daɗe kurciya da dare baka san me take nufi ba, balle kuma ga laya a wuyanta”
“Idan mutum yana addu'ah babu abunda zai same shi, kawai ka halbe min ita idan zaka iya”
“Toh”
Ya nufi wani part ɗin na gidan, da ɓangarensu yake a can, be ɗauki dogon lokaci ba sai ga shi ya dawo da danƙon har da duwatsunsa guda biyar. Ayatul kursiyo ya karanta sannan ya saita inda take ya harba da bismilla. Firr tayi zata tashi sai ta faɗi saboda ya same ta a ƙafa. Da sauri Abdool ya ƙarasa zai kamata sai ta sake unƙurin tashi ta kasa har ya kama ta, sai da yayi bismillah sannan ya cire layar dake wuyanta. Umar ya miƙawa kuciyar ya shiga buɗe layar. Wasu surkulle ne aka yi aka kulle da fatar baƙar akuya, sai wata farar takardar a tsayarki takardar an rubuta sunan Namra da larabci.
“Namra”
Ya maimata sunan cike da mamaki da ɗaurewar kai.
“Miya kawo sunan Namra anan? Waya aikata mata haka?”
Yayi ma kansa tambayar da bashi da amsar ta.
“Umar kasan yadda ka yi da wannan kurciyar”
Ya faɗa sannan ya shiga cikin falon da abun a hannunsa.
KALSOOM POV.
Hannu ya kai ya shafa fuskarta.
“Haba dai baki kishi ranar ɗaura aure ba sai yanzu zaki yi? Ko dai wani ne ya zuga ki?”
Kai ta girgiza masa alamar a'a, ta janye hannunsa daga fuskarta ta miƙe tsaye.
“Zan shiga wanka”
Hannunta ya riƙe.
“Kalsoom ko na miki wani abu da ba daidai bane?”
Ta saka mashi kuka.
“Baka min komai ba, kawai dai...”
miƙewa yayi tsaye ya haɗe bakinsu, yana shafa bayanta alamar rarrashi. Sun ɗauki tsowon lokaci a haka sannan ya sake ta.
“I promise you ba zan miki wani abu da xai cutar da ke ba”
Ya kwantar da kanta ƙirjinsa. Ba shi take ji ba, Amaryar tasa take ji dan bata san da me tazo mata ba, bata son ta sake shiga irin rayuwar da tayi da Rashida a baya. Sai da ya tabbatar ta samu sukuni sannan ya sake ta yana tambayar me zai siyo mata.
“Ina son zogale”
“Okay”
Yayi mata kiss, ya shafi cikinta sannan ya juya ya fice. A gurin ta tsaya har sai da ta ji tashin motarsa sannan ta shiga wankan. Tana cikin wanka taji tsayawar mota sai kuma kamar ba ta Hilal ba, hankali kwance ta yi wankanta ta ɗaura tawul ta fito. Haka kawai ta ji bata da natsuwa idan bata leƙa taga wanda ya shigo ba, dan haka tana fitowa ta zira doguwar riga ta ɗora ɗankwalin a saman kanta ta nufi falon.
Abunda ta gani ya bala'in ɗaga mata hankali Rashida ce zaune saman kujera tana kallonta, fargaba da tsoro suka tunkarota lokaci ɗaya, idonta be gama tantance Rashida ɗin bace ko waninta, dan ta lalace sosai ta rame, idan har ita ɗince mi tazo yi gurinta, ga ta cikin hijabi niƙab a hannunta.
ASIM POV.
Yana saka kuɗin sai ga kiran Hajiya Sadiya, sai da ya shiga mota sannan ya yi picking.
“Hajiya na saka kuɗin”
“To yayi kyau, ina son muyi wata magana da kai Asim mai muhimmaci”
“Okay na zo kenan?”
“A'ah ba sai ka zo ba, saboda ƴata bata riga ta tafi ba”
“Toh ya za'ayi kenan”
“Ka same ni a wacan gidan, akwai zan maka wani tayi ne kuma ina fatar ka amsa”
“Okay what time zan zo?”
“An jima da yamma”
“Okay Allah ya kai mu”
Ta kashe kiran. Kai ya girgiza yana cizon bakinsa.
“Ta tabbata Nably ƴarki ce”
Ya kunna motarsa ya bar gurin. A unguwar su Hajiya sadiya yayi sallah la'asar, 6ana hango lokacin data shiga cikin gidan. Sannan shima yaja motarsa ya shiga cikin gidan.
Yana ta sallama bata amsa masa ba sai da ta fito bedroom sannan ta amsa masa. Cikin ladabi ya gaisheta yana kallon yanayin fuskarta mai ɗauke da damuwa.
Shi ya fara zama sannan itama ta zauna tana kallonsa.
“Asim ya maganar matar ka ta dawo kuwa?”
Ya ɗan sosa kansa.
“A'ah nayi nayi taƙi dawowa, kuma yanzu ta daina ɗaukar wayata ma, gashi ba gidansu ta je ba”
“Yanzu dai babu zancen dawowar ta kenan?”
“Gaskiya babu shi, daman ni dan kin matsa ne shiyasa nake son na dawo da ita”
Ajiyar zuciya ta sauke, sannan ta kalleshi a natse ta ce.
“Asim ina son ka auri yata, kuma auren shekara ɗaya, zan baka miliyan ashiri, zan baka gurin da zaku zauna, bana buƙatar ka yi komai, zan maka lefe zan baka kuɗin sadaki, zan mallaka maka shagona na siyar da zinari da sabuwar kasuwa, kuma duk wani event da za ayi ni zan ɗauki nauyi”
Da sauri Asim ya miƙe tsaye yana mamakin irin wannan narkakkiyar dukiyar da zata bashi, saboda kawai ya auri ƴarta ƴar da bata taɓa labarta masa tana da ita ba.
