ƙasa tana wani irin kuka kamar ranta zai fita, duk yadda taso ta tausa muryarta tayi ma Abbah magana sai ta kasa saboda kuka.
Har Abbah ya gaji da sauraren kukanta, ya kira Maryam ta fita da ita. Ko da aka koma da ita part ɗin Anty Amarya numfashinta har rawa yake. Nan ma barinta akayi daga ita sai Anty Amarya. Amman Anty Amarya ta kasa mata magana saboda kukan da take na rabuwa da ƴarta.
Har lokacin da aka bata ya ci ya cinye, Anty Amarya bata iya cewa Namra komai ba, daga ita har Namra suke. Sai da su Mama Zainab da Hajiya Barau suka shigo zasu fita da Namra sannan Anty Amarya ta iya furta
“Na yafe miki Namra Allah yayi miki albarka”
Juyowa Namra tayi ta rumgume Anty Amarya iya ƙarfinta. Har Hajiya Barau da Mama Zainab sai da idonsu ya cika da ƙwallah. Daker suka ɓanɓareta daga jikin Anty Amarya saboda yadda ta rumgumeta.
Yadda Namra take kuka yasa duk wanda yake falon sai da yayi hawaye. Ƙanen Asim da wasu ƴan'uwansa suna tsaye gefe suna kallo.
Muta ɗaya suka shiga da Maryam da Mama Zainab da Hajiya Barau. Ɗayar motar kuma ƴan'uwan Asim suka shiga daman ciki suka zo. Biyun wasu ƴan'uwan Abbah suka shiga, sai ta su Maryam da Aisha da Hindatu da wasu Cousins ɗin su. Ƙarfe uku da ƴan mintuna suka kama hanyar Katsina.
KALSOOM POV.
Yanayin yadda Doc. Hilal ya shiga yau, ya bata tsoro, sai dai bata damu sosai ba, dan tasan haka rayuwa take yau daɗi gobe ba daɗi. Ballantana ma yau ba ɗakinta bane wata ƙila ma uwargidan tasa ce ta ɓata masa rai.
Sai dai hakan be sa tayi ƙasa a gwuiwa ba, wajen zuwa tayi masa kyakkyawar tarba. Sai ta aje Rafiq a falo ta tashi ta nufi ɗakinsa, tana faɗaɗa murmushinta.
Kwance ta kararda shi saman gado ya lumshe ido yana, hannunsa ɗaya dafe da kansa.
Kusa da shi ta zauna, ta kai hannunta ta shafi gefen fuskarsa.
“Ya Omri lafiya kake kuwa?”
Shiru be amsa ta kamar ba zai yi murmushi ba, can kuma ya buɗe ido ya kalleta, sam baya jindaɗin ransa, amman a haka yayi ƙarfin hali ya ƙirƙiro murmushi ya kai hannu ya shafa bayanta.
“Matar Doc. Yau jina nake sai a hankali Wallahi?”
Duk sai taji babu daɗi, daman tasan ba banza tun da taga ya shigo babu ko sallama, kuma be kulata ba ya shigo ɗakinsa.
“Wani abun ne yake maka ciwo?”
“No”
Ya sake lumshe ido.
“Kawai bana jindaɗin rai nane, shiyasa na baro office ɗin”
“Ko wani ne ya ɓata maka rai?”
Idonshi a lumshe ya girgiza mata kai.
“No haka kawai Wallahi”
“Toh Allah ya sauwaƙe ammn idan irin hakan ya same ka, ka riƙa karanta Innalillahi wa'inna ilaihi raji'un, zaka ji sassauci”
Tashi yayi zaune, ya sakar mata ido kamar yau ya fara ganinta, sai kuma yaja ta jikinsa ya rumgume gam-gam, yana maida numfashi.
Ana kiran Sallah magariba suka isa Katsina. Kai tsaye suka wuce unguwar Nasarawa. Sun yi mamakin ganin gidan da aka sauke su da sunan gidan da Namra zata zauna.
Ba dan komai ba sai dan sanin Asim ɗin ba shida halin da zai iya kama hayar irin wannan gidan balle kuma har ya siye. Daman tun lokacin da aka zo jere an labartawa Hajiya Barau irin tsarin gidan. Gida ne plate mai kyau da shike-shike, ga farin fentin daya ƙawata gidan. A can ciki an ware dinning area da kitchen a gefe sai two bedrooms da babban falo, ga manyan kujerun da Abbah yasa aka zuba mata kamar ƴar wani shugaban ƙasa, duk bedrooms ɗin an saka mata furniture masu kyau da tsada.
