Haleema ji take kamar ta daki yar'uwarta. Har sai da Ummi ta katsa musu tsawa.
“Haleema kar na sake jin irin wannan kalamin a bakin ki, Aisha ke kuma ya isa tun da ba cewa aka yi za a aura masa ita ba, ku Shafa min lafiya dan Allah ku tashi ku bani guri”
Duk miƙewa suka yi suka fita, ban da Amal data laƙe jikin Ummi ita ala dole sai an dafa maya makaroni.
“Ai kema kin iya dafawa, Amal har mota kike tuƙi fa amman ki zo kina min abu kamar jaririya, idan yanzu aka miki aure ai sai zama dan kin girma, ba kece auta ba autana tana nan zuwa”
Ummi ta faɗa da raha a fuskarta. Amal ɗin tasa dariya dan tasan abu ne mai wahala a yanzu.
“Za a ce tsohuwa ta haihu”
Ummi ta tiƙi bayanta tana dariya
“Yes Tsohuwa maman Amal, tashi ki cire uniform”
Tashi ta yi ta fice tana dariya.
*NAMRA POV*
Kamar yadda suka saba yi duk mai ciwo, bayan ta faɗa masu matsalarta sai suka bata gwajin jini da fitsari, suka sa kuma taje ta yanki sabon kati dan duba wacan matsalar nata na robar dake hannunta dan a bayanin da ta yi ma likita ya fahimci ciki ne a jikinta. Sai dai bashi da tabbacin haka tun da ta faɗa masa tana saye da roba, duk da yasan ana samun irin wannan matsalar a wani lokaci.
Awan fitsari kawai ta samu yi, a take, na jini cewa suka yi sai da yamma ta zo ta karɓa, su kuma waɗanda zasu dubata a ɓangaren robar sun tashi aiki.
Tun da karɓo results ɗin ta kasa ta buɗe dan bata son ta ga abinda yake ciki, tasan idan har ciki ne tana cikin matsala dan bata gama warkewar ciwon mahaifarta, kuma ga roba jikinta ace tayi ciki tasan duka ƙarin matsalar ne. Ko da ta koma gurin likitan yana shirin tashi, har ya haɗa kayansa, a tsai-tsaye ya duba takardar tana fuskarsa da mamaki ya ce
“Kina ɗauke da juna biyu”
Ras ras ras gabanta ya faɗi, sai ta faɗi saman kujera tana hawaye. Da sauri likitan ya aje kayan hannunsa.
“Hey wannan ba wata matsala bace ana samun irin haka daman, amman abunda yafi zan rubuta miki hoto sai kije ayi hoto a bincika lafiyar cikin, kuma ki tabbar kin je an cire miki wannan robar”
“Doc mahaifa tana da matsala shiyasa aka samun robar”
“Ba lallai ne har yanzu matsalar ki tana nan ba, shiyasa nake son ki yi hoton”
Ya ɗauki wata takardar yayi rubutu ya miƙa mata.
“Kije ayi miki hoto, zuwa gobe sai ki kawo na duba ki, ko kuma ki dawo wani likitan ya duba ki, ki kwantar da hankalin ki ba wani abu nima mai ɗaki na ta taɓa haka”
Jakarsa ya ɗauka ya rataya ya face. Sannan ita ta tashi ta fito tana hawaye, maimakon taje gurin hoton sai kawai ta yanke shawarar komawa gida dan ita har yanxu jikinta na bata ba ƙalau take ba, balle bata da kuɗin da zasu isheta hoto tun katin ganin likita na asibitin ma kusan ɗari bakwai ne.
Tun cikin Napep take ta kiran Asim amman ya ƙi ya ɗaga saboda yana gaban Hajiya, wacce ta zame masa kamar uwa a yanzu, yadda yake jinta ko Mama data haife sa baya jinta haka nan.
Hakan yasa ta yanke shawarar tura masa saƙon karta kwana.
Ƙin ɗaga wayar yayi dan akwai yana gaban Hajiya, ita ta jidaɗin hakan da yayi ko ba komai tasan ya girmamata, gashi tun da yazo gidan be taɓa fita da sunan yaje gida gurin matarsa ba.
Sai da ta gama lissafa masa abunda zai siyo mata sannan ta bashi kuɗin tana murmushi ciki ladabi ya karɓa ya tashi ya fice.
Sannan Hajiya tayi murmushi ta maida dubanta ga ƙawarta, Hajiya Ubaida.
“Gaskiya yaron nan yana da ladabi ina kika damo shi?”
“Uhmm tsuntsune daga sama gasasshe Allah ya bani daga gyaran gate”
A nan ta kwashe labarin komai ta bawa Aminiyarta yadda suka haɗu da sharaɗin data gundaya masa da kuma zaman gidan da yake, da kuma ƙudirinta a kansa.
Hannu Hajiya Ubaida ta bata suka taɓa
“Shegiya Sadiya duk abunda kika sawa gaba sai kin ga bayansa, hala yarinyar mai kyau ce?”
“Tana da kyau wallahi ta haɗu ba ƙarya, sannan kin ga na samu dama biyu, daman Alhaji Usaini ya dame ni na samo masa sabin shiga, wai duk wanda nake kai masa basa da ladabi kuma an taɓa amfani da su, kwana biyu sai su fara masa tsageranci”
“Ai kin san manyan mutanen nan sun fi son tsaida mutum ɗaya, wanda zasu riƙa amfani da shi kullum”
“Eh shi ma haka yace, wai idan yana bin irin guys ɗin nan za'a iya gane shi, yafi son tsaida mutum ɗaya, kuma kin ga irin wannan zai fi jindaɗinsa dan ga alama zai yi ladabi, sannan garin su ɗaya, idan ta kama ya koma can ma, ni sai ya barmin matar a nan, dan ba zan taɓa nuna masa ina don matarsa ba, shi wata rana zan iya buƙatarsa”
Hajiya Ubaida ta ƙalƙyale da dariya.
