amman hakan ba zai hana na so ki ba, ba xai hana na xauna da ke ba, ina son ki sosai Kalsoom amman ban cancanci abinda kika min ba, nasan mace ce ke kina da rauni shiyasa kawai na ɗaga miki ƙafa_
_Idan kuma har sakin kike so da gaske sai ki kai ni kotu._
*Ur Faithful Husband*
Shine abinda ya rubuta daga ƙarshe cikin manyan harufa. Rumgume takardar tayi a ƙirjinta tana sauke ajiyar zuciyar da bata san lokacin data zo mata ba.
Wani sanyi ta ji ya saukar mata tun daga saman kai har ƙasan ƙafafunta, nan take ta nemi ciwon kanta da kuka da take ta rasa, wani irin ƙaunar Hilal ne ta ji ya ratsa zuciyarta.
Hijabinta da ta bari falo Momi ta jefa mata.
“Tashi ki koma ɗakin ki tun Mahaifin ki be dawo ba”
Buɗe ido tayi tana kallon Momi da murmushi a fuskarta babu ko kunya.
“Bari na yi sallah”
“Idan kin je can kya yi, amman wlh karki sake kuskure cewa ya sake ki, in ba dan Allah yasa yana da tunani ba ai da shikenan”
Bata musa ma Momi ba ta ɗauki hijabin Momi ta saka ta ɗauki takardar da jakarta ta fito falo ranta tasss kamar ba ita ce ta gama kuka ba. Har bakin gate Momi ta rakata tana mata gargadi, sai da ta hau Napep sannan Momi ta koma ciki tana yi Allah Hamdala tare da sawa Hilal albarka...
*NAMRA POV*
Sai da dare Asim ya dawo, kamar yadda ya saba, idan ka ganshi ba zaka ce shine ya fita da tsoro ba ɗazu, yau yayi ciniki shine sirrin farincikin na yau.
Ba laifi ya ɗan sake fuska ya shigo har da sallama, kamar ba shi ba. Ita kanta Namra da mamaki ta amsa masa sallamar tana ƙara kallon fuskarsa dan ta tantancesa. Ya zauna kusa da ita, yana shewa.(fito)
“Sannu da zuwa”
“Yauwa ya gidan?”
“Gida yana nan yadda ka bar shi, masu gidan ma sun zo guba abun su kuma sun ce mu tashi”
“What? To ina za mu koma? Ai kuɗin dana biya be ƙareba, ba zamu tashi ba wallahi”
“Su zaka faɗawa ba ni ba, ni dai na faɗa masa ya zo da safe ko da dare zai same ka”
“Bari ya zo ɗin amman wallahi ba zamu tashi ba, duk inda za a je sai dai aje, amman wannan iskancin ba zan ɗauke shi ba, haka kawai dan ina talaka sai a nemi wulakanta ni”
“Miye abun wulaƙanci dan masu guri sƴn nemi aba su abun su? Sai mu tashi mu basu gidan su, ni dai na roƙe su akan su bar mu mu zauna bq idan har basu yarda ba shikenan sai mu nemi wani gurin kuma”
“Ai kaji matsalar masu kuɗin nan, wallahi duk inda yake baya ƙaunar talaka”
“Ka cika mai da zazzaɓi ciwo Asim, yanzu sun san kai mai kuɗi ne ko talaka? Amman kasan babu talakan da zai iya kama gida kamar wannan ya zauna ko?”
“Sun san talaka nake mana tun da na zauna bq, nima lokaci na yana zuwa zan yi kuɗi har na mamaki”
“A haka za kayi kuɗi matarka tana cikin ƙunci? Ban taɓa ganin ragon namiji irin ka ba Asim, sai dai na girka na baka da ƙarfin ka da komai?”
“Dan Allah ki yi haƙuri Namra, kin ga ɗan aikin da nake be wuce na samu na shan ruwa ba, amman yanzu na samu wani aiki, sai dai aikin mai gidan ya faɗa min cikin gidan zan koma da zama saboda aike-aike idan sun taso, kuma a matsayin driver zai ɗauke ni kuma yaron gida, tun last week muka yi maganar amman nace ba zan kama aikin ba sai na ji ta bakin ki”
Ta jidaɗi dan tasan aikin ya fi wanda yake yi yanzu, sai dai maganar komawa can ne bata gane ba.
“Amman ka koma can har da ni? Ko ya”
“A'a ni kaɗai zan koma can saboda ya fi son ana kwana ta can”
“Amman kai ba aikin gadi ba ce kuma sai ka kwana ina ma laifin kaje da safe wuni”
“Ba kullum zan riƙa kwana can ba, ina jin wani lokaci ne kawai, kin ga ƙara mu samu mu riƙa wannan aikin kamin mu ga abinda Allah zai yi gaba kuma”
“Allah yasa haka shine mafi alheri”
“Amin ya rabb”
Ya rumgume ta yana murmushin jindaɗi, daman ya faɗa mata ne kawai dan ta karta daina ganinsa da dare, amman ko da tace bata aminta ba zai sa ya fasa aikin ba.
*ABDOOL POV*
Suna dinner yake nanatawa Ummi maganar siyen gidan da zai yi, but still bata yarda ba, duk da ta ga alamun da gaske yake.
“Wai mi za ka yi da gida daya ƙone har xaka siye shi 15m?”
“Just”
Ya faɗa yana ɗaga kafaɗu.
“Dude na bar maka, ko kyauta ma zan iya baka ma”
Amal ta faɗa jikin har rawa yake. Kallon Ummi Abdool yayi yadda take watsawa Amal harara yasa shi dariya, sai ya aje spoon ɗin hannunsa ya tashi ya ɗauki kofin tea ya wuce ɗakinsa. Haka kawai ya samu kansa da murmushi ba dalili.
