yaushe zaki dawo, wai yace ke kika ce ba zaki dawo ba”
“Baya son ya faɗa miki ne, saboda yanzu baya so na Kalsoom yake so, idan har kina son na dawo dole ne ki riƙa yin abunda na faɗa miki, idan kina irin haka shine sai za ya tausaya muku yace na dawo”
“Amman ita bata jin daɗin abunda nake mata”
“Ke kina jindaɗin data koreni?”
Ta girgiza kai alamar a'a.
“Idan baki yin abubuwan da nake faɗa miki ke ma wata rana sai tasa Daddy ki ya kore ki, sai ta mallake gidan daga ita sai nata ƴaƴan”
Ezzah ta.yi shiru tana tunani sai kallon ƴan makarantar su take masu kai wa da dawowa.
“Ezzah dik duniyar nan baki da kowa kamar ni, duk wacce zata so ki abaya na take, kuma ƙarya Kalsoom take tace tana son ku, tana nuna muku haka ne dan ta mallaki Daddy, yanzu kina jindaɗi zama da ita? Bata dukan ki? Lokacin da ina nan Daddy ki yana miki faɗa?”
Duk ta girgiza kai.
“Dole ne kiyi mata abunda na saki dan na samu na koma gurin Daddy ku, na yi muku alƙawari ddana koma kullum gida zan riƙa zama ba zan sake fita aiki ba”
“Da gaske?”
“Wallahi, dan haka ki cigaba da abunda kike, har abunda ban saki ba ma ki aikata indai kinsa wanda zai hassalata ne”
“Zan riƙa yi”
“I Love you”
“I Love you too”
Rashida ta rumgume ta kamar da gayya. Sannan ta ciro chocolates da Sweet Candy dake jakarta ta miƙa mata, ta kuma bata ɗari biyu na kashewa sannan ta tashi ta fita.
Daga nan Asibiti ta nufa. Yau ce rana ta farƙo da zata fara bin shawarar likita wajen ɗora kanta akan magani, dan samun tsawaita rayuwarta kamar yadda likita ya faɗa mata.
NAMRA POV.
Two months later....
A zuwa yanzu babu wata matsala da take fuskanta a gurin Asim, tun bayan da aka sallamo daga asibiti, jiki sai ƙara sauƙi yake yana mirmirjewa kamar ba shi ba.
Duk wani mugun ƙudiri dake cikin ransa, ya danne ya barwa zuciyarsa, dan yasan babu yadda zai yi da Namra a yanzu sai kallo, idan yace zai rabu da ita matsala ne a gare shi tun da baya sgi kuɗin auren wata, shi dai yanzu ba shi da wani buri sai na yayi kuɗi.
Irin yadda yake nanata maganar har tsoro abun yake ba Namra, ahi dai yayi kuɗi dai yayi kuɗi. Haka Namra zata zauna tana masa nasiha akan duniya da abunda ya ke cikinta, amman sai dai ya kalleta kawai ya nuna mata wa'azin ya ratsashi bayan a ƙasan zuciyarsa kuma mamakinta yake, wai ita zata zaunar da shi ta nuna masa illar kuɗi, bayan ga ubanta can ya tara su ita kuma da su take tinƙaho.
Sam baya ganin wahalar da take da shi, bata saba wanki ba ko a gidansu amman haka zata zauna ta wanke nata tufafin ta wanke nasa, ta kai masa ruwanka, amman kullum sai ta matsa masa yake wanke dan ganin yake kamar tana takurasa, Allah ya zuba masa ƙuiyar motsa jikinsa indai a bangaren aiki ne.
Maganganun da Namra take masa akan rayuwa da neman kuɗi da yake magana a ko yaushe sai ya ƙara riƙe ta a zuciyarsa, wai bata son sa da alheri ta fi son yayi dauwama cikin baƙin ciki da damuwa tun da ita tana da mafita.
Ga matsalar da ci masa tuwo a ƙwarya a yanzu, wacce yake ganin kamar da ganganci ne tayi masa haka dan bata son haihuwa da shi. Ita kanta tana nadamar sanar da shi da tayi robar da aka saka mata, sai dai babu yadda zatayi dole ce tasa ta faɗa masa, tun kullum sai ya tunkareta kuma jinin har yau be tsaya mata ba, daman wani lokacin haka robar yake yi mutane dan ta ji maƙonta suna firar lokacin data shiga gidan su ƴar fulani.
Ta aika tambayarta ga wani malami ya amsa mata da cewar duk jinin daya zube bana haila bane ya zama kamar jinin rashin lafiya ne dan haka ba zatayi fashin sallah ba balle azumi.
Hakan yasa robar ma sai ta fita ranta dan ita bata son abunda zai riƙa rikitar mata da addini, hakan yasa ta yanke shawawar zuwa a cire mata robar in ya so sai tasha ƴaƴan zurma, dan maƙociyarta nan ta faɗa mata indai har ta sha ƴaƴan zurma ɗaya yana matsayin shekara ɗaya ne idan kuma tasha biyu kuma yana matsayin shekara biyu ne.
Sai dai ba kowa yake yi ma aiki ba, amman ta ga wani a whatsapp wanda Khadeeja Candy take tallah shi kam idan an sha tabbas zai maka aiki, matsalar kawai ita ba a garin take ba, kuma tana buƙatar ta bincike dan ta jin yadda abun an ce mata texted and trusted ne. Ga Kuma Asim ya dame ta da maganar kullum, dan shi gani yake kamar da biyu tayi haka.