“Ke Allah dai ya yafe mana, ya shirya mu”
“Amin kedai ai ina son tuba amman sai nan gaba, dan bana son Zeenat ta san halin da nake ciki”
“Gaskiya kam, ai ƙara ai daina da wuri kar azo aji kunya”
Hajiya Sadiya tayi fuskar tausayi kamar mai tsoron Allah da gaske, tana kallon Hajiya Ubaida wacce sana'arsu ta zama ɗaya.
*ASIM*
Be wuce kasuwar ba, sai da ya bi ta gida dan jin abinda Namra zata faɗa masa, badan saƙonta da yaga ni babu ma abunda zai sashi bi ta gidan. Kamar baƙin haɗari haka ya doshi gidan bakinsa ƙumshe da maganganu kala-kala, dan gani yake a yanzu shi ma ya kai matsayin da zai iya faɗawa magana son ransa, balle Namra da yake gani kamar banza.
A ɗaki ya tararar da ita kwance sai hawaye take. Daker ta ɗago ta kalleshi, duk da tana cikin yanayin damuwa hakan be hanata, kallon irin shigar dake jikinsa ba. Takalmin dake ƙafarsa kaɗai zasu iya kaiwa dubu 10+ balle wando da T-shirt.
Be ji zai iya zama a ɗakinba, sai kawai ya tsaya jikin ƙofa yana mata wani kallo, azuciyaraa yake hantararta ganin yadda ta ƙara lalacewa.
“Ya aka kika samu ciki?”
Wani kallo tayi masa zafin furucinsa yana zuciyarta.
“Kamar ya? Ina da wani mijin ne bayan kai”
“Ni ya za'ayi na sani, yanzu ai ba a shedun mutum”
“Shigowarka Asim irin wannan furucin zaka min? Tun da kasa ƙafa ka bar gidan nan babu ruwanka da ni kamar ba matar ka”
“Ya kike so nayi Namra aikin zan bari na zo na tisaki gaba nayi ta kallo ko me? Yanzu ma a hanya nake saƙon da kika min ne yasa na biyo”
Kawarda kai tayi ta haɗe hawayen da take da tabbacin idan har suka fara zubar mata bata san lokacin tsayawarsu ba.
“Daga Asibiti na ke likita ya ce ina da ciki, kuma akwai roba a jikina”
“To ya aka yi haka?”
“Nima ban sani ba, amman yace min daman akan samu hakan wani lokaci, yace naje nayi hoto aga lafiyar cikin, Asim ina tsoron ko mahaifata bata gama warkewa ba”
“To a zubar da cikin mana”
Miƙewa tayi tsaye tana kallonsa.
“A zubar fa kasa kasan abunda kake faɗa?”
“Na sani mana, Namra wannan ba lokacin samun yara bane, muna planning na neman kuɗi kuma yara zasu shigo, ki duba irin wahalar da muka sha a baya yanxu kuma hanya ta fara buɗe mana sai kuma haihuwa ta zo, gaskiya ni ban shirya ba”
“Ni kuma na shriya Asim, ni nake da matsalar da nake da a mahaifata kuma im ready to give birth saboda nima haihuwata aka yi, Allah ba xai bani kyauta na jefar ba”
Cikin wata murya tayi furucin muryar da bata san tana da ita ba sai a yau. Shi kuma ya gyara tsayusarsa yana mamakin ta
“Wallahi Namra sai yanxu na gane lallai ke ba masoyiyata bace. Kin manta lokacin da nake cewa kije ki cire robar nan amman ki ƙi, ko wannan zubar da ciki da kika sha ban san lokacin da kika sha ba, wata ƙila kin yi zubar da cikin ne shiyasa har mahaifarki ta samu matsala, sai yanxu da kika ga zan yi kuɗi ko shine zaki nuna min baƙin hali ki ɓullo min ta haihuwa, to ni ban shirya haihuwa yanzu ba dan haka dole a zubar da cikin nan”
“Wallahi tallahi ba zan zubar da wannan cikin ba, ko da kuwa wannan cikin yana nufi ya rayu, ni na mutu”
“Haka kika ce?”
“Haka na ce kuma haka xaka gani”
“To sai dai ki zaɓa ko ni ko cikin nan...!”
Wani kallo tayi masa na ƙara tantance zancen daya fito daga bakinsa. Shi kuma sai ya ɗaga mata kai dan ya tabbatar mata da maganarsa.
“Yes Idan har baki xubar ba sai dai kije can gidan ku ki haife ɗan, ke kan ki ba samun lafiyarki bane ace kin haihu cikin kuɗi kuma a lokacin mahaifarki tana lafiya ƙalau, na baki lokaci ki yi tunani akai”
Juyawa yayi ya fice, zuciyarsa cikr da tabbacin abinda yayi be yi kuskure ba.
*ANTY AMARYA POV*
Sai da dare Abbah da Hajiya Barau da Anty suka samo ganin lefen da ka kawo, Abbah ya yaba sosai, Hajiya Barau ma ta yaba amman yabon baka yabon daya zame mata cilas dan sam bata jidaɗin ganin yadda aka zubawa ƴaƴan Anty wannan uban lefen ba. Hindatu kala 54 Maryam kuma 79 cikin su kuma babu shege balle ɗan iska.
“Allah yasa alheri ya nuna mana lokacin, amman na ɗauka Namra zata xo tarbon lefen nan”
Anty Amarya taji babu daɗi, sai dai bata nuna ba, sai kawai ta ce.
