sai a ace a bari ga Allah? Ai musulucin ya ce idan an yi maka cuta ka rama gwargwadon abunda aka yi maka idan ba zaka iya yafewa ba, sannan irin wannan abun bw kamata ace a ba ga Allah ba, sai fa anje lahira kenan fa? Haba ai ƙara ayi mata tun duniya ta kunyata dan Wallahi idan yai wasa har shi sai nasa an kulle”
“A'a Alhaji ya kake magana kamar ba mai tunani ba? Haka sam be dace ba, hukuncin data yanke shine dai-dai”
Ya kawarda fuskarsa daga ta Momy ya kalli Rashida dan a tunaninsa ko Momy ce tayi mata wannan shawarar.
“Ke kina son abi miki kadin yaron ki?”
Ta girgiza kai.
“A'a Abbah na janye, na barta da Allah”
“Akan me?”
“Kawai haka naga ya fi”
“To ni zan bi kadin jika na (grandson) idan ku baku san abunda ake kira da humanity ba, ni na sani... Tashi kije office Allah ya kiyaye hanya”
Ba zata iya musawa Dady ba kar ya zargi wani abu, sai dai zuciyarta bata so haka ba, dan babu banbanci mahaifinta ne yasa ba ita ba. Tasan Hilal zai iya cewa wani sabon salo ne ta mayardar shari'ar gurin Mahaifinta.
A hanyar ta zuwa office ta kira Mom Shuraim, bayan sun gaisa take faɗa mata idan ta tashi daga aiki zata biyo ta gidanta, akwai magana mai muhimmanci da zata yi da ita.har da narke murya tana faɗin wai tana cikin matsala, amman dai sai tazo zata ji komai.
*ABDOOL POV*
Sai ten ya tashi bachi, dan yana yin sallah azuba ya koma bachin gajiya, farkawar da yayi ma a yanzu ba dan ya gaji da bachi bane, sai dan son zuwa gurin da Ummi tayi masa magana ne jiya. Be fito part ɗinsa ba sai da yayi wanka bugaggar shadda mai tsana blue color, ta fito da shi sosai kasancewar fari sol, ga ɓaƙar hulal da ya ɗora akansa kamar wani sabon balarabe,baƙaƙen takalmi ya saka sannan ya feshe jikinsa da turare, ya fito daga part ɗinsa ya nufo part ɗin Ummi shaddar har amsawa take a jikinsa, ga wani maiƙo da take kamar an zuba mata mai.
Ita kanta Ummi sai da tayi murmushi ganin yadda ɗan nata ya fito mashallah kamar ta cinye abunta.
“Ina fatar ka yi addu'ah”
“Addu'ah me?”
“Idan mutum yayi kwaliya ya dubu kansa a madubi yana kyau yace Mashallahu laƙuwwati illa billah, to ko wani yayi maka baki (kanbun baka) Ba zai kama ka ba, idan ma zaka ita ka riƙa karantawa da safe kullum sau uku”
Dariya yayi yana kallon cucumber da Ummi take yankewa ya ɗauki ɗaya ya ci.
“To ni da ba mace ba miye na wani kanbu zai kama ni, amman dai zan riƙa yi”
“It better”
Ya faɗa tana cigaba da yanka cucumber take. Shi kuma ya zauna kusa da ita yana tambayarta yaje yanzu ko sai anjima.
Ƙamshim turarensa ne ya isarwa da Amira saƙon isowarsa a falon. Ras! ras!! ras!!! Ga banta ya faɗi kamar yadda ya basa mata a duk lokacin da ta ji ƙamshin turarensa. Da sauri ta walƙato ta sauko daga saman gadon da take ta nufo falon idonta cike da maitar ganin Abdool kamar bata taɓa ganinsa ba.
Cikin wata irin siga take tafiya, takalmin dake ƙafarta plate ne amman hakan be hana su amsa amon gurin ba saboda yadda take buga da tiles ɗin gurin. Ummi ce kawai ta ɗago ta kalleta wanda kuma ita bata so haka ba. Abdool kam ƙin ɗagowa yayi dan sarai zuciyarsa ta raya masa Amira ce, dan yasan by this time duka ƙanensa suna makaranta.
“Ina kwana”
Ta gaishe shi cikin ladabi har tana son risina masa.
“Lafiya”
A kaikaice ya amsa, yana mai miƙewa tsaye. Wanda hakan be ma Ummi dadi ba,sai kawai ta kada baki ta ce.
“Amira shiga ciki ki ɗauko mayafin ki ki rana yayanki unguwa”
Ta fasa zaman da zata yi ta miƙe ta nufi ɗakin data fito. Sai da ta shige sannan Abdool.ya kalli Ummi yana ware hannayensa ya ce
“Haba Sweet Mom ya za ki min haka? Kin san fa ni Allah be haɗa jinina da mata ba, kuma it so annoying naje da ita unguwa”
Wani Kallo Ummi ta masa.
“Abdool... Karka soma halin Amal, tun da yarinyar nan ta zo kullum tana ciki gida bata fita ita ma ai ƙara ta ga gari ko?”
Be ƙara cewa komai ba ganin Amira ta fito, sai kawai ya jiya ya nufi kowa yana wani shan ƙamshi.
Ko da ta isa har ya tashi motar ita kawao yake jira su wuce. Tana shiga ya fisgi motar kamar baya son ransa har sai da Amira ta tsorata.
Bata ce masa ba, shi ma be ce mata ba haka suka yi ta tafiya har suka isa nasarawa. A bakin gate ɗin gidan yayi parking ya fito yana ƙarewa gidan kallom ganin yadda ya kone.
