ne from the bottom of his heart, like he's seriously saying what is inside him, daman can shi ba mutum ne mai tausayin mace ba, indai zaki shekara kina kuka Abdool kam ko a jikinsa, wata ƙila dan ba shi da lokacin matan ne, ko kuma dan har yanzu idanuwansa basu ga zubar hawayen wacce zuciya take muradi ba. Sannan shi sam baya ganin tausayin ko kuma mutucin yarinyar da ta bar gaban iyayenta, da ma ace korarta suka yi ba ita ta gudu ba.
Babu yadda Amira za ta yi da shi duk da kalamansa sun taɓa zuciyarta, ta daɗe da karantar be iya lafazi ba, kuma babu ruwansa da tauna magana idan zai faɗa.
Sai dai hakan be sa taji haushinsa ba ko kuma ta ji ta tsane shi, sai kusanci da shi take so, dan ta koya masa yadda zai zauna da ita.
“Amman idan na koma da wane ido zan kallesu?me zan ce musu? Ya kake tunanin duniya zata kalle ni?”
“Tun kamin ki baro gidan ku ya kamata ki yi ma kan ki wannan tambayar, idan kika gudu me zaki ce musu? Da wane ido zaki kallesu? Ya kuma duniya zata kalle ki? There's no point of crying dan ke kika sai da mutunci da hannu ki”
Wani irin kallo ta watsa masa da jajayen idanuwanta, sai dai kwarjininsa be barta ta masa kallon daƙiƙa biyar ba ta kau da idon, cikin kakkausan lafazi ta ce .
“Amman mi yasa baka bar ni na mutu ba? So that na huta da rayuwar gaba ɗaya?”
Ya gyara tsayuwarsa ya ɗaga daga jikin ƙofar da yake tsaye yana sa hannayensa aljihu.
“I'm sorry I'm not harassing you I'm just telling the truth”
Har ya juya sai kuma ya juyo ya kalleta.
“Park your things, Doc zai baki sallama, around 10am driver zai kai ki gida”
Be tsaya jiran abunda zata ce ba yasa kai ya fice. Rasss! Rasss! Rasss! Gabanya ya yanke ya faɗi.
“Wane gida? Gidan su ko gidan mu? Ko kuma wani gidan na dabam?”
Ta tambayi kanta, dik sanyin ɗaki be hana gumi zubo mata ba. Babu inda ya fi tsaya mata a rai a kamar gidan su. Wayyo Allah ji take kamar mutuwa za tayi idan har aka maida ita gidan su, ita kanta tana son zuwa gidan amman bata iya iyawa, bata san dalili ba.
Ta kasa sukuni sai safa da marwa take har Doc ya shigo ɗakin, bata ga alamun rahama a fuskarsa ba balle ta tambaye ko yasan inda Abdool zai kai ta, kai ba zata iya tambayarsa ba kar Abdool ya zargi wani abu.
Sai kawai taja bakinta tayi shiru, sai dai tasha alwashin indai gidansu ne ba zata taɓa zuwa ba sai dai komai zai faru ya faru.
Sai da likitan yayi mata binciken ƙwa-ƙwaf sannan ya rubuta takardar sallama ya miƙa mata, ya fice. Kamar yadda Abdool yace 10 na bugawa sai ga wani yazo cikin uniform ɗin soja yace mata ta fito suje. Nan ma sai da gabanta ya faɗi.
“Ina... za...mu....je?”
“Katsina yace a kai ki, gidan Mahaifiyarsa”
Ta lumshe ido na wasu ƴan daƙiƙu, wani irin daɗi ya ziyarci zuciyarta har ta samu maida yawun daya tsaya mata a maƙoshi.
Bata buƙatar ɗaukar komai, daman can duk kayan da tayi amfani da su shine ya kawo mata, dan ita ko waya bata da a hannunta balle wani kayan kuma. Farincikin dake zuciyarta ya kasa ɓoyuwa har sai da ya nuna a fuskarta.
Ko da ta fito Abdool na tsaye kusa da motar, da alama ita yake jira, sai dai kwata-kwata hankalinsa baya gurinta yana wani wajen dabam.
Ɗaya daga cikin boys ɗin sa ne ya buɗe mata mota ta shiga, idonta na kan Abdool.
Yayi kusan minti biyar yana magana da mutanen biyu sannan ya suka shiga motar da take sai kuma wata mota dake gabansu cike da sojoji suka kama. Shi kuma ya juya ya koma cikin.
Juyawa tayi ta cikin motar tana kallonsa. Tana ayyanawa kanta zama abokiyar rayuwarsa, dan wannan karamcin kawai da yayi mata ya isa yasa tayi sha'awar hakan. Mutum me daraja da ƙima kamar wannan? What if ta zama matarsa?
KALSOOM POV.
Tun daga lokacin data fara shan rubutun da Hajiya tasa aka mata, sai ta fara jin sauyi a jikinta, sai mafarkai take wasu ma har bata san kansu ba.
Natsuwar da take ji a yanzu, yana kan tunatar da ita rayuwar rikicin da ta yi a ƴan watanin nan, sai yanzu take mamakin kanta duk wacan abun da ta yi sai ya zama matar kamar mafarki.
Lallai a yanzu ta tabbatar da ta yi wasa da addu'ah, dan bata iya addu'ah safe balle kuma ta yamma da take gani kamar ba komai ba ce. Sai dai har yanzu bata jin ƙarfin yin addu'ah kuma jinin be ɗauke mata ba, amman dai ta dawo normal kamar yadda take, ba kamar baya ba da take jin abu na mata yawo cikin kai kamar tsutsa.