“Ta so tazo mijin nr ya hana ta yace wai ta bari dai nan gaba sai su zo tare”
“Allah ya taimaka, lefe yayi mashallah”
Haka ta taso ta fito daga falon da ƙahon baƙinciki daya tsaya mata a zuciya. Part ɗinta ta shigo tana shiga ta shige ɗakinta ta zauna, babu abunda take tunanu sai duniyar da Abbah xai kashe masu gurin auren, kamar ita ba a ma ƴaƴanta.
Ummi ce ta shigo ƴar gurin Hajiya Barau mai sunan mahaifiyarta hakan yasa take kiranta da Ummi.
Duk cikin ƴaƴanta mata ita kaɗaice tazo tarbon lefen. Kusa da mahaifiyarta ta xauna tana kallon yanayinta kallonta Hajiya Barau tayi
“Kin gani ke kina son kashe na ki aure su kuma suna yi, idan so kike ki dawo gida mu zauna sai ki dawo”
“Haba Hajiya wallahi ni na gaji da irin wannan rayuwar da yake nuna min, kwata kwata bana gabansa, baya da aiki sai neman mata, tun abu na ɓoye har magana ta fara fita, ko fita nayi sai ya kawo wata a gida”
“Ina ruwanki da neman matansa? Ai kedai yana baki ci da sha ko yana baki na kashewa ina ruwan ki da lamarin, yanzu neman maza ma ake balle mata, abun ai yyi ne wanda be yi ba to bashi da kuɗin yin ne, ko ni ya nema kya ce ki kashe auren ki ki dawo gida balle kuma wata can daban”
Miƙewa tayi tsaye cikin ɓacin rai ta fice, dan tasan duk yadda take son mahaifiyarta ta fahimci matsalarta ba fahimta zata yi ba.
Ƙwafa Hajiya Barau tayi taja wayarta tana soma labartawa abokin gulmarta rashin zuwan Namra tarbar lefen ƙannenta.
Duk hirar da suke be nuna mata jindaɗin hakan ko rashin jindaɗin saboda yana gaban Yasmin ne, yawancin maganar bata wuce uhn a'a ato, Har suka gama wayar.
Ƙaton cikin Yasmin ya kalla yana murmushi.
“Allah yasa karki haifa minɓɗa mai kahuwa”
Ta tsuke baki
“Mai hali dai baya fasa halinsa, ni wallahi haushi kake bani sosai”
“Daman duk kina da ciki ai baki ƙaunata kamar na kashe miki wani”
Ya faɗa yana jawo wayarsa da tayi ringing, number abokinsa Tahir ya gani.
“Innalillahi wa'inna ilaihi raji'un ”
Shine abunda ya furta bayan ƴan daƙiƙu da karɓa wayar.
“Okay gani nan zuwa”
Ya tashi tsaye da sauri, har Yasmin ta kalleshi
“Lafiya?”
“Wai Najeeb yayi hatsari, nan cikin gari”
“Subhanallahi, ina fatar be ji ciwo ba”
“Ban sani ba, sai naje tukunan”
Da sauri ya ɗauke Adnan da ke saman jikinsa ya ɗauki wayoyinsa ya zuba aljihu tare da keys ya fice hankali tashe.
*HILAL POV*
Lallaɓata yayi har sai da tayi shiru sannan yaja ta zuwa saman gadonsa ya zaunar da ita ya kama hannayenta ya riƙa.
“Na yarda ba ki aikata ba shikenan?”
“Har zuciyarka ka yarda da ni?”
“Na yarda da ke?”
“Zaka daina fushi da ni?”
“Zan daina”
“Zaka dawo da su Ezzah”
“Idan Hajiya ta yarda”
Haka yake ta amsa mata kamar tambayar babba da yaro, sai ya hau saman gadon yaja ta ƙirjinsa ya rumgume.
“I Love You”
Ƙamkamshi tayi
“I love you too”
Sun daɗe a haka kamin ya sake ta ya shiga yayi wanka ya shirya cikin wasu tufafin sai ta ɗauko masa abinci. Ba dan yana so ba ya zauna yayi ƴan lomomi kaɗan ya tashi ya nufi gidan Hajiyarsa.
Da shigarsa Ezzah da Ulfah da sauran yaran gidan suka rugo da gudu suka tarbeshi. Ulfah ce kawai ta tambayi Kalsoom Ezzah kan ko a jikinta. Bayan ya gama ganinsu ya miƙa musu chocolates ɗin ya shigo da shi sannan ya wuce gurin Hajiyarsa.
Tun daga yanayin yadda ta amsa masa sallamarsa yasan akwai abunda ya faru. Guri ya samu ya zauna yana kallon tv dake ɗakinta, kamin daga bisani ya gaishe ta. A maimakon ta amsa sai kawai ta hau shi da faɗa
“Yanzu fisabilliahi abunda kake ƙoƙarin yi kyautawa ne? Kace xaka kare ta idan kun je kutu bayan ga abunda tayi ma ɗan ka, irin waɗannan matan fa zama da du matsala ne dan kai ma xata iya maka haka”
Daga yanayin maganar ta ya gane Amina ce ta kawo mata zancen, dan ita kaɗai yasan yayi zancen a gabanta sai kuma Alh Bashir.
“Amman Amina munafukace wallahi, zuwa tayi ta faɗa miki ko?”