Yana rufe gambun motar Amira ta buɗe ta fito, sai ya kalleta ya ce
“Ba daɗewa zan yi ba, kina iya zama a cikin kamin na dawo”
Ba musu ta koma cikin motar ta zauna, zuciyarta cike da tunani kala-kala.
Baya tunanin akwai mutane a gidan dan Ummi bata faɗa masa ba, hakan yasa be yi sallama ba ya tura kofar gate ɗin kawai ya shiga ciki. Gaban gidan ya fara dubawa kamin ya zagaya baya, tana nan ya hango mace tana girki a BQ. Hannayensa yasa aljihu ya nufi bq ɗin yana sallamar da kusan shi kaɗai ne zai iya jinta, sai kuma wanda yaga bakinsa ya motsa.
Namra na ganin mutum tayi saurin komawa ciki ta ɗauko hijabinta ta saka sannan ta fito. Ko da ta fito har ya ƙaraso bq ɗin yana ƙare ma bq ɗin kallo dan ita bata yi komai ba.
“Haba Malam waye kai zaka shigo babu sallama”
Dago da dubansa yayi gurin mai maganar. Ganin Namra yasa numfashinsa hijira daga jikinsa ma ɗan wasu daƙiƙu, sannan ya dawo. Be ɗauke idonsa daga gareta ba be kuma kyafta ba, haka ya ƙafe da ido kamar wani hoto. Nan da nan zuciyarsa ta soma rabawa jijiyoyin jikinsa jini da ƙarfi.
Rassss rassss rassss gabansa yake faɗuwa, sai dai kuma ba irin wacan faɗuwar ba, ta tsoro ko fargaba, faɗuwar gaba ne da shi kansa ba zai iya fassara na minene ba.
Ita sai yanzu ta gane ko wanene shi, daman tun ɗazu ta ga ganin kamar fuskar sani, mutume daya bita asibiti. Ƙamshin turaresan ya haddasa mata ciwon kan da bata yi zato ba, daman tun jiya bata cikin daɗin rai.
“Subhanallah malam wannan kallo ya haramta a musulumci”
Daɗin sautinsa yasa shi lumshe ido yana murmushi.
‘A'uzubillahi minal sheidanin rajin’
Ya furta a zuciyarsa yana ƙoƙarin da abunda sheiɗan yake son masa, sannan ya buɗe ido ya haɗe fuska kamar be taba dariya ba.
“Su waye ku?”
“Mu ne waɗanda suka kama hanyar wannan gidan”
Ta amsa masa a gautse.
“Bq kuka kama ko Main house”
“Main house muna ciki aka yi gobara sai muka dawo nan da zama”
“Ina mijin ki?”
“Baya nan ya tafi kasuwa”
“To idan ya zo ki ce an baku one week ku tashi za ayi gyaran gidan”
Gabanta yayi mummunan faɗuwa.
“Innalillahi wa'inna ilaihi dan Allah ku gyara babban gidan sai ku bar mana BQ ɗin wallahi ba mu da gurin zuwa idan muka bar nan, dan Allah ku taimaka mana”
Ta haɗe hannayenta idonta na son cika da ƙwalla.
“Da yaushe ake tarar da mijin ki?”
“Da safe ko kuma da dare guraren goma”
“Okay zan zo na yi magana da shi gobe”
“Allah ya kai mu na gode”
Be sake cewa wani abu ba, ya juyo hannayensa zube a aljihu ya fito gidan. Har lokacin Amira na cikin mota zaune tana jiransa, yana shiga motar yayi mata key suka juya. Wannan karon ita ce ta ke ɗan jansa da fira shi kuma jikinsa duk ya mutu baya ma iya amsa mata. yawancin tambayarta akan gidan ne da kuma unguwar, sai kuma yaba garin Katsina da take. Shi dai har suka isa gida sai dai ya ɗaga mata kai kawai.
Ta rigashi fita daga motar, dan yau ranta fes yake ta ta fita tare da sahibinta. Bata tsaya a falo ba sai kawai ya wuce ɗakinta tana ƙoƙarin ɓoye nishaɗinta. Shi kuma ya zauna a falo, kusa da Ummi da take zaune a inda ya barta ɗazu, sai dai wannan karon ita da Shukura ne kuma carrots take gyarawa.
“Har kun dawo?”
“Yeah ai ba wani nisa”
“Kaga gidan ko?”
“Eh duk ya lalace idan aka ce za a gyara shi sai anci kuɗi kam ”
“ Ai dole a gyara shi tun da gidan marainiya ce, a ciro kuɗinta ayi mata gyaran, daman kasan Amal bata da daɗi ta matsa min tuni kamar ni ce na ƙone gidan.Yanzu sai ci nawa idan za a gyara shi?”
“A lot, nawa kika siya mata shi?”
“Ba da kai aka yi cinikin ba, da Alhaji Ƙasimu da Mansur”
“Kai ai bana iya tunawa kin san abu da yawa”
“Nine million aka siye shi”
“Na siya 15 million”
Ummi tayi saurin dubansa.
“Joking abii?”
“I'm serious wallahi na siya”
“Ba zamu siyar ba”
“Saboda me?”
“Muka sani ko zinari aka gani a gidan zaka mana wayo”
Ta faɗa tana tashi ta nufi kitchen, dan ga dukan alamu yai da kanta zata yi girki. Dariya Abdool yayi ya cire hular kansa ya jingina da kujera yana faɗin
“Indai Amal ce ai abu mai sauƙi ne”
Lumshe ido yayi yana sauke ajiyar zuciya. Babu wacce yake gani sai Namra, da sauri ya buɗe ido ya tashi ta nufi Gardem.
