matso ta ganta gurin ƴarta. Ana saura awa ɗaya su isa Katsina motarsu ta fara basu matsala, Anty ta tsorota sosai ganin a hanya suke, sai direban ya riƙa ƙoƙarin kwantar mata da hankali akan cewar zasu isa lafiya kamin ta tsaya in yaso sai su samu wanda zai duba musu ita a can katsina ɗin.
Sun isa Katsina lafiya, sai a mararraba motar ta soma gaba tana baya, hakan yasa direban fakawa gefe ya fito yana duba motar.
Anty ma fitowa tayi tazo ta tsaya gaban motar gurin da direban yake tana duba abinda yake taɓawa tare da tambayar abinda ya samu motar.
Motocin dake kai da kawo babu wacce ta tsaya, sai wata kafirar mota mai matuƙar kyau da ɗaukar hankali, ita har ta wuce sai ta dawo kusa da su ta faka.
Buɗe motar Abdool yayi ya fito ganin dattijowa kamar Anty a cikin zafin ranar nan ya hana shi wuce ce, dan daga gani yasan motar ce ta tsaya. Cikin wani irin taku ya ƙaraso gurin, shi ba na sauranta ba ba kuma na yana sanye da kakin soja ba.
“Lafiya me ya samu motar?”
“Wallahi muna tafiya ne ta fara bamu matsala ina jin ko ingin ne”
Matsawa yayi ya duba motar ya buɗe abubuwa ya gani, sai ya koma motarsa ya ɗauko ruwa da baƙin mai ya zuba mata sannan ya maida komai ya gyara shi kamar yadda yake.
“Shiga ka tashi motar mu ga”
Da sauri direban ya shiga ya tashi motar yayi baga yayi baya yaga ta dawo normal sai ya faka ya fito yana godiya.
“Mun gode Sosai”
“Ba komai amman a riƙa kula da irin waɗannan idan za'ayi tafiya mai nisa”
“Inshallah mun gode”
“Allah yayi maka albarka”
Anty Amarya ta faɗa tana ɗan murmushi, dan tasan ko waye Abdool tun da tana ganinsa a tv, sai dai bata tabbatar da shi ɗin ne ba tun da ya tsaya ya taimake su, sai dai kuma kakin dake jikinsa da stars sun nuna haka.
Ɗan rinawa yayi yana murmushi.
“Amin Mama na gode”
Juyawa yayi ya koma motarsa. Suma suka shiga tasu, da hau titi sai da ya ɗaga musu hannu sannan ya cigabansu da mugun gudu.
[7/18, 8:12 PM] Khadeeja Candy♥: *55*
*NAMRA POV.*
Yau kan ta ɗan samu sauƙi ba kamar jiya ba. Dan yau har aiki ta samu tayi, ta gyara gidan tas sannan tayi wanke-wanke, sannan ta shiga tayi wanka. Ta shirya cikin baƙar abaya sannan ta fito harabar gidan ta ɗauko murhunta na gawai ta ɗora girkin rana.
Bayan ta ɗora ta tashi ta koma cikin ɗakin ta ɗauko tabarma da filo ta shimfiɗa, dan ta soma jin ciwon kan na taso mata.
Bachine ya soma ɗaukarta, sai gyangyaɗi take, bata son yin bachi ta bar girkinta ya ƙone. Hakan yasa ta tashi ta wanke shimkafa ta zuba ta gyara wutar sai ta koma ta xauna tana kallon gate dan horn ɗin ta take ji ta yi yawa.
Bata jin za ta iya zuwa ta ga mai horn ɗin, duk da tana jin a gidan ake horn amman bata zaton za tayi wani baƙo mai mota, da zai iya zuwa gurinta yanzu.
Kwantawarta tayi tasa ɗan tsinƙe tsintsiya tana gyara akaifarta. Bata ɗago ba har sai da aka turo ƙofar gate ɗin aka shigo. Sannan ta ɗan juyo taga ko waye ne. Ganin Anty yasa ta tashi tsaye da sauri tana mamakin ikon Allah. Mafarki take ko gaske? Anty ce ko aljanarta? Tsaye tayi a gurin kamar an dasata. Idan har da gaske Anty zata yi farinciki ganinta dan tayi marmarinta sai dai kuma bata fatar amAnty taga ganta a halin da take ciki.
Bata gasgata Anty bace har sai da ta ƙaraso inda take ta dafa tana mata kallon mamaki dan duk yadda Yasmin ta faɗa mata sai taga abun yafi haka muni.
“Namra...!”
Rumgume Anty tayi ta fashe da kuka. A maimakon Anty ta rarrashe ta sai kawai ta tureta daga kafaɗarta.
“Wane irin hali ne wannan Namra? Jibe ke, a haka kike zaune kamar baiwa? Namra me yake ƙwaƙwalwarki? Kina rayuwar da ko amafarki ban taɓa tunanin za kiyi ba?”
“Idaba nake Anty, bautar Allah na ke, talauci da arzki duka na Allah. Da ace talakawa Allah yayi mu da sai dai mu hange wasu masu kuɗi suna sha'aninsu, mu muna cikin talauci. Dan kawai ina ƴar mai kuɗi ba shi yake nuna zan dauwama a daular duniya ba, duk wanda yayi arziki dole ne arzikin ya barsa ko kuma shi ya mutu ya bar arzikin, amman ba'a dauwama da duka biyu”
A natse take maganar cikin hikima tana son Anty tayi ma maganarta karatun ta natsu, ƙoƙarin lurar da Anty take kwaɗayin dukiya ba zai sa ta ƙi zaman aure ba. Ajiyar zuciya Anty ta sauke, tabbas ba xata iya canja abinda Allah ya rubuta ga Namra ba, amman tana ganin rashin dacewa a zamantakewar auren ta, wanda abu ne mai wahala da iya ɗauke idonta akan haka, bayan kuma tasan Asim ɗin ba dan Allah yake zaune da ita.
