Jikin ƙofar ɗakin ya jingina yana kallonta da sauraren kukan da take rerawa. Rumgume hannayensa yayi yana tunanin ta ina zai fara. Ita kam bata ma san da shigowarsa ba, ta maida gaba gabas sai rusar kuka take.
Sauke hannayensa yayi ya nufi inta take zaune ya zauna gabanta yana kallon idonta.
“Yanzu abinda kike min adalci ne? Ki zauna kina kuka kin san yadda nake ji kuwa? Na rasa ɗa na ke kuma kin zauna a nan ki na kuka”
Ɗagowa tayi ta kalleshi
“Kai ɗa ka rasa, kuma kana da wasu, ni kuma miji na rasa”
“Ba ki rasa ni, kin san abinda na ke so da ke?”
Ta girgiza nasa kai.
“Zaki zauna nan for a while as zaman idda kamar yadda addini ya ce, ni zan je gida na faɗawa su Momi komai, wannan fushi na Hajiya na kwana biyu ne na nasan nan gaba kaɗan zata sauka, dole ne Hajiya tayi fushi Kalsoom saboda bata fahimce kamar yadda ni na fahimta ba”
“Ta yarda na zauna ne?”
“Bana jin zata hana, abunda na ke so dake ki yi mata uzuri kuma ki bata lokaci. Zan ɗauke ki muje gida anjima a can zan maida aure na”
Kai kawai ta ɗaga masa ta share hawayenta. Har ya mike tsaye sai kuma ya juyo ya kalleta ya ce
“Hajiya ta ce za a maida zaman makoki a can”
Nan ma kai ta ɗaga masa. Sai ya juya ya fice zuciyarsa babu daɗi. Zaune ya hango Hajiya a falon tana kallon ƙofar ɗakin Kalsoom daya fito fuskarta babu annuri. Kai ya girgiza cikin yanayin damuwa ya ƙaraso kusa da ita ya dafa kujera yana kallonta.
“Hajiya karki zama cikin iri surukan nan”
“Ba ƙoƙarin zama nake ba Hilal amman duk abunda yake gaskiya dole a faɗe shi, idan kai ta maka magani ni bata min ba, kuma Wallahi tallahi sai ka ƙara aure ko da kuwa bana numfashi, dole ka auri wacce zata riƙa maka ƴaƴanka mace ƙwarai ba mai ƙoƙarin kashesu ba, ni zan nema maka mata da kai na”
Tana kaiwa nan ta miƙe tsaye ta nufi ƙofar fita ranta na ƙololuwa a ɓaci. Shi dai da kallo ya bita har ta fice sannan ya saka hannyensa aljihu ya nufi ƙofar ransa a jagule.
RASHIDA POV.
A nasu gidan suke nasu amsar gaisuwar daban, duk da kasancewar waɗanda badu san aurenta ya mutu ba suka je can gidan gidan har sai idan sun tambaya ne sai ace musu gata nan. A harabar gidan suka shimfiɗa tabarma duk da kasancewar yaro ne hakan be hana ayi masu taro ba, sai dai ba irin zuwan nan ake na wuni ɗaya ba sai dai su zo su zauna na ƴan mintu su yi mata gaisuwar su wuce.
Tabarmarta daban tana zaune gefe ɗaya, ƴan gidan suna zaune gefe ɗaya. Idonta kumbura sosai duk wanda ya ganta sai ya tausaya mata wasu har da Allah ya isa suke mata duk a tunaninsu tana kuka ne saboda rashin ɗanta, sai dai a gurin Rashida abun ba haka yake ba, ita tana kuka ne saboda tunanin makomarta ganin asirinta ya tonu tun yanzu, tasan dole zamantakewar ta da ƴan gidan dole zai canja dan taga alamun hakan tun yanzu.
Misalin biyu da rabi Teema ta zo gidan gurin gaisuwa, sosai take son magana da Rashida amman babu dama saboda mutanen dake ta kai da kawo. Tana gurin kuma sai ga Asmee bayan ta fito gidan Hilal ta nufo nan.
Duk abunda ya faru a gidan sai da ta bawa Rashida labari. A nan Rashida take labarta musu maganar sakin da Hajiya tasa aka yi ma Kalsoom, dan su ba susan da maganar ba. Duk daɗi suka ji har mutenan dake gurin da kuma Asmee da basu san kan abun ba, amman ban da Teema da ita kan tasan komai.
“Amman Hajiya ta kyauta, daman ai ni za ci tuni zata sata shi aikata sakin, duk wanda yayi maka haka ga jika kan ai be cancanci zama da ɗan ka dan wata shi zata hara”
Gaskiya kam. Abunda suka mutanen suka masa da shi, sannan ƙananan maganganu suka biyo baya. Teema ta kada baki ta ce
“Gaskiya Hajiyar ta kyauta daman tun tun tun Hajiyarmu take cewa ya kamata ace Hajiya ta saka Hilal ya rabu da matar nan”
Rashid ta kalleta tana murza idonta.
“Hajiyar ku ta san ta ne?”
“Eh sukan haɗu a harkar siyasa wani lokacin, suna gaisawa sosai”
“Allah sarki”
Cewar Rashida. Sai kuma ta kawar da fuskarta tana kallon Asmee irin kallon nan da ita kaɗai ta san dalilinsa.
Teema kuma wani gurin take kallo tana wani tunanin na daban. Sai da aka kira la'asar sannan Teema ta wuce gida, Asmee kam a gidan tayi sallah sannan ta fice bakinta cike da magangu amman bat samu damar yi ma Rashida ba, ganin Safiya duk yasa ta tsargu, hakan yasa ta yi a zamar barin gidan.