Yau wake ta dafa da shinka (rice and beans) ta saka mai da taji, daman yana cikin favorite na ta, amman Asim duk lokacin data dafa sai ya riƙa ƙin ci yana ganin kamar tana haka ne dan karta kashi kuɗi da yawa tayi musu abinci mai kyau.
Shi yanzu har ya matso jikinsa ya koma.yadda yake ya fara fita neman kuɗi, dan ya ayyana a ransa kuɗinta zai ranta ya fara sana'ar, har hango kansa yake ya zama wani Alhaji.
Kullum firar da ita kenan, yau bayan ya gama complaint ɗin baya son wake, ya ɗasa mata firar idan yayi kuɗi, ba aza a ƙara cin wake a gidansa ba.
Namra ta yi murmushi tana mamakin yadda idom Asim ya bude haka.
“Asim kenan. Idan ma zaka yi roƙon baka cewa Allah ya baka halalinka, kawai dai kai kayi kuɗi”
“Wallahi sai na yi kuɗi Namra, Wallahi Wallahi sai nayi kuɗi, kawai naji sauƙi ne”
»“Ban ce ba zaka yi kuɗi ba, Amman yana da kyau ka riƙa cewa Inshallah kuma ka riƙa roƙon halak, saboda gudun sherin zuciya, idan Allah ya rubuta zaka yi kuɗi zaka yi ko da kuwa kama kwance gida ne sai sun tararda kai, saboda an riga an rubuta zaka yi kuɗin sai dai idan kayi gajin haƙuri zaka iya samun ta hanyar da be kamata ba”
“Namra kina bani mamaki, ke yanzu da ba dan kuɗi ba iyayen ki ai ba zasu wulaƙanta ni ba”
“Wulaƙanci kamar ya?”
“Wulaƙanci ne mana, saboda an mai dani talaka wanda ba shi da amfani shiyasa aka saka miki wannan robar ba tare da sanina ba”
“Ba haka bane, kawai matsala ce ta taso kuma likitan yace dole ne nayi planning”
“To Allah ya kyauta, amman ko ma minene ai nafi kowa kusanci da ke, taya za'ayi ki yi min haka”
“Asim matsala ce fa kai yanzu kana son na samu ciki ya zo ya zube ko kuma nayi ta wahala?”
“Hmm kina dai ganin kamar ba zan iya hidama dake ba ke da abunda zaki haifa shiyasa kuka ɗauki wannan matakin”
Ta aje kofin ruwan dake hannunta
“Ba zan ɗauki halin nan naka ba Asim, babu yadda zaka riƙa cin zarafina dana iyayena, kullum mune marar mutumci a idonka, duk abunda muka maka baka gani, na sadaukar da yawa Asim, har inda be kamata na sadaukar ba na sadaukar amman baka gani”
Kamar mai jira sai kawai yayi cikinta da masifa.
“Me kika min ke da iyayenki? Me kika sadaukar min? Ran ki? Ko lafiyarki? Kullum da kin tadhi magana kin sadaukar kin sadaukar tun da na aure ki me na ƙara shi in ɓa tsiya ba? Ɗan abunda na tara dik ya ƙara na zo na kwanta a asibiti jiyan babu wani ɗan'uwanki da ya ɗauki wani abu ya ba ni, an so na mutu ban mutu ba shine yanzu zaki fara buɗe min wani babin na rayuwa, kina da kuɗi a jikin ki amman saboda baƙin ciki ba zaki fitar aci ba sai dai a mutu? To Wallahi Asim ikon Allah ne, duk wani mai son ganin bayana sai dai ni naga bayansa”
“Magana kake irin wannan zancen kamar mai magana da maƙiyansa, maitarka ta kasa ɓoyuwa har sai ta fito fili? Kuɗina sana'ah zan yi da abu na, dan ba zan zauna kullum ni ce biyar dangi a bani ba, kuma Allah be ɗora min alhakin ciyar da kai ba, ni aka ce ka ciyar ka tufatar, yanzu ka fito a siffar ka sak Asim daman dan dukiyar gidan mu ka aure ni ko, amman sai ka nuna mik baka son komai sai ni, ashe zagon ƙasa kake min ka ɗauki halin samarin zamani ka ɗorawa kan ka, masu auren jari...”
Wani irin mahaukacin mari ya kifa mata ya rufe ta da duka kamar ma dukan namiji.
Shuri yake aika mata ta ko'ina tana cigaba da dukan jikinta kamar ƴarsa.
Dukanta yayi sai da yaji ya daki iya kalaman data faɗa masa sannan ya sassauta mata ya miƙe tsaye yana ɗingishi.
“Kuma Wallahi kije aci miki wannan robar ko kuma wallahi na lahira ya fiki jindaɗi”
A fusace ya juya ya bar ɗakin. Kuka tayi har ta gode Allah sannan ta tashi zaune tana cigaba da hawaye.
Sai ynz take tabbatar da tayi kuskuren aure, ta auri mutumen da be san darajarta ba, mutumen da be san kowa ba sai kansa. Daman haka halin Asim yake abu kaɗan sai duka.
Ta share hawayenta dan itama kanta tasan ba kuka bane abunda take buƙata, sam Asim be cancanci hawayenta ba, a yanxu ta san wa take aure dole ne kuma ta shirya zama da shi. Bata da buƙatar kokawa kowa damuwarta ita ya kamata ta gyara zaman aurenta da kanta.