Da wuri ta tashi ta shirya musu abun karyawa, sannan ta tashi yaran duka tayi musu wanka da kanta, Izzah ce kawai bata bari anyi mata ba, sai wani cika take tana batsewa kamar wata babbar mace, ada tana yi a dole dan Rashida na sa, amman a yanzu kan na gaske take dan har cikin zuciyarta take jin tsanar Kalsoom bayan kuma bata mata komai ba, sai dai laifinta da take gani na kore musu uwa da ta yi, sannan tana ganim yadda komai ta yi musu Daddy su ba ya magana.
Sai da Kalsoom ta shirya su tsab sannan ya tura su gurin motar Daddy su ta shiga ɗan ta tashi mijinta.
A bakin ƙofar ɗakinsa ta tsaya ta buɗe maɓallin rigarta sannan ta kunna kai cikin ɗakin. Hannunta tasa cikin gashin kansa tana wasa da shi, amman be motsa ba, badan kuma be farka ba, sai dan daɗin da yake ji akan abunda take masa. Ganin be farka ba yasa ta kwantowa jikinsa ta zira halshenta cikin kunnensa. Still be motsa ba amman fuskarsa da murmushi alamar idonsa biyu kenan.
Hannu tasa ta matse masa hancin iya ƙarfinta, sai ya tashi ba shiri yana kallonta.
“K.e...”
Maganarsa ta maƙale lokacin da yayi arba da rigar bachinta dake buɗe. Rabon da ta masa irin haka har ya manta, Kullum sai dai ya haɗe mata yawu, yau ma yasan haka ne tun da jinin har yanzu be tsaya mata ba. Hannu ya kai ya laƙamo wuyanta.
“Let us enjoy ourselves...”
“No way, yara suna waje suna jiran ka”
Ya dafe kansa.
“Ya Subhanallah, gaskiya I'm tired of driving them to school”
Ta wara ido
“Then teach me how to drive!”
“No, ba zan bari ki yi driving ba, wani zai ganemin wannan kyakkyawar fuskar ba, sai dai na nemo direbe, idan kin san inda zamunsamu direba mai natsuwa ki nemo mana”
Ya yaye bedsheet ɗin dake samansa yaja kumatunta, ya sauka saman gadon ya shiga bathroom. Bakinsa ya wanke da fuskarsa sannan ya fito. Tsaye ya same ta jikin bathroom ɗin tana jiransa.
Ya ɗan risina kaɗan yayi mata kiss a baki.
“My Happiness”
Ta moɗe bakin tana hararsa irin na ma'auratan nan masu cike da shauƙin so.
“Ni kike harara?”
Ya kama kunnenta
“Ouuuch Doc it hurt”
Yana janye hannunsa ita tayi masa yadda yayi mata, ta fito falo da gudu shima ya biyota yana murmushi.
Ganin Asmee yasa dik suka tsaya cak, musamman ita dake ƙoƙarin gyara rigarta.
Be ce da ita komai ba, har sai da ita tabfara gaishe shi sannan ya amsa ya nufi ƙofar fita.
Kalsoom kuma ta koma ta ɗauki hijab tasa sannan ta fito falon cike da mamakin sammakon da Asmee ta yi musu haka kamar mai biyar bashi.
Ita kanta taji kunyar kanta, ga kuma baƙinciki ganin da tayi suna cikin walwala, dan tana taya ƙawarta kishi ne.
“Na doko muku sammako, kuna sha'aninku”
Kalsoom ta yi dariya.
“A'a nace dai Allah yasa ba bashin ki muka ci ba”
“A'a wallahi an kwana biyu ban zo ba shine nace bari na leƙo ki ban sirrin da kika bawa mijin ki ya kori Rashida”
Kalsoom ta rufe baki
“A'a sirri kuma? Ai duk wanda kika ga ta bar gidan mijinta inda akan rashin ladabi da biyayya ne to ita ce ta fitar da kan ta”
“Hmmm ba son ba mu sirrin dai ko, kin ga nima daman yara na kai scul shine nace bari na leƙo na gan ki”
“Aiko kin kyauta, an kwana biyu a a gaisa ba”
“To ai ƙara ni ke ba ko zuwa kike ba”
“Ba ya bari ne, cewa yake baya son ina yawan fita”
“Aikam baya son ki yi nisa da shi, kin ga bari na tashi na wuce sai kin zo”
Har gurin motarsa Kalsoom ta raka ta tana bata haƙurin rashin zuwa da ba ta yi ba, da kuma cewar zata zo idan Hilal ya barta.
ASIM POV.
Ba laifi yau kan yayi wanka ya shirya kansa, ko dan yana jumma'ah ne oho, da wanka ma be dame shi sai dai yayi kanta karya ya fita idan fita ta kama shi.
Bayan sun sauko daga sallah jumma'ah ya nufi gurin aikinsa yana mai jin haushin aikin nasa ace kullum sai ya yi zuga sannan ya samu ƴan kuɗin kashewa shi wannan aikin dik ya takura masa, sai jan tsaki yake yana maganganu shi kaɗai.
Tun daga nesa yake kallon wata makekiyar mota data faka gefen gurin da suke aiki, yana ayyanata a cikin jerin motocin da zai siya idan yayi kuɗi, dan kyawon motar ya ɗauki hankalinsa sosai.
