kuma tsantsin da tiles ɗin yake da shi.
Haleema ta yi gaggawar riƙeta

“Be careful”

Amira na kallonta ta san ƙanwar Abdool ce dan ga kamanin Abdool nan shimfiɗe a fuskarta. Ita ta taimaka mata ta sauko saman stairs ɗin, tana riƙe da hannunta har suka ƙarasa tsakiyar falon gurin da sauran ƴan'uwanta suke zaune.

“Welcome Sister”

Fauza ta faɗa tana faɗaɗa murmushinta ga Amira, Meesha kan aikin dannar waya kawai take ko inda Amira take zaune bata kalla ba. Amal ce ta karkace fuska tana mata kallon ƙyama ɗin nan, daman ita ta fi uban kowa wulaƙanci a gidan, cikin ma tana tsoron Ummi da Abdool dan sam basa son wulaƙanta ɗan'adam.

Haleema da kanta ta zaunar Amira a ɗayar kujerun da suke gurin, dan falon ya kasance mai part biyu ko kuma a'ce uku, idan a ka haɗa da dinning area.
Bayan ta zauna Meesha ta ɗaga kai ta kalleta tare da miƙa mata hannunta.

“Hey Sis Welcome, my name is Aisha aka Meesha, ke ce Amira ko?”

Amira ta ɗan ɗaga kai tana murmushin mai nuna tsantsan ladabi da kunya, da kuma sanin kai, kana ta miƙa mata nata hannun ita ma.

“Eh ni ce nice to meet you Meesha”

“Nice to meet you too”

Ta ɗan sakar mata murmushi kaɗan, sannan ta tashi ta nufi ɗakinta, till idonta na kan waya.
Tsire baki Amal tayi ta tashi ta nufi ɗakin Ummi.

“Shukura....”

Fauza ta ƙwala mata kira tana kallon tv kamar ba ita ce tayi kiran ba. Da gudu wata baƙar mace ta fito da gudu daga wani ɓangare na falon ta zo haban Fauza ta tsaya.

“Hasiya ga ni”

“Ba ki ga mun yi baƙuwa ba? A kawo mata abin sha mana”

Wacce aka kira da Shukura ta kalli Amira tana washe baki.

“A'a baiko na mu ne ta zo, sennu sennu, sennu da zuwa, bari ya kawo miki abinse yanzu, ahh sennu baiko”

Ta juya da sauri ta nufi kitchen. Yanayin shigarta da kuma maganar ya tabbar ma da Amira bayarabiya ce. Ƙasa ƙasa Amira take kallon tsarin falon tun daga kujerun har labulayen da flowers da aka ƙawata falon da su komai maroon color ne har center carpet ɗin.
Ga wasu golden gulob da aka ƙawata falon da su, wanda Amira bata taɓa ganin irinsu ba iya tsawon rayuwarta.

Fitowar Ummi ne yasa Amira ta karkata tana kallon yadda Ummi ta doso gun da take tana murmushi. Babu shaka wannan Mahaifiyar Abdool ce dan ga kamaninsa nan sak a fuskarta, dakakkar shaddar dake jikinta ta haske ta sosai, kamar wata sarauniya, hauru makka guda biyu dake a bakinta sun haska fuskarta sosai.

Zubewa Amira ta yi ƙasa tana gaishe ta. Ummi ta dafata tana mai jindaɗin yadda Amira ta bata girma.

“Tashi tashi ƴata”

Wannan furucin da tayi ya faranta ran Amira sosai, cikin kuzari ta tashi amman bata zauna a kujerar ba sai ta zauna ƙasa ta nutsar da kai.
Ummi ta ture Amal da ke riƙe da hannunta tana zuba mata shagwaɓa ta shafa kan Amira.

“Sannu ƴa ta ya hanya?”

“Alhamdulillah”

Ummi ta kalli Haleema tana ɗan zare ido.

“Miyasa ba a kawo mata komai ba?”

Haleema ta juyar da babban yatsanta tana nunawa Ummi kitchen. Sai fmga Shukura ta fito ɗauke da ture da kayan ciye-ciye niƙe-niƙi a saman turen. Har zata dire turen gaban Amira sai Ummi ta girgiza mata kai.

“No kai mata ɗakin Amal”

“Tau Mama Ummie”

Shukura ta faɗa ta nufi ɗakin Amal ɗin.