________________________________
BEST REGARDS 🌹
I LOVE YOU ALL♥️
*77*
Kalsoom ta yi baya-baya kamar zata koma ɗaki, sai Rashida ta yi saurin miƙewa tsaye ta ɗaga mata hannu.
“Dan Allah ki tsaya ki saurare ni, ba cutar da ke zan yi ba, zuwa na yi na roƙe ki kuma na nemi taimakon ki”
“Akan mi, mi zan miki?”
“Ki dubi girman Allah ki taimaka min ki riƙe min ƴaƴana...”
“Ban gane ba, kamar ya ƴaƴanki?”
“Bana son amaryar da Hilal yayi ta riƙe su, saboda bata da tarbiya kuma azzulamace zata iya cutar da su”
Kalsoom ta nuna ta da yatsa tana mai jin duk wani tsoro nata ya tafi.
“Ke Rashida yadda kika yi boko haka nima nayi, karki nemi raina min hankali wato na rikasu a sake cewa zan kashe su ko? Naga dai yanzu mu biyu ne, be kamata ace ni kaɗai kike kishi da ni ba”
Hawaye ya cika idon Rashida.
“Ba kishinki nake ba wallahi, gaskiya nake faɗa miki kuma nake roƙon ki, ki taimaki rayuwar ƴaƴana ki riƙe su”
“Teema ce tafi kowa dacewa data riƙa ƴaƴanki, saboda ita ce ta gari a idon Hajiya, kuma an yarda da tarbiyarta, sannan naga ƙawarki zata kula miki da su kamar ke, dan haka ki fita ki bar min gida ko na kira Hilal yanzu na faɗa masa”
Ta share hawayen da suka zubo mata.
“Ba sai kin kira shi ba, zan fita, na gode da kika saurare ni, ban cancanci ki saurareni ba amman kin saurare ni na gode sosai”
Ta saka niƙab ɗinsa, sannan ta juya cikin kuka ta fice. Rufa nata baya Kalsoom ta yi, ta tsaya bakin ƙofa tana kallonta, har sai da taga ta shiga motarta mai gadi ya buɗe mata gate ta fice sannan hankalinta ya kawanta.
“Allah ya min tsari da sherin ki ni wannan wane irin mugun kishi ne!”
Ta faɗa tana maida ƙofar falon ta rufe.
*** *** ***
Da wani irin kuka Rashida ta ƙarasa gida, tana mai jin zuciyarta kamar zata tsage biyu, saboda baƙinciki da damuwa, ta rasa inda zata sa ranta taji sanyi, ta rasa inda zata saka rayuwarta ta samu sassauci, lokaci ɗaya duniya ta juye mata ta zo mata baibai.
Bata samu gurin faka motarta ba saboda motar Alhaji Bashir da ke waje, hakan ya tabbatar mata da yana ciki kenan.
Tafiya take kamar wata tsohowa, daman bata da wani kuzari saboda rashin cin abincin kirki da kuma damuwar da ta gama karya mata gaɓoɓin jiki.
Safa da marwa ta hango yana yi a ƙofar shiga falonta, ko be faɗa mata ba, tasan Asmee ta kai masa labarin da ta faɗa mata ɗazun ne, dan tana iya hango tashin hankalin dake shimfiɗe saman fuskarsa. Tun kamin ta ƙaraso inda yake, ya soma nuna ta da hannu, cikin wata irin murya da shi kansa be san yana da ita ba.
“Macuciya azzaluma, dan taki rayuwar ta ƙare shine kike neman abokin kuka ko? To nafi ƙarfin ki Wallahi baki isa ki rushe min rayuwa ba”
“Kamin ka zo nan kana min hargagin banza ina fatar kaje asibiti sun tabbatar maka da kana ɗauke da cutar ko? To ni ba abokin kuka nake nema ba, kai ne kake neman abokin mutuwa, dan rayuwa sai ta fi taka tsawo, sannan na gama rushe maka rayuwa Alh Bashir matuƙar baka aure ni, dan ban dace da zama da kowa ba sai kai, kai ne ka sani a halin da nake ciki”
“Ko kuma kika sani ciki ba, daman ai na daɗe ina zarginki, duk mace da zata bada kanta ga wani namiji ba mutum ɗaya zata tsaya ba, waya sani ma ko mijinki ne ya ɗauko cutar ya saka miki ke kuma kika saka mana, ni ban san ƙaddararta kai ni mu'amala da ke ba”
“Ni bance ka zame min ƙaddara ba kai zaka ce na zame maka? Na rasa abubuwa da dama sanadin mu'alama da kai, ƴan'uwana sun guje ni, mijina ya sake ni, na rasa lafiya ta, da duk wani farinciki nawa sanadinka Bashir, duk kai ka jani ga wannan halaka”
“Ko kuma kika jani ba, da baki sake jikinki ba zan gani ne har na yi sha'awa? Idan baki yarda ba fyaɗe zan miki ne? Baki kiji na faɗa miki da zarar naje aka gwada jinina aka tabbatar ina ɗauke da wannan cutar kutu ce zata raba ni da ke...!”
Yana kaiwa nan ya doshi gurin motarsa. Ita kuwa ta raka shi da maganganu tana hawaye.
“Idan ka fasa kai ni kotu baka haifu ga uwarka da ubanka ba Bashir kai ba ɗan halak ba ne, azzalumi macuci wanda be ji kunya keta dokar Allah, sakarai mai neman Matar abokinsa Allah ya isa tsakanina da kai”
Sai ta ta kunna motarsa ya bar gidan sannan ta durƙushe a gurin tana kuka.