Wata ƙaruwar durowa ya buɗe ya ɗauko wata ƴar ƙarmar jaka baƙa. Ya nufo part ɗin Ummi hannunsa ɗaya riƙe da tea ɗin.
Saman kujera ya jefar da jakar yana kallon Meesha dan ya yarda da natsuwarta.
“Aisha zo ki cire min 15m a nan, ko wanne 1m ne”
Dinning ɗin ta baro ta zo ta zauna saman kujera ta buɗe kuɗin ta fara ƙirgiwa har ta cire 15m, ta aje gefe.
“Ga su”
Sai ya kalli Ummi
“Ummi ga kuɗin”
“Abdallah ana ciniki dole ne? Na ce ba xa a siyar ba”
“Amman mai abu tace ta siƴar”
“Wai me za ka yi da gidan ne”
“Kawai ki sai da min”
“An siyar maka, shikenan?”
“Thank you”
Ya ɗauki ragowar kuɗin ya maida ɗakinsa. Saman madubi ya ɗora copin tea ɗin ya faɗa saman gaɗon zuciyarsa cike da nishaɗi.
Haka ya kwana da nishaɗin da be san ta ina yake xo masa ba balle dalilinsa ba. Shi dai baya iya faɗin abunda ɗaya ta san ya shi ne silar farincikinsa tun jiya har zuwa yau.
Yau zai koma abuja ko ba komai dole yayi sammakon tashi, balle kuma Namra tace masa da safe ake samun mijinta.
Be tsaya wani karin kirki ba, dan a tunaninsa kamar idan ya daɗe ba zai samu mijin nata ba
Ko da bakwai tayi yana ƙofar gidan, sai dai be shiga ba sai da ya buga gate ɗin, ganin babu wanda ya fito yasa ya tura gate ɗin ya shiga cikin, black suit ne jikinsa yayi mugun masa kyau kamar balarabe.
Nesa da bq ɗin ya tsaya yayi sallama cikin muryarsa mai sanyin da daɗin saurora, da ace ma'aikatan sa zasu ganshi a yanzu da sun rantse wannan muryar arota yayi.
Asim ne ya fara fitowa yana samawa, daman tun da yaji sallamar ya raya a ransa cewar masu gidan ne. Sai dai yayi mamakin ganin mutuen duk da be san sunansa amman yasan shi ne ya biyo Namra asibiti. Ƙarasowa Asim ya yi yana masa wani kallo da shi kaɗai ya san fassararsa.
Hannu Abdool ya miƙa masa.
“Sunana Abdallah Ahmad Mai-doki, na zo ne a kan maganar wannan gidan, matarka na ciki?”
Be masa hannun nasa ba sai kawai ya ce
“Eh miye haɗin ka da matata?”
Abdool ya ɗan wara ido tare da taɓe baki haɗi da ɗaga kafaɗu.
“Nothing, jiya na zo akan maganar gidan nan ne sai take roƙo na akan dan Allah na taimaka na bar su a bq su zauna dan basu da gurin zama, so shiyasa na yi ƙoƙarin mai da gidan mallakin ku gaba ɗaya”
Asim ya washe baki, tare da miƙa masa hannu
“Mashallah Allah ya saka maka da alheri”
Daga nan da yake ya ƙwalama Namra kira. Sai gata ta fito cikin hijabi, kamin ta ƙaraso gurin asim fuskar Abdool kawai yake kallo ya gani idan ya kalli Namra. Babu abinda yake rayawa a zuciyarsa sai munafurcin da Namra take masa, wai shi za a maida wawa ya kawo mata gida ya ce ya basu dan tasan idan ya bata ita kaɗai dole za a gane abunda yake tsakanin su. A fili kuma murmushi yake kamar gaske yana kallon Namra da take gaishe da Abdool. Kallo ɗaya Abdool yayi mata ya ɗauke kai ya ciro takardar dake aljihunsa ya miƙawa Asim
“Daga yau wannan gidan ya zama na ku, ba zaku sake biyan kuɗin haya ba balle ace ku tashi”
Hannu biyu Asim yasa ya riƙe hannunsa yana masa godiya kamar zai shige cikinsa. Namra kan mamaki ya hana ta tace komai balle har ta yi godiya.
Sai Asim ne yake ta zuba masa godiya yana murna baka da zuci dan yasan shi zai mori gidan ba Namra ba.
“Mun gode sosai Allah ƙara arziki ya ƙara wadata jazakallahu khairan”
“Amin”
Ya faɗa sannan ya juya ya nufi gate, yana ƙara kallon gidan. Har cikin ransa yaji addu'ar da Namra tayi masa. Sai da ya wuce sannan Asim ya juyo ya shigo gida zuciyarsa cike da zarge zarge. Sam be nunawa Namra ya gane shi ba, sai kawai ya nuna mata ya fi kowa farinciki abinda yayi musu duk da zucin ma farinciki ne dan yasam shine zai ci amfanin abun.
“Kin gani ko yanzu kan alheri ya fara shigo mu, yanzu duk wannan gidan na mu ne kai Alhamdulillah Allah”
Namra tayi murmushi dan ita tun ɗazu mamaki take da tunanin dalili kyautar gidan da Abdool yayi mata, bayan acan baya ya taɓa binta yace yana sonta, ko dai akwai biyu a kyautar ne? Bata bar Asim ya gane abunda yake ranta ba, gudun karya zargenta, ko kuma yayi wani tunanin na daban daman can ya taɓa zarginta.