Tashi Rashida tayi ta nufi cikin gidan rayuwarta duk babu daɗi saboda abunda take tunanin su momi sun fara nuna mta na ƙyama tsakanin jiya zuwa yau. Babu abunda ke ranta kamar ta bar musu gidan ta kama wani, tasan hakan zai fi mata kawanciyar hankali.
ASIM POV.
Yana ji a jikinsa akwai rashin dacewa a abinda suka aikata. Musamman yanzu da yake jin abu kamar ƙashi ya tsaya masa a takashinsa, ga wani zafi zafi da yake ji kamar an zuba masa barkono. Wasu ƙwayoyi dattijin Alhajin ya miƙa masa kusan kala huɗu ya ce ya sha, daman kamin su aikata sai da ya bashi wasu, tun jiya da dare suke abu ɗaya har yau da safe, sai yanzu nan ne Asim ya samu kansa. Sai a yanzu yake ƙarema Alhajin kallo, tabbasa ya sanshi a cikin manyan mutane. Amman duk misalin da yake masa jiya be gane shi ba sai yau. Daman tun lokacin daya ji sunansa ta ayyana a ransa ko shi ɗin ne, sai gashi mitumen ya fere ma tun daga biri har wutsiya.
“Na bawa Hajiya miliyan biyu ta baka, na siya maka mota ta miliyan uku. Idan ka riƙe min sirrina nan da ƴan wasu watan ni za'a far ƙirgaka a cikin manyan Alhazai. Zan wuce Abuja yau, idan na dawo zan samr ka a nan ko kuma nas Hajiya ta aika min kai a can sokoto”
Alhajin ya faɗa yana shafa fuskarsa. Asim kan daɗi har cikin kai, hankalinsa da zumuɗi gaba ɗaya sun tattara sun koma gida, babu abunda yake ransa kamar motar nan, a take ya ji duk jikinsa ya warysakr kamar babu wani ciwo jikinsa.
Be bar gidan ba sai da ya ci ya ƙoshi, sannan Alhajin yasa direba ya mai da shi gida.
Yana fita cikin motar sai ga Nably ta kira shi kamar ba zai ɗauka ba dan ya matsu ya ga motar da Alhajin yake ce masa. Sai dai farincikin dake ransa ba zai hana shi ɗaukar wayar Nabila ba.
“Hello my girly”
Ya faɗa cikin wani irin yanayi na shauƙi da annashuwa. Ita kaɗan ta karanci hakan a muryarsa.
“Da alama yau akwai labari mai daɗi a tare da kai..”
Ƙyalƙyalewa ya yi da dariya.
“Labari mai daɗi, na kusa zuwa Abuja na gan ki”
“Nikam ba zan iya jura har jibi ba, akwai birthday friend ɗita da za'ayi yanzu take faɗa min ni kuma na ce dole zan zo ko dan kai”
“Wow Amman gaskiya kin kyauta min, i can't wait to see you”
“I can't wait to see you too, sorry zan katse kiran, Momy na kira na zan kira ka idan mun gama”
Hajiya Sadiya ce ta fito waya a hannunta tana faman kiran waya, fuskarta ɗauke da murmushi, ganin Asim.
Shima Murmushin ya mayar mata ya doshi inda take cike da zumuɗi, sai kawai ta jefa mishi keys ɗin mota ta nuna masa motar tana cigaba da murmushi sai ta nufi wani ɓangaren na gidan tana amsa wayar da aka yi picking yanzu.
Wani irin tsalle Asim ya daga tsinkawo motar da yayi, da gudu ya doshi gurin yana wani irin gurnani kamar mahaukaci.
NAMRA POV.
Abdool na fita Uwani ta karɓi takardar hannun Neine ta duba, tana gani tasan cak ne sai dai bata iya gane ko nawa aka rubuta ba, kasancewar ilminta be kai har can ba, zero da ta ga a rubuce sun mata yawan karantawa.
“Minene?”
Neine ta tambaya, cike da son sanin abunda yake ciki.
“Ni wallahi ban gane kan abun ba, amman dai takardar kuɗi ne”
Uwani ta faɗa, dai Namra ta kai hannu ta karɓa tana dubawa.
“Miliyan ɗaya ne cif”
Uwani da Neina sun daki ƙirji tare da zaro ido.
“Miliyan ɗaya?”
Duk mutane da suka shigo cikin gidan duk ko wanne sai da ya riƙe baki, har ga Allah yawan kuɗin suke gani, Namra kam bat ɗauke su a bakin komai ba, abun ka da wanda yasan kan abu. Wani dogon tsaki Lamido yaja ya kawardar da kansa.
“Sam sam sam mutumen be san darajar mutane ba Wallahi”
Aiko yayi ƙoƙori irin wannan kuɗin haka! Ƴaƴan manyan mutane da da zasu taka rai su bar mutum balle har ya baka wannan kuɗin. Shine abunda mafi yawan matan maƙotan gidan suke ta faɗa.
“Ai dole yayi min mana, tun da ya lalata min Napep dole ya bada kuɗin jinya dan siyen wata”
Neine ce ta saka bakinta wannan karon tana nuna Abdool ya kyauta iya kyautawa.