A ƙaramin ɗaki ta tare ita da ƙannenta, su Hajiya kuma suka fito falo sukayi sallah, bayan sun gama direba ya kawo musu takeaway data aika a siyo musu, sai da suka ci abinci suka ƙoshi sannan Hajiya Barau ta shiga ɗakin da Namra take tana mata sallama, wai zata je gidan wata ƴar'uwarta ita da sauran waɗanda suka zo tare, su Maryam kuma sai idan Ango ya shigo sannan za su je.
Ko da Hajiya Barau ta bar gidan ana kiran sallah I'sha'i. Sai a lokacin Namra ta tashi ta shirya cikin wasu tufafin duk da kasancewar fuskarta a kumbure, ta koma babban ɗakin. Tara da rabi ango ya shigo tare da abokansa, ba a wani yi siyen baki ba, bayan addu'ah da fatan alheri da suka musu. Maryam dai sai ta watsawa abokan nasa wani mugun kallo take, tana Allah-Allah wani yace yana son ta cikin su tayi masa wankin babban bargo.
Tare suka fita da abokan angon, ɗayan yana ƙoƙarin magana da Hindatu dan itace mai ɗan dama a cikin su, sai wata cousin ɗin su Sameera. Lokacin da Namra taji ɗakin yayi tsit sai sabon kuka ya dawo mata, sai dai wannan karon hawaye ne kawai ba kamar na ɗazu ba.
Bayan ya rufe ƙofar gidan ya shigo ya rufe ƙofar falo, sannan ya nufi ɗakin da take da Sallama, bata iya amsa masa ba saboda kukan daya cika zuciyarta, sai shaƙar majina take tana haɗeye yawu da jimmar dannen kuka daya kasa ɓoyuwa.
Kusa da ita ya zauna, ya yaye mayafinta fuskarsa ɗauke da murmushi.
“Namra kukan me kike kuma? Bayan Allah ya cika mana burin mu”
Ɗagowa tayi ta kalle shi, kamar tace wani abu sai hawaye suka silala daga idonta zuwa kumatun ta.
Shi kansa baya buƙatar da faɗa masa dalilinta na kuka tun da yasan iyayenta basa son sa, gashi ya rabo ta da garin su. Shi kan ta ɓangarensa yau take sallah, tun da ya cika burinsa na aurenta ya fita kunya, ga uban dukiyar da aka zuba masa, ga kuma wanda yake jira a matsayin gara a kawo masa.
Jin kawai ta yi ya rumgume ta yana rarrashinta.
“Na san ban kyauta miki ba, dana nesanta ki da iyayenki, amman ni a nawa tunanin hakan shine zai fi mana, Namra a can abubuwa da dama zasu iya faruwa idan muna tare da iyayenki, amman a nan ba komai zasu ji ba, kuma a nan zamu tabbata ba zaman na ɗan wani lokaci ne kawai idan muka ga abunda Allah yayi sai mu koma can, kiyi haƙuri kinji?”
A yanayin da take bata iya magana, sai kawai ta ɗaga masa kai tana sauke ajiyar zuciya, tasa hannayenta ta rumgumeshi.
Har kusan shaɗaya dare suna zaune a gurin, daker ya lallaɓata ta tashi suka yi sallah nafila, kazar ma shi kaɗai ya ci ita kan lemu kawai ta sha ta hau gado ta kwanta. Washe gari guraren takwas na safe ya fita ya siyo musu kayan haɗa tea, ya shiga kitchen ya dafa ruwan zafi a electric, sannan ya dawo ɗakin ya haɗa ya zuba mata nata ya zuba nasa. Nan ma tea kawai ta sha bata ci birede ba, tsakanin jiya zuwa yau ta rame sosai kamar ba ita ba.
Shi kuma be yi matsa mata akan sai ta ci ba, tun da dai ita ba yarinya bace taya zai yi forced ɗinta akan cin abinci, shi duk ma ta cika sa dan yayi hating kuka for no reason, ita kanta ta san babu abunda ya tsana kamar kuka. Daman zuciyarsa ta faɗa masa, dan a rufa mata asiri ne aka yarda aka aura nasa ita, dan yasan babu dalilin da zai sa Abbah ya yarda ya aureta har ya baro garin da ita ya kuma hanata karatunta haka kawai ba tare da wani abu ba.