Yana buɗe shagon da suke aikin, mai motar ta zoƙe gilashin motarta tana masa sallama.
“Assalamu alaikum samari”
‘Tab ashe ma mace ce’
Ya faɗa a ransa, a fili kuma sai ya amsa mata baki har kunne.
“Wa'alaikissalam Hajiya ina wuni?”
“Lafiya ƙalau, dan Allah masu aikin nan gurin nake nema za a gyara min gate ɗina ne”
Ta faɗa cikin yauƙi da rangwaɗa kamar ba babbar mace ba.
“Mu ne ai muke aikin Hajiya, ina gate ɗin na ki yake?”
“Kai ...?!”
Ta faɗa tana nunasa da hannunta, mamaki ne ya isheta, yanzu tsalelen saurayi kamar wannan ace aikin ƙira yake, dubi ko shigarsa fa.
“Okay ga kt na idan kun tashi aikin sai kuje gida ku yi min, gate ɗin be ɓalle bane duka rabi ne za'a gyara min”
Ta miƙa nasa katin. Yasa hannu biyu ya karɓa cikin girmamawa kamar wata uwarsa.
“To Hajiya da zarar abokan aikina sun iso zamu je muyi aikin, sai dai baki bamu time ba”
“Ga number waya na nan a jiki kamin ku zo sai ku kira ni”
“To Hajiya za mu zo inshallah”
Ya miƙa masa 5k
“Ga wannan asha ruwa”
Yayi taku tare da nuna kamar ba zai karɓa ba.
“A'a Hajiya ki bar shi”
“Bana mai da kuɗi idan ya fito jakana, so ka karɓa kawai idan ma watsarwa za kayi sai ka watsar”
Yasa hannu ya karɓa yana mata godiya. Ita kuma ta tashi motarta ta kama hanya. Sai da ta wuce ya kalli jikinsa.
“Ita kan ta ta ga ban yi mata kama da talaka ba, wallahi ni babban mutum ne”
Ya juya ya cigaba da buɗe shagon farinciki fal a ransa.
RASHIDA POV.
Ta kasa zaune ta kasa tsaye tun lokacin da Asmee ta labarta mata irin rayuwar jindaɗin da Kalsoom take da Hilal. Kenan ita sun manta da duniyarta? Hilal ya manta labarinta?
“Ina ba za'a shafe ni a tarihim rayuwarsa, ba zai rayu da wata ba sai ni, wata bata isa ta mallake min miji ba. Amman malamin nan ko dai yaudara yake ne? Dan me zai ce min magani yayi alhalin be yi ba”
Tayi shiru tana nazari, wata ƙila ita ma Kalsoom tana shige-shige shiyasa ta shafe ta a zuciyar Hilal gaba ɗaya. Daman idan kana yin abu gani kake kowa ma haka yake.
Wayarta ta janyo ta kira lamanin dan bata jin zuwa can inda yake a yau tun da ko aikin dake gabanta bata gama ba ma, balle ta yi tunanin fita, kuma tasan ko ta fita kamin taje ta dawo dare yayi sosai.
Kiran farko be ɗauka ba, haka na biyu zuwa na uku, amman bata sarara masa ba, har sai da ta jera masa kira kusan 10+ sai da yayi picking sannan hankalinta ya kwanta.
Sama-sama ta gaisa ta shi sai ta koro masa da bayaninsa
“Ina zuwa bari na binciki ƙasa”
Jimmm yayo shiru na ɗan lokaci sannan ya yi gyaran murya yace
“Lallai wannan matar ta sha gaban ki, ta fiki shiga bokaye, shiyasa wannan aikin be yi wani dogon tasiri a gareta ba”
“Kana nufin aikin be kamata ba?”
“Ya kamata amman yana ƙoƙarin fita jikinta”
“Amman idan har ya kamata ai dole Hilal.zai damu, dan bashi da wata mata sai ita kuma har yanzu ban ji ance sun samu saɓani ba”
“Amman ƙasa ta nuna mana an samu tsaɓani, sai dai idan kece baki sani ba”
“Yanzu malam miye abun yi?”
“Abu ɗaya ya kamata daman na faɗa miki, idan wannan be yi ba sai na biyu zuwa na uku, dole ne mu haukatata idan kuma be yi ba sai mu yi mata halbin kasko”
Ta rufe baki. Rashin imaninta be kai can ba.
“Malam babu wata hanyar ne?”
“Gaskiya wannan ce kawai mafita indai kina son mijin ki, idan ta bar gida sai ki samo sperm mu hada miki wanda Mijinki zai maida ke gidan sa dan dole”
“Zan yi tunani a kai”
“To yayi kyau”
Ta aje wayar tana busar da iskar bakinta.
NAMRA POV.
Yau kam basu fara karatun da wuri ba, hakan yasa har suka wuce goma na dare basu tashi ba. Amman shigowar Asim yasa ta yi addu'ah ta sallami ɗaliban nata da mafi yawansu matan aure ne.
Har gobe ba zata daina girmama Asim ba, tana bashi haƙƙinsa a matsayinsa na mijinta, dan ta karanta ta gani, ta san irin girman da miji yake da shi ga matarsa, ita dai kam ta kan yi ƙoƙarin ganin ta bashi dukanin haƙƙinsa dan tasan ko mutuwa tayi sai dai idan shine ya cuce acan Allah ya yi musu hisabi.