Dumamen shimkafar da tayi ne ya zuba masa, ya ci sannan ta kai masa ruwan wanka yayi wanka ya shirya cikin wasu tufafin data wanke masa. Sannan ya fito waje ya ciro ɗari biyar ya miƙa mata.
“Gashi ayi cefane”
Hannu biyu tasa ta karɓa tana muryar yau mijinta yyi abun kai
“To Allah amfana”
“Amin sai na dawo”
“Allah ya tsare”
Ya nufi gate zuciyarsa cike da ƙunar cin amanar da Namra take masa, abun har ya fara wuce gurin har ana kai ga kyauta gida.
“Hmm Lallai ma wannan matar wai har ni za a rainawa hankali, bari na zama Asim ɗi na na ƙwarai ki ga yadda zan yi da ke, ku yi ta abun ku yanzu na ba ku dama”
Ya filin yake maganar ya miƙe hanyar data zata kai shii babban titi, sai dai hanyar gidan su Mardiya ce, da gangan ya bi dan ya ganta.
Ya ko yi nasarar angota da ɗaura gaba tana tsaye ƙofar gida tana ciniki a warwaro da mai tutu-rutu, ƙirjinta kawai yake kallo yana siffantawa kansa ita, har ta kawo kusa da inda take.
“Barka da safiya Asim”
“Yauwa barka Mardiya ya gida?”
“Lafiya ƙalau, ina Namra?”
Ya ɗan ƙara washe baki dan be yi tunanin zata kawo maganar Namra a yanzu ba.
“Tana nan ba kin guje mu ba”
“A ni na isa ku ne dai kuka guje ni”
Dariya yayi ya ƙarasa gaban mai ɗan kunnen yana kallon kayan
“Me aka siya?”
“A warwaro ne da ɗan kunne”
Babu ko kunya take masa magana kamar bata sam ɗaura gaba ne a jikinta ba. 1k ya ciro ya miƙa mata
“To a siya da yawa”
Hannu tasa ta karɓa.
“Na gode sosai Allah kawo wa su, ayi irin mu huɗu”
Dariya yyi kamar ba shi ba ya amsa da amin yana tsayardar mai okada. Sai da ya hau sannan ya faɗa masa inda zai kai sa.
Hajiya Sadiya tayi mamakin ganinsa sosai dan a ƴan kwanakin daya ɗauka ta zata ko ba zai dawo ba ne, ruwa ta kawo masa da abinci, sai wani ƴauƙi take kamar ta ga mijinta. Shi kuma ya sake jikin sosai kamar gidansa, baya kallonta idan tana kallonsa ko taɓa gabansa sai ta bada baya yake kallonta.
“Baka buƙatar kwaso kayan ka ko wani abu, akwai komai da zaka buƙata a ɗakin da za a sauke ka, ni na ɗauka ma ba zaka dawo ba”
“Me zai hana? Mutum ya bar samu?”
Dariya...
“Aiko dai, ina kallon lokacin da kake ta ciwon nan kamar ba zaka tashi ba”
Gabansa ya faɗi dan be yi tunanin ko ta san shi ba, se dai be gama saƙe saƙensa ba ta cigaba.
“Lokacin da muƙa ɗauko ka daga asibitin Funtua zuwa nan katsina, lokacin kana cikin ciwo ba zaka gane ba, amman na san kana da mata ka ɓoye min ne kawai”
Ido cikin ido yake kallonta dan tantance abinda take faɗa.
“Ban gane ba”
“Hmmm Asim ko? Ni ce na ɗauko ka da mota na na kawo ka Asibitin katsina na biya kuɗin gado da magani, amman nasan ba zaka iya tunawa kancewar lokacin kana cikin ciwo”
“Eh...eh..ha...k...a..ne.... Ashe kin san ni”
“Na san ka nima farko ban gane ka ba sai daga bayan lokacin da nasa ayi min bincike akan ka”
“Bincike kuma?”
“Eh mana ai duk wanda xaka xauna da shi kana da bikatar sanin ko waye shi, gudun abinda zai je ya dawo amman miyasa kace min baka da mata bayan kana da ita?”
Ya ɗan sosa kansa yana cire hannunsa daga abincin daya fita ransa.
“Wallahi Hajiya naga kamar ba ki son mai matar ne shiyasa, ni kuma bana son na rasa wannan aiki na ki”
Tayi murmushin ƙasaita.
“Ba mai mata ne bana so ba, yadda nake son a min spending time ne nasan mai mata ba zai iya ba”
“Zan iya wallahi dan ni na fi ƙarfin matana na, duk abinda kike so zan miki”
“Hakan yana da kyau, namijin duniya irin ka na ke so”
Ya jidaɗi sosai.
“Anything for you Hajiya”
“Gobe aikin ka xai fara, yanzu idan ka gama, sai kaje gurin mai gadi ya nuna maka wasu abubuwan”
“Hajiya ai ni na gama ma”
“Ka daina kirana da Hajiya ka kira ni Sadiya na”
“Ai da nauyi sai dai ko nace Anty Sadiya”
Wata harara ta watsa masa.
“Na yi maka kama da Antyn ka ne?”
Kallonta yayi a zahiri kam tayi yi, dan wannan yasan ba sa'arsa bace sai dai kuma bata isa haihuwarsa ba.
