ya tambaye ni wai ko ka taɓa haɗarin mota nace masa aa, ko ka taɓa yi baka faɗa ba?”

Hawaye suka fara masa zuba.

“Innalillahi wa'inna ilaihi raji'un. Wannan wane irin bala'i ne? Miya faru da ni ne haka, Hajiya ko dai mafarki na ke yi? Allah kasa na farka Allah wayyo ni Allah na”

Haka ƴa ɗinga maganganu Abbah sai kallonsa yake cike da tausayawa, suna haka sai ga wasu friends nasa sun shigo duba shi ciki har da Dr Tahir, da wasu abokanin sha-shancinsu na Abuja. Abbah suka fara tambaya ya mai jiki ya amsa musu da sauƙi sannan suka gaishe da Hajiya dake ta sharar hawaye, suka matsa kusa da Uzair suka tsaya suna masa ya jiki.

Amsa musu kawai yake amman kana ganinsa kasan ya rikice, ba fita hanyyacinsa yayi ba, amman wannan ƙaddarar da ta faɗo masa ya gaza yarda da ita, ta ya zai zama haka mutumen da ke tafiya lafiyarsa ƙalau shi ba faɗowa yayi ba shi ba haɗari ba ace ya haɗu da wannan matsalar, ta ya haka zai faru?
Sun aje masa kuɗi mai yawa ban cin siyayyar da suka masa, Abbah na yayi musu godiya, suka kama hanya suna Allah ya sauwaƙe, sai kawai Uzair ya ƙwalawa Tahir kira, cikin sauri ya juyo ya nufo inda yake su kuma sauran abokan suka fice.

“Ina son mu yi magana da kai Abbah dan Allah ku ɗan ba mu guri”

Daga Hajiya har Abbah tashi suka yi suka fita, sai Tahir ya zauna a kujerar da Abbah ya tashi yana fuskantar Uzair ya ce.

“Na je gida na samu baka nan, matar ka ce kawai, naje na saboda na ta buga wayarka ban samu ba, kuma naje guest house ɗin ka baka nan, babu abunda matarka bata faɗa min ba, har ɗan wuta ta kira ni, daman ta san kana wannan harkar ne?”

“Shekaran jiya ta gano, lokacin da na Amira ta aiko min da saƙo, ni zargin nake ma ko ita ce ta yi min wannan asirin na koma haka ne? Da wannan daga gani lamarin iska ne aljanu ne”

“Ko kuma Amira ba saboda ta dawo na samu labarin gurin Yayanta”

“Lallai zata iya min asiri, yarinyar nan muguwace”

“Zata maka ko kuma zai dawo kan ka idan na jikinta ya kare? Kasan fa bokan nan yace maka idan be kama Namra ba, zai dawo gun ka ne, sai gashi ya kama Amira yanzu kuma Amira ta dawo ina tunanin kai zai dawoma”

“Dan Allah Tahir kaje gurin bokan nan ka faɗa nasa halin da muke ciki, idan ma wani ne yayi min ya san yadda zai yi ya kare shi, idan kuma wannan aikin ne ya kare shi dan Allah Tahir”

Tahir ya dafa shi.

“Zanje karka samu damuwa zan je har can na masa magana duk yadda aka yi zuwa yamma zan dawo na faɗa maka”

“Tahir ba sai yamma ba, kaje yanzu baka ganin halin da nake ciki...?”

Ya ƙarasa cikin kuka mai ban tausayi.

“Okay zanje yanzu Allah ya baka lafiya”

“Na gode”

Ya faɗa hawaye na zuba a idonsa. Jikin sanyin jiki Tahir ya fice yana mamakin lamarin Uzair.

ASIM POV.

Yayi rama sosai a ƴan kwanakin nan da aka yi na amsar gaisuwa, Ranar da aka kwana ɗaya da rasuwar Ƴan gidansu Mardiya suka zo har da Mardiyar gurin gaisuwa, a nan ne yake nunawa wasu ita yana cewar ita ce matar da yake son aure.