Ƙarfe shida suke tashi daga gurin da yake aikin, amman baya dawowa gida sai goma ta gota na dare, zaman majalisa yake irin zaman nan da baya amfanar da komai sai zunubi da hassada, zaman zagin wane da wace, zaman matar wane tafi matar wane, wacce aure ya mutu wacce biyar maza take. Kusan ma shine yaro a cikin masu zaman majalisar dan duk sun girme shi dukansu magidanta ne.
Kicin-kicin ya shigo gidan baya ƙaunar kallon Namra, idan akwai wata maƙiyiyarsa yanzu a duniya to Namra ce. Ita kam idan sabo ta saba dan yanzu ba kasafai take ganin rahamar fuskarsa ba.
Tufafin jikinsa ya kwaɓe ya jefar saman katifar ya ɗauki wata guntuwar jalabiya ya saka yazo ya zauna tsakar ɗakin yana kallon kyanɗir ɗin dake hasken ɗakin
“Ina abinci na?”
Ko rufe baki be yi ba ta dire masa abincin gabansa da ruwan sha, sannan ta ɗauko mafeci tana masa fita, sai murmushi take tana masa fira dan kawar mata da ɓacin ran dake tare da shi. Har ya gama cin tuwon ya sha ruwa be kula taba balle ya tanka ta a firar da take.
Tsabar ƙazanta da rainin wayo cikin kwanon daya gama cin abinci ya wanke mata hannu. Ita kuma ta ɗauka ta kai waje ta aje. Sai gata ta dawo ɗakin da gudu jin wayarta na ringing.
Da murna ta ɗauka ganin number Anty daman haka take kullum kamar ba jiya tayi magana da ita ba, zaka rantse kace ta shekara ba ta yi magana da ita ba.
Bayan sun gaisa Anty take faɗa mata za a kawo lefen Maryam cikin weekend ɗin nan mai ƙarewa, ta kuma nuna mata tana son ta shigo ko dan kwana biyu da suka yi ba su ganta ba, kwanki babu yadda Anty ba tayi akan ta zo amman Namra ta nuna mata karta zo yanzu ta bari har gaba.
Da fargaba ta aje wayar dan tasan ba lallai bane Asim ya bar ta taje, amman a haka ta sake fuska tana faɗa masa Anty ce ta kira.
“Okay”
Kawai ya faɗa irin ina ruwan ɗin nan. Ya hau saman katifa ya kwanta yana mata wani kallo da ita kaɗai ta san kiran da yake mata.
[7/18, 8:12 PM] Khadeeja Candy♥: *50*
AMIRA POV.
Har suka isa katsina babu abinda take tunani sai Abdool saƙe-saƙe kawai take a zuciyarta na yadda zata sace zuciyarsa da kuma iyalansa.
Babu abinda take annawa a zuciyarta sai sabuwar rayuwar da za ta shimfiɗa na kanta.
Duk irin yadda take misalta arzikin gidan su Abdool sai ya ci gaban tunaninta, ya sha banban da abinda take tsamani. Haka ta zaka kamar ba wacce ta fito daga garin Abuja ba. Idonta ya biɗe sosai lokacin da motar da take ciki ta kunna kai cikin gida.
Ga matakan tsaron daya shimfiɗa ma gidan kamar masaukin shigaban ƙasa. Part biyu ta gani a gidan sai dai part ɗin da suka sauka ya fi girma da tsaruwa, hakan ya tabbatar mata da wacan ɗin part ɗin Abbansa ne ko kuma nasa.
Tana fitowa motar idonta ya sauka kan wani ƙaton Garden dake gefen part ɗin, babu abinda kake ji sai sautin kukan tsuntsaye, ga wani swimming pool da tafi ɗaukar hankalin a hangen nata, daga ruwan swimming pool ɗin har itacen da suke gurin komai kore ne. Peacocks sai kai da kawo suke a bakin Garden ɗin.
“Let's go Madam”
Ɗaya daga cikin sojan da suke tarar a gurin ya faɗa yana nuna mata ƙatuwar ƙofar shiga falon, wacce ta kasance abun kallo, idan ba wanda ya sani ba sai kan rantse kace da zinari aka ƙerata.
A hankali ta cira ƙafarta ta fara takawa, zuwa gurin ƙofar dake kashe mata ido saboda kyawonta. Hannu ta kai zata buɗe ƙofar lokacin data ƙarasa sai kawai ta ga sojan ya danna wasu numbers, sannan ya matsa gaban wata ƴar ƙaramar severity camera yayi magana. Bayan kamar minti biyu sai ƙofar ta buɗe da kanta.
Ƙofar kawai ya nuna mata ya juya ya wuce.
Tun kamin ta saka ƙafarta falon wani irin ƙamshi da sanye suka fara mata lale marhabun. Taku ɗaya ta yi a ɗan ƙaramin downstairs dake ƙarasar da mutun cikin falon, zuwa na biyu na uku ta tashi zamewa saboda sulɓi da
Showing 117001 words to 120000 words out of 280121 words
Babu yadda Amira za ta yi da shi duk da kalamansa sun taɓa zuciyarta, ta daɗe da karantar be iya lafazi ba, kuma babu ruwansa da tauna magana idan zai faɗa.
Sai dai hakan be sa taji haushinsa ba ko kuma ta ji ta tsane shi, sai kusanci da shi take so, dan ta koya masa yadda zai zauna da ita.