Sai dai hakan be dame shi, tun da ko ba komai ya taka first step of success, tun da ya auri ƴar masu hannu da shuni, kuma zama da kutuwar uwa dole, a dole dai Abbah ya kyautata masa tun da ya zama surikinsa.
Tashi yayi ya kwashe kofunan ya kai kitchen, sannan ya dawo kusa da ita ya zauna. Sai ya kai hannu ya shafa bayanta, dan tana daga kwance ne.
“Namra ko kina buƙatar wani abun ne? Naga baki ci komai ba”
Tashi tayi zaune hawaye cike a idonta, ta riƙa hannunsa tasa cikin nata, ta kalli ƙwayar idonsa tace
“Asim ka min alƙawarin ba zaka ci amana ta ba, ka min alƙawarin ba zaka taɓa rabuwa da ni ba, ka min alƙawarin ba zaka wulaƙanta ni ba, ka min alƙawarin zaka zauna da ni a duk halin da muka samu kan mu”
Gabansa ya faɗi sosai, a take ya ɗauke idonsa ɗ
Daga kallon da take nasa, yaja jikinsa ya rumgume.
“Taya kika wannan maganar kamar baki san waye Asim ba? Namra bakin ki ya daina furta irin waɗannan kalaman Asim ne naki har abada”
Sallamar su Hajiya Barau da Maryam ne, yasa shu saurin sakinta ya tashi ya fita yana amsa musu, a falo suka yi karo, sai ya kai har ƙasa yana gaida Hajiya Barau, ba laifi Maryam ma ta ɗan sakar masa fuska sun gaisa kamar daman can shiri suke.
Ko da suka shiga ɗakin Namra na gyara fuskarta da hoda, sai ta juyo ta kalli Maryam da murmushi a fuskarta.
“Hajiya Maryam an samu isowa”
“Toh ba dole ba, Hajiya ta sha kai muzo mu kawo miki abinci muyi sallama dake da wuri zamu koma”
Ta faɗa tana dire kular abinci a gaban Namra. Saman gado Namra ta dawo ta zauna tana ɗan ɓata fuska.
“Yanzu tafiya za kuyi ku bar ni?”
“Ahaf to ba aure kika zo yi ba”
Cewar Sameera tana mata kallon zolaya. Zata ƙara cewa wani abu Hajiya Barau ta shigo bakinta ƙumshe da sallama. Duk haɗa baki sukayi gurin amsa mata, Namra ta saukar da kai tana gaishe ta.
“Lafiya ƙalau, Amarya ya tashin ku?”
“Alhamdulillah, ya gajiya”
“Gajiya ta bi lafiya, muna ta sauri a kawo muku breakfast, sai angon yake ce min ai kun karya”
“Eh da safe ne ya haɗa mana tea”
“Toh ai yayi kyau”
Juyawa tayi ta koma falo, Sameera ta bita tana nuna mata abu a wayarta. Sai ya rage daga ita sai Maryam da Aisha. Maryam ta ciro waya a jakarta sabuwa ta miƙawa Namra.
“Gashi inji Anty tace na baki, akwai layi a ciki”
Da murna Namra ta karɓa
“Wayyo Mamana ta kai na”
Cikin zumuɗi ta buɗe kwalin kwayar iPhone 6+ ce golden color yayi kyau sosai. Rumgume Maryam Namra tayi tana rawa.
Sai kusan azahar sannan su Hindatu da sauran mutanen suka ƙaraso. A lokacin ne Hajiya ta shigo ɗakin tayi ma Namra jan kunne akan zamantaewar aure da haƙuri, nan ma kuka Namra tasa mata, bama kamar lokacin da suka fito za su kama hanya. Tayi kuka sosai kamar ranta zai cire, a take taji kewarsu ta kama ta, sai duk taji kamar ta bisu. Tana tsaye bakin gate tana kallon motarsu har sai da ta daina hangota sannan ta dawo cikin gidan da sabon kuka.
Asim kan be dawo ba sai yamma, ya shigo tare da wasu dangin Babansa da suke Bakori, kallo kan kallo suke sun daga kan gidan zuwa kayan da suke cikin gidan.
Da far'ah Namra ta tarbe su, ta zuba musu abincin da Hajiya ta kawo mata ɗazu, waina ce da miya sai doya da ƙwai, sannan ta kawo musu ruwa. Sai daf da magariba suka tafi, ƴar fitar da Asim yayi ya rakasu ya dawo duk tsoro ya kamata tun da bata saba zama ita kaɗai ba a gida.
