa maka bayan ta shiga haƙƙina taje ta tashe ka, kuma ta san yau ba girkin ta bane”
“Ta riga ta saba ne, saboda kina fita sa sassafe ba tare da kin damu da tashi na ba, balle haɗa mana abun karyawa”
“Ni gaskiya ta daina shiga min haƙƙi bana so”
“Shikenan zan mata magana, amman yanzu faɗa min me kike ji yana damun ki”
“Fever, sneeze, headache and nauseous”
“Zan diɓi jininki da fitsari idan zan fita, yanzu tashi mu karya sai ki sha magana”
Ta ƙara manne masa a jiki.
“A'a ni bana so cin komai”
“Tea fa?”
“Sai dai idan kai zaka haɗa min da kan ka”
“Yes ni zan haɗa miki ai”
Ya faɗa yana murmushi, sannan ya tashi ya fice. Ajiyar zuciya Rashida ta sauke, ranta yana mata ba daɗi, idan har zarginta ya tabbata gasjiyar tana da ciki, tana cikin matsala dan bata iya tantance na waye ne,
‘Taya wani zai gane idan ba ni ma faɗa ba?’
Tambayar da tazo mata kenan a zuciyarta, sai kawai ta tashi ta shiga banɗaki.
Hilal sai da ya shiga ɗakinsa ya ɗauko maganinka sannan ya nufo ɗakin Kalsoom, a lokacin tana zaune gaban madubi tana shiryawa dan fitowarta daga wanka kenan.
Daga bakin ƙofa ya tsaya yana kallonta yace
“Wifey Yau madam babu lafiya, ba zata fito ba tea kawai zata sha, ni ma kuma bana jin cin komai”
Kai ta ɗaga masa tayi murmushin da be kai zuci ba. Har ya wuce, sai kuma ya dawo ya tsaya bakin ƙofar ya miƙa mata hannu.
“Taso na haɗa miki breakfast”
Ba musu ta taso ta miƙa masa hannun ba dan ranta na mata daɗi ba. A kujerar data saba zama ya zaunar da ita, ya ɗauki kofi biyu ya haɗa tea, ya aje mata ɗaya gabanta ya zuba mata ƙwai da sauran abubuwan da suke gurin, sannan yaƴi mata kiss ya ɗauki tea ɗin ya nufi ɗakin Rashida.
Da kallo ta bishi, zuciyarta na sosuwa da lamarinsa, tabbas yana son matarsa fiye da yadda yake son kansa, yanzu ya kasa karyawa saboda bata da lafiya, ta lura da yadda yanayinsa ya canja a take, taya zata shiga rayuwar irin waɗannan ma'auratan sannan tace zata samu farinciki?
Hannu ta kai ta shafa cikinta, hawaye masu zafi suka silalo daga idonta.
Sai da ya bata tea ɗin tasha sannan ya bata magani, sai ya sake fita yaje ya ɗauko wasu robobi guda biyu ya miƙa mata babbar.
“Kiyi fitsari a wannan”
Hannunsa sanye da safa, ya ɗibi jininta ya zuba a ƙaramin robar sannan ya manna mata kaɗa ya lunda mata, ya kwance robar daya ɗaure mata hannun da shi, kwashe kayan yayi ya fice. Bayan kamar thirty minutes ya dawo ɗakin da shirinsa na zuwa office.
Robar fitsarin ya ta bashi, ya karɓa yayi mata kiss, sannan ya fice. Ɗakin Kalsoom ya shiga, tana jin motsinta ta lafe kamar tana bachi, itama kiss ɗin yayi mata sannan ya fice.
Rashida na jin tashin motarsa ta janyo wayarta ta danna number Asmee, ringing huɗu tayi sannan ta ɗauka.
“Asmee an tashi lafiya?”
“Lafiya ƙalau ya gidan?”
Ya amsa mata muryarta da alamar damuwa.
“Asmee yau ba zan samu fita ba, bana jindaɗi, sai dai kr kije idan da hali”
“Me ke damun ki?”
“Abubuwa da yawa ga jikin duk ya min nauyi”
“Ko dai ciki ne?”
“Haka nake tunani nima”
“Allah ya raba lafiya”
Jin ta faɗa ba da wani jindaɗi ba yasa Rashida Tambaya.
“Ya naji muryar ki ba daɗi?”
“Ba komai, nima bana jindaɗin ne, amman zan daure a haka naje”
“Yauwa na gode sosai, kin ce dai yana aiki sosai ko?”