“A'a Sunan ne ba zan biya faɗi a fili ba”
“To ka riƙa ce min Sadiya Babe, amman idam cikin mutane ne ka riƙa kirana da Hajiya na”
“To am gama na gode”
Har ya juya tace
“Kuma bana son sa ido, kar ka damu da baƙina ko ƴaƴan 'uwan da suke zuwa gidan nan kai dai kawai ka yi aikin ka”
“Inshallah ba zaki same ni mai tsaɓa uwarnin ki ba”
“Albashin ka 100k per month”
Da sauri ya kalleta fuskarsa ƙarara da mamaki, sai gashi kurfane ƙasa yana mata godiya.
“Allah ya ƙara miki arziki Allah yayi miki yadda kika min”
“Amin kai dai ka cigaba da biyayya kawai zaka iya samun fiye da haka ma”
“Inshallah”
“You can go, sai ya nuna ma ɗakinka da kuma aikin ka”
Ya juya ya fice yana jin wani irin nishaɗi da be taɓa jin irinsa sai yau.
*ABDOOL POV*
Ko da ya isa gida duka ƙanensa sun wuce scul Ummi ce kawai a dinning sai Amira suna karƴawa. Tun daga nesa Ummi ta hango nishaɗin dake fuskar ɗanta. Har ya ƙaraso kusa da su ya zauna a kujera daya saba zama.
“Ina ka je da safen nan haka?”
Be son maganar gaban Amira, sai kawai yayi murmushi ya ɗauki kofi ya soma haɗa ma kansa tea.
“Good Morning Yaya”
“How are you dear..”
_Dear_ taji kalmar har cikin ranta, shi kuma ya amsa mata ne da murmushi kuma ba tare da wata manufa ba.
“Ummi yau zan koma fa”
“Yeah i know i just want to know the secret of your smile?”
Shi kansa be san yana murmushi sai yanzu da Ummi ta yi magana. Yayi saurin kawar da murmushin
“Nothing”
Ya miƙe tsaye yana kallon agogon hannunsa.
“Around 9: za mu tashi”
Amira ta ji babu daɗi. Sai ta tashi jiki a sanyeye ta nufi ɗakinta, sam bata son Abdool yayi nisa. Komawa Abdool yayi ya zauna ganin Amira ta shige ɗaki.
“Ummi ina wata da na taɓa baki labari nace miki na ganta a pharmacy da hospital har na ce ina son ta sai tace min ita matar aure ce?”
“Yeah yeah na tuna what happed?”
“Ita ce take haya a gidan Amal ita da mijinta, sune suka yi wuta yanzu sun koma bq da zama saboda mijin nata talaka ne sasai”
“So...?”
“Shi ne sai na siya musu gidan...”
“Saboda me?”
“Just”
“You still love her ko?”
Ya ɗan yi shiru yana tambayar kansa. Kamin ya ɗaga kai alamar eh
“Yeah and i d....”
Be ƙarasa ba Ummi ta mikr tsaye tana dakan dinning ɗin ta katsa masa tsawa
“That it, baka da lada baka yi da Allah ba, kai baka ji kunyar kanka ba ace matar wani kake so? Kai zaka so wani ya kashe maka aure ne?”
“Ummi ba auren ta zan kashe ba, i just help”
“Help? You want to use her dan kasan mijinta talaka ne, ka kashe mata aure huh? Duk ƴan matan garin na ka rasa wacce zaka so sai matar aure Abdallah mike damun ƙwaƙwalwarka, abunda kake be kamata ba, kallon ta a gareka haramun ne, kamata yayi ace kana yaƙi da sheɗen ba wai kana bari na kai zuciyarka ga halaka ba.
Dole zan yi magana da Mai Martaba dole ayi maka aure ko baka so, dan na fahimci baka da hankali”
Cikin fushi ta ƙarasa maganar tana mai ƙyamar abunda ɗan ta ya aikata. Shikam kasa cewa komai yayi dan be da bakin magana.
Duka abunda suke Amira na jikin ƙofar ɗakinta tana sauraensu duk da akwai ta zara, dan da farko bata ji abunda Abdool da Ummi suke tattaunawa ba sai da Ummi ta ɗaga murya tana masa faɗa.
‘Wace mai sa'ah ce wannan wanda Abdool yake so? Me take da shi?’
Tambayar da tayi ma kanta kenan tana mai ƙarasawa gaban modubi ta dubi kanta.
*HILAL POV*
Yana isa asibitin ya wuce ɗakin da Rafiq yake, zaune ya same shi yana kuka. Amina da wata nurse na kusa da shi tana lalaɓashi, bakinsa ya karkace sai dalalarda yawu yake kamar musaki, ko kuma irin yaran na dolaye. Yana ganin Hilal.ya riƙa ƙokarin sauka yaje inda yake, sai Hilal ya ƙaraso da sauri kusa da shi cike da tausayawa ya ɗauke shi.
“Shiiii Daddy ya zo”
“Good mornig Sir”
Nurse ɗin ta gaishe shi sannan ta fice, Amina ma ta ɗora da nata gaisuwar tana nuna masa abincin da Hajiya tace a kawo masa.
“Okay”
Ya faɗa yana ciro wayarsa dake ringing.
“Ya aka yi?”
“Wallahi nayi lallaɓa Dady yace shi sai ya saka ƙarar”
Showing 141001 words to 144000 words out of 280121 words
_Idan kuma har sakin kike so da gaske sai ki kai ni kotu._
*Ur Faithful Husband*
Shine abinda ya rubuta daga ƙarshe cikin manyan harufa. Rumgume takardar tayi a ƙirjinta tana sauke ajiyar zuciyar da bata san lokacin data zo mata ba.
Wani sanyi ta ji ya saukar mata tun daga saman kai har ƙasan ƙafafunta, nan take ta nemi ciwon kanta da kuka da take ta rasa, wani irin ƙaunar Hilal ne ta ji ya ratsa zuciyarta.