Bayan an yi addu'ah uku ya ɗaure ya ƙara kwana biyu saboda masu zuwa ƙara masa gaisuwa. A ranar ne Mama Inno ta raba yaran ta ɗauki Hajara da ƙanenta biyu wasu daga ɓangaren mahaifinsu suka raba sauran ƴaƴan, abun gwanin tausayi, ranar Asim ya ci kuka kamar zai haɗiye zuciya ya mutu dan baƙin ciki, ashe Mama bata da rabon ta shiga gidan da yake da niyar sai mata, be taɓa baƙin cikin haɗuwa da Hajiya Sadiya ba sai yau, ji yayi kamar ace tana kusa da shi ya kamata yayi mata gunduwa-gunduwa, gashi ita kuma sai damunsa take da kira, yana ce mata bashi da lafiya.
Be yarda ya labartawa Nably abunda ya faru ba, amman yana faɗa mata bashi da lafiya kuma tace zata zo ganinsa ya hana, ita kuma duk hankalinta ya tashi hakan ya hanata komawa Abuja, dan ya faɗa mata ranar da zai dawo.

Ranar da bar sokoto sai da yayi kamar zai kashe kansa, gudu ya riƙayi da motar yana kuka kamar zai tashi sama. Da wuri ya isa Katsina saboda ya tashi tun asuba ne, ɗan kawai kar Hajiya ta gane halin da yake ciki ne yasa ya sauka nasarawa, dan yin wanka ya shirya ya canja tufafi. Daga wankan har shirin be ɗauke shi minti talatin ba, yana gamawa ya fito ya nufi gurin da motarsa take. Juyowa ya yi yana kallon gidan.
  Be taɓa jin yayi missing ɗin Namra ba sai yau, haka kawai yau da ya tuna ta sai ya ji babu daɗi, daya tuna mamarsa sai Namra ta faɗo masa a rai, jikin rashin daɗin rai ya nufi gidan Hajiya Sadiya.

Sai da ya kama hanyar gidan sannan ya kira ya faɗa mata gashi nan ya shigo katsina har ma ya iso gidan.

“Okay okay galni nan zuwa”

Ko minti goma sha biyar ba'ayi ba, sai gata ta iso. Yayita ƙoƙarin danne damuwarsa ya nuna mata mara rashin lafiya ne kawai matsalarsa, bayan sun zauna a falo yake labarta masa yadda rashin lafiyar ta fara da fever kwanansa biyu asibiti.

“Gaskiya ka ji jiki sosai, ka rame Allah ya ƙara lafiya”

Da Amin ya amsa yana mata wani irin kallo wanda shi kaɗai yasan Manufarsa da kuma abinda yake ji a ransa a tare da shi. Ta shi tayi ta shiga ɗaki dan ɗauko masa apple ɗin, shi kuma ya fidɗo wayarsa ya aikawa Nably saƙo.

_Ki same ni a Dahir Exclusive Restaurant, yanzu ina gurin_

In few minutes ta masa reply.

_Okay on my way_

Ya aika mata da saƙon ne a yanzu dan ya samu ta fita gidan kamin Hajiya ta san wani abu kai, dan yasan ba zata bari ta fita ba.

Ta daɗe a ɗakin sannan ta fito riƙe da farin ƙyale da kuma jika ƙarama mai kamar hand bag, jakar ta fara jefa masa.

“Miliyan biyar ne a ciki, dan Allah Asim ka tabbatar ba a samu matsala irin waccan karon ba, ka ɗauki abun nan da muhimmanci sosai”

“Ba za a samu matsala ba wannan karon na miki alƙawari”

Ya faɗa kamar da gaske. Sannan ya miƙa mata hannu, ta bashi apple ɗin ya ɗauki jakar ya fice zuciyarsa har mazari take ya isa gurin da yake zaton Nably ta isa. Yana shiga mota tana kiransa tace masa gata nan gakin gate.

“Gani nan zuwa yanzu”

Ya kashe wayar, a hanya ya tsaya ya siye wani Apple green, sannan ya ƙarasa restaurant ɗin, yana fakin motarsa ya hangota tsaye jikin wata mota da yake zaton ta tace. Tana hangoshi ta ƙaraso kusa da shi idonta tab da ƙwalla, ji tayi kamar ta rumgume shi dan har ga Allah ta yi missing ɗinsa kuma tana son Asim sosai.

“Ya jikinka?”

“Alhamdullah”

Tare suka shiga ciki suka kama tebur, sai yasa aka kawo musu plate da ƴar ƙaramar wuƙa sai fork. Apple ɗin ya fiɗo ya za a mata ɗaya ya ɗauki ɗayan mai green.

“Wannan ita ce tsaraba ta zuciyata na baki ita har abada, wannan kuma ki ɗauke ta a matsayin zuciyarki ce Asim zai cinye”

Dariya ta yi mai cike da shauƙi da kuma so da ƙauna.

“Ai ka daɗe da cinye zuciyata, har ma da ganganjikina gaba ɗaya”

Ya kalli wayarta yana murmushi.