FIVE READ MORE.....🙌🏻
[7/18, 8:12 PM] Khadeeja Candy♥: *57*
Bata taɓa sanin haka jikin da zuciya suke ba idan wani abu marar daɗi ya faru da mutum sai yau. Duk tashin hankalin da ta shiga lokacin da Rafiq ya kamu da ciwo be kai wanda take ciki ba yanzu.
Wannan karon kuka ma yayi ƙaura daga idonta duniyarta sai juya mata take. Gani take kamar mafarki take ba da gaske ba ne Hilal ya miƙa mata wannan takardar.
Miƙewa tayi tsaye sai gata ta dawo xaune saboda rashin ƙarfin jiki, ga wani sanyi da take jin ƙafafunta sun mata.
Wani abu taji yayi mata tsaye a zuciya, hango kanta take a bazarawa, irin rayuwar da tayi ta budurci kuma yanzu ace aurenta ya mutu bayan bata daɗe gidan mijin ba. Takardar ta ƙurawa ido tana auna yadda Mominta zata ji.
Innalillahi wa'inna ilaihi raji'un shi tai ta maimatawa sannan ta samu ƙarfin jiki, har ta unƙura ta tashi. Durowarta ta buɗe ta ɗauki canjin da yake ciki da Atm ta saka a jikarta tare da takardar ta saka hijabin ta fito falo. Saman kujera ta zauna tana maida numfashi kamar wanda tayi gudun fanfalaƙi. Hannu ta kai ta rufe bakinta saboda kukan daya zo mata gadan-gadan.
Sai dai hakan be hana hawayenta zuba ba, ashe da gaske hawaye suna da zafi, sai a yau ta tabbatar dan yau ta ji hawayenta kamar ruwan zafi.
“Me yasa zan yi kuka akan abunda ba zai sauyu ba? Miyasa zan kuka akan mutumen daya zaɓi rabuwa da ni? Anya Hilal ya cancanci hawaye na?”
Sune tambayoyin da tayi ma kanta a fili, sai dai har ta tashi ta kai bakin ƙofar falon bata samu amsarsu ba. Kamin ta ƙarasa gate ta gyara fuskarta, ta goge idonta da Hijabin gudun kar wani ya gani ya zargi wani abu.
Sai da ta yi tafiya mai nisa sannan ta samu Napep, sai da ta shiga sannan ta faɗa masa inda zai kai ta. Har suka isa estate ɗin su idanuwanta basu daina cika da ƙwallah ba.
Tana biyan Mai Napep ɗin ta shiga gida hawaye na bin fuskarta. Bata samu kowa a falon ba, daman by this time ba zata samu kowa a gidan b Sai Momynta. A saman kujera ta zauna ta haɗe kai da gwuiwa tana kuka. Sautin kukanta ne tashi daga bachi da take ta fito da sauri falo. Ganin Kalsoom ya tashi hankalinta, tasan da maganar kotu da Rashida ta sata amman bata zaton shine zai sa Kalsoom wannan kukan bayan ko kotun ba'a shiga ba. Kusa da ita ta zauna tana ƙoƙarin ɗago kanta.
“Ke miya same ki?”
Ɗagowa tayi cikin kukan ta rumgume Mominta. Girgiza Momi tayi
“Ke ki min magana mana, waya mutu? Ko Rafiq ɗin ne ya mutu?”
“Ni ce Momi Hilal ya sake ni...!”
“Innalillahi wa'inna ilaihi raji'un, me kika masa?”
Kasa magana tayi sai kuka take kamar zata shuɗe, Momi ma hawaye take, ita kanta bata jidaɗin maganar da Kalsoom ta faɗa mata ba, babu mace da zata so auren ƴarta ya mutu sai dole, balle Kalsoom da aka samu aka yi auren daker.
“Ya isa bari kuka, aure rai ne da shi idan lokacin yin sa yayi sai an yi, idan kuma mutuwarsa yayi dole ya mutu, ki kwantar da hankalinki”
Ta faɗa tana share mata hawaye, sai dai kuma ita na ta hawayen ba su daina zuba ba. Daker Momi ta lalaɓa Kalsoom tayi shiru, har ta shiga ɗakin Momi ta kwanta, kanta sai sarawa yake, ga wani ɗan banzan nauyi da yayi mata kamar an ɗora mata dutse, idonta kuma har ji take kamar ƙasa ce a ciki.
Momi kan cikin rashin kuzari tayi girkin yau, sai dai har tayi ta gama bata lasa miyar ba balle ma ta ci abincin. Sai da ta zuba a plate sannan ta kaiwa Kalsoom, banɗaki ta tararda ita tana alwala, dan lokacin ɗaya da rabi tayi, ta daɗe a banɗakin tana aikin kuka sannan ta fito.
“Haba Kalsoom ina ce kin saba da irin wannan jarrabawar, komai fa idan an yi haƙuri za'a ga riba”
Momi ta faɗa tana kallon fuskarta data kumbura. Kusa da ita Kalsoom ta zauna, idonta cike da ƙwalla ta ce
“Momi yanzu duniya zata ɗauka da gaske na aikata, yanzu kowa zai zarge ni akan ni ce ma bawa Rafiq guba, tun da ga shi har Mahaifinsa ya zaɓi rabuwa da ni”
“Amman baki masa bayani ba ne? Ko da yake ba lallai ne ya gamsu ba, saboda gidan daga ke sai yaron ne, kuma abun mamaki ne ace ya sha guba, dole duk wanda ya ji ya zarge ki, ni ba ma abunda ya ɓata min rai kamar zuwa kotun nan da za'ayi”
“Ya ce min babu maganar kotu, ɗazu da zai ba ni takarda”
“Allah ya sauwaƙe, idan auren ku akwai alheri a ciki Allah ya maida shi, idan babu kuma Allah ya kawo miki na ƙwarai, shi kuma ya haɗa shi da matar ƙwarai”
“Ina jin saki uku ne, aure ba zai sake shiga tsakamin mu ba”
“Innalillahi wa'inna ilaihi raji'un, miya kai shi aikata wannan babban kuskure? Har saki uku? Ai idan rai ya ɓace hankali baya gushewa, amman Hilal be yi ɗa ba, ai komai bincike yake so”
Ƙasa tayi da kanta tana kuka.