“Ai dole ta faɗa min mana tun da abun yayi mata zafi, ni kama rabu da wannan matar ka nemi wata ka aura”
“Gaskiya ba zan iya rabuwa da ita ba”
“To ko zaka auro wacce zata riƙa maka ƴaƴanka, dole ne ka ƙara aure ko kuma ka rabu da ita idan baka shirya zama da mata biyu ba”
“Haba Hajiya, kuskure ne nima a yanzu na gane ba ita ce ta aikata ba”
“To waya aikata? Ga abu ƙiri da muzu ka nemi takewa dan kana son ta, ah lallai ba banza ta barka ba, Ezzah ma tana ta faɗar irin abunda take musu a gidan, cin amana zalla”
Dariya abun ya bashi yau kuma Hajiya da kanta take irin wannan furucin.
“Babu maganin komai Hajiya, amman wannan matsalar nima ban san kan ta ba”
“To ni dai na faɗa maka ko ka ƙara aure ko ka rabu da ita, tashi ka bani guri”
Kansa ya dafe yana sauke ajiyar zuciya
“Hajiya ki fahimta...”
“Ba zan fahimta ba, ka tafiyarka kawai”
Yasan duk yadda zai yi ba zata fahimta sai kawai ya tashi ya fice da jimmar idan ta huce zai dawo ya fahimtar da ita.
*Jiya naje biki ban samu na yi typing ba, so wannan zai zama na jiya, na yau kuma sai dare zan kawo. Thank you 🖤*
[7/18, 8:12 PM] Khadeeja Candy♥: *60 - NOT EDITED ⚠️*
*RASHIDA POV.*
“Teema ya faɗa min abinda ya fi ƙarfin zuciyata da tunani, ya bani labarin yau da kuma gobe na, ƙoƙari raba ni yake da Ubangijina”
Ta faɗa cikin kuka, tana mai jin tsantsar ƙyama da kuma tsanar bokan a ranta, ta kuɗiri aniyar zata iya aikata komai akan duniyarta amman ba zata iya aikata abunda ya faɗa mata ta aikata ba.
Teema ta tsire baki, tana mamakin ƙawar ta'ta.
“Ai kin daɗe da rabuwa da raba hanya da Ubangijinki, tun da kika soma neman taimakon wani daga cikin bayinsa, Abunda zaki yi kawai ki aikata wannan in yaso daga baya sai ki nemi yafiyar”
“Ya ce min baƙin hudu yana bibiyata, kuma wannan baƙin duhun baƙar rana ce, what if ranar mutuwa na ne? Ba shine na farko daya faɗa min haka ba, Teema ina tsoro”
Kyalƙyalwa Teema tayi da dariya har da taɓawa tana kallon Rashida.
“Amman Wallahi kina da abun dariya, miye abun tsoro kuma? Ashe ke sabowar shiga ce wannan harka, ba lallai baƙar rana ta zama ranar mutuwa ba, yana nufin akwai abunda zai same ki marar daɗi wanda ke da kan ki zaki kira abun da baƙar rana”
Ta ɗan ji sassauci a zuciyarta, har ta samu damar haɗe yawun da ya tsaya mata a maƙoshi.
“Ni dai ina ganin haƙura zan yi, kar naje na sake mata kuma ya dawo kaina dan yace zan yi nasara amman akwai yiyuwar ya dawo kai na”
“Amman wallahi Rash kin ban mamaki, ke da na ke ganin, kamar zaki iya aikata komai akan Hilal, ashe son da kike masa na ƙarya ne, tun da har zaki iya bar wa wata shi, yanzu duk soyayyar da kuka yi ta tashi a banza kenan? Ƴaƴanki sun zama nata mijinki ya zama nata? Ko akwai wani wanda kike so bayan Hilal?”
“Babu shi, Hilal ne kawai, wallahi ina sonsa sosai”
“Kuma kin yarda ki barwa wata shi ko?”
“Na samu matsala akan jifar da nayi mata Teema, na jefeta ya faɗa kan ɗa na, kin ji ai yanzu yana faɗa min, yanzu haka Rafiq yana can kwance asibiti babu lafiya, ya damu matsalar ƙwaƙwalwa”
“Lallai wannan mata ita bata tsaya akan ta, irin wannan matar maganinta ki samu fitsari ki zuba mata a ruwa ya jiƙa ta sha, wallahi duk wani magani na tsari jikin data sha sai ya karye, amman kin ce tana shiga malamai ita ma?”
“Haka nake gani, saboda gaba ɗaya Hilal ya haukace ba shi da magana ta kowa sai na ta, baya kula ni a yanzu, kuma kin ga da dane ba zai iya sakina ba amman yanzu duba ki ga ya sake ni”
“To ina ganin ba tsari bane itama ta iya shige-shigen ne, sai aka bata aljana ta tsare ta, kin san wasu suna haka fa dan akwai su cimma burin su”
“Da gaske? Ballatana ta daɗe ba tayi aure ba zata iya haka”
“Dan haka ki kwantar da hankalin ki, ki share hawayen ki matuƙar ina raye sai kin koma cikin ƴaƴanki, yanzu kin ga mun fito cikin tashin hankali baki masa sallama ba, amman yanzu idan hankalinki ya kwanta natsuwarki ta dawo jikin ki, sai mu koma yayi mana aikin kawai”
“Amman ya ce sai nayi fashin salla fa?”
“To miye a ciki? Wasu
Showing 150001 words to 153000 words out of 280121 words
“Haleema kar na sake jin irin wannan kalamin a bakin ki, Aisha ke kuma ya isa tun da ba cewa aka yi za a aura masa ita ba, ku Shafa min lafiya dan Allah ku tashi ku bani guri”
Duk miƙewa suka yi suka fita, ban da Amal data laƙe jikin Ummi ita ala dole sai an dafa maya makaroni.
“Ai kema kin iya dafawa, Amal har mota kike tuƙi fa amman ki zo kina min abu kamar jaririya, idan yanzu aka miki aure ai sai zama dan kin girma, ba kece auta ba autana tana nan zuwa”
Ummi ta faɗa da raha a fuskarta. Amal ɗin tasa dariya dan tasan abu ne mai wahala a yanzu.