Ta tatsu iya tatsuwa dan haka yanzu ba zata sake bari guminta ya zuba akan Asim ba.
ASIM POV.
Ta ƙarfen dake hannunsa yana dafawa ya fito gate, sai huci yake kamar wani zaki.
Yau ji yake kamar ace ya rumtse ya bude ya gansa yayi kuɗi, ta yadda zai jidaɗin rayuwarsa. Sai yanzu yake nadamar karatunsa daya bari daman can yayi tunanin ko zai samu wani abun a gurin iyayen Namra shiyasa ya baro garin su da ita ta yadda nan zai ta cin karensa ba babbaka sai yayi ta aikata tana samu matsa kuɗi, amman yanzu ya fahimci itama maƙetaciya ce kuma bata sonsa da alheri.
Gashi yanzu ko sana'ah zai yi yasan ba zai samu kuɗi a tashi ɗaya ba, amman idan yana da karatunsa zai iya samun babban aiki.
“Mtssssss aiko karatun na yi ba aiki zan samu ba tun da nigeriyar sai da gata, su kuma waɗannan iyayen nata matsiyata ne ba aiki za su samomin ba, aiko wallahi duk wahalar da zan sha tare da ƴar su zan shata, sai na yi kuɗi tana ganin zata huta kawai na aikata gidan su.
Har ni za'ayi ma mugunta, ai ko sai na yi muku baƙin ciki dan haihuwa yanzu za a fara”
Ya ƙarasa maganar yana kallon Mardiya data doso gurin tana takawa a hankali. Tun daga kan ƙafafunta yake kallonta har zuwa fuskarta.
Shi dai kam yana son farar mace ko ba komai farar mace ko kallonta kawai kayi zata burgeka kuma zakaji kana son ta.
Tsaɓanin Namra da take black beauty, wace yake ganim a yanzu she's not his type, sai dai duk da haka ya ƙudiri aniyar sai ya kai ga jikin cos he need someone near him.
Ba zai je ya kashe kanshi da desires ba, weather blood ɗin ya tsaya mata ko be tsaya ba babu ruwansa yau zai yi yadda yake so da ita.
“Ina wuni”
Mardiya ta gaisheshi cikin ƙirsa da kisinsina. Shi kuma ya amsa mata a far'ah har kunne.
“Lafiya ƙalau Mardiya ya gida”
“Lafiya ƙalau ya jikin na ka?”
“Alhamdulillah”
“Allah ƙara sauƙi”
“Amin na gode”
Da kallo ya bita har ta ɓace masa da gani sannan ya dawo hanyyacin yana yaba kyauwon surarta a zuciyarsa.
KALSOOM POV.
Ita kanta yanzu ta rasa gane kanta balle Hilal da yanzu ya saka mata ido, dan duk ta barkace masa abu kaɗan masifa ta inda take shiga ba ta nan take fita ba.
Da gangan zata ƙi masa girki ko kuma tasa shi gaba tayi masa kuka, bayan be mata komai ba. Tun daga lokacin ya fahimcin akwai abunda yake cikin matarsa, daman can sha'anin ɓacewar cikin nan nata ya bashi mamaki, ga kuma jinin daya ƙi tsaya mata wajen wata huɗu kenan, babu irin maganin da be bata ba amman abun be tsaya ba, tun yana ganin abun kamar wasa har ya fara tsorota da lamarin.
Ita kanta tasan yanzu wannan jinin ya wuce haila ko zubar ciki ya zama na rashin lafiya, kuma ta san hukunci mai jinin rashin lafiya.
Shi kuma jinin rashin lafiya, jini ne da yake zuba ba a lokacin al'ada ba, daga wata jijiya da ake kira da azil. Al'amarin wanda take wannan jinin yana da rikitarwa, saboda kama da jinin haila yake. Idan mace ta zanto jini yana zuba daga gareta jo yaushe, ko kuma a mafi yawan lokaci wanenen zata ɗauka jinin haila da na rashin lafiya? Domin ita mai jinin rashin lafiya hukunce mai tsarki na gareta, kuma irin wannan hukumci shine a gurin mace mai jinin planning irin wanda yake zuba idan anyi planning dan ya zama kamar jinin rashin lafiya.
*Hali na farko* Ta zanto tana da masaniyar kwanakin hailarta, kamin jinin rashin lafiya ya same ta. Misali idan tana jinin haila a kwana biyar ko takwas a farkon wata ko tsakiyarsa, watau tasan kwanakin hailarta da lokacinta. To ita wannan zata zauna gwargwadon kwanakin hailarta ta bar sallah da azumi ta bawa kanta hukunci mai haila. Idan kwanakin sun wuce sai haila sun wuce, sai tayi wanka tayi sallah ta ɗauki jinin da ya cigaba da zubar mata da zuba a matsayin jinin rashin lafiya. Dalili shine faɗin Annabi S. A. W, ga Ummu Habiba : ki zauna gwargwadon kwanakin da hailarki take tsare ki, sannan ki yi wanka ki yi sallah. Muslim ya ruwaito shi. Da kuma faɗarsa Annabi ga Fatima Bintu Abi Hubaish: Wannan jinin jijiya ne, ba haila ba ne. Idan hailarki ta zo sai ki. Bar sallah. Bukhari da Muslim suka ruwaito shi.