“Amman idan na koma da wane ido zan kallesu?me zan ce musu? Ya kake tunanin duniya zata kalle ni?”
“Tun kamin ki baro gidan ku ya kamata ki yi ma kan ki wannan tambayar, idan kika gudu me zaki ce musu? Da wane ido zaki kallesu? Ya kuma duniya zata kalle ki? There's no point of crying dan ke kika sai da mutunci da hannu ki”
Wani irin kallo ta watsa masa da jajayen idanuwanta, sai dai kwarjininsa be barta ta masa kallon daƙiƙa biyar ba ta kau da idon, cikin kakkausan lafazi ta ce .
“Amman mi yasa baka bar ni na mutu ba? So that na huta da rayuwar gaba ɗaya?”
Ya gyara tsayuwarsa ya ɗaga daga jikin ƙofar da yake tsaye yana sa hannayensa aljihu.
“I'm sorry I'm not harassing you I'm just telling the truth”
Har ya juya sai kuma ya juyo ya kalleta.
“Park your things, Doc zai baki sallama, around 10am driver zai kai ki gida”
Be tsaya jiran abunda zata ce ba yasa kai ya fice. Rasss! Rasss! Rasss! Gabanya ya yanke ya faɗi.
“Wane gida? Gidan su ko gidan mu? Ko kuma wani gidan na dabam?”
Ta tambayi kanta, dik sanyin ɗaki be hana gumi zubo mata ba. Babu inda ya fi tsaya mata a rai a kamar gidan su. Wayyo Allah ji take kamar mutuwa za tayi idan har aka maida ita gidan su, ita kanta tana son zuwa gidan amman bata iya iyawa, bata san dalili ba.
Ta kasa sukuni sai safa da marwa take har Doc ya shigo ɗakin, bata ga alamun rahama a fuskarsa ba balle ta tambaye ko yasan inda Abdool zai kai ta, kai ba zata iya tambayarsa ba kar Abdool ya zargi wani abu.
Sai kawai taja bakinta tayi shiru, sai dai tasha alwashin indai gidansu ne ba zata taɓa zuwa ba sai dai komai zai faru ya faru.
Sai da likitan yayi mata binciken ƙwa-ƙwaf sannan ya rubuta takardar sallama ya miƙa mata, ya fice. Kamar yadda Abdool yace 10 na bugawa sai ga wani yazo cikin uniform ɗin soja yace mata ta fito suje. Nan ma sai da gabanta ya faɗi.
“Ina... za...mu....je?”
“Katsina yace a kai ki, gidan Mahaifiyarsa”
Ta lumshe ido na wasu ƴan daƙiƙu, wani irin daɗi ya ziyarci zuciyarta har ta samu maida yawun daya tsaya mata a maƙoshi.
Bata buƙatar ɗaukar komai, daman can duk kayan da tayi amfani da su shine ya kawo mata, dan ita ko waya bata da a hannunta balle wani kayan kuma. Farincikin dake zuciyarta ya kasa ɓoyuwa har sai da ya nuna a fuskarta.
Ko da ta fito Abdool na tsaye kusa da motar, da alama ita yake jira, sai dai kwata-kwata hankalinsa baya gurinta yana wani wajen dabam.
Ɗaya daga cikin boys ɗin sa ne ya buɗe mata mota ta shiga, idonta na kan Abdool.
Yayi kusan minti biyar yana magana da mutanen biyu sannan ya suka shiga motar da take sai kuma wata mota dake gabansu cike da sojoji suka kama. Shi kuma ya juya ya koma cikin.
Juyawa tayi ta cikin motar tana kallonsa. Tana ayyanawa kanta zama abokiyar rayuwarsa, dan wannan karamcin kawai da yayi mata ya isa yasa tayi sha'awar hakan. Mutum me daraja da ƙima kamar wannan? What if ta zama matarsa?
KALSOOM POV.
Tun daga lokacin data fara shan rubutun da Hajiya tasa aka mata, sai ta fara jin sauyi a jikinta, sai mafarkai take wasu ma har bata san kansu ba.
Natsuwar da take ji a yanzu, yana kan tunatar da ita rayuwar rikicin da ta yi a ƴan watanin nan, sai yanzu take mamakin kanta duk wacan abun da ta yi sai ya zama matar kamar mafarki.
Lallai a yanzu ta tabbatar da ta yi wasa da addu'ah, dan bata iya addu'ah safe balle kuma ta yamma da take gani kamar ba komai ba ce. Sai dai har yanzu bata jin ƙarfin yin addu'ah kuma jinin be ɗauke mata ba, amman dai ta dawo normal kamar yadda take, ba kamar baya ba da take jin abu na mata yawo cikin kai kamar tsutsa.
Da wuri ta tashi ta shirya musu abun karyawa, sannan ta tashi yaran duka tayi musu wanka da kanta, Izzah ce kawai bata bari anyi mata ba, sai wani cika take tana batsewa kamar wata babbar mace, ada tana yi a dole dan Rashida na sa, amman a yanzu kan na gaske take dan har cikin zuciyarta take jin tsanar Kalsoom bayan kuma bata mata komai ba, sai dai laifinta da take gani na kore musu uwa da ta yi, sannan tana ganim yadda komai ta yi musu Daddy su ba ya magana.
Sai da Kalsoom ta shirya su tsab sannan ya tura su gurin motar Daddy su ta shiga ɗan ta tashi mijinta.