“Namra wannan rayuwar bata kamace ki, ƴar gata ce dubi inda kike zaune, yaushe gidan ya ƙone? Baki faɗa ba? Kina tunanin zurfin ciki zai miki magani ne?”
Ta share hawayenta ta hannun rigarta.
“An daɗe da yin gobarar, ban faɗa ba ne saboda ba lalle bane ku yarda a wacan lokacin”
“Je ki haɗa kayan ki, gida zamu je yanzu, zaman ki a gidan nan ya ƙare, an faɗa min har dukan ki Asim ya ke Namra wai me ke toshe miki ƙwaƙwalwa ne?”
Gabanta ya faɗi, tana jin rashin kyautawa a abinda Anty take ƙoƙarin aikatawa, dan me zatayi tattaki dan kawai ta kashe mata aure?
“Abbah ne yace ki zo da ni?”
“Ki shiga ki ɗauko hijabin ki na ce...!”
Anty ta katsa mata tsawa... Ja da baya Namra ta yi tana hawayen
“Ba zan biki ba Anty, Abbah ya faɗa min kar na kuskura na tunkaro gidansa da sunan saki ko yaji, ya nanata min lokacin da naje gida, ya ce duk na zauna masa a gidan sai dai ya kore mu ni da ke. Ba zan kashe miki aure ba, ba zan ƙara jefa kai na a halaka ba, mutane ba zasu jefe ni da biyu ba, ace na kashe miki aure kuma na bijirewa mahaifina”
Har cikin zuciyarta take faɗin haka, dan ta haƙiƙance a ranta ba zata taɓa biyar Anty ba, ba zata ja mata wani zagin ba, sai ace taje ta kashe mata aure. Bayan kuma tasan Abbah ba zai taɓa yarda ta zauna a gidan sa ba, ta kuma san Anty zata iya rabuwa da Abbah akan ta.
Wani irin kallo Anty take mata na mamaki da rasa abinda zata ce mata.
“Namra ke ba cikakkiyar mutum ba ce, ke rabin mutum ce! Ban san wanda ta haife ki bayan ni ba, da sai nace ke ba ƴata ba ce, ina da sanyin hali amman be kai ka ki ba ke sakarya ce, marar hankali dabba wace bata san ciwon kan ta ba. Na yi tunanin kin yi hankali na ɗauka kin gane inda duniya take a yanzu, ashe ke wawuya ce....”
Cikin zafin rai da ɓacin rai Anty take maganar sautin muryarta na fita ko'ina da ace ba babban gida bane da tuni an yi musu taro. Hawayen takaici.
“Na yi hankali Anty kuma zan zo gareki idan har Allah ya ƙaddaro rabuwa da tda Asin ya bani takardar sallama”
“Tam Allah ya ba ku haƙuri zama”
Ta duƙa ta ɗauki carbinta daya faɗi sannan ta miƙe tsaye ta kalli Namra da kyau da kyau. Sannan ta juya ta soma tafiya jiki ba ƙwari.
Rugawa Namra tayi a guje ta sha gabanta ta rumgume ƙafatunta, tana kuka sosai.
“Dan Allah Anty karki yi fushi da ni, dan Allah ki fahimci ne”
“Ba zan taɓa fushi dake ba Namra, ba zan tdine miki ba, Allah yayi miki albarka, idan kin lalace dole za a ce ƴata ce, idan kin ɗaukaka dole kuma ace ƴata ce, amman ba zan sake wauwayar gidan auren ki da Asim ba ko da kuwa gawarki ce a ciki, kar kuma ki sake roƙo na komai, ba zan baki ba matuƙar ba ki yi hankali ba kisa wannan a zuciyarki...!”
Ta janye ƙafarta ta bar Namra nan tana aikin kuka, ta nufi gate hawaye ya gangaro a idon Anty. Wani irin kuka Namra take, kukan da ita kanta ta manta when last tayi irinsa, ko ba komai tasan ta ɓata ran Anty, tabbas Asim ba mijin aure ba ne, amman ta yi alƙawarin zama da shi har iya rayuwarta dan kawai ta cika umarnin Abbah. Idan har ta bi Anty a yanzu duniya zasu zage ta ita da Anty kuma zata ƙara ɓata ran Abbah.
Tashi tayi taje gurin gate ɗin ta tsaya tana kuka, tana kallon motar Anty har ta suka bar unguwar. Sai ta zube a gurin ta ƙara fashewa da kuka tan mai jin kamar ta falla da gudu ta bi Anty.
Iya hawayen da Anty tayi a gidan Namra ne hawayen tausayin Namra, har ta suka isa gida bata sake wasu hawayen ba, dan yanzu ta fahimci Namra ba abar tausayu bace tun da bata tausayin kanta. A hanya Namra nata kiranta amman ta ƙi ta ɗaga wayar.
Su Maryam tun kamin ta yi musu bayani suka fahimci komai tun daga yanayinta da kuma ganin ba a zo da Namra ba.
Bayan ta huta ta faɗa musu abinda ya faru, duk basu jidaɗi ba, musamman Maryam da tafi so zafin rai, kasa haƙuri tayi har sai da ta kira Namra ta yi mata faɗa kamar wata yayarta.