Idan iyakar kwanakin hailarta ya zo kamar yadda bayani ya gabata, to wajibi ne a gareta tayi wanka. Kuma wanke gabanta domin ta gusar da abinda yake zuba yayinda ta zo yin kowace salla. Kuma tayi ƙunzugu da auduga (pad) ko abu mai kama da ita wanda zai hana kwararar jinin, sannan tayi alwala daga lokacin kowace salla saboda faɗin Annabi : Ta bar salla a cikin kwanakin hailarta, sannan ta yi wanka kuma ta yi alwala ga kowace salla. Abu Dawud da Ibn Maja da tirmizi ne suka ruwaito shi.
Hakan yasa Kalsoom ta cigaba da salla da duk sauran ibadarta, sai dai har gobe halinta be canja ba a kan Hilal idan yana cikin gidan ji take babu wanda tsana a duniya sai shi. Yara kuma abu kaɗan ta dake su, tun yana haƙuri har abun ya fara isarsa dan yanzu shi da ita basa shan inuwa ɗaya, akan yaransa.
Gashi Ezzah kullum uwarta ƙara hure mata kunne take tana koya abubuwan da take ganin kamar abun ƙwarai ne, bayan ita bata san tana lalata tarbiyar ƴarta bane kawai.
Duk ranar da ba makaranta zai kwashi yaransa ya kai su gidan Hajiyarsa. Hajiya ta lura da yanayin ɗanta damuwa ta bayyana a fuskarsa ga ramar dake jikinsa, yadda ma yake yawan kawo yaran akai-akai ta san ba lau ba.
“Wai likita akwai abunda yake damun ka ne?”
Ajiyar zuciya ya sauke, yana aje plate ɗin abincin da ke hannunsa.
“Wallahi Hajiya ni ban san matsalar, daga ina take ba ma, Kalsoom ce yanzu kwata-kwata na rasa ma gane kanta, indai ina gida bana da kwanciyar hankali, sai kuka zara riƙa min tana masifa”
“Me ya haɗa ku?”
“Ba abunda na haɗa mu haka kawai zata riƙa min masifa sai kuka, kin san cikinta ya ɓace”
“Ya ɓace kamar ya?”
“Jini kawai ta ga yana mata zuba, sai aka yi hoto aka ga babu cikin kwata-kwata a cikin ta, amman jinin har yau be tsaya mata ba, yau kusan wata huɗu kenan”
“Subhanallahi, me ya same ta haka ne?”
“Wallahi nima van sani ba? Na rasa gane kanta”
“Abun kamar lamarin iska shi kesa ciki ya ɓata, ko kuma sihiri”
“Sai maganar saki ta ke min, ita dai na rabu da ita na ta huta”
“Kasan me? Ka samu ƙwarya mai tsarki da za'afaran, sai a ruɓuta suratul Yasin da surar wa'ƙia da fatiha da ƙulhuwallahu ahad da ƙula'uzai da Ayatul kursiyu da kuma amanar rasulu har zuwa ƙarshe da suratul baƙara da ayar : ƙul-a-Allahu azine lakum am alallahi taftarun (10:59) to idan an rubuta sai a karya kummallo da shi idan ta sha sai ta samu dabino ajwah sai kayi mata tawada nan da Al-zaitul muraƙƙa sai ta cinye sauran kuma rubutun kuma ta shafe jikinta, da iKon Allah indai sihiri ne ko aljanu ko wane iri ne zai rabu da ita”
“Amman Hajiya irin wannan ai sai dai kisa waki ya rubuta mata a nan sai na kai mata ta sha”
“To zan nemi wanda zai rubuta mata inshallah, amman wannan ko Rashida ai zata iya ƙulle-ƙulle ganin ta ɓata zamanku”
Yayi ƴar dariya.
“Sai dai ko iska ne, amman ai Rashida bata da irin wannan halin”
“Hmmm Hilal ba a shedun mace, yanzu kasa ran tayi maka wannan abun?”
Ɓacin rai ne shimfiɗe a fuskarsa, idanunsa sun rine zuciyarsa har wani tafarfasa take saboda faɗan d Mai Martaba yake masa.
Har Mai Martaba yayi ya gama Abdool be ce uffan ba, dan yasan akan gaskiya yake faɗansa, kamar yadda Ummi take masa a kullum.
“Ƙanen ka Babana ƙanenka ace yayi aure har ya haihu kai ba kayi ba, kullum girma ƙara tunkararka yake amman baka ganewa, shekarun tafiya suke Babana yanzu da ace kana da mata da wannan abun zai faru da kai? Sai dai ka zauna a gida ta girka maka, ko mutuwa kayi ba mu da abunda zamu kalla mu tuna da kai sai hoton ka, ai ko mutuwa kayi ka bar mai maka addu'ah ka more, rashin
Showing 111001 words to 114000 words out of 280121 words
“Baya son ya faɗa miki ne, saboda yanzu baya so na Kalsoom yake so, idan har kina son na dawo dole ne ki riƙa yin abunda na faɗa miki, idan kina irin haka shine sai za ya tausaya muku yace na dawo”
“Amman ita bata jin daɗin abunda nake mata”
“Ke kina jindaɗin data koreni?”
Ta girgiza kai alamar a'a.
“Idan baki yin abubuwan da nake faɗa miki ke ma wata rana sai tasa Daddy ki ya kore ki, sai ta mallake gidan daga ita sai nata ƴaƴan”
Ezzah ta.yi shiru tana tunani sai kallon ƴan makarantar su take masu kai wa da dawowa.