A bakin ƙofar ɗakinsa ta tsaya ta buɗe maɓallin rigarta sannan ta kunna kai cikin ɗakin. Hannunta tasa cikin gashin kansa tana wasa da shi, amman be motsa ba, badan kuma be farka ba, sai dan daɗin da yake ji akan abunda take masa. Ganin be farka ba yasa ta kwantowa jikinsa ta zira halshenta cikin kunnensa. Still be motsa ba amman fuskarsa da murmushi alamar idonsa biyu kenan.
Hannu tasa ta matse masa hancin iya ƙarfinta, sai ya tashi ba shiri yana kallonta.
“K.e...”
Maganarsa ta maƙale lokacin da yayi arba da rigar bachinta dake buɗe. Rabon da ta masa irin haka har ya manta, Kullum sai dai ya haɗe mata yawu, yau ma yasan haka ne tun da jinin har yanzu be tsaya mata ba. Hannu ya kai ya laƙamo wuyanta.
“Let us enjoy ourselves...”
“No way, yara suna waje suna jiran ka”
Ya dafe kansa.
“Ya Subhanallah, gaskiya I'm tired of driving them to school”
Ta wara ido
“Then teach me how to drive!”
“No, ba zan bari ki yi driving ba, wani zai ganemin wannan kyakkyawar fuskar ba, sai dai na nemo direbe, idan kin san inda zamunsamu direba mai natsuwa ki nemo mana”
Ya yaye bedsheet ɗin dake samansa yaja kumatunta, ya sauka saman gadon ya shiga bathroom. Bakinsa ya wanke da fuskarsa sannan ya fito. Tsaye ya same ta jikin bathroom ɗin tana jiransa.
Ya ɗan risina kaɗan yayi mata kiss a baki.
“My Happiness”
Ta moɗe bakin tana hararsa irin na ma'auratan nan masu cike da shauƙin so.
“Ni kike harara?”
Ya kama kunnenta
“Ouuuch Doc it hurt”
Yana janye hannunsa ita tayi masa yadda yayi mata, ta fito falo da gudu shima ya biyota yana murmushi.
Ganin Asmee yasa dik suka tsaya cak, musamman ita dake ƙoƙarin gyara rigarta.
Be ce da ita komai ba, har sai da ita tabfara gaishe shi sannan ya amsa ya nufi ƙofar fita.
Kalsoom kuma ta koma ta ɗauki hijab tasa sannan ta fito falon cike da mamakin sammakon da Asmee ta yi musu haka kamar mai biyar bashi.
Ita kanta taji kunyar kanta, ga kuma baƙinciki ganin da tayi suna cikin walwala, dan tana taya ƙawarta kishi ne.
“Na doko muku sammako, kuna sha'aninku”
Kalsoom ta yi dariya.
“A'a nace dai Allah yasa ba bashin ki muka ci ba”
“A'a wallahi an kwana biyu ban zo ba shine nace bari na leƙo ki ban sirrin da kika bawa mijin ki ya kori Rashida”
Kalsoom ta rufe baki
“A'a sirri kuma? Ai duk wanda kika ga ta bar gidan mijinta inda akan rashin ladabi da biyayya ne to ita ce ta fitar da kan ta”
“Hmmm ba son ba mu sirrin dai ko, kin ga nima daman yara na kai scul shine nace bari na leƙo na gan ki”
“Aiko kin kyauta, an kwana biyu a a gaisa ba”
“To ai ƙara ni ke ba ko zuwa kike ba”
“Ba ya bari ne, cewa yake baya son ina yawan fita”
“Aikam baya son ki yi nisa da shi, kin ga bari na tashi na wuce sai kin zo”
Har gurin motarsa Kalsoom ta raka ta tana bata haƙurin rashin zuwa da ba ta yi ba, da kuma cewar zata zo idan Hilal ya barta.
ASIM POV.
Ba laifi yau kan yayi wanka ya shirya kansa, ko dan yana jumma'ah ne oho, da wanka ma be dame shi sai dai yayi kanta karya ya fita idan fita ta kama shi.
Bayan sun sauko daga sallah jumma'ah ya nufi gurin aikinsa yana mai jin haushin aikin nasa ace kullum sai ya yi zuga sannan ya samu ƴan kuɗin kashewa shi wannan aikin dik ya takura masa, sai jan tsaki yake yana maganganu shi kaɗai.
Tun daga nesa yake kallon wata makekiyar mota data faka gefen gurin da suke aiki, yana ayyanata a cikin jerin motocin da zai siya idan yayi kuɗi, dan kyawon motar ya ɗauki hankalinsa sosai.
Yana buɗe shagon da suke aikin, mai motar ta zoƙe gilashin motarta tana masa sallama.
“Assalamu alaikum samari”
‘Tab ashe ma mace ce’
Ya faɗa a ransa, a fili kuma sai ya amsa mata baki har kunne.
“Wa'alaikissalam Hajiya ina wuni?”
“Lafiya ƙalau, dan Allah masu aikin nan gurin nake nema za a gyara min gate ɗina ne”
Ta faɗa cikin yauƙi da rangwaɗa kamar ba babbar mace ba.
“Mu ne ai muke aikin Hajiya, ina gate ɗin na ki yake?”
“Kai ...?!”
Ta faɗa tana nunasa da hannunta, mamaki ne ya isheta, yanzu tsalelen saurayi kamar wannan ace aikin ƙira yake, dubi ko shigarsa fa.