Ko da ya dawo tana tsaye bakin ƙofar falon tana jiransa, da murmushi ya riƙa hannunta, ya lago ɗayan hannunsa a ƙogunta suka koma cikin falon. A tare suka zauna saman kujera maƙalle da juna
“Aiko.kina da aiki duk kika sakawa ran ki tsoro dan ke kaɗai zaki riƙa rayuwa a cikin gidan nan ƙara ma tun wuri ki cire tsoro a ranki”
Maganar yake yana kallon ƙirginta, rigar lace ce a jikinta, kuma kalar ɗinkin da aka mata ya bayyana breast ɗinta. Ita kanta ta lura da yadda yanayinsa ya canja, hakan yasa ta tashi ta nufi da jimmar shiga ɗaki. Sai yayi sauri riƙe hannunta.
“Ina zaki je?”
“Ɗa... Ɗaki”
“Okay”
Sai ya tashi tsaye yayi mata side hug suka nufi ɗakin tare, har suka isa ɗakin mazaunanta yake shafawa, tana zaunawa sai ya kwanto mata saman jikin ta yadda breast ɗinta zasu shafi ƙirjinsa, ya kai ɗayan hannunsa yana shafa ta.
Lumshe ido tayi ta buɗe tana murmushi, sai ta haɗe bakinta da nashi, duk yadda tayi ƙoƙarin abandoned na ƙin yarda sauri yarda da shi sai ta kasa, saboda yadda ya kashe mata jiki, ga kuma irin kayan mata data sha tun jiya suke damunta, a take ta shiga mayar masa da martanin irin saƙon da yake aiko mata.
Basu samu kansu ba sai kusan asuba. Basu yi bachi daya kai minti ashiriba aka kira sallah asuba, shi ne ya riga ta tashi ya shiga bathroom yayi wanka tsarki sannan ya zuba wasu ruwan yayi alwala. Sai da ya canja ya saka jallabiya sannan ya tashe ta dan tayi sallah.
Daker ta unƙura ta tashi zaune, har ta samu ta ɗauki zanenta ta ɗaura sannan ta tashi tana wata tafiya kamar wanda aka ɓarewa kafafu ta nufi banɗaki.
Shi dai da kallo ya bita zuciyarsa cike da zarge zarge, sam shi be ga alamun budurci a tare da itaba, jinin da aka ce ana ganin idan anyi sex da virgin shi be gan shi ba, an faɗa musu wasu har kasa tafiya suke amman ita gashi har ta kai kanta banɗaki.
Kuma the way da take mayar masa da kiss da yadda take romance ɗinsa ya nuna ta taɓa sanin wani namiji kamin shi, daman yasan za'a rina, zargin mahaifiyarsa ya zama gaskiya.
A take wani ƙololon baƙinciki ya taso masa, yana ayyana irin cin amanar da Namra tayi masa, zuciyarsa na nuna masa tayi masa zagon ƙasa, shi take son ta yaudara.
Har sukayi sallah suka gama be kalli inda take ba, har sai da ta gama addu'o'inta sannan ta gaishe shi cikin kunya. Duk wani abu da yake ji a zuciyarsa sai ya dannesa ya ƙirƙiro far'ah da murmushi ya yaɓa a fuskarsa.
“Lafiya ƙalau Amarya, ya gajiyar jiya?”
Tayi saurin sauke kanta, tana mai jin kunya, shi kuma ya watsa mata wani kallo ƙasa-ƙasa, zuciyarsa na ayyana masa abubuwa ƙala-ƙala.
Tashi yayi ya je ya siyo musu kayan tea, ita kuma ta hau gadon ta kwanta saboda ta gaji da yawa. Shi ya haɗa musu tea kamar jiya, har yayi ya gama tana bachi abunta.
Bayan ya kawo kayan tea falo wayarsa tayi ringing, ganin number mahaifiyarsa yasa ta fita daga harabar falo gaba ɗaya, ya nufi can bayan kitchen sannan ya ɗaga wayar.
“Mama ina kwana”
“Lafiya ƙalau Ibrahim ya gida?”
“Lafiya ƙalau”
“Kina lafiya dai ko?”
“Lafiya ƙalau muke, ina su Amma?”
“Kowa lafiya ƙalau, nace ba a aiko da komai ba ko?”
“Eh kin san ai yau kwana biyu da auren a ɗan jira tukuna kuma ko zasu aiko a nan gida zasu kawo sai ku aiko mana ko?”