A ɓangaren nan kam
Haka ta wuni cikin kuka daman aikinta ne shine ya zame mata abokin fira. Sai goman dare Asim ya dawo kamar yadda ya daba yana ganin yanayin Namra ya san ba lafiya ba, amman saboda mugun hali yaƙi ya tambaye ta damuwarta.
Sai ƙoƙare kai mata buƙatarsa yake. Ture masa hannun tayi ta tashi zaune cikin ƙunar zuciya ta ce
“Aikin kenan, Asim ka rako maza duniya, kai wayayye amman wayewar ka bata maka amfani ba, babu ruwanka da damuwa kai dai na gurka kawai ka ci, dare yayi ka kawo min buƙata, shine kawai...!”
Nuna kansa yayi duk da ɗakin babu wani haske sosai.
“Ke ni kika faɗa ma wannan maganar? Wuyanki yayi kauri ko Namra? Kin rai nani saboda bana da naira saboda ni takala ne ko?”
“Idan har talaucin ya dame ka miyasa baka yi ihun arxikin ya zo maka ba? Miyasa idonka ya rufe akan neman abinda za ka mutu ka bari, kai ne baƙon arziki shiyasa kake yawantar faɗarsa”
Tashi yayi ya ƙara motsa kusa da ita da zimmar dukanta, jikinsa har bari yake.
“Ni kike faɗawa wannan maganar Namra? Ni sa'anki ne?”
Mari ya kai mata ta gauce, ta fita waje da sauri. Bata zame ko'ina ba sai inda take girki, wuƙa ta ɗauko ta shigo ɗakin da ita idonta a kafe irin yau ba imani ɗin nan ta nuna sa da ita.
“Karka kuskura kace zaka taɓa ni Asim, zan iya kashe ka Asim, baƙin cikin da yake rai na zan iya juye maka shi a yau, tun da ka shigo gidan nan baka tambaye damuwa na ba, baka tambaye waya mutu waya rayu ba kai dai kawai matsalarka ka sani, saboda kai na ɓata ran mahaifina, saboda kai yau mahaifiyata ta koma gida cikin ɓacin rai, na kira ta bata ɗaga ba Maryam.ta kira ki babu irin cin mutumcin da bata min ba duk a kan ka Asim. Tam ya ƙare yanzu wuta ba zata sake cin ƙara ba, sai dai quta ta ci wuta...!”
A baki take furucin zuciyarta cike da yaƙinin ita ɗin zata iya, shi kansa Asim yaga hka idonta sai dai babu abinda zuciyarsa ta ayyana masa sai aljanu, ganin yake aljanun Namra ne suka taso cikin daren nan. Nan da nan marar ta cika da fitsari, be nuna tsoro a fuska ba, amman a zuci tsoron har yayi masa yawa, ala-ala yake kar aljanun su caka masa wukar, dan shi dai yasan Namra da kanta ba zata iya masa haka ba.
Uffan be ƙara cewa ba, sai kawai ya ɗauki tabarma da filo da abin rufa ya koma waje ya kwanta, dan baya jin zai iya kwana ɗakin karya kasheshi cikin dare.
A wajen ma sai ya koma can nesa da ƙofar ɗakin sannan ya shinfiɗa ya kwanta. Duk bayan minti ɗaya biyu yake farkawa ya tofe kansa da addu'a sannan ya sake komawa. Kamin safiya ta qaye har ya matsu. Yana fita salla asuba, yai fitar gaba ɗaya.
*AMIRA POV*
Tana jin parking ɗin mota, ta ayyana a ranta cewar Abdool. Da sauri ta ƙarasa shafa hodar da take ta ɗauki ɗankwalinta ta yafa saman kai ta biyo sawun kannensa dake masa oyoyo.
Amal ce taje da gudu ta rumgume shi, Ummi da sauran ƙannensa kuma suka tsaya a jikin ƙofar falo suna jiran ya ƙaraso. Hannu Amal ya riƙa suka nufo falon hularsa a hannu yana murmushin data ƙayata kyausa.
Ɗan risinawa ya yi lokacin daya kawo bakin ƙofar falon, ya gasheta da Ummi kamar yadda ya saba. Sai ta amsa masa murmushi tana faɗin.
“Mu duk mun ɗauka jirgi zaka biyo fa”
“Wallahi haka kawai naji ina buƙatar driving da kai na”
“Amman ka biyo haka babu kp ƴan rakiya Abdallah abinda Mai Martaba yayi ta maka magana akai kenan, kana da maƙiya fa ya kamata kana bawa kan ka tsoro mana”
Murmushi yayi ya lanƙama Ummi suka shiga falon tana faɗin.
“Abinda Allah ya bututa babu mahani”
Amira bata jidaɗin yadda ya wuce ta ba, sai yayi kamar be ganta ba. Ba kuma dan be ganta ba ɗin sai dai rashin kular da yake nuna mata, dan shi sam bata burge shi.
Saman kujera ya zauna tare da Mahaifiyarsa yana dariyar yadda take masa faɗan ya take masa na zuwan da yayi ba tare da bodyguards ɗinsa ba.
“Haba ummi bodygrsd zasu tsare ni ko Allah?”
“Ni ba wani wa'azi na ce ka min ba”
Ya ɗaga hannayensa sama yana dariya. Kallonsa kawai Amira take cike da shauƙi, bata zaci yana dariya haka ba.