“Okay ga kt na idan kun tashi aikin sai kuje gida ku yi min, gate ɗin be ɓalle bane duka rabi ne za'a gyara min”
Ta miƙa nasa katin. Yasa hannu biyu ya karɓa cikin girmamawa kamar wata uwarsa.
“To Hajiya da zarar abokan aikina sun iso zamu je muyi aikin, sai dai baki bamu time ba”
“Ga number waya na nan a jiki kamin ku zo sai ku kira ni”
“To Hajiya za mu zo inshallah”
Ya miƙa masa 5k
“Ga wannan asha ruwa”
Yayi taku tare da nuna kamar ba zai karɓa ba.
“A'a Hajiya ki bar shi”
“Bana mai da kuɗi idan ya fito jakana, so ka karɓa kawai idan ma watsarwa za kayi sai ka watsar”
Yasa hannu ya karɓa yana mata godiya. Ita kuma ta tashi motarta ta kama hanya. Sai da ta wuce ya kalli jikinsa.
“Ita kan ta ta ga ban yi mata kama da talaka ba, wallahi ni babban mutum ne”
Ya juya ya cigaba da buɗe shagon farinciki fal a ransa.
RASHIDA POV.
Ta kasa zaune ta kasa tsaye tun lokacin da Asmee ta labarta mata irin rayuwar jindaɗin da Kalsoom take da Hilal. Kenan ita sun manta da duniyarta? Hilal ya manta labarinta?
“Ina ba za'a shafe ni a tarihim rayuwarsa, ba zai rayu da wata ba sai ni, wata bata isa ta mallake min miji ba. Amman malamin nan ko dai yaudara yake ne? Dan me zai ce min magani yayi alhalin be yi ba”
Tayi shiru tana nazari, wata ƙila ita ma Kalsoom tana shige-shige shiyasa ta shafe ta a zuciyar Hilal gaba ɗaya. Daman idan kana yin abu gani kake kowa ma haka yake.
Wayarta ta janyo ta kira lamanin dan bata jin zuwa can inda yake a yau tun da ko aikin dake gabanta bata gama ba ma, balle ta yi tunanin fita, kuma tasan ko ta fita kamin taje ta dawo dare yayi sosai.
Kiran farko be ɗauka ba, haka na biyu zuwa na uku, amman bata sarara masa ba, har sai da ta jera masa kira kusan 10+ sai da yayi picking sannan hankalinta ya kwanta.
Sama-sama ta gaisa ta shi sai ta koro masa da bayaninsa
“Ina zuwa bari na binciki ƙasa”
Jimmm yayo shiru na ɗan lokaci sannan ya yi gyaran murya yace
“Lallai wannan matar ta sha gaban ki, ta fiki shiga bokaye, shiyasa wannan aikin be yi wani dogon tasiri a gareta ba”
“Kana nufin aikin be kamata ba?”
“Ya kamata amman yana ƙoƙarin fita jikinta”
“Amman idan har ya kamata ai dole Hilal.zai damu, dan bashi da wata mata sai ita kuma har yanzu ban ji ance sun samu saɓani ba”
“Amman ƙasa ta nuna mana an samu tsaɓani, sai dai idan kece baki sani ba”
“Yanzu malam miye abun yi?”
“Abu ɗaya ya kamata daman na faɗa miki, idan wannan be yi ba sai na biyu zuwa na uku, dole ne mu haukatata idan kuma be yi ba sai mu yi mata halbin kasko”
Ta rufe baki. Rashin imaninta be kai can ba.
“Malam babu wata hanyar ne?”
“Gaskiya wannan ce kawai mafita indai kina son mijin ki, idan ta bar gida sai ki samo sperm mu hada miki wanda Mijinki zai maida ke gidan sa dan dole”
“Zan yi tunani a kai”
“To yayi kyau”
Ta aje wayar tana busar da iskar bakinta.
NAMRA POV.
Yau kam basu fara karatun da wuri ba, hakan yasa har suka wuce goma na dare basu tashi ba. Amman shigowar Asim yasa ta yi addu'ah ta sallami ɗaliban nata da mafi yawansu matan aure ne.
Har gobe ba zata daina girmama Asim ba, tana bashi haƙƙinsa a matsayinsa na mijinta, dan ta karanta ta gani, ta san irin girman da miji yake da shi ga matarsa, ita dai kam ta kan yi ƙoƙarin ganin ta bashi dukanin haƙƙinsa dan tasan ko mutuwa tayi sai dai idan shine ya cuce acan Allah ya yi musu hisabi.
Ƙarfe shida suke tashi daga gurin da yake aikin, amman baya dawowa gida sai goma ta gota na dare, zaman majalisa yake irin zaman nan da baya amfanar da komai sai zunubi da hassada, zaman zagin wane da wace, zaman matar wane tafi matar wane, wacce aure ya mutu wacce biyar maza take. Kusan ma shine yaro a cikin masu zaman majalisar dan duk sun girme shi dukansu magidanta ne.
Kicin-kicin ya shigo gidan baya ƙaunar kallon Namra, idan akwai wata maƙiyiyarsa yanzu a duniya to Namra ce. Ita kam idan sabo ta saba dan yanzu ba kasafai take ganin rahamar fuskarsa ba.
Tufafin jikinsa ya kwaɓe ya jefar saman katifar ya ɗauki wata guntuwar jalabiya ya saka yazo ya zauna tsakar ɗakin yana kallon kyanɗir ɗin dake hasken ɗakin
“Ina abinci na?”