“Za a ce tsohuwa ta haihu”
Ummi ta tiƙi bayanta tana dariya
“Yes Tsohuwa maman Amal, tashi ki cire uniform”
Tashi ta yi ta fice tana dariya.
*NAMRA POV*
Kamar yadda suka saba yi duk mai ciwo, bayan ta faɗa masu matsalarta sai suka bata gwajin jini da fitsari, suka sa kuma taje ta yanki sabon kati dan duba wacan matsalar nata na robar dake hannunta dan a bayanin da ta yi ma likita ya fahimci ciki ne a jikinta. Sai dai bashi da tabbacin haka tun da ta faɗa masa tana saye da roba, duk da yasan ana samun irin wannan matsalar a wani lokaci.
Awan fitsari kawai ta samu yi, a take, na jini cewa suka yi sai da yamma ta zo ta karɓa, su kuma waɗanda zasu dubata a ɓangaren robar sun tashi aiki.
Tun da karɓo results ɗin ta kasa ta buɗe dan bata son ta ga abinda yake ciki, tasan idan har ciki ne tana cikin matsala dan bata gama warkewar ciwon mahaifarta, kuma ga roba jikinta ace tayi ciki tasan duka ƙarin matsalar ne. Ko da ta koma gurin likitan yana shirin tashi, har ya haɗa kayansa, a tsai-tsaye ya duba takardar tana fuskarsa da mamaki ya ce
“Kina ɗauke da juna biyu”
Ras ras ras gabanta ya faɗi, sai ta faɗi saman kujera tana hawaye. Da sauri likitan ya aje kayan hannunsa.
“Hey wannan ba wata matsala bace ana samun irin haka daman, amman abunda yafi zan rubuta miki hoto sai kije ayi hoto a bincika lafiyar cikin, kuma ki tabbar kin je an cire miki wannan robar”
“Doc mahaifa tana da matsala shiyasa aka samun robar”
“Ba lallai ne har yanzu matsalar ki tana nan ba, shiyasa nake son ki yi hoton”
Ya ɗauki wata takardar yayi rubutu ya miƙa mata.
“Kije ayi miki hoto, zuwa gobe sai ki kawo na duba ki, ko kuma ki dawo wani likitan ya duba ki, ki kwantar da hankalin ki ba wani abu nima mai ɗaki na ta taɓa haka”
Jakarsa ya ɗauka ya rataya ya face. Sannan ita ta tashi ta fito tana hawaye, maimakon taje gurin hoton sai kawai ta yanke shawarar komawa gida dan ita har yanxu jikinta na bata ba ƙalau take ba, balle bata da kuɗin da zasu isheta hoto tun katin ganin likita na asibitin ma kusan ɗari bakwai ne.
Tun cikin Napep take ta kiran Asim amman ya ƙi ya ɗaga saboda yana gaban Hajiya, wacce ta zame masa kamar uwa a yanzu, yadda yake jinta ko Mama data haife sa baya jinta haka nan.
Hakan yasa ta yanke shawarar tura masa saƙon karta kwana.
Ƙin ɗaga wayar yayi dan akwai yana gaban Hajiya, ita ta jidaɗin hakan da yayi ko ba komai tasan ya girmamata, gashi tun da yazo gidan be taɓa fita da sunan yaje gida gurin matarsa ba.
Sai da ta gama lissafa masa abunda zai siyo mata sannan ta bashi kuɗin tana murmushi ciki ladabi ya karɓa ya tashi ya fice.
Sannan Hajiya tayi murmushi ta maida dubanta ga ƙawarta, Hajiya Ubaida.
“Gaskiya yaron nan yana da ladabi ina kika damo shi?”
“Uhmm tsuntsune daga sama gasasshe Allah ya bani daga gyaran gate”
A nan ta kwashe labarin komai ta bawa Aminiyarta yadda suka haɗu da sharaɗin data gundaya masa da kuma zaman gidan da yake, da kuma ƙudirinta a kansa.
Hannu Hajiya Ubaida ta bata suka taɓa
“Shegiya Sadiya duk abunda kika sawa gaba sai kin ga bayansa, hala yarinyar mai kyau ce?”
“Tana da kyau wallahi ta haɗu ba ƙarya, sannan kin ga na samu dama biyu, daman Alhaji Usaini ya dame ni na samo masa sabin shiga, wai duk wanda nake kai masa basa da ladabi kuma an taɓa amfani da su, kwana biyu sai su fara masa tsageranci”
“Ai kin san manyan mutanen nan sun fi son tsaida mutum ɗaya, wanda zasu riƙa amfani da shi kullum”
“Eh shi ma haka yace, wai idan yana bin irin guys ɗin nan za'a iya gane shi, yafi son tsaida mutum ɗaya, kuma kin ga irin wannan zai fi jindaɗinsa dan ga alama zai yi ladabi, sannan garin su ɗaya, idan ta kama ya koma can ma, ni sai ya barmin matar a nan, dan ba zan taɓa nuna masa ina don matarsa ba, shi wata rana zan iya buƙatarsa”
Hajiya Ubaida ta ƙalƙyale da dariya.
“Ke Allah dai ya yafe mana, ya shirya mu”
“Amin kedai ai ina son tuba amman sai nan gaba, dan bana son Zeenat ta san halin da nake ciki”
“Gaskiya kam, ai ƙara ai daina da wuri kar azo aji kunya”
Hajiya Sadiya tayi fuskar tausayi kamar mai tsoron Allah da gaske, tana kallon Hajiya Ubaida wacce sana'arsu ta zama ɗaya.