Ruwan sanyi Amal ta kawo masa tare da kofi, ya sha ruwan sosai ya jiƙa maƙoshinsa. Sannan ya tashi ya fice daga part ɗin ya nufi part ɗinsa. Tuɓewa yai ya ɗaura tawul ya shiga banɗaki yai wanka tare da alwala, sannan ya fito ya shirya cikin ƙananan tufafin daman sune tufafin daya fi so inda a gida yake. Sai da ya feshe jikinsa da turare sannan ya fito. Ya nufi masallacin gidansu yai salla azahar, bayan ya gama ya gaisa da wasu mutanen unguwar tare da sojojin da suke gadin gidan. Be fita da komai a aljihunsa ba shi kuma mutum ne mai alheri baya jindaɗin ya ganka be baka komai ba, sai dai kam akwai zuciya dan baya ɗaukar raini. Tsayar da mutanen yayi ya dawo cikin gida ya ɗauki kuɗi masu ɗan yawa ya miƙawa wani soja yace ya raba masu. Aiko har da waɗanda ba su yi salla a masallacin ba sai sheƙowa suke suna samun nasu rabo.
Sai da ya tabbatar kowa ya samu sannan ya juyo ya dawo cikin gida. Part ɗin Ummi ya nufa dan cin abincinsa na rana.
Duka ƙanensa suna dinning har Ummi suna cin abinci, Amira ma ta maida hankalinta sai cin abincin take kamar bata ga shigowarsa ba, Amal ce kawai ta kawarda kai tana yamutsa fuska kamar mai ƙyanƙyami.
Kujerarsa yaja ya zauna yana naɗe hannun T-shirt ɗinsa yana rabon ido, dan be san wane abinci zai fara ci ba.
“Dude don't..!”
Amal ta faɗa tana yarfar da hannu.
“Why?”
“All these things wannan yarinyar ce ta girka”
Ta faɗa tana nuna Amira. Daga Ummi har Abdool ɗin da kansa be jidaɗin abinda Amal tayi ba. Ɗan murmushi Amira ta yi, irin murmushin na rashin jidaɗi ta tashi daga cin abincin da take ta nufi ɗakin Amal ɗin wanda yanzu ya zame mata kamar ɗakinta a yanzu.
Sai ta ta shige sannan Ummi ta kalli Amal cikin xafin rai tace
“Dan ta girki abinci kike cewa karya ci ita ba mutum bace? Bata taimake ku ba? Bata fiye muku wannan inyamurar da take girka muku abinci ba? Miyasa kika ɗauki rayuwa da zafi ne Amal, ke dai baki rayu da babanki ba, balle na ce shine ya koya miki, wannan sam sam ba ɗabi'ar ƙwarai ba ce, ɗan 'adam ba abun wulaƙamtawa be ne”
Fashewa Amal.tayi da kuka ta tashi da gudu ta shiga ɗakin Meesha. Abdool ya zuba abinci ya soma ci yana faɗin
“Ummi you shouldn't talk to her that way marainiya ce”
“Ai daman kai kake buɗe mata ƙofar yin abinda duk take so, babu dama ayi ama Amal faɗa a gidan nan, duk abinda take yi hundred percent kai kake supporting ɗinta”
“Ummi ba haka bane, Amal itace ƙarama a cikin mu, kuma yarinyar nan ko da ta yashi bata san mahaifinta ba, ya kamata ace tana jin sanyi wani gurin”
Ummi tayi shiru tana cigaba da cin abinci. Tasna abinda Abdool yake faɗa gaskiya ne da acw mahaifin su an nan da ko hararsu Ummi bata isa tayi ba, dan game da yaransa ba shi da kyau babu mai taɓa masa komai kusancinsa da kai, musamman Amal da yake jin ta kamar ransa. Sai dan tana marainiya ba zai bata damar wulaƙanta kowa ba, Ummi bata da wannan halin daman can halin mahaifinsu baya burgeta, Amal ce ta kwashe halin gaba ɗaya, sai kuma Meesha dake ko-in-kula da mutane.
“Amman shi kenan, dan tana marainiya sai ta riƙa irin wannan halin? Dubi ka ga yarinyar nan wai har warin mutane take ji haba wannan iskanci ai har yayi yawa”
Abdool ya yi dariya
“Ƙurciya ne zata daina nan gaba kaɗan”
“Allah yasa”
“Amin”
Yaja tissue ya goge bakinsa, sannan yaja kujerar ta yi baya, ya miƙe tsaye ya nufi ɗakin da Amira take.
Kife ya tarar da ita saman gadon tana kuka. Sai ya zauna a kujerar dake ɗakin yana ƙarema ɗakin kallo kamar baƙonsa.
“Funny you indai akan Amal zaki riƙa kuka zaki ƙarar da hawayen ki ne kawai baki gama kukan ba, the more Amal knowing you are crying for her the more she will do something to insult you, haka rayuwarta take akwai ƙuruciya a cikin ta sosai”
Daga lokacin da kalaman Abdool suka fara
Showing 132001 words to 135000 words out of 280121 words
Sun isa Katsina lafiya, sai a mararraba motar ta soma gaba tana baya, hakan yasa direban fakawa gefe ya fito yana duba motar.
Anty ma fitowa tayi tazo ta tsaya gaban motar gurin da direban yake tana duba abinda yake taɓawa tare da tambayar abinda ya samu motar.
Motocin dake kai da kawo babu wacce ta tsaya, sai wata kafirar mota mai matuƙar kyau da ɗaukar hankali, ita har ta wuce sai ta dawo kusa da su ta faka.