“Wallahi da wani can ba zai kula ka ba Abdool ba gasu nan muna gani ba, wannan kuɗin ka siye sabon Napep har ka rage. A dole ya nuna wannan halin kasan a jinin su yake, babban mutum kamar wannan”
“Da Sarauta kawai zai fi ni, amman ina tabbacin be fini ilmi zamani ba, balle ma na addini, ji yadda yake kallon mutane warwatse”
Har cikin ransa yake maganar yana mai jin tsanar Abdool sosai. Namra kam bata ce komai ba hankalinta ma gaba ɗaya yana wani gurin, sam bata lura da kallon baƙuwar fuskar da mutanen dake shigowa cikin gidan suke mata ba. Murɗawar da taji mararta na mata ne yasa ta miƙe tsaye ta nufi ɗakinsu. Ƙasa ta zauna tana riƙe tsararta tana dannar baki alamar tana jin zogi sosai. Tun tana juriya a zaune har ta kasa ta kai kwance tana rumtse ido.
SAI MUN HAƊU BAYAN SALLAH 😍
INA NEMAN YAFIYAR DUK WANDA NA ƁATAWA, ƊAN A'ADAM AJIZINE. WATA ƘILA ZAN KAI BAYAN SALLAH, WATA ƘILA BA ZAN KAI BA. KU MIN ADDU'A IDAN LABARIN MUTUWA NA YA SAME KU KUMA KU YAFE MIN ALFARMAR ANNABIN RAHAMA S.A.W 🙏
[7/18, 8:12 PM] Khadeeja Candy♥: *63*
Kasa cin tuwon masarar Namra ta yi sai kawai ta sha ruwan tulun mai jiƙa maƙoshi kamar ruwan freezer.
Da fulatanci matar da ba zata wuce mai shekaru hansin da huɗu ba ta yi ma yaran magana akan ba su gaishe da Namra ba. Sai duk suka taso cikin ladabi suka gaisheta cikin su har da manyan ƴan'mata da kuma ƙanana. Da murmushi Namra ta amsa su sannan ta maida kanta ƙasa tana murza yatsun hannunta.
“Ban wayence ta ba”
Neina ta faɗa da yaren fulatanci tana kallon Saurayin. Shima da yaren ya maida mata da amsa.
“Ni ban san ta ba, kawai na ɗauko daga tasha ne, sai tace bata da gurin zuwa na taimaka mata shine na kawo ta nan”
“Amman Lamido taya zaka ɗauko yarinya baka santa, baka san inda ta fito ba? Kasan ko wace iri ce?”
“To Inna idan na bar ta can ban san halin da zata faɗa ba, kuma kin ga tace bata da kowa nan”
“Bata da kowa a nan zata zo? Lamido karka mana jaye-jaye muna neman abinda mu ka ci”
Da yaren fulatanci suke maganar, a zahirin gaskiya Namra bata jin yaren duk kuwa da kansacewar kakaninta fulani ne. Amman hakan be hanata fahimtar zancen ne suke ba.
“Ni ba macuciya ba ce lalura ce ta kawo ni nan, mijina ne ya sake ni kuma mahaifina ya riga daya gargaɗe ni akan karna kuskura na je gidansa, shiyasa na zo garin kaduna, amman idan ba ku yarda da ni ba ba zan zauna a nan ba, dan ba zan takura ku ba”
Wannan karon cikin halshen hausa Neinah ta ce
“Duniya ce a yanzu ake tsoron mutane, ba kowa ake yarda da shi ba, amman me kika aikatawa mahaifinki ya yi miki haka kuma a ina mahaifinki ya ke?”
“Mahaifina yana garin sokoto da zama, ni kuma a Katsina nake aure, sai dai ba zan iya labarta muku labarin aure na a yanzu ba, ina neman ku min lamani har zuwa gobe zan faɗa muku ba zan ɓoye ba”
Daga Neinah har Lamido shiru suka yi babu wanda ya iya cewa uffan, shi baya son yayi magana mahaifiyarsa ta ga kamar yayi mata katsa ladan ita kuma har yanzu bata gama gamsuwa da ita ba saboda halin da duniyar yau take ciki. Ɗaya daga cikin ƴan matan da suke zaune gurin ne ta taso ta dafa Namra tana murmushi ta ce
“Ba komai mun yarda da ke, ba ki yi kama da mugayen mutane ba, kuma na san ba zaki cutar da mu ba”
“Na gode”
Namra ta faɗa cikin muryar kuka.
“Uwani zuba mata ruwa ta yi salla”
Lamido ya faɗa cikin halshen fulatancin yayinda yake ƙoƙarin miƙewa tsaye ya jefar da ledar kifin dake hannunsa. Cikin ladabi ta tashi ya ɗauko mata buta ta miƙe mata sannan ta nuna mata banɗaki. Kamin namra ta yi alwala har ta shinfiɗa mata tabarma ta ɗosa mata sallaya sama ta aje mata carbi. Sannan ya ɗauko ɗayar tabarmar ta shimfiɗa mata gefe ɗaya ta ɗauko zanen gado ta shimfiɗa mata ta aje mata matashin kai. Sai ta dawo ta ɗauki abincin taje can kusa da tabarma ta aje mata.
Namra bata tashi daga saman sallayar ba sai da tayi salla insha'i sannan ta ƙara faɗawa Allah buƙatarta ta sai ta tashi ta koma inda Uwani tayi mata shimfiɗa ta kwanta. Babu abunda ya zo mata a rai sai gidan su, a ɗayan ɓangaren kuma idan ta tuna irin abunda Asim yayi mata sai ta ji kamar zuciyarta zata rabe biyu tsabar baƙinciki.
Kusa da ita Uwanin ta zo tayi shimfiɗa, ta kwanta, sauran yaran gidan kam sai da dare ƴa raba sannan suka nemi guri suka kwanta. Juyi Namra ta yi ta yi har safe ba yi bachi ba, abun nan da take jin ya tsaya mata a ƙahon zuciya yaƙi saukar mata har yanzu numfashinta ma daker take yinsa.