“Ezzah dik duniyar nan baki da kowa kamar ni, duk wacce zata so ki abaya na take, kuma ƙarya Kalsoom take tace tana son ku, tana nuna muku haka ne dan ta mallaki Daddy, yanzu kina jindaɗi zama da ita? Bata dukan ki? Lokacin da ina nan Daddy ki yana miki faɗa?”
Duk ta girgiza kai.
“Dole ne kiyi mata abunda na saki dan na samu na koma gurin Daddy ku, na yi muku alƙawari ddana koma kullum gida zan riƙa zama ba zan sake fita aiki ba”
“Da gaske?”
“Wallahi, dan haka ki cigaba da abunda kike, har abunda ban saki ba ma ki aikata indai kinsa wanda zai hassalata ne”
“Zan riƙa yi”
“I Love you”
“I Love you too”
Rashida ta rumgume ta kamar da gayya. Sannan ta ciro chocolates da Sweet Candy dake jakarta ta miƙa mata, ta kuma bata ɗari biyu na kashewa sannan ta tashi ta fita.
Daga nan Asibiti ta nufa. Yau ce rana ta farƙo da zata fara bin shawarar likita wajen ɗora kanta akan magani, dan samun tsawaita rayuwarta kamar yadda likita ya faɗa mata.
NAMRA POV.
Two months later....
A zuwa yanzu babu wata matsala da take fuskanta a gurin Asim, tun bayan da aka sallamo daga asibiti, jiki sai ƙara sauƙi yake yana mirmirjewa kamar ba shi ba.
Duk wani mugun ƙudiri dake cikin ransa, ya danne ya barwa zuciyarsa, dan yasan babu yadda zai yi da Namra a yanzu sai kallo, idan yace zai rabu da ita matsala ne a gare shi tun da baya sgi kuɗin auren wata, shi dai yanzu ba shi da wani buri sai na yayi kuɗi.
Irin yadda yake nanata maganar har tsoro abun yake ba Namra, ahi dai yayi kuɗi dai yayi kuɗi. Haka Namra zata zauna tana masa nasiha akan duniya da abunda ya ke cikinta, amman sai dai ya kalleta kawai ya nuna mata wa'azin ya ratsashi bayan a ƙasan zuciyarsa kuma mamakinta yake, wai ita zata zaunar da shi ta nuna masa illar kuɗi, bayan ga ubanta can ya tara su ita kuma da su take tinƙaho.
Sam baya ganin wahalar da take da shi, bata saba wanki ba ko a gidansu amman haka zata zauna ta wanke nata tufafin ta wanke nasa, ta kai masa ruwanka, amman kullum sai ta matsa masa yake wanke dan ganin yake kamar tana takurasa, Allah ya zuba masa ƙuiyar motsa jikinsa indai a bangaren aiki ne.
Maganganun da Namra take masa akan rayuwa da neman kuɗi da yake magana a ko yaushe sai ya ƙara riƙe ta a zuciyarsa, wai bata son sa da alheri ta fi son yayi dauwama cikin baƙin ciki da damuwa tun da ita tana da mafita.
Ga matsalar da ci masa tuwo a ƙwarya a yanzu, wacce yake ganin kamar da ganganci ne tayi masa haka dan bata son haihuwa da shi. Ita kanta tana nadamar sanar da shi da tayi robar da aka saka mata, sai dai babu yadda zatayi dole ce tasa ta faɗa masa, tun kullum sai ya tunkareta kuma jinin har yau be tsaya mata ba, daman wani lokacin haka robar yake yi mutane dan ta ji maƙonta suna firar lokacin data shiga gidan su ƴar fulani.
Ta aika tambayarta ga wani malami ya amsa mata da cewar duk jinin daya zube bana haila bane ya zama kamar jinin rashin lafiya ne dan haka ba zatayi fashin sallah ba balle azumi.
Hakan yasa robar ma sai ta fita ranta dan ita bata son abunda zai riƙa rikitar mata da addini, hakan yasa ta yanke shawawar zuwa a cire mata robar in ya so sai tasha ƴaƴan zurma, dan maƙociyarta nan ta faɗa mata indai har ta sha ƴaƴan zurma ɗaya yana matsayin shekara ɗaya ne idan kuma tasha biyu kuma yana matsayin shekara biyu ne.
Sai dai ba kowa yake yi ma aiki ba, amman ta ga wani a whatsapp wanda Khadeeja Candy take tallah shi kam idan an sha tabbas zai maka aiki, matsalar kawai ita ba a garin take ba, kuma tana buƙatar ta bincike dan ta jin yadda abun an ce mata texted and trusted ne. Ga Kuma Asim ya dame ta da maganar kullum, dan shi gani yake kamar da biyu tayi haka.
Yau wake ta dafa da shinka (rice and beans) ta saka mai da taji, daman yana cikin favorite na ta, amman Asim duk lokacin data dafa sai ya riƙa ƙin ci yana ganin kamar tana haka ne dan karta kashi kuɗi da yawa tayi musu abinci mai kyau.
Shi yanzu har ya matso jikinsa ya koma.yadda yake ya fara fita neman kuɗi, dan ya ayyana a ransa kuɗinta zai ranta ya fara sana'ar, har hango kansa yake ya zama wani Alhaji.
Kullum firar da ita kenan, yau bayan ya gama complaint ɗin baya son wake, ya ɗasa mata firar idan yayi kuɗi, ba aza a ƙara cin wake a gidansa ba.