*ASIM*
Be wuce kasuwar ba, sai da ya bi ta gida dan jin abinda Namra zata faɗa masa, badan saƙonta da yaga ni babu ma abunda zai sashi bi ta gidan. Kamar baƙin haɗari haka ya doshi gidan bakinsa ƙumshe da maganganu kala-kala, dan gani yake a yanzu shi ma ya kai matsayin da zai iya faɗawa magana son ransa, balle Namra da yake gani kamar banza.
A ɗaki ya tararar da ita kwance sai hawaye take. Daker ta ɗago ta kalleshi, duk da tana cikin yanayin damuwa hakan be hanata, kallon irin shigar dake jikinsa ba. Takalmin dake ƙafarsa kaɗai zasu iya kaiwa dubu 10+ balle wando da T-shirt.
Be ji zai iya zama a ɗakinba, sai kawai ya tsaya jikin ƙofa yana mata wani kallo, azuciyaraa yake hantararta ganin yadda ta ƙara lalacewa.
“Ya aka kika samu ciki?”
Wani kallo tayi masa zafin furucinsa yana zuciyarta.
“Kamar ya? Ina da wani mijin ne bayan kai”
“Ni ya za'ayi na sani, yanzu ai ba a shedun mutum”
“Shigowarka Asim irin wannan furucin zaka min? Tun da kasa ƙafa ka bar gidan nan babu ruwanka da ni kamar ba matar ka”
“Ya kike so nayi Namra aikin zan bari na zo na tisaki gaba nayi ta kallo ko me? Yanzu ma a hanya nake saƙon da kika min ne yasa na biyo”
Kawarda kai tayi ta haɗe hawayen da take da tabbacin idan har suka fara zubar mata bata san lokacin tsayawarsu ba.
“Daga Asibiti na ke likita ya ce ina da ciki, kuma akwai roba a jikina”
“To ya aka yi haka?”
“Nima ban sani ba, amman yace min daman akan samu hakan wani lokaci, yace naje nayi hoto aga lafiyar cikin, Asim ina tsoron ko mahaifata bata gama warkewa ba”
“To a zubar da cikin mana”
Miƙewa tayi tsaye tana kallonsa.
“A zubar fa kasa kasan abunda kake faɗa?”
“Na sani mana, Namra wannan ba lokacin samun yara bane, muna planning na neman kuɗi kuma yara zasu shigo, ki duba irin wahalar da muka sha a baya yanxu kuma hanya ta fara buɗe mana sai kuma haihuwa ta zo, gaskiya ni ban shirya ba”
“Ni kuma na shriya Asim, ni nake da matsalar da nake da a mahaifata kuma im ready to give birth saboda nima haihuwata aka yi, Allah ba xai bani kyauta na jefar ba”
Cikin wata murya tayi furucin muryar da bata san tana da ita ba sai a yau. Shi kuma ya gyara tsayusarsa yana mamakin ta
“Wallahi Namra sai yanxu na gane lallai ke ba masoyiyata bace. Kin manta lokacin da nake cewa kije ki cire robar nan amman ki ƙi, ko wannan zubar da ciki da kika sha ban san lokacin da kika sha ba, wata ƙila kin yi zubar da cikin ne shiyasa har mahaifarki ta samu matsala, sai yanxu da kika ga zan yi kuɗi ko shine zaki nuna min baƙin hali ki ɓullo min ta haihuwa, to ni ban shirya haihuwa yanzu ba dan haka dole a zubar da cikin nan”
“Wallahi tallahi ba zan zubar da wannan cikin ba, ko da kuwa wannan cikin yana nufi ya rayu, ni na mutu”
“Haka kika ce?”
“Haka na ce kuma haka xaka gani”
“To sai dai ki zaɓa ko ni ko cikin nan...!”
Wani kallo tayi masa na ƙara tantance zancen daya fito daga bakinsa. Shi kuma sai ya ɗaga mata kai dan ya tabbatar mata da maganarsa.
“Yes Idan har baki xubar ba sai dai kije can gidan ku ki haife ɗan, ke kan ki ba samun lafiyarki bane ace kin haihu cikin kuɗi kuma a lokacin mahaifarki tana lafiya ƙalau, na baki lokaci ki yi tunani akai”
Juyawa yayi ya fice, zuciyarsa cikr da tabbacin abinda yayi be yi kuskure ba.
*ANTY AMARYA POV*
Sai da dare Abbah da Hajiya Barau da Anty suka samo ganin lefen da ka kawo, Abbah ya yaba sosai, Hajiya Barau ma ta yaba amman yabon baka yabon daya zame mata cilas dan sam bata jidaɗin ganin yadda aka zubawa ƴaƴan Anty wannan uban lefen ba. Hindatu kala 54 Maryam kuma 79 cikin su kuma babu shege balle ɗan iska.
“Allah yasa alheri ya nuna mana lokacin, amman na ɗauka Namra zata xo tarbon lefen nan”
Anty Amarya taji babu daɗi, sai dai bata nuna ba, sai kawai ta ce.
“Ta so tazo mijin nr ya hana ta yace wai ta bari dai nan gaba sai su zo tare”
“Allah ya taimaka, lefe yayi mashallah”
Haka ta taso ta fito daga falon da ƙahon baƙinciki daya tsaya mata a zuciya. Part ɗinta ta shigo tana shiga ta shige ɗakinta ta zauna, babu abunda take tunanu sai duniyar da Abbah xai kashe masu gurin auren, kamar ita ba a ma ƴaƴanta.
Ummi ce ta shigo ƴar gurin Hajiya Barau mai sunan mahaifiyarta hakan yasa take kiranta da Ummi.