“Eh toh haka ne, kasan dashen da aka shiga ne jiya ta aiko mana”
“A ɗan jira dai Mama na san suna kan hanya”
“Toh Allah ya taimaka, amman dai karka yi wasa da kuɗin nan ana kawo su ka samu wata sana'ah babba ka riƙa”
“Haka zan yi ai, ko abokaina haka suke cewa”
“Toh Allah ya taimaka, ina Namra ɗin take ne?”
“Bachi take”
“Toh idan ta tashi a gaishe ta”
Daga haka suka yi sallama, sai ya dawo falon ya cigaba da haɗa tea, sannan ya shiga ya tashe ta.
Sai da tayi brush shima yayi sannan suka dawo falo suka karya. Bayan sun gama ya kwashe kayan ya kai kitchen, ita kuma ta shiga kiran wayar Anty Amarya suka gaisa.
Kowa dai da ta kira a gida har Hajiya Barau, sannan ta kira Abbah, kira biyu tayi masa be ɗauka ba saboda sabon layi ne, sai a na uku yayi picking, be wani sake sosai ba sama sama suka gaisa, sannan ta kashe wayar.
Duk tsawon lokacin data ɗauka tana gaisawa da ƴan'gidan su Asim na kusa da ita yana lalabenta, tana aje wayar ya shiga saka mata hannu ƙasanta. Sanin abunda yake nufi da ita yasa ta unƙura ta tana tureshi, cikin yanayin damuwa take masa magana tana son ya fahimceta
“Asim, not now please, Wallahi na gaji kuma har yanzu zafi nake ji”
Kallonta kawai yayi ba dan yana da niyar fasa abunda yake yi ba, idonsa sun rikiɗe sun canja sosai, sai wani numfashi yake.
Ita kanta tasan a yanzu ko da wane yare tayi masa magana ba ganewa zai yi ba, a dole ta ƙyaleshi ya riƙa wasa da ɓangare jikinta, kamin ya jata su koma ɗaki.
Har yayi abunda zai yi gama, be ji ya gamsu ba, ita kuma duk ta ƙosa ya fita ma ya bata ɗakin, da ita kaɗai tasan irin azabar da take ji. Daker ta samu ya rabu da ita, ta tashi a wahale tayi wanka dan ta karanta ta gani kuma ta sha ji a wa'azi ana faɗar cewa ba kyau ka kwanta bachi da janaba a jikinka, ko yaya ne ƙara dai kayi wankan. Ta gasa jikinta sosai da sosai sannan ta fito kamar da rarrafe ta dawo bedroom ɗin. Ko tufafi bata tsaya sawa ba ta hau saman gado, sai bachi.
KALSOOM POV.
A cikin ƴan kwanakin nan kwata-kwata ta rasa gane kan mijinta, duk yabi ya birkice mata kamar ba shi ba, abu kaɗan sai ya hauta da faɗa, ko kuma yayi ta haɗe mata fuska yana nuna baya son tana zama kusa da shi. Sai dai a ɗayan ɓangaren ta samu sassauci gurin Rashida yanzu kan zamansu babu laifi tana ɗan sakewa da ita, har ma tayi mata godiya a wani lokacin.
Yau ta kama weekend Rashida bata da aiki, kuma Doc yau a ɗakinta yake. Sai ta tashi tun da asuba ta haɗa musu breakfast, sai ta gama shirya komai sannan yaje ta tasheshi, ta shiga ɗakin Kalsoom ita ta taso ta.
Da gangan Rashida ta ɗauki dinner set mai plantain da kuma mai kifi ta aza gaban kujerar Kalsoom.
Sannan ta shiga haɗa masa tea dan tuni ya iso gurin yana duba chat ɗinsa na whatsapp. Har Kalsoom ta iso gurin ta
Showing 42001 words to 45000 words out of 280121 words
Har Abbah ya gaji da sauraren kukanta, ya kira Maryam ta fita da ita. Ko da aka koma da ita part ɗin Anty Amarya numfashinta har rawa yake. Nan ma barinta akayi daga ita sai Anty Amarya. Amman Anty Amarya ta kasa mata magana saboda kukan da take na rabuwa da ƴarta.
Har lokacin da aka bata ya ci ya cinye, Anty Amarya bata iya cewa Namra komai ba, daga ita har Namra suke. Sai da su Mama Zainab da Hajiya Barau suka shigo zasu fita da Namra sannan Anty Amarya ta iya furta
“Na yafe miki Namra Allah yayi miki albarka”
Juyowa Namra tayi ta rumgume Anty Amarya iya ƙarfinta. Har Hajiya Barau da Mama Zainab sai da idonsu ya cika da ƙwallah. Daker suka ɓanɓareta daga jikin Anty Amarya saboda yadda ta rumgumeta.