“Daddyn ki ba zai ji daɗin wannan lamarin ba, ana murna an yi abu sai gashi kuma ya zama na riƙici, ko da yake malamai sun ce idan saki uku aka yi shi a lokaci ɗaya za a iya ɗaukarsa a matsayin ɗaya”
“Ba furtawa yayi ba, a rubuce ya bani”
“Rubuta ya yi saki ɗaya, biyu, uku? Kalsoom bana son ki dawo xaman gidan nan ne, sannan duk wanda ya ji dalilin mutuwar auren ki ba zai aure ki ba, saboda wannan ɓacin suna ne. Nasan ba halin ki bane ko kin ji kin haɗu da mugayen ƙawaye ne masu kai mutum kai hallaka”
“Wallahi ban aikata ba, ke ma zargina kike ko?”
“Ba zargi bane Kalsoom kawai ina tsoron sherin zuciya ne, da kuma kishi, babu abunda basa sawa”
“Innalillahi wa'inna ilaihi raji'un, Allah kaɗai zai shede ni shi kaɗai zai shede ni da ban aikata ba”
“Ba zargin ki na ke ba Kalsoom, amman wannan lamarin abu ne mai sarƙaƙiya, ga abincinki ki ci”
Kai ta girgiza hawaye na mata zuba.
“Ki daure dai ki ci, Allah zai kawo mafita inshallah, wallahi wahala bata taɓa tabbata, kuma tun da har ya ci amanar ki sai Allah ya saka miki, Hilal butulu ne”
“Karki ga laifinsa Momi ni na nemi ya sake ni, a tunani na hakan shine mafita, ashe bala'i ne, ni ce na ce yayi min saki uku”
“Subhanallah Kalsoom ke kika jawa kan ki matsala, dam me zaki yi haka? Kin fi son ki dawo gida ki zauna tare da ni? Mutane da suka zage ki lokacin da aure yayi miki tsawaiko su sake buɗe miki sabon shafi? Kin tonawa kan ki asiri kowa zai ji dalilin fitar ki gidan miji, gashi ba saki ɗaya bane balle a gyara saki har uku wallahi baki da hankali Kalsoom kin yi wa kan ki, da wane ido zaki kalli baban ki? So kike ciwon zuciyarsa ya tashi ko?”
Ta ƙasara da kuka. Tana mai jin kamar ta kama Kalsoom ɗin tayi ta dukanta. Wani irin kuka Kalsoom take sai yanzu take nadamar abunda ta aikata.
“Ina takardar take?”
Momi ta katsa mata tsawo. Jikarta ta nunawa Momi tana cigaba da kuka. Tashi Momi tayi taje ta ɗauki jakar ta zazzage kayan ciki sai ga takardar ta faɗo, ita kanta ta ji wani ɗarrr kamar ka ta ɗauki takardar sai dai tana da buƙatar sanin ko saki nawa ne idan da gyara a gyara tun kowa be ji ba.
Warware takardar tayi tana karantawa. Wani dogon tsaki taja lokacin data gama karantawar ta jefa ma Kalsoom takardar ta fice tana faɗin.
“Yayi tunani da hankali wallahi...”
Sai da Kalsoom ta ci kukanta ta ƙoshi sannan ta ɗauki takardar tana dubawa cikin kuka.
_Idan na sake ki ina za ki? Wa kike tunanin zai aure ki a halin da kike ciki yanzu? Kowa yana zargin ki da kin kore Rashida kina son kashe ƴaƴata, saboda basu san dalilin sakinta da na yi ba._
_Zan miki uzuri Kalsoom akan abinda kika aikatawa ɗa na, saboda kin nuna musu so a can baya, xuciya bata da ƙashi, dukan abunda kika aikata dan kina so na ne, kina kishi na shiyasa kika aikata, kina ganin kamar ina son ƴaƴan da ba naki ba da yawa ko?_
_Ba zan sake ki ba, saboda naga so na a idonki, kina neman sakin ne saboda kina ganin kamar shine mafita a gareki ko? To ba zan sake ki ba, har abada haka zamu zauna da ke, amman ba zan sake barin ƴaƴana a tare da ke ba, ba zasu sake raɓar ki ba, saboda zuciyarki ta sauya a yanzu, kin tashi daga Kalsoom ɗin da nasan ki kin koma wata dabam,
Showing 138001 words to 141000 words out of 280121 words
“A'a Alhaji ya kake magana kamar ba mai tunani ba? Haka sam be dace ba, hukuncin data yanke shine dai-dai”
Ya kawarda fuskarsa daga ta Momy ya kalli Rashida dan a tunaninsa ko Momy ce tayi mata wannan shawarar.
“Ke kina son abi miki kadin yaron ki?”
Ta girgiza kai.
“A'a Abbah na janye, na barta da Allah”
“Akan me?”