Namra ta yi murmushi tana mamakin yadda idom Asim ya bude haka.
“Asim kenan. Idan ma zaka yi roƙon baka cewa Allah ya baka halalinka, kawai dai kai kayi kuɗi”
“Wallahi sai na yi kuɗi Namra, Wallahi Wallahi sai nayi kuɗi, kawai naji sauƙi ne”
»“Ban ce ba zaka yi kuɗi ba, Amman yana da kyau ka riƙa cewa Inshallah kuma ka riƙa roƙon halak, saboda gudun sherin zuciya, idan Allah ya rubuta zaka yi kuɗi zaka yi ko da kuwa kama kwance gida ne sai sun tararda kai, saboda an riga an rubuta zaka yi kuɗin sai dai idan kayi gajin haƙuri zaka iya samun ta hanyar da be kamata ba”
“Namra kina bani mamaki, ke yanzu da ba dan kuɗi ba iyayen ki ai ba zasu wulaƙanta ni ba”
“Wulaƙanci kamar ya?”
“Wulaƙanci ne mana, saboda an mai dani talaka wanda ba shi da amfani shiyasa aka saka miki wannan robar ba tare da sanina ba”
“Ba haka bane, kawai matsala ce ta taso kuma likitan yace dole ne nayi planning”
“To Allah ya kyauta, amman ko ma minene ai nafi kowa kusanci da ke, taya za'ayi ki yi min haka”
“Asim matsala ce fa kai yanzu kana son na samu ciki ya zo ya zube ko kuma nayi ta wahala?”
“Hmm kina dai ganin kamar ba zan iya hidama dake ba ke da abunda zaki haifa shiyasa kuka ɗauki wannan matakin”
Ta aje kofin ruwan dake hannunta
“Ba zan ɗauki halin nan naka ba Asim, babu yadda zaka riƙa cin zarafina dana iyayena, kullum mune marar mutumci a idonka, duk abunda muka maka baka gani, na sadaukar da yawa Asim, har inda be kamata na sadaukar ba na sadaukar amman baka gani”
Kamar mai jira sai kawai yayi cikinta da masifa.
“Me kika min ke da iyayenki? Me kika sadaukar min? Ran ki? Ko lafiyarki? Kullum da kin tadhi magana kin sadaukar kin sadaukar tun da na aure ki me na ƙara shi in ɓa tsiya ba? Ɗan abunda na tara dik ya ƙara na zo na kwanta a asibiti jiyan babu wani ɗan'uwanki da ya ɗauki wani abu ya ba ni, an so na mutu ban mutu ba shine yanzu zaki fara buɗe min wani babin na rayuwa, kina da kuɗi a jikin ki amman saboda baƙin ciki ba zaki fitar aci ba sai dai a mutu? To Wallahi Asim ikon Allah ne, duk wani mai son ganin bayana sai dai ni naga bayansa”
“Magana kake irin wannan zancen kamar mai magana da maƙiyansa, maitarka ta kasa ɓoyuwa har sai ta fito fili? Kuɗina sana'ah zan yi da abu na, dan ba zan zauna kullum ni ce biyar dangi a bani ba, kuma Allah be ɗora min alhakin ciyar da kai ba, ni aka ce ka ciyar ka tufatar, yanzu ka fito a siffar ka sak Asim daman dan dukiyar gidan mu ka aure ni ko, amman sai ka nuna mik baka son komai sai ni, ashe zagon ƙasa kake min ka ɗauki halin samarin zamani ka ɗorawa kan ka, masu auren jari...”
Wani irin mahaukacin mari ya kifa mata ya rufe ta da duka kamar ma dukan namiji.
Shuri yake aika mata ta ko'ina tana cigaba da dukan jikinta kamar ƴarsa.
Dukanta yayi sai da yaji ya daki iya kalaman data faɗa masa sannan ya sassauta mata ya miƙe tsaye yana ɗingishi.
“Kuma Wallahi kije aci miki wannan robar ko kuma wallahi na lahira ya fiki jindaɗi”
A fusace ya juya ya bar ɗakin. Kuka tayi har ta gode Allah sannan ta tashi zaune tana cigaba da hawaye.
Sai ynz take tabbatar da tayi kuskuren aure, ta auri mutumen da be san darajarta ba, mutumen da be san kowa ba sai kansa. Daman haka halin Asim yake abu kaɗan sai duka.
Ta share hawayenta dan itama kanta tasan ba kuka bane abunda take buƙata, sam Asim be cancanci hawayenta ba, a yanxu ta san wa take aure dole ne kuma ta shirya zama da shi. Bata da buƙatar kokawa kowa damuwarta ita ya kamata ta gyara zaman aurenta da kanta.
Ta tatsu iya tatsuwa dan haka yanzu ba zata sake bari guminta ya zuba akan Asim ba.
ASIM POV.
Ta ƙarfen dake hannunsa yana dafawa ya fito gate, sai huci yake kamar wani zaki.
Yau ji yake kamar ace ya rumtse ya bude ya gansa yayi kuɗi, ta yadda zai jidaɗin rayuwarsa. Sai yanzu yake nadamar karatunsa daya bari daman can yayi tunanin ko zai samu wani abun a gurin iyayen Namra shiyasa ya baro garin su da ita ta yadda nan zai ta cin karensa ba babbaka sai yayi ta aikata tana samu matsa kuɗi, amman yanzu ya fahimci itama maƙetaciya ce kuma bata sonsa da alheri.