“Ki kashe wayarki kar wani ya dame mu da kira”

Ba musu ta kashe wayar, shi kuma tsoron yake kar Hajiya ta kirata.

“Bana son ki raga komai daga zuciyata. I love you”

“I love you too”

Ta faɗa sannan ta fara hanya apple ɗin ta tasoma ci kamar yadda shi ma ya fara cin nasa, sai fira yake mata kamar gaske ita kuma sai faman murmushi tana faɗa masa irin yadda ta yi missing ɗinsa.

Sai da suka gama cin apple ɗin sannan ya haɗa ma wayarsa alarm ɗin ƙarya ta yadda zai yi kamar an kira shi.

“Ko na miki oder abinci...?”

“A'a na ƙoshi wannan zuciyar taka ba zata bar ni na ci komai ba”

Ya fiddo wayarsa dake saman cinyarsa, yana faɗin.

“Kai Ogaba na kirana”

Yayi picking cikin ladabi kamar gaske.

“Okay to gani zuwa”

Ya sauke wayar tare da miƙewa tsaye.

“Am so sorry Dear Wallahi ana nema Urgent, amman idan kin min izinin tafiya”

“Ba komai daman ni dai burina na ganka, kuma na ganka, take care of yourself”

“I will my love, ke ma ki kula min da kan ki, bari ma saukeki gida ko?”

“No da mota na na zo”

Sai da yaje ya biya kuɗi sannan suka jero suka fito tare, har gurin motarta ya rakata ta kama hannunta ya riƙa ya ɗan murza, yana mai jin tausayinta a ransa, sai dai kuma idan ta tuna Mama sai yaji babu wani tausayi a zuciyarsa. Sai da ta kama hanya sannan ya nufi motarsa ya shiga.




SORRY MY FAN'S🙏
[7/18, 8:14 PM] Khadeeja Candy♥: *84*

*Shafin na ku ne ƴan ZAGON ƘASA CONVERSATION I HEART YOU ALL*

Wani irin taku Abdallah yake mai ɗaukar hankali da burge duk wata mace mai kallonsa. Ko da wasa be kalli gurin da Lamido yake ba, yayi kamar ma be san da shi a gurin ba.

“Surprise...”

Namra ta faɗa tana tare hawayen da ke ƙoƙarin zubo mata. Ɗaya daga cikin murmushinsa mai tsadar nan ya ɗauka ya miƙa mata, yana kallonta cike da shauƙi dan ta masa kyau sosai.

“Surprise is better than disappointed, haka naji turawa na faɗa, faɗa min wanda ya saka idon nan nawa kumbura, na hukuntasa”

Ya faɗa dai-dai lokacin da ya ɗoro ƙafarsa saman matattakar balcony ɗin da suke tsaye. Kallon mamaki na musamman Namra ta yi masa.

“Idon ka ko nawa?”

“Idon ki ai nawa ne”


Ya bata amsa kai tsaye, and yana acting like akwai wani abu a tsakaninsu. Saurin kawar da maganar tare da cewa.

“Meet my Brother. Lamido meet Abdallah”

Lamido ya danne abunda ke zuciyarsa, na kalaman da ya ji Abdallah yayi a yanzu, ya miƙa masa hannu.

“Am Aliyu Adam Lamido”

Wani kallo Abdallah ya watsa masa irin like sai a yanzu ma ya lura da shi, sai kuma ya tsaya kallon hannun kamar mai karantar abu a jikin hannun. Sai kawai ya zuba hannayensa duka biyu a aljihunsa yana ɗaga masa.

“Nice to meet you Lamido”

Ɗan murmushin ƙarfin hali Lamido yayi ya janye hannunsa, abunda be yi ma Namra daɗi ba.

“Baka ga ne shi ba ne? Lamido ne fa wanda...”

“Na gane shi *ABNAM* let talk something important”

New name ɗin da Abdool ya bata ya bata mamaki yana abu kamar su ɗin daman can masoyana, a ɗayan ɓangaren kuma bata jidaɗin kalmarsa ta ƙarshe da ya furta akan Lamido ba. Sai kawai ta kalli Lamido ta ce

“Zan kawo maka keys ɗin kaje ka duba”

Kai kawai ya iya ɗaga mata, fuskarsa na nuna rashin jindaɗin da ke zuciyarsa. Saukowa ta yi saman balcony ɗin ita da Abdool suka nufi ɓangare Abbah gurin da yake sauke baƙinsa.