“Tashi ki bita ki shiga ciki ki yi wanka sai ki ci abincin”

“To”

Amira ta unƙura ta tashi ta bi bayan Shukura tana ƙarema ɗayan ɓangaren na falon kallo.
Sai da ta shige ɗakin sannan Amal ta fashe da kuka kamar wata ƴar shekara uku ta narke a jikin Ummi har da kuka.

»“Ummi za ki ce ta je ɗakina ni warinta na ƙe ji”

“That's why na ce ta je ɗakin ki, ba kece mai jin warin mutane ba? Wannan wane irin iskanci ne zaki ce kina jin warin mutane, dan iskanci”

“Wallahi Ummi mutane wari suke”

“Tau yayi kyau, kullum ina rabaki da wannan halin kina ƙarawa ko? Wannan dai baƙuwar Yarima ce idan kika wulaƙanta ta Dude ɗin ki kuka wulaƙanta”

Ta ƙara ɓare baki tana kuka, sai duk ƴan'uwan suka sa mata dariya, especially Haleema data fi kowa raina ta. Ummi kan tashi ta yi ta bar mata falon ta nufi kitchen.


RASHIDA POV.

Duk yadda take misalta yadda zata rayu ba tare da Hilal ba sai ta farka daga mafarkin da take, bata san son da take ma Hilal yayi yawa a zuciyarta ba sai yanzu, ta take ƙoƙorin lallasar zuciyarta ta haƙuri da rashinsa.
Saka wayarta da ya yi a blacklist ya dame ta sosai, tun da ko text ɗinta ba ya iya karantawa a yanzu. Gashi yayi blocking ɗinta a facebook da whatsapp duk inda take iya ganinsa ta samu sanyin zuciya bata ganinsa a yanzu.

Yau weekend ne ba ta zuwa aiki, amman kwata-kwata ta kwacewa abinci da kuma zaman falon da take ɗan yi dan ragewa kanta damuwa.

Bata fito ba sai da ta ji motsin ƴaƴan ƴar'uwarta Ummul Faisak, da suka zo weekend, sannan ta fito dan bata son kowa ya gane damuwarta.
Tayi ƙoƙarin yin far'ah dan da ɓoye damuwarta, amman hakan be hana Momy yi mata magana ba.

“Yau yanzu aka fito”

Ta zauna kusa da ƙanwarta tana sotsar kanta.

“Bana jindaɗi ne”

“Ai kullum ba za ki taɓa jindaɗi ba matuƙar baki cire Hilal a zuciyarki ba, ai mutumen be mana hallaci ba kuma ya ci amana”

Ta yi ƙasa da kanta hawaye na mata zuba, sai ta shiga murza yatsun hannunta. Ummu ta dafa ta

“Ki kwantar da hankalin ki duk abinda take taƙamar ta miki wallahi sai ya karye, kowa ya san wannan ba halin Hilal ba ne, mutumen da ke son ki kamar ya mutu sai kuma.ace yau shine ya sake ki hmmm sherin mata yawa ne da shi”

Momy ta girgiza kai ta tashi ta nufi gurin da yaran suke wasa tana faɗin

“Addu'ah itace kawai mafita, idan ma wani abun ta yi miki sai kiga ya karye”

Sai da ta shige ɗakin tana gargaɗin yaran kar su mata ɓanna sannan Ummu ta Kalli Rashida tace

“Ke ma.fa sai kin tashi tsaye, ai tun farko kece kika yi sakkiyi har haka ta faru gashi nan kina nadama, ƴan matan nan na zamani, ai dole sai ka tashi musu tsaye balle ance yarinyar nan ta daɗe fa ba tayi aure ba, kin ga ko ai dole ta nemi ƙorar ki dan ta mallake miki miji”

“Ina ta ƙoƙarin yaƙar zuciyata ne wajen ganin ma fitar da son Hilal a rai na, ina tsoron kar son da na ke masa ya kai ni ga hallaka”

“Au shikenan kin yarda ki bar mijin ki? Uban ƴaƴanki? Saboda wata can ta mallake miki shi? Ashe ƙaryar so kike tun da ba ki iya yaƙi nemawa kan ki ƴan ci, ai yanzu ko wani auren kika yi baki san inda zaki faɗa ba ƙila ma ta fi wannan bala'i ƙara ma wannan ki ƙyaƙeta wallahi tun wuri”