“Kawai haka naga ya fi”
“To ni zan bi kadin jika na (grandson) idan ku baku san abunda ake kira da humanity ba, ni na sani... Tashi kije office Allah ya kiyaye hanya”
Ba zata iya musawa Dady ba kar ya zargi wani abu, sai dai zuciyarta bata so haka ba, dan babu banbanci mahaifinta ne yasa ba ita ba. Tasan Hilal zai iya cewa wani sabon salo ne ta mayardar shari'ar gurin Mahaifinta.
A hanyar ta zuwa office ta kira Mom Shuraim, bayan sun gaisa take faɗa mata idan ta tashi daga aiki zata biyo ta gidanta, akwai magana mai muhimmanci da zata yi da ita.har da narke murya tana faɗin wai tana cikin matsala, amman dai sai tazo zata ji komai.
*ABDOOL POV*
Sai ten ya tashi bachi, dan yana yin sallah azuba ya koma bachin gajiya, farkawar da yayi ma a yanzu ba dan ya gaji da bachi bane, sai dan son zuwa gurin da Ummi tayi masa magana ne jiya. Be fito part ɗinsa ba sai da yayi wanka bugaggar shadda mai tsana blue color, ta fito da shi sosai kasancewar fari sol, ga ɓaƙar hulal da ya ɗora akansa kamar wani sabon balarabe,baƙaƙen takalmi ya saka sannan ya feshe jikinsa da turare, ya fito daga part ɗinsa ya nufo part ɗin Ummi shaddar har amsawa take a jikinsa, ga wani maiƙo da take kamar an zuba mata mai.
Ita kanta Ummi sai da tayi murmushi ganin yadda ɗan nata ya fito mashallah kamar ta cinye abunta.
“Ina fatar ka yi addu'ah”
“Addu'ah me?”
“Idan mutum yayi kwaliya ya dubu kansa a madubi yana kyau yace Mashallahu laƙuwwati illa billah, to ko wani yayi maka baki (kanbun baka) Ba zai kama ka ba, idan ma zaka ita ka riƙa karantawa da safe kullum sau uku”
Dariya yayi yana kallon cucumber da Ummi take yankewa ya ɗauki ɗaya ya ci.
“To ni da ba mace ba miye na wani kanbu zai kama ni, amman dai zan riƙa yi”
“It better”
Ya faɗa tana cigaba da yanka cucumber take. Shi kuma ya zauna kusa da ita yana tambayarta yaje yanzu ko sai anjima.
Ƙamshim turarensa ne ya isarwa da Amira saƙon isowarsa a falon. Ras! ras!! ras!!! Ga banta ya faɗi kamar yadda ya basa mata a duk lokacin da ta ji ƙamshin turarensa. Da sauri ta walƙato ta sauko daga saman gadon da take ta nufo falon idonta cike da maitar ganin Abdool kamar bata taɓa ganinsa ba.
Cikin wata irin siga take tafiya, takalmin dake ƙafarta plate ne amman hakan be hana su amsa amon gurin ba saboda yadda take buga da tiles ɗin gurin. Ummi ce kawai ta ɗago ta kalleta wanda kuma ita bata so haka ba. Abdool kam ƙin ɗagowa yayi dan sarai zuciyarsa ta raya masa Amira ce, dan yasan by this time duka ƙanensa suna makaranta.
“Ina kwana”
Ta gaishe shi cikin ladabi har tana son risina masa.
“Lafiya”
A kaikaice ya amsa, yana mai miƙewa tsaye. Wanda hakan be ma Ummi dadi ba,sai kawai ta kada baki ta ce.
“Amira shiga ciki ki ɗauko mayafin ki ki rana yayanki unguwa”
Ta fasa zaman da zata yi ta miƙe ta nufi ɗakin data fito. Sai da ta shige sannan Abdool.ya kalli Ummi yana ware hannayensa ya ce
“Haba Sweet Mom ya za ki min haka? Kin san fa ni Allah be haɗa jinina da mata ba, kuma it so annoying naje da ita unguwa”
Wani Kallo Ummi ta masa.
“Abdool... Karka soma halin Amal, tun da yarinyar nan ta zo kullum tana ciki gida bata fita ita ma ai ƙara ta ga gari ko?”
Be ƙara cewa komai ba ganin Amira ta fito, sai kawai ya jiya ya nufi kowa yana wani shan ƙamshi.
Ko da ta isa har ya tashi motar ita kawao yake jira su wuce. Tana shiga ya fisgi motar kamar baya son ransa har sai da Amira ta tsorata.
Bata ce masa ba, shi ma be ce mata ba haka suka yi ta tafiya har suka isa nasarawa. A bakin gate ɗin gidan yayi parking ya fito yana ƙarewa gidan kallom ganin yadda ya kone.
Yana rufe gambun motar Amira ta buɗe ta fito, sai ya kalleta ya ce
“Ba daɗewa zan yi ba, kina iya zama a cikin kamin na dawo”
Ba musu ta koma cikin motar ta zauna, zuciyarta cike da tunani kala-kala.
Baya tunanin akwai mutane a gidan dan Ummi bata faɗa masa ba, hakan yasa be yi sallama ba ya tura kofar gate ɗin kawai ya shiga ciki. Gaban gidan ya fara dubawa kamin ya zagaya baya, tana nan ya hango mace tana girki a BQ. Hannayensa yasa aljihu ya nufi bq ɗin yana sallamar da kusan shi kaɗai ne zai iya jinta, sai kuma wanda yaga bakinsa ya motsa.