“Kaico na ni Rashida, ina ake siyar da farinciki ne na siya! Ina zan yi musanyar damuwa da kuka na samu sanyin zuciya! Mi na ma duniya haka ne? Miyasa suka ƙaddarori zasu taru a kai na ne? Allah na tuba ka yafe idan zunubi na ne yasa ni a wannan halin”
Kuka take sosai tana ji kamar ƙasa ta haɗiyeta ta mutu ta huta gaba ɗaya da wannan rayuwar. Ra rasa dalilin daya sa rayuwa take koya mata darussan da take ganin bata cancanci koyansu ba.
NAMRA POV.
Kai tsaye direban ya nufi gidan Mai Martaba kamar yadda Yarima ya umarce shi, horn ɗaya yayi aka buɗe musu gate, ɗayan part ɗin gidan ya nufa da su, sai ya faka daidai ƙofar part ɗin ya fito da sauri ya buɗe ma Abbah ƙofa.
“Ya ce akwai komai a ciki, idan akwai abunda kuke buƙata zaku min magana”
Kai kawai Abbah ya ɗaga masa ya nufi ƙofar. Anty Amarya ce ta amsa masa da to, Namra na riƙe da hannun Anty kanta kuma kwance saman kafaɗar Anty, har suka shiga falo, sanyin ac ne ya fara musu martabun, daga bisani ƙamshi ya biyo baya. Kai tsaye Abbah ya nufi wani ɗaki dake ɗayan ɓangare da wasu ɗakunan, yana shiga ya hango manya tufafi kala biyu saman gadon, sai kuma kayan bachi da ba a cire daga leda ba kala ɗaya, an ɗora takalmi da turare da hula mai kyau saman kayan, hakan ya tabbatar masa nan ne ɗakinsa, ɗan murmushi yayi kaɗan ya rage kayan jikinsa ya nufi bathroom.
Mamaki ya cika Namra da Anty Amarya lokacin kowa ya samu tufafin sajawa da kayan bachi saman gadonsa, bama kamar Namra da ta tarar har da pants da pad ya aje mata, ya akayi yasan bata sallah shine abunda ya fi tsaya mata a rai. Bathroom ta shiga, ta yi wanka, sannan ta shirya cikin kayan bachi masu kama da na maza, ta fito ta nufo falo. Anty Amarya da Abbah ta samu zaune a dinning suna cin abinci. Abbah ne ya fara ɗagowa ya kalleta, murmushin da ta gani a fuskarta yasa idonta cika da ƙwalla.
“Toh Sarkin kuka zaki fara ko?”
Cewar Anty Amarya fuskarta ɗauke da annuri, tana miƙawa Abbah tea da ta haɗa masa.
“Komai ya zo min kamar mafarki, gani nake kamar ba gaske bane, ban yi zaton Abbah zai saurare ni haka da wuri ba har ya yafe min, nasan nayi muku abubuwa marar kyau da yawa, amman duk da haka suka samu fili a zuciyarku kuka yafe min”
“Kin cancanci yafiya Mamana, saboda kin gane kuskurenki, sai dai kin shiga rigar mutane masu mutunci wanda hakan yasa kika samu yafiyata a kusa, sai dai ina fatar ba zaki ƙara aikata irin wannan kuskuren ba”
“Wallahi ba zan sake ba Abbah, na maka alƙawari har na koma ga mahallici na,ba zan sake aikata kwatankwacin wannan kuskuren ba”
“Allah yayi miki albarka”
“Amin Abbah na gode, i love you so much”
Ta zo da sauri ta rumgume shi tana kuka. Anty Amarya ta share hawayen idonta tana kallon Abbah.
“Allah ya saka maka da alheri, na gode”
“Yanzu ai ta kuka da ciwon zuciya ya ƙare ko?”
Cewar Abbah fuskarsa da murmushi yana kallon Anty Amarya cike da son Amaryarsa. Daga bisani ya kalli wayarsa da ke saman dinning tana ringing. Hajiya Barau ce rubuce a screem ɗin wayar. Miƙewa yayi tsaye, sannan ya kai hannu ya ɗauki wayar yana danna picking ya nufi bedroom.
A kujerar da ke kusa da Anty Namra ta zauna, tana share hawayen da suka ƙi tsaya mata.
“Na haɗa miki tea zaki sha?”
Ta gyaɗa kai.
“To ki zuba abincin ki ci idan kin gama zan haɗa miki”
“Bana jin yunwa Anty, tea kawai ya isa”
Ajiyar zuciya Anty ta sauke, ta shiga haɗa mata tea, tana faɗin.
“Namra duk kin rame kin koma wata iri, kin yi baƙi sosai, Yarima ya faɗa mana Asim ya sake ki ne saboda kina da ciki!”
Ta gyaɗa kai tana share hawaye.
“Kuma har yanzu be neme ni ba, ina gidansu Lamido cikin ya zube”
“Kin san ciki ba zai taɓa tsayawa a mahaifarki ba Namra saboda matsalar da kika samu, na yi mamaki ma da kika samu ciki bayan an saka miki roba”
“Shi yace sai na cire, kuma da ma samu cikin yace be shirya haihuwa yanzu ba, sai dai na zaɓa tsakanin cikin da shi, ni kuma na ƙi yarda na zubar shiyasa ya sake ni”
“Kin samu ƴancin kan ki yanzu, Allah zai bi miki haƙƙin ki. Amman ina kika haɗu da wannan yaron”
A nan Namra ta kwashe labarin komai na sanin da tayi ma Abdool ta faɗa ma Anty.
“Yana da mutunci sosai, kuma ina fatar zaki masa hallacci duk ranar da ya nemi ladan alherin da yayi miki”
“Kamar ya?”