Bata san kan gidan ba amman haka be hanata tashi da wuri ba dan gabatar da salla azuba, sai duk sakkon tashin da tayi sai ta hango Lamido a ƙofar ɗayan ɗakin 6ana salla nafila, kallo ɗaƴa tayi masa ta ɗauke kai. Sai da tayi alwala tana daf da gamawa sai ga Neina ta tashi sai ta tashi dukan sauran yaran gidan har da waɗanda ba su wuce shekara bakwai ba zuwa takwas.
Bayan sun yi alwala dukan mazan sai suka tafi masallaci su kuma suka yi nasu salla a gida. Tun da Neina ta maida gabanta gaban bata juyo ba sai ta ta gama lazumin da take. Uwani ma ta maida gabanta gabas tana nata karatun ƙur'ane, ɗayar ma da tsawon su zai iya zuwa ɗaya da uwani ita karatun take, duk yaran masu ɗan tsawo da wayo kowa ya kama surar da yake yana karantawa. Ƙananen kawai suka koma bachi, sai ita kuma ta jingina jikin icecen dake tsakar gidan tana tasbihi da hannu. A hankali ta karkata kanta tana kallon Lamido take can ƙofar wani ɗaki yana nashi karatun cikin natsuwa da ƙira'ah mai daɗin saurara.
Hakan ya karantar ita irin tsantsar natsuwa da kuma ilmin da ƴaƴan gidan suke da shi, tun daga yaran su har ƙanana, ta samu kanta da ɗan sakewar zuciya tun bayan daga irin karatun ƙur'anen ta suke, daman sauraren karatun ƙur'ane yana saukar da natsuwa karanta shi kuma yana sa kwanciyar hankali da walwalah.
Bayan duk sun gama sai suka duk suka zo suka gaishe ta, ta amsa musu da far'ah sannan ta gaishe da Neina, kamin ta kalli Uwani dake mata murmushi ta ce.
“Ina kwana?”
“Lafiya ƙalau ai daman na ce sai dai ki gaishe ni, ba dai ni na gaishe ki ba, dan nayi ƙanwa da ke”
“Ni...?”
“Eh mana Lamido da kike gani ni nake binsa kin ga kuwa ni yayarki ce”
“Gaskiya ban yarda ba”
“Ta girme ki ƴar nan, jikin ne haka ba'a gane girman ta, yaran nan da kika gani duka ƴaƴanta ne”
Neina ta saka baki a maganar su da Namra tana murmushi. Namra tayi mata kallon mamaki.
“Amman ba za a ce ke ce kika haifesu ba, dube ki fa”
“Kowa haka yake cewa sai wanda ya sani, kin san jikin fulani”
“Allah sarki Allah ya shirya miki su”
“Amin. Maryam tashi ki ɗumama mana tuwon can”
Da sauri Namra ta kalli wacce uwani ta kira da Maryam ɗin tana murmushi.
“Marƴam sunan ƙanwata kenan, amman ita kam uwar masifa ce”
“Hmm wannan ma ai ba baya ba, ga shegen rashin kunya da kauɗi ɗuk ta tara kamar ya kashe ta”
Neina tayi dariya tana ƙoƙarin tashin tana faɗin.
“Maryam bar ni na gyara abu na da kai na, karki je ki min ƙire-ƙire da shi”
Uwani ta kalli Namra.
“Ke kan sai dai asiyo miki koko ko shayi ko? Naga ko jiya ba ki ci komai ba”
“A'a kawai bana jin cin abincin ne”
“Saboda me?”
“Damuwar da ke raina ba zata bar ni na ci abinci ba”
“Hmm idan kika ce zaki saka damuwa a ranki zaki samu matsala, kin gan ni nan damuwar da take rai na mai yawa ce, amman a haka na ke sakewa ina walwalah kamar komai”
“Wata ƙila damuwar ki bata kai tawa ba”
“Ko kuma ke na ce damuwarki bata kai tawa ba, kin ki yaran can? Ubansu yana nan da ransa amman babu ruwansa da mu, saboda mahaifiyarsa bata so na tun ina auren fari, sai take ganin kamar na mallake mata ɗa, kullum kalar masiba daban har na haifi yara biyar ina da cikin na shida can ne tasa ya sake ni, kuma tun daga lokacin babu ruwansa da cin mu da sham mu, balle sutura yau tsawon shekara biyu kenan, Lamido ne da Neina kawai suke hidima da mu, sai kuma ƴar sana'ar da na ke. Kin ga kuwa damuwarki bata kai tawa ba”
“Kowa dai irin ƙaddararsa, amman miyasa ba ku sashi kotu ba? Ai kamata yayi ace an karɓa muku
Showing 165001 words to 168000 words out of 280121 words
HILAL POV.
Jikin ƙofar ɗakin ya jingina yana kallonta da sauraren kukan da take rerawa. Rumgume hannayensa yayi yana tunanin ta ina zai fara. Ita kam bata ma san da shigowarsa ba, ta maida gaba gabas sai rusar kuka take.
Sauke hannayensa yayi ya nufi inta take zaune ya zauna gabanta yana kallon idonta.
“Yanzu abinda kike min adalci ne? Ki zauna kina kuka kin san yadda nake ji kuwa? Na rasa ɗa na ke kuma kin zauna a nan ki na kuka”
Ɗagowa tayi ta kalleshi
“Kai ɗa ka rasa, kuma kana da wasu, ni kuma miji na rasa”
“Ba ki rasa ni, kin san abinda na ke so da ke?”