“Sosai Wallahi kamar yan kan wuƙa, duk yadda mu kayi zan faɗa miki”
“Okay na gode”
Rashida na kashe wayar Asmee ta fashe da kuka.
‘Allah kasa ba gaske bane Allah, idan har da gaske ne ya ci amanata, tun da yasan yana da shi kuma ya nemi ya kwana da ni, Wallahi dana sani ni dama ban je gunsa neman magani ba, mugun Malami kawai’
Abunda take ta tunani a zuciyarta kenan, a fili kam kuka kawai take, kamar ta cire idonta.
_________________________________________
Kuyi Haƙuri da wannan idan Allah ya bani iko zan kara muku wani anjima.
BEST REGARDS 💖🌺
KHADEEJA CANDY 😘
*🌺🌺🌺 ZAGON ƘASA 🌺🌺🌺*
Website
www.khadeejacandy.com.ng
Godiya marar iyaka gareki Daughter, na gode na gode I really did not expect this awesome surprise from your side
Allah ya kara arziki 😘
*PAGE - 31*
NOT EDITED ⚠️
Ƴan seconds ya rage wayar ta fara ringing sai kawai ta kashe, tana tunanin yadda za fallasawa kanta asiri idan har ta yarda ta faɗa masa danuwarta, ba duka ɗan'uwane yake taimako dan Allah ba, ballanta shi data san dole ne ya faɗawa Hajiya Barau, ita kuma fitar da maganar zata yi, sai a fara cewa tana roƙon dangi.
Juyowa tayi ta nufo gurin da Hajara take zaune, ita ma ta zauna tana miƙa mata wayar.
“Har kin kira?”
“A'a ban kira ba na fasa ne”
Ta faɗa tana murmushi, isowar Mama yasa ta sadda kanta ƙasa tana watsa da yatsun hannunta.
“Wai gida za mu koma yanzu”
Daga Hajara har Namra kallonta suka yi
“Gida kuma? Ina ba dai sokoto ba ko?”
Namra ta tambaya cike da mamaki.
“Can fa, wai so nake muje yanzu kamin yamma mun isa sai da gobe kuma mu juyo”
“Amman zuwa lafiya ne?”
Mama ta ɗan yi shiru kamar mai tunanin abunda zata ce mata.
“A'a wai kuɗi zan je na ranto idan har Allah yasa an samu sai a siye maganin da likita ya rubuta ta, tun da naga alamun sauƙi a jikinsa amman kumburin nan na kansa yana bani tsoro. Kuma ina son naje na ɗauko wasu tufafin gashi mai son Hajara shi ma ya damu yaushe za mu dawo”
Namra ta sauke ajiyar zuciya cike da tausayawa, ji take kamar ace tana da mafitar su ta ɗauka ta bada, ba sai taje neman rance ba.
“Amman Mama da zaki yi haƙuri har gobe, saboda yanzu rana yayi sosai, kuma zaku iya zuwa ku tarar da jira a tasha, ƙara ki haƙura har da safe sai ki tafi, amman tafiyar dare ba kyau,
Book Chapters
Chapter 1Chapter 2Chapter 3Chapter 4Chapter 5Chapter 6Chapter 7Chapter 8Chapter 9Chapter 10Chapter 11Chapter 12Chapter 13Chapter 14Chapter 15Chapter 16Chapter 17Chapter 18Chapter 19Chapter 20Chapter 21Chapter 22 Chapter 23Chapter 24Chapter 25Chapter 26Chapter 27Chapter 28Chapter 29Chapter 30Chapter 31Chapter 32Chapter 33Chapter 34Chapter 35Chapter 36Chapter 37Chapter 38Chapter 39Chapter 40Chapter 41Chapter 42Chapter 43Chapter 44Chapter 45Chapter 46Chapter 47Chapter 48Chapter 49Chapter 50Chapter 51Chapter 52Chapter 53Chapter 54Chapter 55Chapter 56Chapter 57Chapter 58Chapter 59Chapter 60Chapter 61Chapter 62Chapter 63Chapter 64Chapter 65Chapter 66Chapter 67Chapter 68Chapter 69Chapter 70Chapter 71Chapter 72Chapter 73Chapter 74Chapter 75Chapter 76Chapter 77Chapter 78Chapter 79Chapter 80Chapter 81Chapter 82Chapter 83Chapter 84Chapter 85Chapter 86Chapter 87Chapter 88Chapter 89Chapter 90Chapter 91Chapter 92Chapter 93Chapter 94