Ta tambaya dan har ga Allah ita bata gane inda zancen Anty ya dosa ba. Anty ya miƙe tsaye tana murmushi.
“Kamar haka, ki je ki kwanta dare ya yi, zan kira Maryam na ce ta shirya zan vata mamaki, daman ta fi kowa damuwa da auren nan na ki”
“Na gode sosai Anty sai da safe”
Ta daɗe a gurin zaune sai ƙarewa falon kallo take sannan ta tashi ta nufi bedroom.
Har garin Allah ya waye, dan har yanzu ta kasa yarda da abunda ya faru, ganin komai take kamar mafarki. Idonta biyu aka yi kiran sallah asuba, unƙurawa ta yi ta tashi, sai ta nufi gurin maɓallin kutar ɗakin ta kunna. Ta shiga toilet ta tsabtace kanta sannan ta yi wanka ta fito.
Bata tsaya shafa mai ba, ta ɗauki abaya ta saka, sannan ta ɗora da hijab, gefen gado ta zauna sai ta ɗauki carbi tana lazimi, ba ita ta tashi ba sai bakwai da rabi saura, shi ma dan ta ji ana buga ƙofar falon ne.
Bata damu da tambayi ko waye ba kawai ta kai hannu ta buɗe ƙofar. Suna haɗa ido gabanta yayi mugun faɗuwa, da sauri ta sadda kanta ƙasa, shi kam ƙin sauke idonsa ƴayi har ta miƙa masa gaisuwa.
“Ina kwana?”
“Nan ba ina kwana suke cewa ba”
Ɗan murmushi ta yi wanda be kai zuci ba.
“An tashi lafiya?”
“Lafiya ƙalau, i hope you sleep well?”
“I did”
“Amman idonki ya nuna kamar ba ki yi bachi ba”
“Kana da buƙatar wani abun ne?”
Ta tambaya da nufin kawar da maganar. Wani dogon numfashi yaja ya sauke
“Ban sani ba ko kuna da bukata ne, yanzu zan kama hanya, Mai martaba ya kira ni yana da buƙatar gani na, ajima direba zai ɗauke ki zai kai ki a miki passport, da ƙarfe uku jirgi zai tashi, so za a muku duk wani abun da ya kamata, around nine za a kawo muku breakfast. I think Abbah suna bachi, ki faɗa musu na tafi”
Kai ra gyaɗa masa, sai ya zuba hannyensa aljihu ya juya zai wuce.
“Ab...da...llah”
Ta kira sunansa cikin wata irin siga da ba'a taɓa kiransa sunan yayi masa daɗi kamar yadda ita ɗin ta kira shi ba, har cikin zuciyarsa ya ji kiran nata da muryarta dake kamar zata fasa masa kuka. Juyowa yayi ya kalleta da manyan idanuwansa.
“Thank you”
Gira ɗaya ya ɗaga mata, alamar for?
“For helping me out”
Murmushi yayi mata mai fidda annurin fuskarsa.
“Safe flight”
“Wish you the same”
Murmushi yayi mata as respond ya juya ya cigaba da tafiya abunsa, kamar wanda baya son taka ƙasa. Haka kawai ta samu kanta da kasa ɗauke ido a kansa har sai da ya shige part ɗinsa.
ASIM POV.
Kallo Hajiya Sadiya ta bishi da shi, zuciyarta Allah-Allah ya amince.
“Miyasa zaki min tayi mai tsada akan kawai na auri ƴarki?”
“Saboda kai ne kaɗai na yarda da tarbiyarka, kuma nasan ƴata tana son ka, saboda ta nuna min hoton ka har tace zaka zo ka gaishe ni”
“Ko baki bani komai ba zan iya aurenta saboda aurenta na yi niyar yi, amman ki faɗa min gaskiyar abuda kike ɓoyewa wata ƙila zan iya taimakon ki”
“Ko da baka aureta ba, na yarda ka yi zina da ita, idan ta samu ciki sai ka rabu da ita”
“Miyasa sai ni?”
“Saboda ba zan iya facing yata na faɗa mata ta auri wanda bata so ba, kuma nasan ba zan saka ta aikata zina ba”
“Da baki yi gaggauwa ba, da aurin ƴarƙi zan yi, miyasa baki bar ni na aureta ba, iya ka kice min na turo iyayen Sai a ɗaura mana aure. Ki faɗa min gaskiya mana Hajiya”
“Zauna zan faɗa maka komai, saboda na yarda da kai kuma ina fatar zaka taimake ni”
Ya zauna yana fuskantar ta.
“Sunana Hajiya Sadiya kamar yadda ka sani, an haife ni a garin nan, amman ko da na tashi ban san iyayena ba, mahaifina da mahaifiyata duka Allah yayi musu rasuwar tun kamin na mallaki hankalin kai na, dan haka na tashi a gidan kakana Sarkin Katsina na wacan lokacin, na samu gata iya gata a gidan, duk da bani kaɗai bace wacce ake riƙo a gidan, amman saboda ni marainiyace, be yarda ya bar mu mun yi
Showing 210001 words to 213000 words out of 280121 words
“Idan mutum yana addu'ah babu abunda zai same shi, kawai ka halbe min ita idan zaka iya”
“Toh”
Ya nufi wani part ɗin na gidan, da ɓangarensu yake a can, be ɗauki dogon lokaci ba sai ga shi ya dawo da danƙon har da duwatsunsa guda biyar. Ayatul kursiyo ya karanta sannan ya saita inda take ya harba da bismilla. Firr tayi zata tashi sai ta faɗi saboda ya same ta a ƙafa. Da sauri Abdool ya ƙarasa zai kamata sai ta sake unƙurin tashi ta kasa har ya kama ta, sai da yayi bismillah sannan ya cire layar dake wuyanta. Umar ya miƙawa kuciyar ya shiga buɗe layar. Wasu surkulle ne aka yi aka kulle da fatar baƙar akuya, sai wata farar takardar a tsayarki takardar an rubuta sunan Namra da larabci.