Ta girgiza nasa kai.
“Zaki zauna nan for a while as zaman idda kamar yadda addini ya ce, ni zan je gida na faɗawa su Momi komai, wannan fushi na Hajiya na kwana biyu ne na nasan nan gaba kaɗan zata sauka, dole ne Hajiya tayi fushi Kalsoom saboda bata fahimce kamar yadda ni na fahimta ba”
“Ta yarda na zauna ne?”
“Bana jin zata hana, abunda na ke so dake ki yi mata uzuri kuma ki bata lokaci. Zan ɗauke ki muje gida anjima a can zan maida aure na”
Kai kawai ta ɗaga masa ta share hawayenta. Har ya mike tsaye sai kuma ya juyo ya kalleta ya ce
“Hajiya ta ce za a maida zaman makoki a can”
Nan ma kai ta ɗaga masa. Sai ya juya ya fice zuciyarsa babu daɗi. Zaune ya hango Hajiya a falon tana kallon ƙofar ɗakin Kalsoom daya fito fuskarta babu annuri. Kai ya girgiza cikin yanayin damuwa ya ƙaraso kusa da ita ya dafa kujera yana kallonta.
“Hajiya karki zama cikin iri surukan nan”
“Ba ƙoƙarin zama nake ba Hilal amman duk abunda yake gaskiya dole a faɗe shi, idan kai ta maka magani ni bata min ba, kuma Wallahi tallahi sai ka ƙara aure ko da kuwa bana numfashi, dole ka auri wacce zata riƙa maka ƴaƴanka mace ƙwarai ba mai ƙoƙarin kashesu ba, ni zan nema maka mata da kai na”
Tana kaiwa nan ta miƙe tsaye ta nufi ƙofar fita ranta na ƙololuwa a ɓaci. Shi dai da kallo ya bita har ta fice sannan ya saka hannyensa aljihu ya nufi ƙofar ransa a jagule.
RASHIDA POV.
A nasu gidan suke nasu amsar gaisuwar daban, duk da kasancewar waɗanda badu san aurenta ya mutu ba suka je can gidan gidan har sai idan sun tambaya ne sai ace musu gata nan. A harabar gidan suka shimfiɗa tabarma duk da kasancewar yaro ne hakan be hana ayi masu taro ba, sai dai ba irin zuwan nan ake na wuni ɗaya ba sai dai su zo su zauna na ƴan mintu su yi mata gaisuwar su wuce.
Tabarmarta daban tana zaune gefe ɗaya, ƴan gidan suna zaune gefe ɗaya. Idonta kumbura sosai duk wanda ya ganta sai ya tausaya mata wasu har da Allah ya isa suke mata duk a tunaninsu tana kuka ne saboda rashin ɗanta, sai dai a gurin Rashida abun ba haka yake ba, ita tana kuka ne saboda tunanin makomarta ganin asirinta ya tonu tun yanzu, tasan dole zamantakewar ta da ƴan gidan dole zai canja dan taga alamun hakan tun yanzu.
Misalin biyu da rabi Teema ta zo gidan gurin gaisuwa, sosai take son magana da Rashida amman babu dama saboda mutanen dake ta kai da kawo. Tana gurin kuma sai ga Asmee bayan ta fito gidan Hilal ta nufo nan.
Duk abunda ya faru a gidan sai da ta bawa Rashida labari. A nan Rashida take labarta musu maganar sakin da Hajiya tasa aka yi ma Kalsoom, dan su ba susan da maganar ba. Duk daɗi suka ji har mutenan dake gurin da kuma Asmee da basu san kan abun ba, amman ban da Teema da ita kan tasan komai.
“Amman Hajiya ta kyauta, daman ai ni za ci tuni zata sata shi aikata sakin, duk wanda yayi maka haka ga jika kan ai be cancanci zama da ɗan ka dan wata shi zata hara”
Gaskiya kam. Abunda suka mutanen suka masa da shi, sannan ƙananan maganganu suka biyo baya. Teema ta kada baki ta ce
“Gaskiya Hajiyar ta kyauta daman tun tun tun Hajiyarmu take cewa ya kamata ace Hajiya ta saka Hilal ya rabu da matar nan”
Rashid ta kalleta tana murza idonta.
“Hajiyar ku ta san ta ne?”
“Eh sukan haɗu a harkar siyasa wani lokacin, suna gaisawa sosai”
“Allah sarki”
Cewar Rashida. Sai kuma ta kawar da fuskarta tana kallon Asmee irin kallon nan da ita kaɗai ta san dalilinsa.
Teema kuma wani gurin take kallo tana wani tunanin na daban. Sai da aka kira la'asar sannan Teema ta wuce gida, Asmee kam a gidan tayi sallah sannan ta fice bakinta cike da magangu amman bat samu damar yi ma Rashida ba, ganin Safiya duk yasa ta tsargu, hakan yasa ta yi a zamar barin gidan.
Tashi Rashida tayi ta nufi cikin gidan rayuwarta duk babu daɗi saboda abunda take tunanin su momi sun fara nuna mta na ƙyama tsakanin jiya zuwa yau. Babu abunda ke ranta kamar ta bar musu gidan ta kama wani, tasan hakan zai fi mata kawanciyar hankali.
ASIM POV.