Yadda Namra take kuka yasa duk wanda yake falon sai da yayi hawaye. Ƙanen Asim da wasu ƴan'uwansa suna tsaye gefe suna kallo.
Muta ɗaya suka shiga da Maryam da Mama Zainab da Hajiya Barau. Ɗayar motar kuma ƴan'uwan Asim suka shiga daman ciki suka zo. Biyun wasu ƴan'uwan Abbah suka shiga, sai ta su Maryam da Aisha da Hindatu da wasu Cousins ɗin su. Ƙarfe uku da ƴan mintuna suka kama hanyar Katsina.
KALSOOM POV.
Yanayin yadda Doc. Hilal ya shiga yau, ya bata tsoro, sai dai bata damu sosai ba, dan tasan haka rayuwa take yau daɗi gobe ba daɗi. Ballantana ma yau ba ɗakinta bane wata ƙila ma uwargidan tasa ce ta ɓata masa rai.
Sai dai hakan be sa tayi ƙasa a gwuiwa ba, wajen zuwa tayi masa kyakkyawar tarba. Sai ta aje Rafiq a falo ta tashi ta nufi ɗakinsa, tana faɗaɗa murmushinta.
Kwance ta kararda shi saman gado ya lumshe ido yana, hannunsa ɗaya dafe da kansa.
Kusa da shi ta zauna, ta kai hannunta ta shafi gefen fuskarsa.
“Ya Omri lafiya kake kuwa?”
Shiru be amsa ta kamar ba zai yi murmushi ba, can kuma ya buɗe ido ya kalleta, sam baya jindaɗin ransa, amman a haka yayi ƙarfin hali ya ƙirƙiro murmushi ya kai hannu ya shafa bayanta.
“Matar Doc. Yau jina nake sai a hankali Wallahi?”
Duk sai taji babu daɗi, daman tasan ba banza tun da taga ya shigo babu ko sallama, kuma be kulata ba ya shigo ɗakinsa.
“Wani abun ne yake maka ciwo?”
“No”
Ya sake lumshe ido.
“Kawai bana jindaɗin rai nane, shiyasa na baro office ɗin”
“Ko wani ne ya ɓata maka rai?”
Idonshi a lumshe ya girgiza mata kai.
“No haka kawai Wallahi”
“Toh Allah ya sauwaƙe ammn idan irin hakan ya same ka, ka riƙa karanta Innalillahi wa'inna ilaihi raji'un, zaka ji sassauci”
Tashi yayi zaune, ya sakar mata ido kamar yau ya fara ganinta, sai kuma yaja ta jikinsa ya rumgume gam-gam, yana maida numfashi.
________________________________________
Yan Katsina ga Amanar Namra nan mun kawo muku 😢
Anya Hilal lafiya yake kuwa?🤔
#Comment
#Share
#Blogger
https://www.khadeejacandy.com.ng/2019/03/zagon-asa21.html
*🌺🌺🌺 ZAGON ƘASA 🌺🌺🌺*
Website
www.khadeejacandy.com.ng
NOT EDITED ⚠️
*PAGE - 21*
Ana kiran Sallah magariba suka isa Katsina. Kai tsaye suka wuce unguwar Nasarawa. Sun yi mamakin ganin gidan da aka sauke su da sunan gidan da Namra zata zauna.
Ba dan komai ba sai dan sanin Asim ɗin ba shida halin da zai iya kama hayar irin wannan gidan balle kuma har ya siye. Daman tun lokacin da aka zo jere an labartawa Hajiya Barau irin tsarin gidan. Gida ne plate mai kyau da shike-shike, ga farin fentin daya ƙawata gidan. A can ciki an ware dinning area da kitchen a gefe sai two bedrooms da babban falo, ga manyan kujerun da Abbah yasa aka zuba mata kamar ƴar wani shugaban ƙasa, duk bedrooms ɗin an saka mata furniture masu kyau da tsada.
A ƙaramin ɗaki ta tare ita da ƙannenta, su Hajiya kuma suka fito falo sukayi sallah, bayan sun gama direba ya kawo musu takeaway data aika a siyo musu, sai da suka ci abinci suka ƙoshi sannan Hajiya Barau ta shiga ɗakin da Namra take tana mata sallama, wai zata je gidan wata ƴar'uwarta ita da sauran waɗanda suka zo tare, su Maryam kuma sai idan Ango ya shigo sannan za su je.