Namra na ganin mutum tayi saurin komawa ciki ta ɗauko hijabinta ta saka sannan ta fito. Ko da ta fito har ya ƙaraso bq ɗin yana ƙare ma bq ɗin kallo dan ita bata yi komai ba.
“Haba Malam waye kai zaka shigo babu sallama”
Dago da dubansa yayi gurin mai maganar. Ganin Namra yasa numfashinsa hijira daga jikinsa ma ɗan wasu daƙiƙu, sannan ya dawo. Be ɗauke idonsa daga gareta ba be kuma kyafta ba, haka ya ƙafe da ido kamar wani hoto. Nan da nan zuciyarsa ta soma rabawa jijiyoyin jikinsa jini da ƙarfi.
Rassss rassss rassss gabansa yake faɗuwa, sai dai kuma ba irin wacan faɗuwar ba, ta tsoro ko fargaba, faɗuwar gaba ne da shi kansa ba zai iya fassara na minene ba.
Ita sai yanzu ta gane ko wanene shi, daman tun ɗazu ta ga ganin kamar fuskar sani, mutume daya bita asibiti. Ƙamshin turaresan ya haddasa mata ciwon kan da bata yi zato ba, daman tun jiya bata cikin daɗin rai.
“Subhanallah malam wannan kallo ya haramta a musulumci”
Daɗin sautinsa yasa shi lumshe ido yana murmushi.
‘A'uzubillahi minal sheidanin rajin’
Ya furta a zuciyarsa yana ƙoƙarin da abunda sheiɗan yake son masa, sannan ya buɗe ido ya haɗe fuska kamar be taba dariya ba.
“Su waye ku?”
“Mu ne waɗanda suka kama hanyar wannan gidan”
Ta amsa masa a gautse.
“Bq kuka kama ko Main house”
“Main house muna ciki aka yi gobara sai muka dawo nan da zama”
“Ina mijin ki?”
“Baya nan ya tafi kasuwa”
“To idan ya zo ki ce an baku one week ku tashi za ayi gyaran gidan”
Gabanta yayi mummunan faɗuwa.
“Innalillahi wa'inna ilaihi dan Allah ku gyara babban gidan sai ku bar mana BQ ɗin wallahi ba mu da gurin zuwa idan muka bar nan, dan Allah ku taimaka mana”
Ta haɗe hannayenta idonta na son cika da ƙwalla.
“Da yaushe ake tarar da mijin ki?”
“Da safe ko kuma da dare guraren goma”
“Okay zan zo na yi magana da shi gobe”
“Allah ya kai mu na gode”
Be sake cewa wani abu ba, ya juyo hannayensa zube a aljihu ya fito gidan. Har lokacin Amira na cikin mota zaune tana jiransa, yana shiga motar yayi mata key suka juya. Wannan karon ita ce ta ke ɗan jansa da fira shi kuma jikinsa duk ya mutu baya ma iya amsa mata. yawancin tambayarta akan gidan ne da kuma unguwar, sai kuma yaba garin Katsina da take. Shi dai har suka isa gida sai dai ya ɗaga mata kai kawai.
Ta rigashi fita daga motar, dan yau ranta fes yake ta ta fita tare da sahibinta. Bata tsaya a falo ba sai kawai ya wuce ɗakinta tana ƙoƙarin ɓoye nishaɗinta. Shi kuma ya zauna a falo, kusa da Ummi da take zaune a inda ya barta ɗazu, sai dai wannan karon ita da Shukura ne kuma carrots take gyarawa.
“Har kun dawo?”
“Yeah ai ba wani nisa”
“Kaga gidan ko?”
“Eh duk ya lalace idan aka ce za a gyara shi sai anci kuɗi kam ”
“ Ai dole a gyara shi tun da gidan marainiya ce, a ciro kuɗinta ayi mata gyaran, daman kasan Amal bata da daɗi ta matsa min tuni kamar ni ce na ƙone gidan.Yanzu sai ci nawa idan za a gyara shi?”
“A lot, nawa kika siya mata shi?”
“Ba da kai aka yi cinikin ba, da Alhaji Ƙasimu da Mansur”
“Kai ai bana iya tunawa kin san abu da yawa”
“Nine million aka siye shi”
“Na siya 15 million”
Ummi tayi saurin dubansa.
“Joking abii?”
“I'm serious wallahi na siya”
“Ba zamu siyar ba”
“Saboda me?”
“Muka sani ko zinari aka gani a gidan zaka mana wayo”
Ta faɗa tana tashi ta nufi kitchen, dan ga dukan alamu yai da kanta zata yi girki. Dariya Abdool yayi ya cire hular kansa ya jingina da kujera yana faɗin
“Indai Amal ce ai abu mai sauƙi ne”
Lumshe ido yayi yana sauke ajiyar zuciya. Babu wacce yake gani sai Namra, da sauri ya buɗe ido ya tashi ta nufi Gardem.
FIVE READ MORE.....🙌🏻
[7/18, 8:12 PM] Khadeeja Candy♥: *57*
Bata taɓa sanin haka jikin da zuciya suke ba idan wani abu marar daɗi ya faru da mutum sai yau. Duk tashin hankalin da ta shiga lokacin da Rafiq ya kamu da ciwo be kai wanda take ciki ba yanzu.
Wannan karon kuka ma yayi ƙaura daga idonta duniyarta sai juya mata take. Gani take kamar mafarki take ba da gaske ba ne Hilal ya miƙa mata wannan takardar.
Miƙewa tayi tsaye sai gata ta dawo xaune saboda rashin ƙarfin jiki, ga wani sanyi da take jin ƙafafunta sun mata.