“Namra”
Ya maimata sunan cike da mamaki da ɗaurewar kai.
“Miya kawo sunan Namra anan? Waya aikata mata haka?”
Yayi ma kansa tambayar da bashi da amsar ta.
“Umar kasan yadda ka yi da wannan kurciyar”
Ya faɗa sannan ya shiga cikin falon da abun a hannunsa.
KALSOOM POV.
Hannu ya kai ya shafa fuskarta.
“Haba dai baki kishi ranar ɗaura aure ba sai yanzu zaki yi? Ko dai wani ne ya zuga ki?”
Kai ta girgiza masa alamar a'a, ta janye hannunsa daga fuskarta ta miƙe tsaye.
“Zan shiga wanka”
Hannunta ya riƙe.
“Kalsoom ko na miki wani abu da ba daidai bane?”
Ta saka mashi kuka.
“Baka min komai ba, kawai dai...”
miƙewa yayi tsaye ya haɗe bakinsu, yana shafa bayanta alamar rarrashi. Sun ɗauki tsowon lokaci a haka sannan ya sake ta.
“I promise you ba zan miki wani abu da xai cutar da ke ba”
Ya kwantar da kanta ƙirjinsa. Ba shi take ji ba, Amaryar tasa take ji dan bata san da me tazo mata ba, bata son ta sake shiga irin rayuwar da tayi da Rashida a baya. Sai da ya tabbatar ta samu sukuni sannan ya sake ta yana tambayar me zai siyo mata.
“Ina son zogale”
“Okay”
Yayi mata kiss, ya shafi cikinta sannan ya juya ya fice. A gurin ta tsaya har sai da ta ji tashin motarsa sannan ta shiga wankan. Tana cikin wanka taji tsayawar mota sai kuma kamar ba ta Hilal ba, hankali kwance ta yi wankanta ta ɗaura tawul ta fito. Haka kawai ta ji bata da natsuwa idan bata leƙa taga wanda ya shigo ba, dan haka tana fitowa ta zira doguwar riga ta ɗora ɗankwalin a saman kanta ta nufi falon.
Abunda ta gani ya bala'in ɗaga mata hankali Rashida ce zaune saman kujera tana kallonta, fargaba da tsoro suka tunkarota lokaci ɗaya, idonta be gama tantance Rashida ɗin bace ko waninta, dan ta lalace sosai ta rame, idan har ita ɗince mi tazo yi gurinta, ga ta cikin hijabi niƙab a hannunta.
ASIM POV.
Yana saka kuɗin sai ga kiran Hajiya Sadiya, sai da ya shiga mota sannan ya yi picking.
“Hajiya na saka kuɗin”
“To yayi kyau, ina son muyi wata magana da kai Asim mai muhimmaci”
“Okay na zo kenan?”
“A'ah ba sai ka zo ba, saboda ƴata bata riga ta tafi ba”
“Toh ya za'ayi kenan”
“Ka same ni a wacan gidan, akwai zan maka wani tayi ne kuma ina fatar ka amsa”
“Okay what time zan zo?”
“An jima da yamma”
“Okay Allah ya kai mu”
Ta kashe kiran. Kai ya girgiza yana cizon bakinsa.
“Ta tabbata Nably ƴarki ce”
Ya kunna motarsa ya bar gurin. A unguwar su Hajiya sadiya yayi sallah la'asar, 6ana hango lokacin data shiga cikin gidan. Sannan shima yaja motarsa ya shiga cikin gidan.
Yana ta sallama bata amsa masa ba sai da ta fito bedroom sannan ta amsa masa. Cikin ladabi ya gaisheta yana kallon yanayin fuskarta mai ɗauke da damuwa.
Shi ya fara zama sannan itama ta zauna tana kallonsa.
“Asim ya maganar matar ka ta dawo kuwa?”
Ya ɗan sosa kansa.
“A'ah nayi nayi taƙi dawowa, kuma yanzu ta daina ɗaukar wayata ma, gashi ba gidansu ta je ba”
“Yanzu dai babu zancen dawowar ta kenan?”
“Gaskiya babu shi, daman ni dan kin matsa ne shiyasa nake son na dawo da ita”
Ajiyar zuciya ta sauke, sannan ta kalleshi a natse ta ce.
“Asim ina son ka auri yata, kuma auren shekara ɗaya, zan baka miliyan ashiri, zan baka gurin da zaku zauna, bana buƙatar ka yi komai, zan maka lefe zan baka kuɗin sadaki, zan mallaka maka shagona na siyar da zinari da sabuwar kasuwa, kuma duk wani event da za ayi ni zan ɗauki nauyi”
Da sauri Asim ya miƙe tsaye yana mamakin irin wannan narkakkiyar dukiyar da zata bashi, saboda kawai ya auri ƴarta ƴar da bata taɓa labarta masa tana da ita ba.
________________________________
BEST REGARDS 🌹
I LOVE YOU ALL♥️
*77*
Kalsoom ta yi baya-baya kamar zata koma ɗaki, sai Rashida ta yi saurin miƙewa tsaye ta ɗaga mata hannu.
“Dan Allah ki tsaya ki saurare ni, ba cutar da ke zan yi ba, zuwa na yi na roƙe ki kuma na nemi taimakon ki”
“Akan mi, mi zan miki?”
“Ki dubi girman Allah ki taimaka min ki riƙe min ƴaƴana...”
“Ban gane ba, kamar ya ƴaƴanki?”