Ko da Hajiya Barau ta bar gidan ana kiran sallah I'sha'i. Sai a lokacin Namra ta tashi ta shirya cikin wasu tufafin duk da kasancewar fuskarta a kumbure, ta koma babban ɗakin. Tara da rabi ango ya shigo tare da abokansa, ba a wani yi siyen baki ba, bayan addu'ah da fatan alheri da suka musu. Maryam dai sai ta watsawa abokan nasa wani mugun kallo take, tana Allah-Allah wani yace yana son ta cikin su tayi masa wankin babban bargo.
Tare suka fita da abokan angon, ɗayan yana ƙoƙarin magana da Hindatu dan itace mai ɗan dama a cikin su, sai wata cousin ɗin su Sameera. Lokacin da Namra taji ɗakin yayi tsit sai sabon kuka ya dawo mata, sai dai wannan karon hawaye ne kawai ba kamar na ɗazu ba.
Bayan ya rufe ƙofar gidan ya shigo ya rufe ƙofar falo, sannan ya nufi ɗakin da take da Sallama, bata iya amsa masa ba saboda kukan daya cika zuciyarta, sai shaƙar majina take tana haɗeye yawu da jimmar dannen kuka daya kasa ɓoyuwa.
Kusa da ita ya zauna, ya yaye mayafinta fuskarsa ɗauke da murmushi.
“Namra kukan me kike kuma? Bayan Allah ya cika mana burin mu”
Ɗagowa tayi ta kalle shi, kamar tace wani abu sai hawaye suka silala daga idonta zuwa kumatun ta.
Shi kansa baya buƙatar da faɗa masa dalilinta na kuka tun da yasan iyayenta basa son sa, gashi ya rabo ta da garin su. Shi kan ta ɓangarensa yau take sallah, tun da ya cika burinsa na aurenta ya fita kunya, ga uban dukiyar da aka zuba masa, ga kuma wanda yake jira a matsayin gara a kawo masa.
Jin kawai ta yi ya rumgume ta yana rarrashinta.
“Na san ban kyauta miki ba, dana nesanta ki da iyayenki, amman ni a nawa tunanin hakan shine zai fi mana, Namra a can abubuwa da dama zasu iya faruwa idan muna tare da iyayenki, amman a nan ba komai zasu ji ba, kuma a nan zamu tabbata ba zaman na ɗan wani lokaci ne kawai idan muka ga abunda Allah yayi sai mu koma can, kiyi haƙuri kinji?”
A yanayin da take bata iya magana, sai kawai ta ɗaga masa kai tana sauke ajiyar zuciya, tasa hannayenta ta rumgumeshi.
Har kusan shaɗaya dare suna zaune a gurin, daker ya lallaɓata ta tashi suka yi sallah nafila, kazar ma shi kaɗai ya ci ita kan lemu kawai ta sha ta hau gado ta kwanta. Washe gari guraren takwas na safe ya fita ya siyo musu kayan haɗa tea, ya shiga kitchen ya dafa ruwan zafi a electric, sannan ya dawo ɗakin ya haɗa ya zuba mata nata ya zuba nasa. Nan ma tea kawai ta sha bata ci birede ba, tsakanin jiya zuwa yau ta rame sosai kamar ba ita ba.
Shi kuma be yi matsa mata akan sai ta ci ba, tun da dai ita ba yarinya bace taya zai yi forced ɗinta akan cin abinci, shi duk ma ta cika sa dan yayi hating kuka for no reason, ita kanta ta san babu abunda ya tsana kamar kuka. Daman zuciyarsa ta faɗa masa, dan a rufa mata asiri ne aka yarda aka aura nasa ita, dan yasan babu dalilin da zai sa Abbah ya yarda ya aureta har ya baro garin da ita ya kuma hanata karatunta haka kawai ba tare da wani abu ba.
Sai dai hakan be dame shi, tun da ko ba komai ya taka first step of success, tun da ya auri ƴar masu hannu da shuni, kuma zama da kutuwar uwa dole, a dole dai Abbah ya kyautata masa tun da ya zama surikinsa.
Tashi yayi ya kwashe kofunan ya kai kitchen, sannan ya dawo kusa da ita ya zauna. Sai ya kai hannu ya shafa bayanta, dan tana daga kwance ne.