Hijabinta da ta bari falo Momi ta jefa mata.
“Tashi ki koma ɗakin ki tun Mahaifin ki be dawo ba”
Buɗe ido tayi tana kallon Momi da murmushi a fuskarta babu ko kunya.
“Bari na yi sallah”
“Idan kin je can kya yi, amman wlh karki sake kuskure cewa ya sake ki, in ba dan Allah yasa yana da tunani ba ai da shikenan”
Bata musa ma Momi ba ta ɗauki hijabin Momi ta saka ta ɗauki takardar da jakarta ta fito falo ranta tasss kamar ba ita ce ta gama kuka ba. Har bakin gate Momi ta rakata tana mata gargadi, sai da ta hau Napep sannan Momi ta koma ciki tana yi Allah Hamdala tare da sawa Hilal albarka...
*NAMRA POV*
Sai da dare Asim ya dawo, kamar yadda ya saba, idan ka ganshi ba zaka ce shine ya fita da tsoro ba ɗazu, yau yayi ciniki shine sirrin farincikin na yau.
Ba laifi ya ɗan sake fuska ya shigo har da sallama, kamar ba shi ba. Ita kanta Namra da mamaki ta amsa masa sallamar tana ƙara kallon fuskarsa dan ta tantancesa. Ya zauna kusa da ita, yana shewa.(fito)
“Sannu da zuwa”
“Yauwa ya gidan?”
“Gida yana nan yadda ka bar shi, masu gidan ma sun zo guba abun su kuma sun ce mu tashi”
“What? To ina za mu koma? Ai kuɗin dana biya be ƙareba, ba zamu tashi ba wallahi”
“Su zaka faɗawa ba ni ba, ni dai na faɗa masa ya zo da safe ko da dare zai same ka”
“Bari ya zo ɗin amman wallahi ba zamu tashi ba, duk inda za a je sai dai aje, amman wannan iskancin ba zan ɗauke shi ba, haka kawai dan ina talaka sai a nemi wulakanta ni”
“Miye abun wulaƙanci dan masu guri sƴn nemi aba su abun su? Sai mu tashi mu basu gidan su, ni dai na roƙe su akan su bar mu mu zauna bq idan har basu yarda ba shikenan sai mu nemi wani gurin kuma”
“Ai kaji matsalar masu kuɗin nan, wallahi duk inda yake baya ƙaunar talaka”
“Ka cika mai da zazzaɓi ciwo Asim, yanzu sun san kai mai kuɗi ne ko talaka? Amman kasan babu talakan da zai iya kama gida kamar wannan ya zauna ko?”
“Sun san talaka nake mana tun da na zauna bq, nima lokaci na yana zuwa zan yi kuɗi har na mamaki”
“A haka za kayi kuɗi matarka tana cikin ƙunci? Ban taɓa ganin ragon namiji irin ka ba Asim, sai dai na girka na baka da ƙarfin ka da komai?”
“Dan Allah ki yi haƙuri Namra, kin ga ɗan aikin da nake be wuce na samu na shan ruwa ba, amman yanzu na samu wani aiki, sai dai aikin mai gidan ya faɗa min cikin gidan zan koma da zama saboda aike-aike idan sun taso, kuma a matsayin driver zai ɗauke ni kuma yaron gida, tun last week muka yi maganar amman nace ba zan kama aikin ba sai na ji ta bakin ki”
Ta jidaɗi dan tasan aikin ya fi wanda yake yi yanzu, sai dai maganar komawa can ne bata gane ba.
“Amman ka koma can har da ni? Ko ya”
“A'a ni kaɗai zan koma can saboda ya fi son ana kwana ta can”
“Amman kai ba aikin gadi ba ce kuma sai ka kwana ina ma laifin kaje da safe wuni”
“Ba kullum zan riƙa kwana can ba, ina jin wani lokaci ne kawai, kin ga ƙara mu samu mu riƙa wannan aikin kamin mu ga abinda Allah zai yi gaba kuma”
“Allah yasa haka shine mafi alheri”
“Amin ya rabb”
Ya rumgume ta yana murmushin jindaɗi, daman ya faɗa mata ne kawai dan ta karta daina ganinsa da dare, amman ko da tace bata aminta ba zai sa ya fasa aikin ba.
*ABDOOL POV*
Suna dinner yake nanatawa Ummi maganar siyen gidan da zai yi, but still bata yarda ba, duk da ta ga alamun da gaske yake.
“Wai mi za ka yi da gida daya ƙone har xaka siye shi 15m?”
“Just”
Ya faɗa yana ɗaga kafaɗu.
“Dude na bar maka, ko kyauta ma zan iya baka ma”
Amal ta faɗa jikin har rawa yake. Kallon Ummi Abdool yayi yadda take watsawa Amal harara yasa shi dariya, sai ya aje spoon ɗin hannunsa ya tashi ya ɗauki kofin tea ya wuce ɗakinsa. Haka kawai ya samu kansa da murmushi ba dalili.
Wata ƙaruwar durowa ya buɗe ya ɗauko wata ƴar ƙarmar jaka baƙa. Ya nufo part ɗin Ummi hannunsa ɗaya riƙe da tea ɗin.
Saman kujera ya jefar da jakar yana kallon Meesha dan ya yarda da natsuwarta.
“Aisha zo ki cire min 15m a nan, ko wanne 1m ne”
Dinning ɗin ta baro ta zo ta zauna saman kujera ta buɗe kuɗin ta fara ƙirgiwa har ta cire 15m, ta aje gefe.