“Bana son amaryar da Hilal yayi ta riƙe su, saboda bata da tarbiya kuma azzulamace zata iya cutar da su”
Kalsoom ta nuna ta da yatsa tana mai jin duk wani tsoro nata ya tafi.
“Ke Rashida yadda kika yi boko haka nima nayi, karki nemi raina min hankali wato na rikasu a sake cewa zan kashe su ko? Naga dai yanzu mu biyu ne, be kamata ace ni kaɗai kike kishi da ni ba”
Hawaye ya cika idon Rashida.
“Ba kishinki nake ba wallahi, gaskiya nake faɗa miki kuma nake roƙon ki, ki taimaki rayuwar ƴaƴana ki riƙe su”
“Teema ce tafi kowa dacewa data riƙa ƴaƴanki, saboda ita ce ta gari a idon Hajiya, kuma an yarda da tarbiyarta, sannan naga ƙawarki zata kula miki da su kamar ke, dan haka ki fita ki bar min gida ko na kira Hilal yanzu na faɗa masa”
Ta share hawayen da suka zubo mata.
“Ba sai kin kira shi ba, zan fita, na gode da kika saurare ni, ban cancanci ki saurareni ba amman kin saurare ni na gode sosai”
Ta saka niƙab ɗinsa, sannan ta juya cikin kuka ta fice. Rufa nata baya Kalsoom ta yi, ta tsaya bakin ƙofa tana kallonta, har sai da taga ta shiga motarta mai gadi ya buɗe mata gate ta fice sannan hankalinta ya kawanta.
“Allah ya min tsari da sherin ki ni wannan wane irin mugun kishi ne!”
Ta faɗa tana maida ƙofar falon ta rufe.
*** *** ***
Da wani irin kuka Rashida ta ƙarasa gida, tana mai jin zuciyarta kamar zata tsage biyu, saboda baƙinciki da damuwa, ta rasa inda zata sa ranta taji sanyi, ta rasa inda zata saka rayuwarta ta samu sassauci, lokaci ɗaya duniya ta juye mata ta zo mata baibai.
Bata samu gurin faka motarta ba saboda motar Alhaji Bashir da ke waje, hakan ya tabbatar mata da yana ciki kenan.
Tafiya take kamar wata tsohowa, daman bata da wani kuzari saboda rashin cin abincin kirki da kuma damuwar da ta gama karya mata gaɓoɓin jiki.
Safa da marwa ta hango yana yi a ƙofar shiga falonta, ko be faɗa mata ba, tasan Asmee ta kai masa labarin da ta faɗa mata ɗazun ne, dan tana iya hango tashin hankalin dake shimfiɗe saman fuskarsa. Tun kamin ta ƙaraso inda yake, ya soma nuna ta da hannu, cikin wata irin murya da shi kansa be san yana da ita ba.
“Macuciya azzaluma, dan taki rayuwar ta ƙare shine kike neman abokin kuka ko? To nafi ƙarfin ki Wallahi baki isa ki rushe min rayuwa ba”
“Kamin ka zo nan kana min hargagin banza ina fatar kaje asibiti sun tabbatar maka da kana ɗauke da cutar ko? To ni ba abokin kuka nake nema ba, kai ne kake neman abokin mutuwa, dan rayuwa sai ta fi taka tsawo, sannan na gama rushe maka rayuwa Alh Bashir matuƙar baka aure ni, dan ban dace da zama da kowa ba sai kai, kai ne ka sani a halin da nake ciki”
“Ko kuma kika sani ciki ba, daman ai na daɗe ina zarginki, duk mace da zata bada kanta ga wani namiji ba mutum ɗaya zata tsaya ba, waya sani ma ko mijinki ne ya ɗauko cutar ya saka miki ke kuma kika saka mana, ni ban san ƙaddararta kai ni mu'amala da ke ba”
“Ni bance ka zame min ƙaddara ba kai zaka ce na zame maka? Na rasa abubuwa da dama sanadin mu'alama da kai, ƴan'uwana sun guje ni, mijina ya sake ni, na rasa lafiya ta, da duk wani farinciki nawa sanadinka Bashir, duk kai ka jani ga wannan halaka”
“Ko kuma kika jani ba, da baki sake jikinki ba zan gani ne har na yi sha'awa? Idan baki yarda ba fyaɗe zan miki ne? Baki kiji na faɗa miki da zarar naje aka gwada jinina aka tabbatar ina ɗauke da wannan cutar kutu ce zata raba ni da ke...!”
Yana kaiwa nan ya doshi gurin motarsa. Ita kuwa ta raka shi da maganganu tana hawaye.
“Idan ka fasa kai ni kotu baka haifu ga uwarka da ubanka ba Bashir kai ba ɗan halak ba ne, azzalumi macuci wanda be ji kunya keta dokar Allah, sakarai mai neman Matar abokinsa Allah ya isa tsakanina da kai”
Sai ta ta kunna motarsa ya bar gidan sannan ta durƙushe a gurin tana kuka.
“Kaico na ni Rashida, ina ake siyar da farinciki ne na siya! Ina zan yi musanyar damuwa da kuka na samu sanyin zuciya! Mi na ma duniya haka ne? Miyasa suka ƙaddarori zasu taru a kai na ne? Allah na tuba ka yafe idan zunubi na ne yasa ni a wannan halin”
Kuka take sosai tana ji kamar ƙasa ta haɗiyeta ta mutu ta huta gaba ɗaya da wannan rayuwar. Ra rasa dalilin daya sa rayuwa take koya mata darussan da take ganin bata cancanci koyansu ba.
NAMRA POV.