Buɗe motar Abdool yayi ya fito ganin dattijowa kamar Anty a cikin zafin ranar nan ya hana shi wuce ce, dan daga gani yasan motar ce ta tsaya. Cikin wani irin taku ya ƙaraso gurin, shi ba na sauranta ba ba kuma na yana sanye da kakin soja ba.
“Lafiya me ya samu motar?”
“Wallahi muna tafiya ne ta fara bamu matsala ina jin ko ingin ne”
Matsawa yayi ya duba motar ya buɗe abubuwa ya gani, sai ya koma motarsa ya ɗauko ruwa da baƙin mai ya zuba mata sannan ya maida komai ya gyara shi kamar yadda yake.
“Shiga ka tashi motar mu ga”
Da sauri direban ya shiga ya tashi motar yayi baga yayi baya yaga ta dawo normal sai ya faka ya fito yana godiya.
“Mun gode Sosai”
“Ba komai amman a riƙa kula da irin waɗannan idan za'ayi tafiya mai nisa”
“Inshallah mun gode”
“Allah yayi maka albarka”
Anty Amarya ta faɗa tana ɗan murmushi, dan tasan ko waye Abdool tun da tana ganinsa a tv, sai dai bata tabbatar da shi ɗin ne ba tun da ya tsaya ya taimake su, sai dai kuma kakin dake jikinsa da stars sun nuna haka.
Ɗan rinawa yayi yana murmushi.
“Amin Mama na gode”
Juyawa yayi ya koma motarsa. Suma suka shiga tasu, da hau titi sai da ya ɗaga musu hannu sannan ya cigabansu da mugun gudu.
[7/18, 8:12 PM] Khadeeja Candy♥: *55*
*NAMRA POV.*
Yau kan ta ɗan samu sauƙi ba kamar jiya ba. Dan yau har aiki ta samu tayi, ta gyara gidan tas sannan tayi wanke-wanke, sannan ta shiga tayi wanka. Ta shirya cikin baƙar abaya sannan ta fito harabar gidan ta ɗauko murhunta na gawai ta ɗora girkin rana.
Bayan ta ɗora ta tashi ta koma cikin ɗakin ta ɗauko tabarma da filo ta shimfiɗa, dan ta soma jin ciwon kan na taso mata.
Bachine ya soma ɗaukarta, sai gyangyaɗi take, bata son yin bachi ta bar girkinta ya ƙone. Hakan yasa ta tashi ta wanke shimkafa ta zuba ta gyara wutar sai ta koma ta xauna tana kallon gate dan horn ɗin ta take ji ta yi yawa.
Bata jin za ta iya zuwa ta ga mai horn ɗin, duk da tana jin a gidan ake horn amman bata zaton za tayi wani baƙo mai mota, da zai iya zuwa gurinta yanzu.
Kwantawarta tayi tasa ɗan tsinƙe tsintsiya tana gyara akaifarta. Bata ɗago ba har sai da aka turo ƙofar gate ɗin aka shigo. Sannan ta ɗan juyo taga ko waye ne. Ganin Anty yasa ta tashi tsaye da sauri tana mamakin ikon Allah. Mafarki take ko gaske? Anty ce ko aljanarta? Tsaye tayi a gurin kamar an dasata. Idan har da gaske Anty zata yi farinciki ganinta dan tayi marmarinta sai dai kuma bata fatar amAnty taga ganta a halin da take ciki.
Bata gasgata Anty bace har sai da ta ƙaraso inda take ta dafa tana mata kallon mamaki dan duk yadda Yasmin ta faɗa mata sai taga abun yafi haka muni.
“Namra...!”
Rumgume Anty tayi ta fashe da kuka. A maimakon Anty ta rarrashe ta sai kawai ta tureta daga kafaɗarta.
“Wane irin hali ne wannan Namra? Jibe ke, a haka kike zaune kamar baiwa? Namra me yake ƙwaƙwalwarki? Kina rayuwar da ko amafarki ban taɓa tunanin za kiyi ba?”
“Idaba nake Anty, bautar Allah na ke, talauci da arzki duka na Allah. Da ace talakawa Allah yayi mu da sai dai mu hange wasu masu kuɗi suna sha'aninsu, mu muna cikin talauci. Dan kawai ina ƴar mai kuɗi ba shi yake nuna zan dauwama a daular duniya ba, duk wanda yayi arziki dole ne arzikin ya barsa ko kuma shi ya mutu ya bar arzikin, amman ba'a dauwama da duka biyu”
A natse take maganar cikin hikima tana son Anty tayi ma maganarta karatun ta natsu, ƙoƙarin lurar da Anty take kwaɗayin dukiya ba zai sa ta ƙi zaman aure ba. Ajiyar zuciya Anty ta sauke, tabbas ba xata iya canja abinda Allah ya rubuta ga Namra ba, amman tana ganin rashin dacewa a zamantakewar auren ta, wanda abu ne mai wahala da iya ɗauke idonta akan haka, bayan kuma tasan Asim ɗin ba dan Allah yake zaune da ita.
“Namra wannan rayuwar bata kamace ki, ƴar gata ce dubi inda kike zaune, yaushe gidan ya ƙone? Baki faɗa ba? Kina tunanin zurfin ciki zai miki magani ne?”
Ta share hawayenta ta hannun rigarta.
“An daɗe da yin gobarar, ban faɗa ba ne saboda ba lalle bane ku yarda a wacan lokacin”
“Je ki haɗa kayan ki, gida zamu je yanzu, zaman ki a gidan nan ya ƙare, an faɗa min har dukan ki Asim ya ke Namra wai me ke toshe miki ƙwaƙwalwa ne?”