Yana ji a jikinsa akwai rashin dacewa a abinda suka aikata. Musamman yanzu da yake jin abu kamar ƙashi ya tsaya masa a takashinsa, ga wani zafi zafi da yake ji kamar an zuba masa barkono. Wasu ƙwayoyi dattijin Alhajin ya miƙa masa kusan kala huɗu ya ce ya sha, daman kamin su aikata sai da ya bashi wasu, tun jiya da dare suke abu ɗaya har yau da safe, sai yanzu nan ne Asim ya samu kansa. Sai a yanzu yake ƙarema Alhajin kallo, tabbasa ya sanshi a cikin manyan mutane. Amman duk misalin da yake masa jiya be gane shi ba sai yau. Daman tun lokacin daya ji sunansa ta ayyana a ransa ko shi ɗin ne, sai gashi mitumen ya fere ma tun daga biri har wutsiya.
“Na bawa Hajiya miliyan biyu ta baka, na siya maka mota ta miliyan uku. Idan ka riƙe min sirrina nan da ƴan wasu watan ni za'a far ƙirgaka a cikin manyan Alhazai. Zan wuce Abuja yau, idan na dawo zan samr ka a nan ko kuma nas Hajiya ta aika min kai a can sokoto”
Alhajin ya faɗa yana shafa fuskarsa. Asim kan daɗi har cikin kai, hankalinsa da zumuɗi gaba ɗaya sun tattara sun koma gida, babu abunda yake ransa kamar motar nan, a take ya ji duk jikinsa ya warysakr kamar babu wani ciwo jikinsa.
Be bar gidan ba sai da ya ci ya ƙoshi, sannan Alhajin yasa direba ya mai da shi gida.
Yana fita cikin motar sai ga Nably ta kira shi kamar ba zai ɗauka ba dan ya matsu ya ga motar da Alhajin yake ce masa. Sai dai farincikin dake ransa ba zai hana shi ɗaukar wayar Nabila ba.
“Hello my girly”
Ya faɗa cikin wani irin yanayi na shauƙi da annashuwa. Ita kaɗan ta karanci hakan a muryarsa.
“Da alama yau akwai labari mai daɗi a tare da kai..”
Ƙyalƙyalewa ya yi da dariya.
“Labari mai daɗi, na kusa zuwa Abuja na gan ki”
“Nikam ba zan iya jura har jibi ba, akwai birthday friend ɗita da za'ayi yanzu take faɗa min ni kuma na ce dole zan zo ko dan kai”
“Wow Amman gaskiya kin kyauta min, i can't wait to see you”
“I can't wait to see you too, sorry zan katse kiran, Momy na kira na zan kira ka idan mun gama”
Hajiya Sadiya ce ta fito waya a hannunta tana faman kiran waya, fuskarta ɗauke da murmushi, ganin Asim.
Shima Murmushin ya mayar mata ya doshi inda take cike da zumuɗi, sai kawai ta jefa mishi keys ɗin mota ta nuna masa motar tana cigaba da murmushi sai ta nufi wani ɓangaren na gidan tana amsa wayar da aka yi picking yanzu.
Wani irin tsalle Asim ya daga tsinkawo motar da yayi, da gudu ya doshi gurin yana wani irin gurnani kamar mahaukaci.
NAMRA POV.
Abdool na fita Uwani ta karɓi takardar hannun Neine ta duba, tana gani tasan cak ne sai dai bata iya gane ko nawa aka rubuta ba, kasancewar ilminta be kai har can ba, zero da ta ga a rubuce sun mata yawan karantawa.
“Minene?”
Neine ta tambaya, cike da son sanin abunda yake ciki.
“Ni wallahi ban gane kan abun ba, amman dai takardar kuɗi ne”
Uwani ta faɗa, dai Namra ta kai hannu ta karɓa tana dubawa.
“Miliyan ɗaya ne cif”
Uwani da Neina sun daki ƙirji tare da zaro ido.
“Miliyan ɗaya?”
Duk mutane da suka shigo cikin gidan duk ko wanne sai da ya riƙe baki, har ga Allah yawan kuɗin suke gani, Namra kam bat ɗauke su a bakin komai ba, abun ka da wanda yasan kan abu. Wani dogon tsaki Lamido yaja ya kawardar da kansa.
“Sam sam sam mutumen be san darajar mutane ba Wallahi”
Aiko yayi ƙoƙori irin wannan kuɗin haka! Ƴaƴan manyan mutane da da zasu taka rai su bar mutum balle har ya baka wannan kuɗin. Shine abunda mafi yawan matan maƙotan gidan suke ta faɗa.
“Ai dole yayi min mana, tun da ya lalata min Napep dole ya bada kuɗin jinya dan siyen wata”
Neine ce ta saka bakinta wannan karon tana nuna Abdool ya kyauta iya kyautawa.
“Wallahi da wani can ba zai kula ka ba Abdool ba gasu nan muna gani ba, wannan kuɗin ka siye sabon Napep har ka rage. A dole ya nuna wannan halin kasan a jinin su yake, babban mutum kamar wannan”
“Da Sarauta kawai zai fi ni, amman ina tabbacin be fini ilmi zamani ba, balle ma na addini, ji yadda yake kallon mutane warwatse”
Har cikin ransa yake maganar yana mai jin tsanar Abdool sosai. Namra kam bata ce komai ba hankalinta ma gaba ɗaya yana wani gurin, sam bata lura da kallon baƙuwar fuskar da mutanen dake shigowa cikin gidan suke mata ba. Murɗawar da taji mararta na mata ne yasa ta miƙe tsaye ta nufi ɗakinsu. Ƙasa ta zauna tana riƙe tsararta tana dannar baki alamar tana jin zogi sosai. Tun tana juriya a zaune har ta kasa ta kai kwance tana rumtse ido.