“Ga su”
Sai ya kalli Ummi
“Ummi ga kuɗin”
“Abdallah ana ciniki dole ne? Na ce ba xa a siyar ba”
“Amman mai abu tace ta siƴar”
“Wai me za ka yi da gidan ne”
“Kawai ki sai da min”
“An siyar maka, shikenan?”
“Thank you”
Ya ɗauki ragowar kuɗin ya maida ɗakinsa. Saman madubi ya ɗora copin tea ɗin ya faɗa saman gaɗon zuciyarsa cike da nishaɗi.
Haka ya kwana da nishaɗin da be san ta ina yake xo masa ba balle dalilinsa ba. Shi dai baya iya faɗin abunda ɗaya ta san ya shi ne silar farincikinsa tun jiya har zuwa yau.
Yau zai koma abuja ko ba komai dole yayi sammakon tashi, balle kuma Namra tace masa da safe ake samun mijinta.
Be tsaya wani karin kirki ba, dan a tunaninsa kamar idan ya daɗe ba zai samu mijin nata ba
Ko da bakwai tayi yana ƙofar gidan, sai dai be shiga ba sai da ya buga gate ɗin, ganin babu wanda ya fito yasa ya tura gate ɗin ya shiga cikin, black suit ne jikinsa yayi mugun masa kyau kamar balarabe.
Nesa da bq ɗin ya tsaya yayi sallama cikin muryarsa mai sanyin da daɗin saurora, da ace ma'aikatan sa zasu ganshi a yanzu da sun rantse wannan muryar arota yayi.
Asim ne ya fara fitowa yana samawa, daman tun da yaji sallamar ya raya a ransa cewar masu gidan ne. Sai dai yayi mamakin ganin mutuen duk da be san sunansa amman yasan shi ne ya biyo Namra asibiti. Ƙarasowa Asim ya yi yana masa wani kallo da shi kaɗai ya san fassararsa.
Hannu Abdool ya miƙa masa.
“Sunana Abdallah Ahmad Mai-doki, na zo ne a kan maganar wannan gidan, matarka na ciki?”
Be masa hannun nasa ba sai kawai ya ce
“Eh miye haɗin ka da matata?”
Abdool ya ɗan wara ido tare da taɓe baki haɗi da ɗaga kafaɗu.
“Nothing, jiya na zo akan maganar gidan nan ne sai take roƙo na akan dan Allah na taimaka na bar su a bq su zauna dan basu da gurin zama, so shiyasa na yi ƙoƙarin mai da gidan mallakin ku gaba ɗaya”
Asim ya washe baki, tare da miƙa masa hannu
“Mashallah Allah ya saka maka da alheri”
Daga nan da yake ya ƙwalama Namra kira. Sai gata ta fito cikin hijabi, kamin ta ƙaraso gurin asim fuskar Abdool kawai yake kallo ya gani idan ya kalli Namra. Babu abinda yake rayawa a zuciyarsa sai munafurcin da Namra take masa, wai shi za a maida wawa ya kawo mata gida ya ce ya basu dan tasan idan ya bata ita kaɗai dole za a gane abunda yake tsakanin su. A fili kuma murmushi yake kamar gaske yana kallon Namra da take gaishe da Abdool. Kallo ɗaya Abdool yayi mata ya ɗauke kai ya ciro takardar dake aljihunsa ya miƙawa Asim
“Daga yau wannan gidan ya zama na ku, ba zaku sake biyan kuɗin haya ba balle ace ku tashi”
Hannu biyu Asim yasa ya riƙe hannunsa yana masa godiya kamar zai shige cikinsa. Namra kan mamaki ya hana ta tace komai balle har ta yi godiya.
Sai Asim ne yake ta zuba masa godiya yana murna baka da zuci dan yasan shi zai mori gidan ba Namra ba.
“Mun gode sosai Allah ƙara arziki ya ƙara wadata jazakallahu khairan”
“Amin”
Ya faɗa sannan ya juya ya nufi gate, yana ƙara kallon gidan. Har cikin ransa yaji addu'ar da Namra tayi masa. Sai da ya wuce sannan Asim ya juyo ya shigo gida zuciyarsa cike da zarge zarge. Sam be nunawa Namra ya gane shi ba, sai kawai ya nuna mata ya fi kowa farinciki abinda yayi musu duk da zucin ma farinciki ne dan yasam shine zai ci amfanin abun.
“Kin gani ko yanzu kan alheri ya fara shigo mu, yanzu duk wannan gidan na mu ne kai Alhamdulillah Allah”
Namra tayi murmushi dan ita tun ɗazu mamaki take da tunanin dalili kyautar gidan da Abdool yayi mata, bayan acan baya ya taɓa binta yace yana sonta, ko dai akwai biyu a kyautar ne? Bata bar Asim ya gane abunda yake ranta ba, gudun karya zargenta, ko kuma yayi wani tunanin na daban daman can ya taɓa zarginta.
Dumamen shimkafar da tayi ne ya zuba masa, ya ci sannan ta kai masa ruwan wanka yayi wanka ya shirya cikin wasu tufafin data wanke masa. Sannan ya fito waje ya ciro ɗari biyar ya miƙa mata.
“Gashi ayi cefane”
Hannu biyu tasa ta karɓa tana muryar yau mijinta yyi abun kai
“To Allah amfana”
“Amin sai na dawo”
“Allah ya tsare”
Ya nufi gate zuciyarsa cike da ƙunar cin amanar da Namra take masa, abun har ya fara wuce gurin har ana kai ga kyauta gida.