Gabanta ya faɗi, tana jin rashin kyautawa a abinda Anty take ƙoƙarin aikatawa, dan me zatayi tattaki dan kawai ta kashe mata aure?
“Abbah ne yace ki zo da ni?”
“Ki shiga ki ɗauko hijabin ki na ce...!”
Anty ta katsa mata tsawa... Ja da baya Namra ta yi tana hawayen
“Ba zan biki ba Anty, Abbah ya faɗa min kar na kuskura na tunkaro gidansa da sunan saki ko yaji, ya nanata min lokacin da naje gida, ya ce duk na zauna masa a gidan sai dai ya kore mu ni da ke. Ba zan kashe miki aure ba, ba zan ƙara jefa kai na a halaka ba, mutane ba zasu jefe ni da biyu ba, ace na kashe miki aure kuma na bijirewa mahaifina”
Har cikin zuciyarta take faɗin haka, dan ta haƙiƙance a ranta ba zata taɓa biyar Anty ba, ba zata ja mata wani zagin ba, sai ace taje ta kashe mata aure. Bayan kuma tasan Abbah ba zai taɓa yarda ta zauna a gidan sa ba, ta kuma san Anty zata iya rabuwa da Abbah akan ta.
Wani irin kallo Anty take mata na mamaki da rasa abinda zata ce mata.
“Namra ke ba cikakkiyar mutum ba ce, ke rabin mutum ce! Ban san wanda ta haife ki bayan ni ba, da sai nace ke ba ƴata ba ce, ina da sanyin hali amman be kai ka ki ba ke sakarya ce, marar hankali dabba wace bata san ciwon kan ta ba. Na yi tunanin kin yi hankali na ɗauka kin gane inda duniya take a yanzu, ashe ke wawuya ce....”
Cikin zafin rai da ɓacin rai Anty take maganar sautin muryarta na fita ko'ina da ace ba babban gida bane da tuni an yi musu taro. Hawayen takaici.
“Na yi hankali Anty kuma zan zo gareki idan har Allah ya ƙaddaro rabuwa da tda Asin ya bani takardar sallama”
“Tam Allah ya ba ku haƙuri zama”
Ta duƙa ta ɗauki carbinta daya faɗi sannan ta miƙe tsaye ta kalli Namra da kyau da kyau. Sannan ta juya ta soma tafiya jiki ba ƙwari.
Rugawa Namra tayi a guje ta sha gabanta ta rumgume ƙafatunta, tana kuka sosai.
“Dan Allah Anty karki yi fushi da ni, dan Allah ki fahimci ne”
“Ba zan taɓa fushi dake ba Namra, ba zan tdine miki ba, Allah yayi miki albarka, idan kin lalace dole za a ce ƴata ce, idan kin ɗaukaka dole kuma ace ƴata ce, amman ba zan sake wauwayar gidan auren ki da Asim ba ko da kuwa gawarki ce a ciki, kar kuma ki sake roƙo na komai, ba zan baki ba matuƙar ba ki yi hankali ba kisa wannan a zuciyarki...!”
Ta janye ƙafarta ta bar Namra nan tana aikin kuka, ta nufi gate hawaye ya gangaro a idon Anty. Wani irin kuka Namra take, kukan da ita kanta ta manta when last tayi irinsa, ko ba komai tasan ta ɓata ran Anty, tabbas Asim ba mijin aure ba ne, amman ta yi alƙawarin zama da shi har iya rayuwarta dan kawai ta cika umarnin Abbah. Idan har ta bi Anty a yanzu duniya zasu zage ta ita da Anty kuma zata ƙara ɓata ran Abbah.
Tashi tayi taje gurin gate ɗin ta tsaya tana kuka, tana kallon motar Anty har ta suka bar unguwar. Sai ta zube a gurin ta ƙara fashewa da kuka tan mai jin kamar ta falla da gudu ta bi Anty.
Iya hawayen da Anty tayi a gidan Namra ne hawayen tausayin Namra, har ta suka isa gida bata sake wasu hawayen ba, dan yanzu ta fahimci Namra ba abar tausayu bace tun da bata tausayin kanta. A hanya Namra nata kiranta amman ta ƙi ta ɗaga wayar.
Su Maryam tun kamin ta yi musu bayani suka fahimci komai tun daga yanayinta da kuma ganin ba a zo da Namra ba.
Bayan ta huta ta faɗa musu abinda ya faru, duk basu jidaɗi ba, musamman Maryam da tafi so zafin rai, kasa haƙuri tayi har sai da ta kira Namra ta yi mata faɗa kamar wata yayarta.
A ɓangaren nan kam
Haka ta wuni cikin kuka daman aikinta ne shine ya zame mata abokin fira. Sai goman dare Asim ya dawo kamar yadda ya daba yana ganin yanayin Namra ya san ba lafiya ba, amman saboda mugun hali yaƙi ya tambaye ta damuwarta.
Sai ƙoƙare kai mata buƙatarsa yake. Ture masa hannun tayi ta tashi zaune cikin ƙunar zuciya ta ce
“Aikin kenan, Asim ka rako maza duniya, kai wayayye amman wayewar ka bata maka amfani ba, babu ruwanka da damuwa kai dai na gurka kawai ka ci, dare yayi ka kawo min buƙata, shine kawai...!”
Nuna kansa yayi duk da ɗakin babu wani haske sosai.