Wani abu taji yayi mata tsaye a zuciya, hango kanta take a bazarawa, irin rayuwar da tayi ta budurci kuma yanzu ace aurenta ya mutu bayan bata daɗe gidan mijin ba. Takardar ta ƙurawa ido tana auna yadda Mominta zata ji.
Innalillahi wa'inna ilaihi raji'un shi tai ta maimatawa sannan ta samu ƙarfin jiki, har ta unƙura ta tashi. Durowarta ta buɗe ta ɗauki canjin da yake ciki da Atm ta saka a jikarta tare da takardar ta saka hijabin ta fito falo. Saman kujera ta zauna tana maida numfashi kamar wanda tayi gudun fanfalaƙi. Hannu ta kai ta rufe bakinta saboda kukan daya zo mata gadan-gadan.
Sai dai hakan be hana hawayenta zuba ba, ashe da gaske hawaye suna da zafi, sai a yau ta tabbatar dan yau ta ji hawayenta kamar ruwan zafi.
“Me yasa zan yi kuka akan abunda ba zai sauyu ba? Miyasa zan kuka akan mutumen daya zaɓi rabuwa da ni? Anya Hilal ya cancanci hawaye na?”
Sune tambayoyin da tayi ma kanta a fili, sai dai har ta tashi ta kai bakin ƙofar falon bata samu amsarsu ba. Kamin ta ƙarasa gate ta gyara fuskarta, ta goge idonta da Hijabin gudun kar wani ya gani ya zargi wani abu.
Sai da ta yi tafiya mai nisa sannan ta samu Napep, sai da ta shiga sannan ta faɗa masa inda zai kai ta. Har suka isa estate ɗin su idanuwanta basu daina cika da ƙwallah ba.
Tana biyan Mai Napep ɗin ta shiga gida hawaye na bin fuskarta. Bata samu kowa a falon ba, daman by this time ba zata samu kowa a gidan b Sai Momynta. A saman kujera ta zauna ta haɗe kai da gwuiwa tana kuka. Sautin kukanta ne tashi daga bachi da take ta fito da sauri falo. Ganin Kalsoom ya tashi hankalinta, tasan da maganar kotu da Rashida ta sata amman bata zaton shine zai sa Kalsoom wannan kukan bayan ko kotun ba'a shiga ba. Kusa da ita ta zauna tana ƙoƙarin ɗago kanta.
“Ke miya same ki?”
Ɗagowa tayi cikin kukan ta rumgume Mominta. Girgiza Momi tayi
“Ke ki min magana mana, waya mutu? Ko Rafiq ɗin ne ya mutu?”
“Ni ce Momi Hilal ya sake ni...!”
“Innalillahi wa'inna ilaihi raji'un, me kika masa?”
Kasa magana tayi sai kuka take kamar zata shuɗe, Momi ma hawaye take, ita kanta bata jidaɗin maganar da Kalsoom ta faɗa mata ba, babu mace da zata so auren ƴarta ya mutu sai dole, balle Kalsoom da aka samu aka yi auren daker.
“Ya isa bari kuka, aure rai ne da shi idan lokacin yin sa yayi sai an yi, idan kuma mutuwarsa yayi dole ya mutu, ki kwantar da hankalinki”
Ta faɗa tana share mata hawaye, sai dai kuma ita na ta hawayen ba su daina zuba ba. Daker Momi ta lalaɓa Kalsoom tayi shiru, har ta shiga ɗakin Momi ta kwanta, kanta sai sarawa yake, ga wani ɗan banzan nauyi da yayi mata kamar an ɗora mata dutse, idonta kuma har ji take kamar ƙasa ce a ciki.
Momi kan cikin rashin kuzari tayi girkin yau, sai dai har tayi ta gama bata lasa miyar ba balle ma ta ci abincin. Sai da ta zuba a plate sannan ta kaiwa Kalsoom, banɗaki ta tararda ita tana alwala, dan lokacin ɗaya da rabi tayi, ta daɗe a banɗakin tana aikin kuka sannan ta fito.
“Haba Kalsoom ina ce kin saba da irin wannan jarrabawar, komai fa idan an yi haƙuri za'a ga riba”
Momi ta faɗa tana kallon fuskarta data kumbura. Kusa da ita Kalsoom ta zauna, idonta cike da ƙwalla ta ce
“Momi yanzu duniya zata ɗauka da gaske na aikata, yanzu kowa zai zarge ni akan ni ce ma bawa Rafiq guba, tun da ga shi har Mahaifinsa ya zaɓi rabuwa da ni”
“Amman baki masa bayani ba ne? Ko da yake ba lallai ne ya gamsu ba, saboda gidan daga ke sai yaron ne, kuma abun mamaki ne ace ya sha guba, dole duk wanda ya ji ya zarge ki, ni ba ma abunda ya ɓata min rai kamar zuwa kotun nan da za'ayi”
“Ya ce min babu maganar kotu, ɗazu da zai ba ni takarda”
“Allah ya sauwaƙe, idan auren ku akwai alheri a ciki Allah ya maida shi, idan babu kuma Allah ya kawo miki na ƙwarai, shi kuma ya haɗa shi da matar ƙwarai”
“Ina jin saki uku ne, aure ba zai sake shiga tsakamin mu ba”
“Innalillahi wa'inna ilaihi raji'un, miya kai shi aikata wannan babban kuskure? Har saki uku? Ai idan rai ya ɓace hankali baya gushewa, amman Hilal be yi ɗa ba, ai komai bincike yake so”
Ƙasa tayi da kanta tana kuka.