Ko rufe baki be yi ba ta dire masa abincin gabansa da ruwan sha, sannan ta ɗauko mafeci tana masa fita, sai murmushi take tana masa fira dan kawar mata da ɓacin ran dake tare da shi. Har ya gama cin tuwon ya sha ruwa be kula taba balle ya tanka ta a firar da take.
Tsabar ƙazanta da rainin wayo cikin kwanon daya gama cin abinci ya wanke mata hannu. Ita kuma ta ɗauka ta kai waje ta aje. Sai gata ta dawo ɗakin da gudu jin wayarta na ringing.
Da murna ta ɗauka ganin number Anty daman haka take kullum kamar ba jiya tayi magana da ita ba, zaka rantse kace ta shekara ba ta yi magana da ita ba.
Bayan sun gaisa Anty take faɗa mata za a kawo lefen Maryam cikin weekend ɗin nan mai ƙarewa, ta kuma nuna mata tana son ta shigo ko dan kwana biyu da suka yi ba su ganta ba, kwanki babu yadda Anty ba tayi akan ta zo amman Namra ta nuna mata karta zo yanzu ta bari har gaba.
Da fargaba ta aje wayar dan tasan ba lallai bane Asim ya bar ta taje, amman a haka ta sake fuska tana faɗa masa Anty ce ta kira.
“Okay”
Kawai ya faɗa irin ina ruwan ɗin nan. Ya hau saman katifa ya kwanta yana mata wani kallo da ita kaɗai ta san kiran da yake mata.
[7/18, 8:12 PM] Khadeeja Candy♥: *50*
AMIRA POV.
Har suka isa katsina babu abinda take tunani sai Abdool saƙe-saƙe kawai take a zuciyarta na yadda zata sace zuciyarsa da kuma iyalansa.
Babu abinda take annawa a zuciyarta sai sabuwar rayuwar da za ta shimfiɗa na kanta.
Duk irin yadda take misalta arzikin gidan su Abdool sai ya ci gaban tunaninta, ya sha banban da abinda take tsamani. Haka ta zaka kamar ba wacce ta fito daga garin Abuja ba. Idonta ya biɗe sosai lokacin da motar da take ciki ta kunna kai cikin gida.
Ga matakan tsaron daya shimfiɗa ma gidan kamar masaukin shigaban ƙasa. Part biyu ta gani a gidan sai dai part ɗin da suka sauka ya fi girma da tsaruwa, hakan ya tabbatar mata da wacan ɗin part ɗin Abbansa ne ko kuma nasa.
Tana fitowa motar idonta ya sauka kan wani ƙaton Garden dake gefen part ɗin, babu abinda kake ji sai sautin kukan tsuntsaye, ga wani swimming pool da tafi ɗaukar hankalin a hangen nata, daga ruwan swimming pool ɗin har itacen da suke gurin komai kore ne. Peacocks sai kai da kawo suke a bakin Garden ɗin.
“Let's go Madam”
Ɗaya daga cikin sojan da suke tarar a gurin ya faɗa yana nuna mata ƙatuwar ƙofar shiga falon, wacce ta kasance abun kallo, idan ba wanda ya sani ba sai kan rantse kace da zinari aka ƙerata.
A hankali ta cira ƙafarta ta fara takawa, zuwa gurin ƙofar dake kashe mata ido saboda kyawonta. Hannu ta kai zata buɗe ƙofar lokacin data ƙarasa sai kawai ta ga sojan ya danna wasu numbers, sannan ya matsa gaban wata ƴar ƙaramar severity camera yayi magana. Bayan kamar minti biyu sai ƙofar ta buɗe da kanta.
Ƙofar kawai ya nuna mata ya juya ya wuce.
Tun kamin ta saka ƙafarta falon wani irin ƙamshi da sanye suka fara mata lale marhabun. Taku ɗaya ta yi a ɗan ƙaramin downstairs dake ƙarasar da mutun cikin falon, zuwa na biyu na uku ta tashi zamewa saboda sulɓi da
Book Chapters
Chapter 1Chapter 2Chapter 3Chapter 4Chapter 5Chapter 6Chapter 7Chapter 8Chapter 9Chapter 10Chapter 11Chapter 12Chapter 13Chapter 14Chapter 15Chapter 16Chapter 17Chapter 18Chapter 19Chapter 20Chapter 21Chapter 22Chapter 23Chapter 24Chapter 25Chapter 26Chapter 27Chapter 28Chapter 29Chapter 30Chapter 31Chapter 32Chapter 33Chapter 34Chapter 35Chapter 36Chapter 37Chapter 38Chapter 39Chapter 40 Chapter 41Chapter 42Chapter 43Chapter 44Chapter 45Chapter 46Chapter 47Chapter 48Chapter 49Chapter 50Chapter 51Chapter 52Chapter 53Chapter 54Chapter 55Chapter 56Chapter 57Chapter 58Chapter 59Chapter 60Chapter 61Chapter 62Chapter 63Chapter 64Chapter 65Chapter 66Chapter 67Chapter 68Chapter 69Chapter 70Chapter 71Chapter 72Chapter 73Chapter 74Chapter 75Chapter 76Chapter 77Chapter 78Chapter 79Chapter 80Chapter 81Chapter 82Chapter 83Chapter 84Chapter 85Chapter 86Chapter 87Chapter 88Chapter 89Chapter 90Chapter 91Chapter 92Chapter 93Chapter 94