“Ke ni kika faɗa ma wannan maganar? Wuyanki yayi kauri ko Namra? Kin rai nani saboda bana da naira saboda ni takala ne ko?”
“Idan har talaucin ya dame ka miyasa baka yi ihun arxikin ya zo maka ba? Miyasa idonka ya rufe akan neman abinda za ka mutu ka bari, kai ne baƙon arziki shiyasa kake yawantar faɗarsa”
Tashi yayi ya ƙara motsa kusa da ita da zimmar dukanta, jikinsa har bari yake.
“Ni kike faɗawa wannan maganar Namra? Ni sa'anki ne?”
Mari ya kai mata ta gauce, ta fita waje da sauri. Bata zame ko'ina ba sai inda take girki, wuƙa ta ɗauko ta shigo ɗakin da ita idonta a kafe irin yau ba imani ɗin nan ta nuna sa da ita.
“Karka kuskura kace zaka taɓa ni Asim, zan iya kashe ka Asim, baƙin cikin da yake rai na zan iya juye maka shi a yau, tun da ka shigo gidan nan baka tambaye damuwa na ba, baka tambaye waya mutu waya rayu ba kai dai kawai matsalarka ka sani, saboda kai na ɓata ran mahaifina, saboda kai yau mahaifiyata ta koma gida cikin ɓacin rai, na kira ta bata ɗaga ba Maryam.ta kira ki babu irin cin mutumcin da bata min ba duk a kan ka Asim. Tam ya ƙare yanzu wuta ba zata sake cin ƙara ba, sai dai quta ta ci wuta...!”
A baki take furucin zuciyarta cike da yaƙinin ita ɗin zata iya, shi kansa Asim yaga hka idonta sai dai babu abinda zuciyarsa ta ayyana masa sai aljanu, ganin yake aljanun Namra ne suka taso cikin daren nan. Nan da nan marar ta cika da fitsari, be nuna tsoro a fuska ba, amman a zuci tsoron har yayi masa yawa, ala-ala yake kar aljanun su caka masa wukar, dan shi dai yasan Namra da kanta ba zata iya masa haka ba.
Uffan be ƙara cewa ba, sai kawai ya ɗauki tabarma da filo da abin rufa ya koma waje ya kwanta, dan baya jin zai iya kwana ɗakin karya kasheshi cikin dare.
A wajen ma sai ya koma can nesa da ƙofar ɗakin sannan ya shinfiɗa ya kwanta. Duk bayan minti ɗaya biyu yake farkawa ya tofe kansa da addu'a sannan ya sake komawa. Kamin safiya ta qaye har ya matsu. Yana fita salla asuba, yai fitar gaba ɗaya.
*AMIRA POV*
Tana jin parking ɗin mota, ta ayyana a ranta cewar Abdool. Da sauri ta ƙarasa shafa hodar da take ta ɗauki ɗankwalinta ta yafa saman kai ta biyo sawun kannensa dake masa oyoyo.
Amal ce taje da gudu ta rumgume shi, Ummi da sauran ƙannensa kuma suka tsaya a jikin ƙofar falo suna jiran ya ƙaraso. Hannu Amal ya riƙa suka nufo falon hularsa a hannu yana murmushin data ƙayata kyausa.
Ɗan risinawa ya yi lokacin daya kawo bakin ƙofar falon, ya gasheta da Ummi kamar yadda ya saba. Sai ta amsa masa murmushi tana faɗin.
“Mu duk mun ɗauka jirgi zaka biyo fa”
“Wallahi haka kawai naji ina buƙatar driving da kai na”
“Amman ka biyo haka babu kp ƴan rakiya Abdallah abinda Mai Martaba yayi ta maka magana akai kenan, kana da maƙiya fa ya kamata kana bawa kan ka tsoro mana”
Murmushi yayi ya lanƙama Ummi suka shiga falon tana faɗin.
“Abinda Allah ya bututa babu mahani”
Amira bata jidaɗin yadda ya wuce ta ba, sai yayi kamar be ganta ba. Ba kuma dan be ganta ba ɗin sai dai rashin kular da yake nuna mata, dan shi sam bata burge shi.
Saman kujera ya zauna tare da Mahaifiyarsa yana dariyar yadda take masa faɗan ya take masa na zuwan da yayi ba tare da bodyguards ɗinsa ba.
“Haba ummi bodygrsd zasu tsare ni ko Allah?”
“Ni ba wani wa'azi na ce ka min ba”
Ya ɗaga hannayensa sama yana dariya. Kallonsa kawai Amira take cike da shauƙi, bata zaci yana dariya haka ba.
Ruwan sanyi Amal ta kawo masa tare da kofi, ya sha ruwan sosai ya jiƙa maƙoshinsa. Sannan ya tashi ya fice daga part ɗin ya nufi part ɗinsa. Tuɓewa yai ya ɗaura tawul ya shiga banɗaki yai wanka tare da alwala, sannan ya fito ya shirya cikin ƙananan tufafin daman sune tufafin daya fi so inda a gida yake. Sai da ya feshe jikinsa da turare sannan ya fito. Ya nufi masallacin gidansu yai salla azahar, bayan ya gama ya gaisa da wasu mutanen unguwar tare da sojojin da suke gadin gidan. Be fita da komai a aljihunsa ba shi kuma mutum ne mai alheri baya jindaɗin ya ganka be baka komai ba, sai dai kam akwai zuciya dan baya ɗaukar raini. Tsayar da mutanen yayi ya dawo cikin gida ya ɗauki kuɗi masu ɗan yawa ya miƙawa wani soja yace ya raba masu. Aiko har da waɗanda ba su yi salla a masallacin ba sai sheƙowa suke suna samun nasu rabo.