SAI MUN HAƊU BAYAN SALLAH 😍
INA NEMAN YAFIYAR DUK WANDA NA ƁATAWA, ƊAN A'ADAM AJIZINE. WATA ƘILA ZAN KAI BAYAN SALLAH, WATA ƘILA BA ZAN KAI BA. KU MIN ADDU'A IDAN LABARIN MUTUWA NA YA SAME KU KUMA KU YAFE MIN ALFARMAR ANNABIN RAHAMA S.A.W 🙏
[7/18, 8:12 PM] Khadeeja Candy♥: *63*
Kasa cin tuwon masarar Namra ta yi sai kawai ta sha ruwan tulun mai jiƙa maƙoshi kamar ruwan freezer.
Da fulatanci matar da ba zata wuce mai shekaru hansin da huɗu ba ta yi ma yaran magana akan ba su gaishe da Namra ba. Sai duk suka taso cikin ladabi suka gaisheta cikin su har da manyan ƴan'mata da kuma ƙanana. Da murmushi Namra ta amsa su sannan ta maida kanta ƙasa tana murza yatsun hannunta.
“Ban wayence ta ba”
Neina ta faɗa da yaren fulatanci tana kallon Saurayin. Shima da yaren ya maida mata da amsa.
“Ni ban san ta ba, kawai na ɗauko daga tasha ne, sai tace bata da gurin zuwa na taimaka mata shine na kawo ta nan”
“Amman Lamido taya zaka ɗauko yarinya baka santa, baka san inda ta fito ba? Kasan ko wace iri ce?”
“To Inna idan na bar ta can ban san halin da zata faɗa ba, kuma kin ga tace bata da kowa nan”
“Bata da kowa a nan zata zo? Lamido karka mana jaye-jaye muna neman abinda mu ka ci”
Da yaren fulatanci suke maganar, a zahirin gaskiya Namra bata jin yaren duk kuwa da kansacewar kakaninta fulani ne. Amman hakan be hanata fahimtar zancen ne suke ba.
“Ni ba macuciya ba ce lalura ce ta kawo ni nan, mijina ne ya sake ni kuma mahaifina ya riga daya gargaɗe ni akan karna kuskura na je gidansa, shiyasa na zo garin kaduna, amman idan ba ku yarda da ni ba ba zan zauna a nan ba, dan ba zan takura ku ba”
Wannan karon cikin halshen hausa Neinah ta ce
“Duniya ce a yanzu ake tsoron mutane, ba kowa ake yarda da shi ba, amman me kika aikatawa mahaifinki ya yi miki haka kuma a ina mahaifinki ya ke?”
“Mahaifina yana garin sokoto da zama, ni kuma a Katsina nake aure, sai dai ba zan iya labarta muku labarin aure na a yanzu ba, ina neman ku min lamani har zuwa gobe zan faɗa muku ba zan ɓoye ba”
Daga Neinah har Lamido shiru suka yi babu wanda ya iya cewa uffan, shi baya son yayi magana mahaifiyarsa ta ga kamar yayi mata katsa ladan ita kuma har yanzu bata gama gamsuwa da ita ba saboda halin da duniyar yau take ciki. Ɗaya daga cikin ƴan matan da suke zaune gurin ne ta taso ta dafa Namra tana murmushi ta ce
“Ba komai mun yarda da ke, ba ki yi kama da mugayen mutane ba, kuma na san ba zaki cutar da mu ba”
“Na gode”
Namra ta faɗa cikin muryar kuka.
“Uwani zuba mata ruwa ta yi salla”
Lamido ya faɗa cikin halshen fulatancin yayinda yake ƙoƙarin miƙewa tsaye ya jefar da ledar kifin dake hannunsa. Cikin ladabi ta tashi ya ɗauko mata buta ta miƙe mata sannan ta nuna mata banɗaki. Kamin namra ta yi alwala har ta shinfiɗa mata tabarma ta ɗosa mata sallaya sama ta aje mata carbi. Sannan ya ɗauko ɗayar tabarmar ta shimfiɗa mata gefe ɗaya ta ɗauko zanen gado ta shimfiɗa mata ta aje mata matashin kai. Sai ta dawo ta ɗauki abincin taje can kusa da tabarma ta aje mata.
Namra bata tashi daga saman sallayar ba sai da tayi salla insha'i sannan ta ƙara faɗawa Allah buƙatarta ta sai ta tashi ta koma inda Uwani tayi mata shimfiɗa ta kwanta. Babu abunda ya zo mata a rai sai gidan su, a ɗayan ɓangaren kuma idan ta tuna irin abunda Asim yayi mata sai ta ji kamar zuciyarta zata rabe biyu tsabar baƙinciki.
Kusa da ita Uwanin ta zo tayi shimfiɗa, ta kwanta, sauran yaran gidan kam sai da dare ƴa raba sannan suka nemi guri suka kwanta. Juyi Namra ta yi ta yi har safe ba yi bachi ba, abun nan da take jin ya tsaya mata a ƙahon zuciya yaƙi saukar mata har yanzu numfashinta ma daker take yinsa.
Bata san kan gidan ba amman haka be hanata tashi da wuri ba dan gabatar da salla azuba, sai duk sakkon tashin da tayi sai ta hango Lamido a ƙofar ɗayan ɗakin 6ana salla nafila, kallo ɗaƴa tayi masa ta ɗauke kai. Sai da tayi alwala tana daf da gamawa sai ga Neina ta tashi sai ta tashi dukan sauran yaran gidan har da waɗanda ba su wuce shekara bakwai ba zuwa takwas.