Tayi shiru tana share hawayen ta, tare da nazarin kalaman Ummu Faisak babu shakka tana son mijinta kuma wannan juya bayan da Hilal yayi mata a take ya tabbatar mata da lallai ba a banza ba ne ya yi mata haka. Kuma idan bata zauna da Hilal ba waye zai aure ta? Tasan ta gama aure duniya dan yanzu da wahala ta samu wanda xai aure inda har wayayyen mutum ne sai ya nemi su yi gwaji idan ko har ya gano tana ɗauke da cutar ba zai aure ta ba. Kuma a halin yanzu babu wanda ya kamata ya zauna da ita sai shi tun da shine ya mori jikinta sai yanzu dan wannan matsalar ta same ta sai kuma ya guje wannan ma ai butulci ne, ko da yake baya cikin hayyacinsa.

“Ke....”

Ummu ta girgizata ganin tana ta mata magana tun ɗazu amman bata jinta.

“Ke kwantar da hankalin ki, akwai wani buzu da yake unguwar mu, kuma ance yana aiki sosai, zan masa magana yayi mana aiki akai a kare abunda ta yi masa ”

Rashida ta yi saurin dafata.

“A'a ki barsa kawai ina nan ina faɗawa Allah buƙata na kuma na san zai karɓa min, very soon za ki ga asirin ya karye”

“Toh Allah ya amsa, amman duk da haka ta kin shiga malamai kinjinta bakin su, kin san fa asiri ko Annabi ya kama balle wani Hilal”

“Haka ne, zan gwada amman ba yanzu ba, sai hankalina ya kwanta sosai”

“To amman ni bana son ki cika idda ba tare daya mai da ke gidansa ba”

“Karki da mu komai za yi dai-dai inshallah, bari na leƙa gidan su ƙawata Asmee”

“Ai ƙara kan kina fita ko damuwa zata rage miki. Bari na shiga na gaida Dady”

“Ai baya nan ya tafi ɗaurin aure”

“Okay”

Rashida na shiga ɗakinta ta ɗauki jakarta ta saka hijabinta ta ɗauki makullin mota ta fito a gaggauwacw tayi ma Momy sallama fitar ta fice daga gidan kamar zata tashi sama...

Ba gidan Asmee zata ce je ba, daman ta faɗa ne dan ta yi hujja da gidan kawai.
Garin da Malamin ya ke ta nufa, bata ko tsoron tuƙi ita kaɗai gata mace yadda take gudu kai ka ce wani ne ya biyota. Sai kuwa gashi ta isa garin cikin ƙanƙanen lokaci.

Yau bata tararda layi kamar ko yaushe ba. Bayan mutane dake gabanta sun gama abinda zasu yi sun fito sai ta shiga da kuzarinta.
Haka ta zauna gabanta tana zayyana masa irin son da take ma mijinta da kuma neman komawa gidansa ta ko wane hali.

Kuɗi mai tsoka ta ciro a jakarta ta miƙa masa da sunan somin taɓi, sannan tayi masa alƙawarin idam har aiki yayi zata kai shi makka ta siya masa mota kuma ta bashi gidan ta dake a cikin garin Zaria.

A take ya fara tsiface-tsifancesa sannan ya ɗauko wani kanko mai ruwa, ya aje gabansa ya karanta wasu dala'ilai sannan ya kira kwari da baka suka zo da kansu gabansa suka tsaya. Rashida taji tsoro sosai amman a haka ta dake ta tsaya a inda take tana ƙara girmama iya aikinsa.

Kwari da bakan ya haɗa ya saita ruwan yana karanta wasu abubuwan da shi kaɗai yasan yaren da yake sannan ya ɗora da

“Ajib ya dala'ilu, ajib ya sargirfir... Kalsoom Kalsoom Kalsoom...”

Haka ya kira sunanta har sau uku, sai ga hoton Kalsoom ya bayyana tana zaune a falo tare da Rafiq sai wasa take masa. Sai Malamin ya harba kwarin cikin ruwan. Sai ta yi tsaye tsakiyar ruwan, a take ruwan ya soma sauya kala zuwa launin ja kamin daga bisani ya zama jini gaba ɗaya.