Gashi yanzu ko sana'ah zai yi yasan ba zai samu kuɗi a tashi ɗaya ba, amman idan yana da karatunsa zai iya samun babban aiki.
“Mtssssss aiko karatun na yi ba aiki zan samu ba tun da nigeriyar sai da gata, su kuma waɗannan iyayen nata matsiyata ne ba aiki za su samomin ba, aiko wallahi duk wahalar da zan sha tare da ƴar su zan shata, sai na yi kuɗi tana ganin zata huta kawai na aikata gidan su.
Har ni za'ayi ma mugunta, ai ko sai na yi muku baƙin ciki dan haihuwa yanzu za a fara”
Ya ƙarasa maganar yana kallon Mardiya data doso gurin tana takawa a hankali. Tun daga kan ƙafafunta yake kallonta har zuwa fuskarta.
Shi dai kam yana son farar mace ko ba komai farar mace ko kallonta kawai kayi zata burgeka kuma zakaji kana son ta.
Tsaɓanin Namra da take black beauty, wace yake ganim a yanzu she's not his type, sai dai duk da haka ya ƙudiri aniyar sai ya kai ga jikin cos he need someone near him.
Ba zai je ya kashe kanshi da desires ba, weather blood ɗin ya tsaya mata ko be tsaya ba babu ruwansa yau zai yi yadda yake so da ita.
“Ina wuni”
Mardiya ta gaisheshi cikin ƙirsa da kisinsina. Shi kuma ya amsa mata a far'ah har kunne.
“Lafiya ƙalau Mardiya ya gida”
“Lafiya ƙalau ya jikin na ka?”
“Alhamdulillah”
“Allah ƙara sauƙi”
“Amin na gode”
Da kallo ya bita har ta ɓace masa da gani sannan ya dawo hanyyacin yana yaba kyauwon surarta a zuciyarsa.
KALSOOM POV.
Ita kanta yanzu ta rasa gane kanta balle Hilal da yanzu ya saka mata ido, dan duk ta barkace masa abu kaɗan masifa ta inda take shiga ba ta nan take fita ba.
Da gangan zata ƙi masa girki ko kuma tasa shi gaba tayi masa kuka, bayan be mata komai ba. Tun daga lokacin ya fahimcin akwai abunda yake cikin matarsa, daman can sha'anin ɓacewar cikin nan nata ya bashi mamaki, ga kuma jinin daya ƙi tsaya mata wajen wata huɗu kenan, babu irin maganin da be bata ba amman abun be tsaya ba, tun yana ganin abun kamar wasa har ya fara tsorota da lamarin.
Ita kanta tasan yanzu wannan jinin ya wuce haila ko zubar ciki ya zama na rashin lafiya, kuma ta san hukunci mai jinin rashin lafiya.
Shi kuma jinin rashin lafiya, jini ne da yake zuba ba a lokacin al'ada ba, daga wata jijiya da ake kira da azil. Al'amarin wanda take wannan jinin yana da rikitarwa, saboda kama da jinin haila yake. Idan mace ta zanto jini yana zuba daga gareta jo yaushe, ko kuma a mafi yawan lokaci wanenen zata ɗauka jinin haila da na rashin lafiya? Domin ita mai jinin rashin lafiya hukunce mai tsarki na gareta, kuma irin wannan hukumci shine a gurin mace mai jinin planning irin wanda yake zuba idan anyi planning dan ya zama kamar jinin rashin lafiya.
*Hali na farko* Ta zanto tana da masaniyar kwanakin hailarta, kamin jinin rashin lafiya ya same ta. Misali idan tana jinin haila a kwana biyar ko takwas a farkon wata ko tsakiyarsa, watau tasan kwanakin hailarta da lokacinta. To ita wannan zata zauna gwargwadon kwanakin hailarta ta bar sallah da azumi ta bawa kanta hukunci mai haila. Idan kwanakin sun wuce sai haila sun wuce, sai tayi wanka tayi sallah ta ɗauki jinin da ya cigaba da zubar mata da zuba a matsayin jinin rashin lafiya. Dalili shine faɗin Annabi S. A. W, ga Ummu Habiba : ki zauna gwargwadon kwanakin da hailarki take tsare ki, sannan ki yi wanka ki yi sallah. Muslim ya ruwaito shi. Da kuma faɗarsa Annabi ga Fatima Bintu Abi Hubaish: Wannan jinin jijiya ne, ba haila ba ne. Idan hailarki ta zo sai ki. Bar sallah. Bukhari da Muslim suka ruwaito shi.
Idan iyakar kwanakin hailarta ya zo kamar yadda bayani ya gabata, to wajibi ne a gareta tayi wanka. Kuma wanke gabanta domin ta gusar da abinda yake zuba yayinda ta zo yin kowace salla. Kuma tayi ƙunzugu da auduga (pad) ko abu mai kama da ita wanda zai hana kwararar jinin, sannan tayi alwala daga lokacin kowace salla saboda faɗin Annabi : Ta bar salla a cikin kwanakin hailarta, sannan ta yi wanka kuma ta yi alwala ga kowace salla. Abu Dawud da Ibn Maja da tirmizi ne suka ruwaito shi.
Hakan yasa Kalsoom ta cigaba da salla da duk sauran ibadarta, sai dai har gobe halinta be canja ba a kan Hilal idan yana cikin gidan ji take babu wanda tsana a duniya sai shi. Yara kuma abu kaɗan ta dake su, tun yana haƙuri har abun ya fara isarsa dan yanzu shi da ita basa shan inuwa ɗaya, akan yaransa.