Kai tsaye direban ya nufi gidan Mai Martaba kamar yadda Yarima ya umarce shi, horn ɗaya yayi aka buɗe musu gate, ɗayan part ɗin gidan ya nufa da su, sai ya faka daidai ƙofar part ɗin ya fito da sauri ya buɗe ma Abbah ƙofa.
“Ya ce akwai komai a ciki, idan akwai abunda kuke buƙata zaku min magana”
Kai kawai Abbah ya ɗaga masa ya nufi ƙofar. Anty Amarya ce ta amsa masa da to, Namra na riƙe da hannun Anty kanta kuma kwance saman kafaɗar Anty, har suka shiga falo, sanyin ac ne ya fara musu martabun, daga bisani ƙamshi ya biyo baya. Kai tsaye Abbah ya nufi wani ɗaki dake ɗayan ɓangare da wasu ɗakunan, yana shiga ya hango manya tufafi kala biyu saman gadon, sai kuma kayan bachi da ba a cire daga leda ba kala ɗaya, an ɗora takalmi da turare da hula mai kyau saman kayan, hakan ya tabbatar masa nan ne ɗakinsa, ɗan murmushi yayi kaɗan ya rage kayan jikinsa ya nufi bathroom.
Mamaki ya cika Namra da Anty Amarya lokacin kowa ya samu tufafin sajawa da kayan bachi saman gadonsa, bama kamar Namra da ta tarar har da pants da pad ya aje mata, ya akayi yasan bata sallah shine abunda ya fi tsaya mata a rai. Bathroom ta shiga, ta yi wanka, sannan ta shirya cikin kayan bachi masu kama da na maza, ta fito ta nufo falo. Anty Amarya da Abbah ta samu zaune a dinning suna cin abinci. Abbah ne ya fara ɗagowa ya kalleta, murmushin da ta gani a fuskarta yasa idonta cika da ƙwalla.
“Toh Sarkin kuka zaki fara ko?”
Cewar Anty Amarya fuskarta ɗauke da annuri, tana miƙawa Abbah tea da ta haɗa masa.
“Komai ya zo min kamar mafarki, gani nake kamar ba gaske bane, ban yi zaton Abbah zai saurare ni haka da wuri ba har ya yafe min, nasan nayi muku abubuwa marar kyau da yawa, amman duk da haka suka samu fili a zuciyarku kuka yafe min”
“Kin cancanci yafiya Mamana, saboda kin gane kuskurenki, sai dai kin shiga rigar mutane masu mutunci wanda hakan yasa kika samu yafiyata a kusa, sai dai ina fatar ba zaki ƙara aikata irin wannan kuskuren ba”
“Wallahi ba zan sake ba Abbah, na maka alƙawari har na koma ga mahallici na,ba zan sake aikata kwatankwacin wannan kuskuren ba”
“Allah yayi miki albarka”
“Amin Abbah na gode, i love you so much”
Ta zo da sauri ta rumgume shi tana kuka. Anty Amarya ta share hawayen idonta tana kallon Abbah.
“Allah ya saka maka da alheri, na gode”
“Yanzu ai ta kuka da ciwon zuciya ya ƙare ko?”
Cewar Abbah fuskarsa da murmushi yana kallon Anty Amarya cike da son Amaryarsa. Daga bisani ya kalli wayarsa da ke saman dinning tana ringing. Hajiya Barau ce rubuce a screem ɗin wayar. Miƙewa yayi tsaye, sannan ya kai hannu ya ɗauki wayar yana danna picking ya nufi bedroom.
A kujerar da ke kusa da Anty Namra ta zauna, tana share hawayen da suka ƙi tsaya mata.
“Na haɗa miki tea zaki sha?”
Ta gyaɗa kai.
“To ki zuba abincin ki ci idan kin gama zan haɗa miki”
“Bana jin yunwa Anty, tea kawai ya isa”
Ajiyar zuciya Anty ta sauke, ta shiga haɗa mata tea, tana faɗin.
“Namra duk kin rame kin koma wata iri, kin yi baƙi sosai, Yarima ya faɗa mana Asim ya sake ki ne saboda kina da ciki!”
Ta gyaɗa kai tana share hawaye.
“Kuma har yanzu be neme ni ba, ina gidansu Lamido cikin ya zube”
“Kin san ciki ba zai taɓa tsayawa a mahaifarki ba Namra saboda matsalar da kika samu, na yi mamaki ma da kika samu ciki bayan an saka miki roba”
“Shi yace sai na cire, kuma da ma samu cikin yace be shirya haihuwa yanzu ba, sai dai na zaɓa tsakanin cikin da shi, ni kuma na ƙi yarda na zubar shiyasa ya sake ni”
“Kin samu ƴancin kan ki yanzu, Allah zai bi miki haƙƙin ki. Amman ina kika haɗu da wannan yaron”
A nan Namra ta kwashe labarin komai na sanin da tayi ma Abdool ta faɗa ma Anty.
“Yana da mutunci sosai, kuma ina fatar zaki masa hallacci duk ranar da ya nemi ladan alherin da yayi miki”
“Kamar ya?”
Ta tambaya dan har ga Allah ita bata gane inda zancen Anty ya dosa ba. Anty ya miƙe tsaye tana murmushi.
“Kamar haka, ki je ki kwanta dare ya yi, zan kira Maryam na ce ta shirya zan vata mamaki, daman ta fi kowa damuwa da auren nan na ki”
“Na gode sosai Anty sai da safe”
Ta daɗe a gurin zaune sai ƙarewa falon kallo take sannan ta tashi ta nufi bedroom.
Har garin Allah ya waye, dan har yanzu ta kasa yarda da abunda ya faru, ganin komai take kamar mafarki. Idonta biyu aka yi kiran sallah asuba, unƙurawa ta yi ta tashi, sai ta nufi gurin maɓallin kutar ɗakin ta kunna. Ta shiga toilet ta tsabtace kanta sannan ta yi wanka ta fito.