Sannan ya kalleta

“An jima zamu yanka baƙar kaza, da kuma kaza mai wake-wake, ke kuma ki dafa tuwon dawa ki yi sadaka, idan ba zaki iyaba sai ki siye”

“Na gode Malam shikenan yanzu?”

“Eh yanzu kam shikenan ki koma gida kawai ki saurari sakamako”

Ta ji babu daɗi duk da tasan bata da wata mafita sai wannan, yanzu kam tasan tun da akayi ma Kalsoom harbin kanko shikenan haukacewa za ta yi, dole ne kO Hilal.ya rabu da ita ko kuma ya mayarda ita gidansu dan ya nemo wanda zata riƙa masa ɗansa.
Cike da farinciki ta dawo gida wani ɓangaren kuma tana ganin rashin dacewar abunda ta aikata, sai xuciyarta ta kan zuga wajen ganin abun ya gushem mata a zuciya, tana ayyana yadda ita ma Kalsoom tayi mata ta raba ta da mijinta........






Pray for my mother she's sick.
[7/18, 8:12 PM] Khadeeja Candy♥: *51*

NAMRA POV.

Ashe wuya tana canja mutum, iɗan ka hango Namra a yanzu ba zaka taɓa cewa ita ce ba, ta canja sosai tun daga kan hallitarta zuwa suturar dake jikinta. Zane daban riga dabam sai faman hurin wuta take hayaƙi duk ya boɗe gurin, sai fama.take ta itacen kamar wata tsohuwa.
Sam bata damu ba da hanin zuwa tarbar lefen da Asim yayi mata, ta san ko ba komai ita tana shakar zuwa yanzu dan bata san yadda ƴan'uwanta za su kalleta ba, duk ta wani koɗe kamar ba ita ba.
Daker ta samu wutar ta kama har ta dumama tuwo sannan ta wanke kular da take sakawa Asim abinci ta zuba masa ta kai masa sai ta sake fita ta ɗebo masa ruwa ta aje masa.
Gefensa ta zo ta zauna ta lanƙwashe ƙafafunta irin ladabin nan, sannan ta soma magana gabanta sai faɗuwa yake

“Asim magana nake son mu yi ina son ka ba ni aron hankalin ka”

“Ai kunne ne yake ji ko?”

Ya faɗa yana auna ɗummen a bakinsa.

“Asim ba zai yiyu kullum na riƙa ci da kai na ba, Allah be ɗora min ciyar da kai na ba, fisabilillahi abinda kake min baka kyauta min, bana yin abinci ka yaba, baka bani abin dafawa balle ma kuɗin cefani yanzu tsakani da Allah ka kyauta kenan?”

Ya ɗaga kai ya kalleta yana suɗar hannu.

“Namra kenan, wallahi kina da matsala wani lokacin ƙwaƙwalwarki ƙarama ce, yanzu idan nace zan baki abinci kawai ko kuɗin cefane ina su ke? Ba sai da abu ake yinsa ba? Ko babu zan ba ki?”

“Amman naga kana fita aiki Asim ba za ace kullum baka samowa ba ki kaɗan ne dole wata rana sai ka samo”

“To ɗan abinda na ke samowa ai ba zai wuce na hau achaɓa ba, ba fa wani samu muke sosai ba, ni kaina na fiki son na ciyar da ke dan Aallah ya fi bawa mai yi iyalansa, sannan babu Namijin da zai so mace ta ciyar da shi ko dan gudun irin wannan gorin”

“Ba gori na ke maka ba, gaskiya nake faɗa, idan mu ka zauna muka ce wannan kuɗin na sana'ah kullum shi za'a ci, sai mu cinye sana'ar mu zauna a haka babu komai”

“To ya zan yi Namra? Sata zan yi na baki ko kuma kai na zan siyar na ciyar da ke? Kina gani ba wata sana'ah ce da ni ba daga yanzu ki lissafa duk abinda san kin kashe na ciyar da kan ki da ni idan na yi kuɗi zan biya ki, ni bana son gori akai na farau rashin arxiki? Ko kuma ni na kawo tauasaci duniya? Idan ma kin gaji da zama da ni ne sai ki faɗa min kawai ba wai ki riƙa min magana any how ba”