“Daddyn ki ba zai ji daɗin wannan lamarin ba, ana murna an yi abu sai gashi kuma ya zama na riƙici, ko da yake malamai sun ce idan saki uku aka yi shi a lokaci ɗaya za a iya ɗaukarsa a matsayin ɗaya”
“Ba furtawa yayi ba, a rubuce ya bani”
“Rubuta ya yi saki ɗaya, biyu, uku? Kalsoom bana son ki dawo xaman gidan nan ne, sannan duk wanda ya ji dalilin mutuwar auren ki ba zai aure ki ba, saboda wannan ɓacin suna ne. Nasan ba halin ki bane ko kin ji kin haɗu da mugayen ƙawaye ne masu kai mutum kai hallaka”
“Wallahi ban aikata ba, ke ma zargina kike ko?”
“Ba zargi bane Kalsoom kawai ina tsoron sherin zuciya ne, da kuma kishi, babu abunda basa sawa”
“Innalillahi wa'inna ilaihi raji'un, Allah kaɗai zai shede ni shi kaɗai zai shede ni da ban aikata ba”
“Ba zargin ki na ke ba Kalsoom, amman wannan lamarin abu ne mai sarƙaƙiya, ga abincinki ki ci”
Kai ta girgiza hawaye na mata zuba.
“Ki daure dai ki ci, Allah zai kawo mafita inshallah, wallahi wahala bata taɓa tabbata, kuma tun da har ya ci amanar ki sai Allah ya saka miki, Hilal butulu ne”
“Karki ga laifinsa Momi ni na nemi ya sake ni, a tunani na hakan shine mafita, ashe bala'i ne, ni ce na ce yayi min saki uku”
“Subhanallah Kalsoom ke kika jawa kan ki matsala, dam me zaki yi haka? Kin fi son ki dawo gida ki zauna tare da ni? Mutane da suka zage ki lokacin da aure yayi miki tsawaiko su sake buɗe miki sabon shafi? Kin tonawa kan ki asiri kowa zai ji dalilin fitar ki gidan miji, gashi ba saki ɗaya bane balle a gyara saki har uku wallahi baki da hankali Kalsoom kin yi wa kan ki, da wane ido zaki kalli baban ki? So kike ciwon zuciyarsa ya tashi ko?”
Ta ƙasara da kuka. Tana mai jin kamar ta kama Kalsoom ɗin tayi ta dukanta. Wani irin kuka Kalsoom take sai yanzu take nadamar abunda ta aikata.
“Ina takardar take?”
Momi ta katsa mata tsawo. Jikarta ta nunawa Momi tana cigaba da kuka. Tashi Momi tayi taje ta ɗauki jakar ta zazzage kayan ciki sai ga takardar ta faɗo, ita kanta ta ji wani ɗarrr kamar ka ta ɗauki takardar sai dai tana da buƙatar sanin ko saki nawa ne idan da gyara a gyara tun kowa be ji ba.
Warware takardar tayi tana karantawa. Wani dogon tsaki taja lokacin data gama karantawar ta jefa ma Kalsoom takardar ta fice tana faɗin.
“Yayi tunani da hankali wallahi...”
Sai da Kalsoom ta ci kukanta ta ƙoshi sannan ta ɗauki takardar tana dubawa cikin kuka.
_Idan na sake ki ina za ki? Wa kike tunanin zai aure ki a halin da kike ciki yanzu? Kowa yana zargin ki da kin kore Rashida kina son kashe ƴaƴata, saboda basu san dalilin sakinta da na yi ba._
_Zan miki uzuri Kalsoom akan abinda kika aikatawa ɗa na, saboda kin nuna musu so a can baya, xuciya bata da ƙashi, dukan abunda kika aikata dan kina so na ne, kina kishi na shiyasa kika aikata, kina ganin kamar ina son ƴaƴan da ba naki ba da yawa ko?_
_Ba zan sake ki ba, saboda naga so na a idonki, kina neman sakin ne saboda kina ganin kamar shine mafita a gareki ko? To ba zan sake ki ba, har abada haka zamu zauna da ke, amman ba zan sake barin ƴaƴana a tare da ke ba, ba zasu sake raɓar ki ba, saboda zuciyarki ta sauya a yanzu, kin tashi daga Kalsoom ɗin da nasan ki kin koma wata dabam,
Book Chapters
Chapter 1Chapter 2Chapter 3Chapter 4Chapter 5Chapter 6Chapter 7Chapter 8Chapter 9Chapter 10Chapter 11Chapter 12Chapter 13Chapter 14Chapter 15Chapter 16Chapter 17Chapter 18Chapter 19Chapter 20Chapter 21Chapter 22Chapter 23Chapter 24Chapter 25Chapter 26Chapter 27Chapter 28Chapter 29Chapter 30Chapter 31Chapter 32Chapter 33Chapter 34Chapter 35Chapter 36Chapter 37Chapter 38Chapter 39Chapter 40Chapter 41Chapter 42Chapter 43Chapter 44Chapter 45Chapter 46Chapter 47 Chapter 48Chapter 49Chapter 50Chapter 51Chapter 52Chapter 53Chapter 54Chapter 55Chapter 56Chapter 57Chapter 58Chapter 59Chapter 60Chapter 61Chapter 62Chapter 63Chapter 64Chapter 65Chapter 66Chapter 67Chapter 68Chapter 69Chapter 70Chapter 71Chapter 72Chapter 73Chapter 74Chapter 75Chapter 76Chapter 77Chapter 78Chapter 79Chapter 80Chapter 81Chapter 82Chapter 83Chapter 84Chapter 85Chapter 86Chapter 87Chapter 88Chapter 89Chapter 90Chapter 91Chapter 92Chapter 93Chapter 94