Bata tsaya shafa mai ba, ta ɗauki abaya ta saka, sannan ta ɗora da hijab, gefen gado ta zauna sai ta ɗauki carbi tana lazimi, ba ita ta tashi ba sai bakwai da rabi saura, shi ma dan ta ji ana buga ƙofar falon ne.
Bata damu da tambayi ko waye ba kawai ta kai hannu ta buɗe ƙofar. Suna haɗa ido gabanta yayi mugun faɗuwa, da sauri ta sadda kanta ƙasa, shi kam ƙin sauke idonsa ƴayi har ta miƙa masa gaisuwa.
“Ina kwana?”
“Nan ba ina kwana suke cewa ba”
Ɗan murmushi ta yi wanda be kai zuci ba.
“An tashi lafiya?”
“Lafiya ƙalau, i hope you sleep well?”
“I did”
“Amman idonki ya nuna kamar ba ki yi bachi ba”
“Kana da buƙatar wani abun ne?”
Ta tambaya da nufin kawar da maganar. Wani dogon numfashi yaja ya sauke
“Ban sani ba ko kuna da bukata ne, yanzu zan kama hanya, Mai martaba ya kira ni yana da buƙatar gani na, ajima direba zai ɗauke ki zai kai ki a miki passport, da ƙarfe uku jirgi zai tashi, so za a muku duk wani abun da ya kamata, around nine za a kawo muku breakfast. I think Abbah suna bachi, ki faɗa musu na tafi”
Kai ra gyaɗa masa, sai ya zuba hannyensa aljihu ya juya zai wuce.
“Ab...da...llah”
Ta kira sunansa cikin wata irin siga da ba'a taɓa kiransa sunan yayi masa daɗi kamar yadda ita ɗin ta kira shi ba, har cikin zuciyarsa ya ji kiran nata da muryarta dake kamar zata fasa masa kuka. Juyowa yayi ya kalleta da manyan idanuwansa.
“Thank you”
Gira ɗaya ya ɗaga mata, alamar for?
“For helping me out”
Murmushi yayi mata mai fidda annurin fuskarsa.
“Safe flight”
“Wish you the same”
Murmushi yayi mata as respond ya juya ya cigaba da tafiya abunsa, kamar wanda baya son taka ƙasa. Haka kawai ta samu kanta da kasa ɗauke ido a kansa har sai da ya shige part ɗinsa.
ASIM POV.
Kallo Hajiya Sadiya ta bishi da shi, zuciyarta Allah-Allah ya amince.
“Miyasa zaki min tayi mai tsada akan kawai na auri ƴarki?”
“Saboda kai ne kaɗai na yarda da tarbiyarka, kuma nasan ƴata tana son ka, saboda ta nuna min hoton ka har tace zaka zo ka gaishe ni”
“Ko baki bani komai ba zan iya aurenta saboda aurenta na yi niyar yi, amman ki faɗa min gaskiyar abuda kike ɓoyewa wata ƙila zan iya taimakon ki”
“Ko da baka aureta ba, na yarda ka yi zina da ita, idan ta samu ciki sai ka rabu da ita”
“Miyasa sai ni?”
“Saboda ba zan iya facing yata na faɗa mata ta auri wanda bata so ba, kuma nasan ba zan saka ta aikata zina ba”
“Da baki yi gaggauwa ba, da aurin ƴarƙi zan yi, miyasa baki bar ni na aureta ba, iya ka kice min na turo iyayen Sai a ɗaura mana aure. Ki faɗa min gaskiya mana Hajiya”
“Zauna zan faɗa maka komai, saboda na yarda da kai kuma ina fatar zaka taimake ni”
Ya zauna yana fuskantar ta.
“Sunana Hajiya Sadiya kamar yadda ka sani, an haife ni a garin nan, amman ko da na tashi ban san iyayena ba, mahaifina da mahaifiyata duka Allah yayi musu rasuwar tun kamin na mallaki hankalin kai na, dan haka na tashi a gidan kakana Sarkin Katsina na wacan lokacin, na samu gata iya gata a gidan, duk da bani kaɗai bace wacce ake riƙo a gidan, amman saboda ni marainiyace, be yarda ya bar mu mun yi
Book Chapters
Chapter 1Chapter 2Chapter 3Chapter 4Chapter 5Chapter 6Chapter 7Chapter 8Chapter 9Chapter 10Chapter 11Chapter 12Chapter 13Chapter 14Chapter 15Chapter 16Chapter 17Chapter 18Chapter 19Chapter 20Chapter 21Chapter 22Chapter 23Chapter 24Chapter 25Chapter 26Chapter 27Chapter 28Chapter 29Chapter 30Chapter 31Chapter 32Chapter 33Chapter 34Chapter 35Chapter 36Chapter 37Chapter 38Chapter 39Chapter 40Chapter 41Chapter 42Chapter 43Chapter 44Chapter 45Chapter 46Chapter 47Chapter 48Chapter 49Chapter 50Chapter 51Chapter 52Chapter 53Chapter 54Chapter 55Chapter 56Chapter 57Chapter 58Chapter 59Chapter 60Chapter 61Chapter 62Chapter 63Chapter 64Chapter 65Chapter 66Chapter 67Chapter 68Chapter 69Chapter 70Chapter 71 Chapter 72Chapter 73Chapter 74Chapter 75Chapter 76Chapter 77Chapter 78Chapter 79Chapter 80Chapter 81Chapter 82Chapter 83Chapter 84Chapter 85Chapter 86Chapter 87Chapter 88Chapter 89Chapter 90Chapter 91Chapter 92Chapter 93Chapter 94