“Babu mace da zata zauna da kai a yadda na zauna da kai Asim, na watsar da jindaɗin gidan mu dan kawai na yi maka biyayah na zo na zauna a nan gidan ina rayuwar da ban taɓa mafrkin shiga, ka dubi jikina, duk wanda yasan ni ya gan ni a yanzu ba zai ce ni ba ce, amman kullum baka gani sai anbanta ni kake”

“Mtssswww kaji ba, sai jawabi da ƙaryar arziki, duk arzikin gidan ku me suka ƙulla miki? Babu wanda zai gan ki yace ke ƴar gidan ce, tun da kika yi aure har yau babu wanda ya taɓa tako ƙafarsa ya zo gidanki, haka ake rayuwa, ai ko bunsuru kike aure idan basu yi dan ni ba sayi dan ke, ko riƙon ki ake ya kamata ace wani naki yazo garin nan ganin amman ko ciwon da nayi har na warke babu wanda ya leƙo kamar na kashe musu wani”

“Me zai kawo ƴan uwana a gidan ka, bayan sun san dalilin aure na da ka yi? Me za su zo su yi? Ciwon da ka yi wane irin jawabi ne ba ka min akan jinyar da kayi sai ka ce sune suke da alhakin ɗaukar naunyin ɗawainiya da kai, Mama da take mahaifiyarka me tayi maka? Kuɗin data karɓo ai dashen da kuke ne, duk ni nayi ɗawainiya da kai”

Tasss ya watsa wanke mata fuska da mari, ya hau shurinta sai kaurar fuskarta yake yana faɗin.

“Duk iskancin ki ya tsaya a kan ki, karki kuskura saka uwata a cikin sheɗancin ki, dan ba warin ki ba ce”


Kuka take yi sosai tana rufe idonta da ta ke jin kamar ƙasa ta watsar mata a cikin. Be kula irin aika-aikar da yayi ba yasa ƙafa ya fice.
Haka ya wuni a ɗakin tana aikin kuka kamar ta cire idonta, sai da aka kira salla azahar sannan ta samu kukan ya tsaraita mata har ta unƙura ta tashi.

Wanka tayi tare da alwala sannan ta saka wasu tufafin tayi salla. Sai ta ɗauko qur'ane tana karatu.
Guraren uku da kwata wayarta tayi ringing ita har ta manta da sha'anin wayar sai yanzu. Bata kula wayar ba sai data ta kai ƙarshen suratul Yasin, sannan ta rufe qur'anen ta yi addu'ah daga bisani ta maida alƙur'anen mazauninsa, sannan ta nufi wayar ta duba.

Number Anty Yasmin ce. Ta yi mamakin ganin kiran Yasmin har four miss calls, ta manta when ma Yasmin ta kirata tun suna shiri. Bata da kuɗin da zasu isheta magana amman tasan ba zata rasa na flashing ba.
Kamin ta kira sai ga Yasmin ta ƙara kira. Namra tayi saurin picking ta kara a kunne.

“Assalamu alaikum Anty”

“Na'am My Sis ykk”

“Lafiya ƙalau, ya Gwaggo”

“Tana can gida, ni na zo katsina seminar ne, tun shekaran jiya yau zan koma, kuma bana son na wuce ban gan ki ba”

Gaban Namra ya faɗi bata ƙaunar wani yace zai kawo mata ziyara a yanzu, sai dai bata jin zata iya hana Yasmin zuwa gidanta tun da har ta nuna son zuwa.

“Ayyah Anty Yasmin yanzu za ki zo?”

“Eh anjima kaɗan zamu koma”

“Okay ki ce a kawo ki Nasarawa, idan an kawo ki sai ki shiga ta cikin unguwar zaki ga gidan daya ƙone sai ki shigo nan”

“Okay gani nan zuwa yanzu”

Ta kashe wayar. Namra ta juya tana kallon ɗakinta, to be frank bata son kowa ya san halin da take ciki, sai dai babu yadda ta iya.
Kimtsa ɗakin ta shiga yi dan yau duk batayi shara ba tun da wuni tayi kukan dukan da Asim yayi mata.
Wajen gidan ma ta gyara bakin inda zata iya dan baɗin gidan ba mutum ɗaya ne zai iya share shi duka ba, yaro ta aika da kuɗi aka siyo ma Yasmin gala da ruwan sanye ta aje mata. Sannan ya canja tufafin jikinta ta saka masu ɗan kyau ta zauna
Showing 120001 words to 123000 words out of 280121 words