Duk cikin ƴaƴanta mata ita kaɗaice tazo tarbon lefen. Kusa da mahaifiyarta ta xauna tana kallon yanayinta kallonta Hajiya Barau tayi
“Kin gani ke kina son kashe na ki aure su kuma suna yi, idan so kike ki dawo gida mu zauna sai ki dawo”
“Haba Hajiya wallahi ni na gaji da irin wannan rayuwar da yake nuna min, kwata kwata bana gabansa, baya da aiki sai neman mata, tun abu na ɓoye har magana ta fara fita, ko fita nayi sai ya kawo wata a gida”
“Ina ruwanki da neman matansa? Ai kedai yana baki ci da sha ko yana baki na kashewa ina ruwan ki da lamarin, yanzu neman maza ma ake balle mata, abun ai yyi ne wanda be yi ba to bashi da kuɗin yin ne, ko ni ya nema kya ce ki kashe auren ki ki dawo gida balle kuma wata can daban”
Miƙewa tayi tsaye cikin ɓacin rai ta fice, dan tasan duk yadda take son mahaifiyarta ta fahimci matsalarta ba fahimta zata yi ba.
Ƙwafa Hajiya Barau tayi taja wayarta tana soma labartawa abokin gulmarta rashin zuwan Namra tarbar lefen ƙannenta.
Duk hirar da suke be nuna mata jindaɗin hakan ko rashin jindaɗin saboda yana gaban Yasmin ne, yawancin maganar bata wuce uhn a'a ato, Har suka gama wayar.
Ƙaton cikin Yasmin ya kalla yana murmushi.
“Allah yasa karki haifa minɓɗa mai kahuwa”
Ta tsuke baki
“Mai hali dai baya fasa halinsa, ni wallahi haushi kake bani sosai”
“Daman duk kina da ciki ai baki ƙaunata kamar na kashe miki wani”
Ya faɗa yana jawo wayarsa da tayi ringing, number abokinsa Tahir ya gani.
“Innalillahi wa'inna ilaihi raji'un ”
Shine abunda ya furta bayan ƴan daƙiƙu da karɓa wayar.
“Okay gani nan zuwa”
Ya tashi tsaye da sauri, har Yasmin ta kalleshi
“Lafiya?”
“Wai Najeeb yayi hatsari, nan cikin gari”
“Subhanallahi, ina fatar be ji ciwo ba”
“Ban sani ba, sai naje tukunan”
Da sauri ya ɗauke Adnan da ke saman jikinsa ya ɗauki wayoyinsa ya zuba aljihu tare da keys ya fice hankali tashe.
*HILAL POV*
Lallaɓata yayi har sai da tayi shiru sannan yaja ta zuwa saman gadonsa ya zaunar da ita ya kama hannayenta ya riƙa.
“Na yarda ba ki aikata ba shikenan?”
“Har zuciyarka ka yarda da ni?”
“Na yarda da ke?”
“Zaka daina fushi da ni?”
“Zan daina”
“Zaka dawo da su Ezzah”
“Idan Hajiya ta yarda”
Haka yake ta amsa mata kamar tambayar babba da yaro, sai ya hau saman gadon yaja ta ƙirjinsa ya rumgume.
“I Love You”
Ƙamkamshi tayi
“I love you too”
Sun daɗe a haka kamin ya sake ta ya shiga yayi wanka ya shirya cikin wasu tufafin sai ta ɗauko masa abinci. Ba dan yana so ba ya zauna yayi ƴan lomomi kaɗan ya tashi ya nufi gidan Hajiyarsa.
Da shigarsa Ezzah da Ulfah da sauran yaran gidan suka rugo da gudu suka tarbeshi. Ulfah ce kawai ta tambayi Kalsoom Ezzah kan ko a jikinta. Bayan ya gama ganinsu ya miƙa musu chocolates ɗin ya shigo da shi sannan ya wuce gurin Hajiyarsa.
Tun daga yanayin yadda ta amsa masa sallamarsa yasan akwai abunda ya faru. Guri ya samu ya zauna yana kallon tv dake ɗakinta, kamin daga bisani ya gaishe ta. A maimakon ta amsa sai kawai ta hau shi da faɗa
“Yanzu fisabilliahi abunda kake ƙoƙarin yi kyautawa ne? Kace xaka kare ta idan kun je kutu bayan ga abunda tayi ma ɗan ka, irin waɗannan matan fa zama da du matsala ne dan kai ma xata iya maka haka”
Daga yanayin maganar ta ya gane Amina ce ta kawo mata zancen, dan ita kaɗai yasan yayi zancen a gabanta sai kuma Alh Bashir.
“Amman Amina munafukace wallahi, zuwa tayi ta faɗa miki ko?”
“Ai dole ta faɗa min mana tun da abun yayi mata zafi, ni kama rabu da wannan matar ka nemi wata ka aura”
“Gaskiya ba zan iya rabuwa da ita ba”
“To ko zaka auro wacce zata riƙa maka ƴaƴanka, dole ne ka ƙara aure ko kuma ka rabu da ita idan baka shirya zama da mata biyu ba”
“Haba Hajiya, kuskure ne nima a yanzu na gane ba ita ce ta aikata ba”
“To waya aikata? Ga abu ƙiri da muzu ka nemi takewa dan kana son ta, ah lallai ba banza ta barka ba, Ezzah ma tana ta faɗar irin abunda take musu a gidan, cin amana zalla”
Dariya abun ya bashi yau kuma Hajiya da kanta take irin wannan furucin.
“Babu maganin komai Hajiya, amman wannan matsalar nima ban san kan ta ba”
“To ni dai na faɗa maka ko ka ƙara aure ko ka rabu da ita, tashi ka bani guri”
Kansa ya dafe yana sauke ajiyar zuciya
“Hajiya ki fahimta...”