“Faɗa abunda yasa ki kuka mana Abnan”

“Abun farinciki ne da tsoro da mamaki a lokaci ɗaya”

“Kamar...”

Ajiyar zuciyarta ta sauke ta kai hannu ta tura ƙofar falon.

“Bismillah”

“Thank you”

Ya faɗa sannan ya saka ƙafafunsa cikin falon, sai da ya shiga sannan ita ta shiga ta maida ƙofar ta rufe, sai ta nufi wata ƙofar da zata sadata da part Anty Amarya.

Bata samu kowa a falon Anty ba, sai kawai ta nufi ɗakinta dan labarta mata zuwan Abdallah nan ma sai ta samu bata nan, ɗakin Aisha ta shiga.

“Ke Anty ta shigo nan?”

Ko kallonta Aisha bata yi hankalinta yana kan computer ta, ta kaɗa mata biro alamar no. Namra ta janyo ƙofar ɗakin, ta nufi freezer tana ta tunanin abunda zata haɗa masa, ya zo mata a bazata, bata shirya masa komai ba, Lamido ma bata masa komai ba, su biyu ɗin sun zame mata ƴan uwa babu na wulaƙantawa a cikinsu. Hannu tasa ta dafe kanta kamin ta kai hannu ta buɗe firiza ta ɗauko fruits ta haɗa masa fruit salad, sannan ta haɗa tea da coffee ko wane one cup sai kuma ta ɗauki ƙaton ture ta ɗora kayan sama. Wani tunani ya zo mata na ta canja tufafin da ke jikinta, kar kuma ya ɗauka dan ta ganshi ta canja kaya he may think otherwise. Kai ta girgiza sai kawai ta ɗauki turen ta nufi part ɗin Abbah.

Zaune ta same shi ƙafarsa ɗaya kan ɗaya yana kallon tv, sam ta manta ma bata kunna masa tv ba. Ta dire turen gabansa tana faɗin.

“Na manta ban kunna maka kallon ba”

“Ai na kunna ni ba baƙo ba ne”

Yayi maganar cikin wata kalar murya.

“Ka zo unexpected, ba a shirya maka komai ba”

Ta faɗa tana ɗora fruit salad ɗin da Drink a saman wani ƙaramin tebur da ta janyo ta aje gabansa.

“Tea or coffee?”

Ya daɗe yana kallon gashin kanta da ya buɗe kamar ba zai ce komai ba.

“Da rana”

“Ban san abunda zan kawo maka ba ne... Wai ka ɗan ci kamin na girka maka abinci”

Ta faɗa kamar wacce ta ji kunya.

“Ban zo dan ki girka min komai ba, i just come to see you, kuma na gan ki hankalina ya kwanta”

Ya koma saman kujera ta zauna tana murmushi. Ya sauko da ƙafafunsa ya ɗauki fruit salad ɗin ya fara sha, still idonsa na kan ta yace.

“Ba ni labari”

“Kamar na me...?”

“Komai da komai”

“Nothing new”

“Seriously! What bought Lamido here?”

“Oh... He's my new driver”

“Driver...?”

“Yep Abbah ya kawo min shi ɗazu, zan fara zuwa scul Monday shine Abbah ya samo min sabon direba”

“Nice”

Ya faɗa kamar ba komai. Wayarsa ya fiddo ya kashe flash camera sannan ya shiga ɗaukarta hoto ba tare da ta sani ba, dan yasan idan har yace zai ɗauke hoto ba zata bari ba, kuma sisters nasa da Ummi sun dame shi akan suna son ganinta.
Haka suka ɗauki dogon lokaci a falon ita da shi babu wanda ya iya sake cewa ɗan'uwansa wani abu, kowa da abunda yake tunani, Namra gaba ɗaya hankalinta ya tafi akan halin da Uzair yake ciki, shi kuma hankalinsa ya tafi gurin Lamido dan yana ganin kamar zai masa zagon ƙasa ne, taya zai zauna ya zuba mata ido shi ya riƙa driving ɗinta scul ya sace zuciyarsa shi ya bar shi a nan.

“Zamu iya gaisawa da Abbah?”

“Yeah Yeah yes, bari na kira shi”

Ya miƙe tsaye tana taɓa kanta dan gaba ɗaya hankalinta ya tafi gurin wacan tunanin nata.

Ƙofar da zata sadata da ɗayan falon Abbah ta nufa, tana tura ƙofar falon ta jiyo muryar Abbah sai ruwan bala'i yake, shesshekar kuka na tashi, cike da faɗuwa gaba ta shiga ɗakin Abbah, sai ta samu Anty Amarya da Hajiya Barau zaune ƙasan carpet ko wannensu na kuka. Hajiya Barau ta rashi tana kuka ta fice daga falon, Anty Amarya ta kama ƙafafun Abbah ta riƙe tana kuka.