“Hmm Lallai ma wannan matar wai har ni za a rainawa hankali, bari na zama Asim ɗi na na ƙwarai ki ga yadda zan yi da ke, ku yi ta abun ku yanzu na ba ku dama”
Ya filin yake maganar ya miƙe hanyar data zata kai shii babban titi, sai dai hanyar gidan su Mardiya ce, da gangan ya bi dan ya ganta.
Ya ko yi nasarar angota da ɗaura gaba tana tsaye ƙofar gida tana ciniki a warwaro da mai tutu-rutu, ƙirjinta kawai yake kallo yana siffantawa kansa ita, har ta kawo kusa da inda take.
“Barka da safiya Asim”
“Yauwa barka Mardiya ya gida?”
“Lafiya ƙalau, ina Namra?”
Ya ɗan ƙara washe baki dan be yi tunanin zata kawo maganar Namra a yanzu ba.
“Tana nan ba kin guje mu ba”
“A ni na isa ku ne dai kuka guje ni”
Dariya yayi ya ƙarasa gaban mai ɗan kunnen yana kallon kayan
“Me aka siya?”
“A warwaro ne da ɗan kunne”
Babu ko kunya take masa magana kamar bata sam ɗaura gaba ne a jikinta ba. 1k ya ciro ya miƙa mata
“To a siya da yawa”
Hannu tasa ta karɓa.
“Na gode sosai Allah kawo wa su, ayi irin mu huɗu”
Dariya yyi kamar ba shi ba ya amsa da amin yana tsayardar mai okada. Sai da ya hau sannan ya faɗa masa inda zai kai sa.
Hajiya Sadiya tayi mamakin ganinsa sosai dan a ƴan kwanakin daya ɗauka ta zata ko ba zai dawo ba ne, ruwa ta kawo masa da abinci, sai wani ƴauƙi take kamar ta ga mijinta. Shi kuma ya sake jikin sosai kamar gidansa, baya kallonta idan tana kallonsa ko taɓa gabansa sai ta bada baya yake kallonta.
“Baka buƙatar kwaso kayan ka ko wani abu, akwai komai da zaka buƙata a ɗakin da za a sauke ka, ni na ɗauka ma ba zaka dawo ba”
“Me zai hana? Mutum ya bar samu?”
Dariya...
“Aiko dai, ina kallon lokacin da kake ta ciwon nan kamar ba zaka tashi ba”
Gabansa ya faɗi dan be yi tunanin ko ta san shi ba, se dai be gama saƙe saƙensa ba ta cigaba.
“Lokacin da muƙa ɗauko ka daga asibitin Funtua zuwa nan katsina, lokacin kana cikin ciwo ba zaka gane ba, amman na san kana da mata ka ɓoye min ne kawai”
Ido cikin ido yake kallonta dan tantance abinda take faɗa.
“Ban gane ba”
“Hmmm Asim ko? Ni ce na ɗauko ka da mota na na kawo ka Asibitin katsina na biya kuɗin gado da magani, amman nasan ba zaka iya tunawa kancewar lokacin kana cikin ciwo”
“Eh...eh..ha...k...a..ne.... Ashe kin san ni”
“Na san ka nima farko ban gane ka ba sai daga bayan lokacin da nasa ayi min bincike akan ka”
“Bincike kuma?”
“Eh mana ai duk wanda xaka xauna da shi kana da bikatar sanin ko waye shi, gudun abinda zai je ya dawo amman miyasa kace min baka da mata bayan kana da ita?”
Ya ɗan sosa kansa yana cire hannunsa daga abincin daya fita ransa.
“Wallahi Hajiya naga kamar ba ki son mai matar ne shiyasa, ni kuma bana son na rasa wannan aiki na ki”
Tayi murmushin ƙasaita.
“Ba mai mata ne bana so ba, yadda nake son a min spending time ne nasan mai mata ba zai iya ba”
“Zan iya wallahi dan ni na fi ƙarfin matana na, duk abinda kike so zan miki”
“Hakan yana da kyau, namijin duniya irin ka na ke so”
Ya jidaɗi sosai.
“Anything for you Hajiya”
“Gobe aikin ka xai fara, yanzu idan ka gama, sai kaje gurin mai gadi ya nuna maka wasu abubuwan”
“Hajiya ai ni na gama ma”
“Ka daina kirana da Hajiya ka kira ni Sadiya na”
“Ai da nauyi sai dai ko nace Anty Sadiya”
Wata harara ta watsa masa.
“Na yi maka kama da Antyn ka ne?”
Kallonta yayi a zahiri kam tayi yi, dan wannan yasan ba sa'arsa bace sai dai kuma bata isa haihuwarsa ba.
“A'a Sunan ne ba zan biya faɗi a fili ba”
“To ka riƙa ce min Sadiya Babe, amman idam cikin mutane ne ka riƙa kirana da Hajiya na”
“To am gama na gode”
Har ya juya tace
“Kuma bana son sa ido, kar ka damu da baƙina ko ƴaƴan 'uwan da suke zuwa gidan nan kai dai kawai ka yi aikin ka”
“Inshallah ba zaki same ni mai tsaɓa uwarnin ki ba”
“Albashin ka 100k per month”
Da sauri ya kalleta fuskarsa ƙarara da mamaki, sai gashi kurfane ƙasa yana mata godiya.
“Allah ya ƙara miki arziki Allah yayi miki yadda kika min”
“Amin kai dai ka cigaba da biyayya kawai zaka iya samun fiye da haka ma”
“Inshallah”
“You can go, sai ya nuna ma ɗakinka da kuma aikin ka”
Ya juya ya fice yana jin wani irin nishaɗi da be taɓa jin irinsa sai yau.