Bayan sun yi alwala dukan mazan sai suka tafi masallaci su kuma suka yi nasu salla a gida. Tun da Neina ta maida gabanta gaban bata juyo ba sai ta ta gama lazumin da take. Uwani ma ta maida gabanta gabas tana nata karatun ƙur'ane, ɗayar ma da tsawon su zai iya zuwa ɗaya da uwani ita karatun take, duk yaran masu ɗan tsawo da wayo kowa ya kama surar da yake yana karantawa. Ƙananen kawai suka koma bachi, sai ita kuma ta jingina jikin icecen dake tsakar gidan tana tasbihi da hannu. A hankali ta karkata kanta tana kallon Lamido take can ƙofar wani ɗaki yana nashi karatun cikin natsuwa da ƙira'ah mai daɗin saurara.
Hakan ya karantar ita irin tsantsar natsuwa da kuma ilmin da ƴaƴan gidan suke da shi, tun daga yaran su har ƙanana, ta samu kanta da ɗan sakewar zuciya tun bayan daga irin karatun ƙur'anen ta suke, daman sauraren karatun ƙur'ane yana saukar da natsuwa karanta shi kuma yana sa kwanciyar hankali da walwalah.
Bayan duk sun gama sai suka duk suka zo suka gaishe ta, ta amsa musu da far'ah sannan ta gaishe da Neina, kamin ta kalli Uwani dake mata murmushi ta ce.
“Ina kwana?”
“Lafiya ƙalau ai daman na ce sai dai ki gaishe ni, ba dai ni na gaishe ki ba, dan nayi ƙanwa da ke”
“Ni...?”
“Eh mana Lamido da kike gani ni nake binsa kin ga kuwa ni yayarki ce”
“Gaskiya ban yarda ba”
“Ta girme ki ƴar nan, jikin ne haka ba'a gane girman ta, yaran nan da kika gani duka ƴaƴanta ne”
Neina ta saka baki a maganar su da Namra tana murmushi. Namra tayi mata kallon mamaki.
“Amman ba za a ce ke ce kika haifesu ba, dube ki fa”
“Kowa haka yake cewa sai wanda ya sani, kin san jikin fulani”
“Allah sarki Allah ya shirya miki su”
“Amin. Maryam tashi ki ɗumama mana tuwon can”
Da sauri Namra ta kalli wacce uwani ta kira da Maryam ɗin tana murmushi.
“Marƴam sunan ƙanwata kenan, amman ita kam uwar masifa ce”
“Hmm wannan ma ai ba baya ba, ga shegen rashin kunya da kauɗi ɗuk ta tara kamar ya kashe ta”
Neina tayi dariya tana ƙoƙarin tashin tana faɗin.
“Maryam bar ni na gyara abu na da kai na, karki je ki min ƙire-ƙire da shi”
Uwani ta kalli Namra.
“Ke kan sai dai asiyo miki koko ko shayi ko? Naga ko jiya ba ki ci komai ba”
“A'a kawai bana jin cin abincin ne”
“Saboda me?”
“Damuwar da ke raina ba zata bar ni na ci abinci ba”
“Hmm idan kika ce zaki saka damuwa a ranki zaki samu matsala, kin gan ni nan damuwar da take rai na mai yawa ce, amman a haka na ke sakewa ina walwalah kamar komai”
“Wata ƙila damuwar ki bata kai tawa ba”
“Ko kuma ke na ce damuwarki bata kai tawa ba, kin ki yaran can? Ubansu yana nan da ransa amman babu ruwansa da mu, saboda mahaifiyarsa bata so na tun ina auren fari, sai take ganin kamar na mallake mata ɗa, kullum kalar masiba daban har na haifi yara biyar ina da cikin na shida can ne tasa ya sake ni, kuma tun daga lokacin babu ruwansa da cin mu da sham mu, balle sutura yau tsawon shekara biyu kenan, Lamido ne da Neina kawai suke hidima da mu, sai kuma ƴar sana'ar da na ke. Kin ga kuwa damuwarki bata kai tawa ba”
“Kowa dai irin ƙaddararsa, amman miyasa ba ku sashi kotu ba? Ai kamata yayi ace an karɓa muku
Book Chapters
Chapter 1Chapter 2Chapter 3Chapter 4Chapter 5Chapter 6Chapter 7Chapter 8Chapter 9Chapter 10Chapter 11Chapter 12Chapter 13Chapter 14Chapter 15Chapter 16Chapter 17Chapter 18Chapter 19Chapter 20Chapter 21Chapter 22Chapter 23Chapter 24Chapter 25Chapter 26Chapter 27Chapter 28Chapter 29Chapter 30Chapter 31Chapter 32Chapter 33Chapter 34Chapter 35Chapter 36Chapter 37Chapter 38Chapter 39Chapter 40Chapter 41Chapter 42Chapter 43Chapter 44Chapter 45Chapter 46Chapter 47Chapter 48Chapter 49Chapter 50Chapter 51Chapter 52Chapter 53Chapter 54Chapter 55Chapter 56 Chapter 57Chapter 58Chapter 59Chapter 60Chapter 61Chapter 62Chapter 63Chapter 64Chapter 65Chapter 66Chapter 67Chapter 68Chapter 69Chapter 70Chapter 71Chapter 72Chapter 73Chapter 74Chapter 75Chapter 76Chapter 77Chapter 78Chapter 79Chapter 80Chapter 81Chapter 82Chapter 83Chapter 84Chapter 85Chapter 86Chapter 87Chapter 88Chapter 89Chapter 90Chapter 91Chapter 92Chapter 93Chapter 94