Sai da ya tabbatar kowa ya samu sannan ya juyo ya dawo cikin gida. Part ɗin Ummi ya nufa dan cin abincinsa na rana.
Duka ƙanensa suna dinning har Ummi suna cin abinci, Amira ma ta maida hankalinta sai cin abincin take kamar bata ga shigowarsa ba, Amal ce kawai ta kawarda kai tana yamutsa fuska kamar mai ƙyanƙyami.
Kujerarsa yaja ya zauna yana naɗe hannun T-shirt ɗinsa yana rabon ido, dan be san wane abinci zai fara ci ba.
“Dude don't..!”
Amal ta faɗa tana yarfar da hannu.
“Why?”
“All these things wannan yarinyar ce ta girka”
Ta faɗa tana nuna Amira. Daga Ummi har Abdool ɗin da kansa be jidaɗin abinda Amal tayi ba. Ɗan murmushi Amira ta yi, irin murmushin na rashin jidaɗi ta tashi daga cin abincin da take ta nufi ɗakin Amal ɗin wanda yanzu ya zame mata kamar ɗakinta a yanzu.
Sai ta ta shige sannan Ummi ta kalli Amal cikin xafin rai tace
“Dan ta girki abinci kike cewa karya ci ita ba mutum bace? Bata taimake ku ba? Bata fiye muku wannan inyamurar da take girka muku abinci ba? Miyasa kika ɗauki rayuwa da zafi ne Amal, ke dai baki rayu da babanki ba, balle na ce shine ya koya miki, wannan sam sam ba ɗabi'ar ƙwarai ba ce, ɗan 'adam ba abun wulaƙamtawa be ne”
Fashewa Amal.tayi da kuka ta tashi da gudu ta shiga ɗakin Meesha. Abdool ya zuba abinci ya soma ci yana faɗin
“Ummi you shouldn't talk to her that way marainiya ce”
“Ai daman kai kake buɗe mata ƙofar yin abinda duk take so, babu dama ayi ama Amal faɗa a gidan nan, duk abinda take yi hundred percent kai kake supporting ɗinta”
“Ummi ba haka bane, Amal itace ƙarama a cikin mu, kuma yarinyar nan ko da ta yashi bata san mahaifinta ba, ya kamata ace tana jin sanyi wani gurin”
Ummi tayi shiru tana cigaba da cin abinci. Tasna abinda Abdool yake faɗa gaskiya ne da acw mahaifin su an nan da ko hararsu Ummi bata isa tayi ba, dan game da yaransa ba shi da kyau babu mai taɓa masa komai kusancinsa da kai, musamman Amal da yake jin ta kamar ransa. Sai dan tana marainiya ba zai bata damar wulaƙanta kowa ba, Ummi bata da wannan halin daman can halin mahaifinsu baya burgeta, Amal ce ta kwashe halin gaba ɗaya, sai kuma Meesha dake ko-in-kula da mutane.
“Amman shi kenan, dan tana marainiya sai ta riƙa irin wannan halin? Dubi ka ga yarinyar nan wai har warin mutane take ji haba wannan iskanci ai har yayi yawa”
Abdool ya yi dariya
“Ƙurciya ne zata daina nan gaba kaɗan”
“Allah yasa”
“Amin”
Yaja tissue ya goge bakinsa, sannan yaja kujerar ta yi baya, ya miƙe tsaye ya nufi ɗakin da Amira take.
Kife ya tarar da ita saman gadon tana kuka. Sai ya zauna a kujerar dake ɗakin yana ƙarema ɗakin kallo kamar baƙonsa.
“Funny you indai akan Amal zaki riƙa kuka zaki ƙarar da hawayen ki ne kawai baki gama kukan ba, the more Amal knowing you are crying for her the more she will do something to insult you, haka rayuwarta take akwai ƙuruciya a cikin ta sosai”
Daga lokacin da kalaman Abdool suka fara
Book Chapters
Chapter 1Chapter 2Chapter 3Chapter 4Chapter 5Chapter 6Chapter 7Chapter 8Chapter 9Chapter 10Chapter 11Chapter 12Chapter 13Chapter 14Chapter 15Chapter 16Chapter 17Chapter 18Chapter 19Chapter 20Chapter 21Chapter 22Chapter 23Chapter 24Chapter 25Chapter 26Chapter 27Chapter 28Chapter 29Chapter 30Chapter 31Chapter 32Chapter 33Chapter 34Chapter 35Chapter 36Chapter 37Chapter 38Chapter 39Chapter 40Chapter 41Chapter 42Chapter 43Chapter 44Chapter 45 Chapter 46Chapter 47Chapter 48Chapter 49Chapter 50Chapter 51Chapter 52Chapter 53Chapter 54Chapter 55Chapter 56Chapter 57Chapter 58Chapter 59Chapter 60Chapter 61Chapter 62Chapter 63Chapter 64Chapter 65Chapter 66Chapter 67Chapter 68Chapter 69Chapter 70Chapter 71Chapter 72Chapter 73Chapter 74Chapter 75Chapter 76Chapter 77Chapter 78Chapter 79Chapter 80Chapter 81Chapter 82Chapter 83Chapter 84Chapter 85Chapter 86Chapter 87Chapter 88Chapter 89Chapter 90Chapter 91Chapter 92Chapter 93Chapter 94