*ABDOOL POV*
Ko da ya isa gida duka ƙanensa sun wuce scul Ummi ce kawai a dinning sai Amira suna karƴawa. Tun daga nesa Ummi ta hango nishaɗin dake fuskar ɗanta. Har ya ƙaraso kusa da su ya zauna a kujera daya saba zama.
“Ina ka je da safen nan haka?”
Be son maganar gaban Amira, sai kawai yayi murmushi ya ɗauki kofi ya soma haɗa ma kansa tea.
“Good Morning Yaya”
“How are you dear..”
_Dear_ taji kalmar har cikin ranta, shi kuma ya amsa mata ne da murmushi kuma ba tare da wata manufa ba.
“Ummi yau zan koma fa”
“Yeah i know i just want to know the secret of your smile?”
Shi kansa be san yana murmushi sai yanzu da Ummi ta yi magana. Yayi saurin kawar da murmushin
“Nothing”
Ya miƙe tsaye yana kallon agogon hannunsa.
“Around 9: za mu tashi”
Amira ta ji babu daɗi. Sai ta tashi jiki a sanyeye ta nufi ɗakinta, sam bata son Abdool yayi nisa. Komawa Abdool yayi ya zauna ganin Amira ta shige ɗaki.
“Ummi ina wata da na taɓa baki labari nace miki na ganta a pharmacy da hospital har na ce ina son ta sai tace min ita matar aure ce?”
“Yeah yeah na tuna what happed?”
“Ita ce take haya a gidan Amal ita da mijinta, sune suka yi wuta yanzu sun koma bq da zama saboda mijin nata talaka ne sasai”
“So...?”
“Shi ne sai na siya musu gidan...”
“Saboda me?”
“Just”
“You still love her ko?”
Ya ɗan yi shiru yana tambayar kansa. Kamin ya ɗaga kai alamar eh
“Yeah and i d....”
Be ƙarasa ba Ummi ta mikr tsaye tana dakan dinning ɗin ta katsa masa tsawa
“That it, baka da lada baka yi da Allah ba, kai baka ji kunyar kanka ba ace matar wani kake so? Kai zaka so wani ya kashe maka aure ne?”
“Ummi ba auren ta zan kashe ba, i just help”
“Help? You want to use her dan kasan mijinta talaka ne, ka kashe mata aure huh? Duk ƴan matan garin na ka rasa wacce zaka so sai matar aure Abdallah mike damun ƙwaƙwalwarka, abunda kake be kamata ba, kallon ta a gareka haramun ne, kamata yayi ace kana yaƙi da sheɗen ba wai kana bari na kai zuciyarka ga halaka ba.
Dole zan yi magana da Mai Martaba dole ayi maka aure ko baka so, dan na fahimci baka da hankali”
Cikin fushi ta ƙarasa maganar tana mai ƙyamar abunda ɗan ta ya aikata. Shikam kasa cewa komai yayi dan be da bakin magana.
Duka abunda suke Amira na jikin ƙofar ɗakinta tana sauraensu duk da akwai ta zara, dan da farko bata ji abunda Abdool da Ummi suke tattaunawa ba sai da Ummi ta ɗaga murya tana masa faɗa.
‘Wace mai sa'ah ce wannan wanda Abdool yake so? Me take da shi?’
Tambayar da tayi ma kanta kenan tana mai ƙarasawa gaban modubi ta dubi kanta.
*HILAL POV*
Yana isa asibitin ya wuce ɗakin da Rafiq yake, zaune ya same shi yana kuka. Amina da wata nurse na kusa da shi tana lalaɓashi, bakinsa ya karkace sai dalalarda yawu yake kamar musaki, ko kuma irin yaran na dolaye. Yana ganin Hilal.ya riƙa ƙokarin sauka yaje inda yake, sai Hilal ya ƙaraso da sauri kusa da shi cike da tausayawa ya ɗauke shi.
“Shiiii Daddy ya zo”
“Good mornig Sir”
Nurse ɗin ta gaishe shi sannan ta fice, Amina ma ta ɗora da nata gaisuwar tana nuna masa abincin da Hajiya tace a kawo masa.
“Okay”
Ya faɗa yana ciro wayarsa dake ringing.
“Ya aka yi?”
“Wallahi nayi lallaɓa Dady yace shi sai ya saka ƙarar”
Book Chapters
Chapter 1Chapter 2Chapter 3Chapter 4Chapter 5Chapter 6Chapter 7Chapter 8Chapter 9Chapter 10Chapter 11Chapter 12Chapter 13Chapter 14Chapter 15Chapter 16Chapter 17Chapter 18Chapter 19Chapter 20Chapter 21Chapter 22Chapter 23Chapter 24Chapter 25Chapter 26Chapter 27Chapter 28Chapter 29Chapter 30Chapter 31Chapter 32Chapter 33Chapter 34Chapter 35Chapter 36Chapter 37Chapter 38Chapter 39Chapter 40Chapter 41Chapter 42Chapter 43Chapter 44Chapter 45Chapter 46Chapter 47Chapter 48 Chapter 49Chapter 50Chapter 51Chapter 52Chapter 53Chapter 54Chapter 55Chapter 56Chapter 57Chapter 58Chapter 59Chapter 60Chapter 61Chapter 62Chapter 63Chapter 64Chapter 65Chapter 66Chapter 67Chapter 68Chapter 69Chapter 70Chapter 71Chapter 72Chapter 73Chapter 74Chapter 75Chapter 76Chapter 77Chapter 78Chapter 79Chapter 80Chapter 81Chapter 82Chapter 83Chapter 84Chapter 85Chapter 86Chapter 87Chapter 88Chapter 89Chapter 90Chapter 91Chapter 92Chapter 93Chapter 94