Gashi Ezzah kullum uwarta ƙara hure mata kunne take tana koya abubuwan da take ganin kamar abun ƙwarai ne, bayan ita bata san tana lalata tarbiyar ƴarta bane kawai.
Duk ranar da ba makaranta zai kwashi yaransa ya kai su gidan Hajiyarsa. Hajiya ta lura da yanayin ɗanta damuwa ta bayyana a fuskarsa ga ramar dake jikinsa, yadda ma yake yawan kawo yaran akai-akai ta san ba lau ba.
“Wai likita akwai abunda yake damun ka ne?”
Ajiyar zuciya ya sauke, yana aje plate ɗin abincin da ke hannunsa.
“Wallahi Hajiya ni ban san matsalar, daga ina take ba ma, Kalsoom ce yanzu kwata-kwata na rasa ma gane kanta, indai ina gida bana da kwanciyar hankali, sai kuka zara riƙa min tana masifa”
“Me ya haɗa ku?”
“Ba abunda na haɗa mu haka kawai zata riƙa min masifa sai kuka, kin san cikinta ya ɓace”
“Ya ɓace kamar ya?”
“Jini kawai ta ga yana mata zuba, sai aka yi hoto aka ga babu cikin kwata-kwata a cikin ta, amman jinin har yau be tsaya mata ba, yau kusan wata huɗu kenan”
“Subhanallahi, me ya same ta haka ne?”
“Wallahi nima van sani ba? Na rasa gane kanta”
“Abun kamar lamarin iska shi kesa ciki ya ɓata, ko kuma sihiri”
“Sai maganar saki ta ke min, ita dai na rabu da ita na ta huta”
“Kasan me? Ka samu ƙwarya mai tsarki da za'afaran, sai a ruɓuta suratul Yasin da surar wa'ƙia da fatiha da ƙulhuwallahu ahad da ƙula'uzai da Ayatul kursiyu da kuma amanar rasulu har zuwa ƙarshe da suratul baƙara da ayar : ƙul-a-Allahu azine lakum am alallahi taftarun (10:59) to idan an rubuta sai a karya kummallo da shi idan ta sha sai ta samu dabino ajwah sai kayi mata tawada nan da Al-zaitul muraƙƙa sai ta cinye sauran kuma rubutun kuma ta shafe jikinta, da iKon Allah indai sihiri ne ko aljanu ko wane iri ne zai rabu da ita”
“Amman Hajiya irin wannan ai sai dai kisa waki ya rubuta mata a nan sai na kai mata ta sha”
“To zan nemi wanda zai rubuta mata inshallah, amman wannan ko Rashida ai zata iya ƙulle-ƙulle ganin ta ɓata zamanku”
Yayi ƴar dariya.
“Sai dai ko iska ne, amman ai Rashida bata da irin wannan halin”
“Hmmm Hilal ba a shedun mace, yanzu kasa ran tayi maka wannan abun?”
Yayi shiru yana nazarin maganar Hajiya.
[7/18, 8:12 PM] Khadeeja Candy♥: »»4»»»»»»8»»»»»»»»»
ABDOOL POV.
Ɓacin rai ne shimfiɗe a fuskarsa, idanunsa sun rine zuciyarsa har wani tafarfasa take saboda faɗan d Mai Martaba yake masa.
Har Mai Martaba yayi ya gama Abdool be ce uffan ba, dan yasan akan gaskiya yake faɗansa, kamar yadda Ummi take masa a kullum.
“Ƙanen ka Babana ƙanenka ace yayi aure har ya haihu kai ba kayi ba, kullum girma ƙara tunkararka yake amman baka ganewa, shekarun tafiya suke Babana yanzu da ace kana da mata da wannan abun zai faru da kai? Sai dai ka zauna a gida ta girka maka, ko mutuwa kayi ba mu da abunda zamu kalla mu tuna da kai sai hoton ka, ai ko mutuwa kayi ka bar mai maka addu'ah ka more, rashin
Book Chapters
Chapter 1Chapter 2Chapter 3Chapter 4Chapter 5Chapter 6Chapter 7Chapter 8Chapter 9Chapter 10Chapter 11Chapter 12Chapter 13Chapter 14Chapter 15Chapter 16Chapter 17Chapter 18Chapter 19Chapter 20Chapter 21Chapter 22Chapter 23Chapter 24Chapter 25Chapter 26Chapter 27Chapter 28Chapter 29Chapter 30Chapter 31Chapter 32Chapter 33Chapter 34Chapter 35Chapter 36Chapter 37Chapter 38 Chapter 39Chapter 40Chapter 41Chapter 42Chapter 43Chapter 44Chapter 45Chapter 46Chapter 47Chapter 48Chapter 49Chapter 50Chapter 51Chapter 52Chapter 53Chapter 54Chapter 55Chapter 56Chapter 57Chapter 58Chapter 59Chapter 60Chapter 61Chapter 62Chapter 63Chapter 64Chapter 65Chapter 66Chapter 67Chapter 68Chapter 69Chapter 70Chapter 71Chapter 72Chapter 73Chapter 74Chapter 75Chapter 76Chapter 77Chapter 78Chapter 79Chapter 80Chapter 81Chapter 82Chapter 83Chapter 84Chapter 85Chapter 86Chapter 87Chapter 88Chapter 89Chapter 90Chapter 91Chapter 92Chapter 93Chapter 94