“Ba zan fahimta ba, ka tafiyarka kawai”
Yasan duk yadda zai yi ba zata fahimta sai kawai ya tashi ya fice da jimmar idan ta huce zai dawo ya fahimtar da ita.
-----------------------------------------------------------------
*Jiya naje biki ban samu na yi typing ba, so wannan zai zama na jiya, na yau kuma sai dare zan kawo. Thank you 🖤*
[7/18, 8:12 PM] Khadeeja Candy♥: *60 - NOT EDITED ⚠️*
*RASHIDA POV.*
“Teema ya faɗa min abinda ya fi ƙarfin zuciyata da tunani, ya bani labarin yau da kuma gobe na, ƙoƙari raba ni yake da Ubangijina”
Ta faɗa cikin kuka, tana mai jin tsantsar ƙyama da kuma tsanar bokan a ranta, ta kuɗiri aniyar zata iya aikata komai akan duniyarta amman ba zata iya aikata abunda ya faɗa mata ta aikata ba.
Teema ta tsire baki, tana mamakin ƙawar ta'ta.
“Ai kin daɗe da rabuwa da raba hanya da Ubangijinki, tun da kika soma neman taimakon wani daga cikin bayinsa, Abunda zaki yi kawai ki aikata wannan in yaso daga baya sai ki nemi yafiyar”
“Ya ce min baƙin hudu yana bibiyata, kuma wannan baƙin duhun baƙar rana ce, what if ranar mutuwa na ne? Ba shine na farko daya faɗa min haka ba, Teema ina tsoro”
Kyalƙyalwa Teema tayi da dariya har da taɓawa tana kallon Rashida.
“Amman Wallahi kina da abun dariya, miye abun tsoro kuma? Ashe ke sabowar shiga ce wannan harka, ba lallai baƙar rana ta zama ranar mutuwa ba, yana nufin akwai abunda zai same ki marar daɗi wanda ke da kan ki zaki kira abun da baƙar rana”
Ta ɗan ji sassauci a zuciyarta, har ta samu damar haɗe yawun da ya tsaya mata a maƙoshi.
“Ni dai ina ganin haƙura zan yi, kar naje na sake mata kuma ya dawo kaina dan yace zan yi nasara amman akwai yiyuwar ya dawo kai na”
“Amman wallahi Rash kin ban mamaki, ke da na ke ganin, kamar zaki iya aikata komai akan Hilal, ashe son da kike masa na ƙarya ne, tun da har zaki iya bar wa wata shi, yanzu duk soyayyar da kuka yi ta tashi a banza kenan? Ƴaƴanki sun zama nata mijinki ya zama nata? Ko akwai wani wanda kike so bayan Hilal?”
“Babu shi, Hilal ne kawai, wallahi ina sonsa sosai”
“Kuma kin yarda ki barwa wata shi ko?”
“Na samu matsala akan jifar da nayi mata Teema, na jefeta ya faɗa kan ɗa na, kin ji ai yanzu yana faɗa min, yanzu haka Rafiq yana can kwance asibiti babu lafiya, ya damu matsalar ƙwaƙwalwa”
“Lallai wannan mata ita bata tsaya akan ta, irin wannan matar maganinta ki samu fitsari ki zuba mata a ruwa ya jiƙa ta sha, wallahi duk wani magani na tsari jikin data sha sai ya karye, amman kin ce tana shiga malamai ita ma?”
“Haka nake gani, saboda gaba ɗaya Hilal ya haukace ba shi da magana ta kowa sai na ta, baya kula ni a yanzu, kuma kin ga da dane ba zai iya sakina ba amman yanzu duba ki ga ya sake ni”
“To ina ganin ba tsari bane itama ta iya shige-shigen ne, sai aka bata aljana ta tsare ta, kin san wasu suna haka fa dan akwai su cimma burin su”
“Da gaske? Ballatana ta daɗe ba tayi aure ba zata iya haka”
“Dan haka ki kwantar da hankalin ki, ki share hawayen ki matuƙar ina raye sai kin koma cikin ƴaƴanki, yanzu kin ga mun fito cikin tashin hankali baki masa sallama ba, amman yanzu idan hankalinki ya kwanta natsuwarki ta dawo jikin ki, sai mu koma yayi mana aikin kawai”
“Amman ya ce sai nayi fashin salla fa?”
“To miye a ciki? Wasu
Book Chapters
Chapter 1Chapter 2Chapter 3Chapter 4Chapter 5Chapter 6Chapter 7Chapter 8Chapter 9Chapter 10Chapter 11Chapter 12Chapter 13Chapter 14Chapter 15Chapter 16Chapter 17Chapter 18Chapter 19Chapter 20Chapter 21Chapter 22Chapter 23Chapter 24Chapter 25Chapter 26Chapter 27Chapter 28Chapter 29Chapter 30Chapter 31Chapter 32Chapter 33Chapter 34Chapter 35Chapter 36Chapter 37Chapter 38Chapter 39Chapter 40Chapter 41Chapter 42Chapter 43Chapter 44Chapter 45Chapter 46Chapter 47Chapter 48Chapter 49Chapter 50Chapter 51 Chapter 52Chapter 53Chapter 54Chapter 55Chapter 56Chapter 57Chapter 58Chapter 59Chapter 60Chapter 61Chapter 62Chapter 63Chapter 64Chapter 65Chapter 66Chapter 67Chapter 68Chapter 69Chapter 70Chapter 71Chapter 72Chapter 73Chapter 74Chapter 75Chapter 76Chapter 77Chapter 78Chapter 79Chapter 80Chapter 81Chapter 82Chapter 83Chapter 84Chapter 85Chapter 86Chapter 87Chapter 88Chapter 89Chapter 90Chapter 91Chapter 92Chapter 93Chapter 94