“Dan Allah karka aikata abunda zaka dawo kana nadama a lokacin da bata da amfani, dukanninmu ƴan'adam ne kuma ajizai masu yawan laifi da kuskure”

“Idan baki daina saka min baki a lamarin gidana ba, ke ma zaki haɗu da ɓacin rai na...”

Juyawa Namra ta yi ta koma jikinta a sanyaye, ba tare da ta kalleshi ba tace.

“Maybe idan ka sake dawowa zaku gaisa”

“Why...?”

“Abbah is not in the mood now”

Hawayen dake idonsa ya zubo muryarta kuma ya soma rawa alamar kuka yana tare da ita. Da sauri Abdool ya taso ya nufo inda take tsaye.

“Faɗa min Abnam, minene? You can't hide the truth”

“Mutumen da na taɓa baka labarin yace ƴana so na kuma ɗan luwaɗi ne, yanzu haka yana asibiti cikin mawuyancin hali, kuma ɗazu ya tara mu ya faɗi gaskiyar duk abunda yayi, ciki har da asirin da ya haɗa kai da Aminiyata Amira yayi min akan na gudu na bar gida, sai gashi asirin be kama ni sai ya kama Amirar Amiyar tawa ita ta gudu ta bar gidansu bata dawo ba sai ranar da na dawo garin nan...”

Ta ƙarasa cikin kuka.

‘Amira...’

Ya maimaita sunan a zuciyarsa, yana kallon zubar hawayen gimbiyarsa.

“Wannan ba abun kuka ba ne abun dariya ne da murna, amman komai daren daɗewa sai gaskiya ta bayyana kuma mai haƙuri mawadaci”

“Aminiyata ce fa, ace ta min irin wannan aikin ai dole na yi kuka, babu yadda ƴan'uwana ba su yi ba akan na rabu da ita amman na ƙi”

“Kin share hawayen ki, shiga ciki ki canja kamin na dawo, zan nuna miki wani abu”

“A'a Abbah ba zai bari ba”

“Zai bari just go”

Be jira amsarta ba, ya juya ya fice yana danna wayarsa.






MANAGE IT PLEASE 🙏
[7/18, 8:14 PM] Khadeeja Candy♥: *83*

Cikin nishaɗi da walwalah ta isa gida, tana faka Motarta Hajiya Sadiya ta fito hankalinta a tashe ta nufi inda take tsaye ta riƙa ta.

“Daga ina kike Nabila?”

“Mun ɗan fita ne da Asim, Lafiya”

“Na kira wayarki a kashe, ina kika je ne?”

“Munje cin abinci ne”

“Me kuka ci? Talk to me”

Ta riƙa fuskarta tana girgizawa. Itakam mamaki duk ya cika ta tashin hankalin da ta gani a fuskar Mahaifiyarta ta ruɗa ta.

“Miyasa kika tambaya?”

Hannunta ta riƙa ta jata suka nufi cikin falon sannan ta zaunar da ita saman kujera itama ta zauna fuskarta da damuwa ta ce.

“Ina tsoron kar ya baki wani abun ne, kin san mutane ba abun yarda ba ne”

“Hmmm Momi Asim ba irin mutanen da kike tunani ba ne, yana da kirki sosai”

“Ba daga nan take ba, Nabila ina fatar be baki Apple kin ci ba?”

“Ya bani apple kam kuma shi ma ya ci”

Ta dafa kanta ta sauko ƙasa ta riƙa hannayen Nably tana kuka.

“Wane irin apple ya ba ki? Na shiga uku na lalace, ya kai ki ya baro Nabila shi kenan, tawa ta ƙare”

“Momi me ke damunki ne?”

Kuka ta yi sosai har hankalin Nably ta tashi sannan ta labarta mata abunda ta shekara da shekaru tana aikatawa. Kuka Nabila ta saka zuciyarta ta cika da baƙinciki.

“Asim yayi daidai idan har da gaske ya bani apple ɗin na ci, na cancanci mutuwa a yanzu, ke ba uwa ba ce Momi, kin shirya kashe wata saboda tsiratar da ƴarki, kin shirya aikata komai saboda duniyarki”

Ta tashi da gudu ta nufi ɗaki tana kuka, saman gado ta zauna tana
Showing 234001 words to 237000 words out of 280121 words