“Namra ko kina buƙatar wani abun ne? Naga baki ci komai ba”
Tashi tayi zaune hawaye cike a idonta, ta riƙa hannunsa tasa cikin nata, ta kalli ƙwayar idonsa tace
“Asim ka min alƙawarin ba zaka ci amana ta ba, ka min alƙawarin ba zaka taɓa rabuwa da ni ba, ka min alƙawarin ba zaka wulaƙanta ni ba, ka min alƙawarin zaka zauna da ni a duk halin da muka samu kan mu”
Gabansa ya faɗi sosai, a take ya ɗauke idonsa ɗ
Daga kallon da take nasa, yaja jikinsa ya rumgume.
“Taya kika wannan maganar kamar baki san waye Asim ba? Namra bakin ki ya daina furta irin waɗannan kalaman Asim ne naki har abada”
Sallamar su Hajiya Barau da Maryam ne, yasa shu saurin sakinta ya tashi ya fita yana amsa musu, a falo suka yi karo, sai ya kai har ƙasa yana gaida Hajiya Barau, ba laifi Maryam ma ta ɗan sakar masa fuska sun gaisa kamar daman can shiri suke.
Ko da suka shiga ɗakin Namra na gyara fuskarta da hoda, sai ta juyo ta kalli Maryam da murmushi a fuskarta.
“Hajiya Maryam an samu isowa”
“Toh ba dole ba, Hajiya ta sha kai muzo mu kawo miki abinci muyi sallama dake da wuri zamu koma”
Ta faɗa tana dire kular abinci a gaban Namra. Saman gado Namra ta dawo ta zauna tana ɗan ɓata fuska.
“Yanzu tafiya za kuyi ku bar ni?”
“Ahaf to ba aure kika zo yi ba”
Cewar Sameera tana mata kallon zolaya. Zata ƙara cewa wani abu Hajiya Barau ta shigo bakinta ƙumshe da sallama. Duk haɗa baki sukayi gurin amsa mata, Namra ta saukar da kai tana gaishe ta.
“Lafiya ƙalau, Amarya ya tashin ku?”
“Alhamdulillah, ya gajiya”
“Gajiya ta bi lafiya, muna ta sauri a kawo muku breakfast, sai angon yake ce min ai kun karya”
“Eh da safe ne ya haɗa mana tea”
“Toh ai yayi kyau”
Juyawa tayi ta koma falo, Sameera ta bita tana nuna mata abu a wayarta. Sai ya rage daga ita sai Maryam da Aisha. Maryam ta ciro waya a jakarta sabuwa ta miƙawa Namra.
“Gashi inji Anty tace na baki, akwai layi a ciki”
Da murna Namra ta karɓa
“Wayyo Mamana ta kai na”
Cikin zumuɗi ta buɗe kwalin kwayar iPhone 6+ ce golden color yayi kyau sosai. Rumgume Maryam Namra tayi tana rawa.
Sai kusan azahar sannan su Hindatu da sauran mutanen suka ƙaraso. A lokacin ne Hajiya ta shigo ɗakin tayi ma Namra jan kunne akan zamantaewar aure da haƙuri, nan ma kuka Namra tasa mata, bama kamar lokacin da suka fito za su kama hanya. Tayi kuka sosai kamar ranta zai cire, a take taji kewarsu ta kama ta, sai duk taji kamar ta bisu. Tana tsaye bakin gate tana kallon motarsu har sai da ta daina hangota sannan ta dawo cikin gidan da sabon kuka.
Asim kan be dawo ba sai yamma, ya shigo tare da wasu dangin Babansa da suke Bakori, kallo kan kallo suke sun daga kan gidan zuwa kayan da suke cikin gidan.
Da far'ah Namra ta tarbe su, ta zuba musu abincin da Hajiya ta kawo mata ɗazu, waina ce da miya sai doya da ƙwai, sannan ta kawo musu ruwa. Sai daf da magariba suka tafi, ƴar fitar da Asim yayi ya rakasu ya dawo duk tsoro ya kamata tun da bata saba zama ita kaɗai ba a gida.
Ko da ya dawo tana tsaye bakin ƙofar falon tana jiransa, da murmushi ya riƙa hannunta, ya lago ɗayan hannunsa a ƙogunta suka koma cikin falon. A tare suka zauna saman kujera maƙalle da juna
“Aiko.kina da aiki duk kika sakawa ran ki tsoro dan ke kaɗai zaki riƙa rayuwa a cikin gidan nan ƙara ma tun wuri ki cire tsoro a ranki”
Maganar yake yana kallon ƙirginta, rigar lace ce a jikinta, kuma kalar ɗinkin da aka mata ya bayyana breast ɗinta. Ita kanta ta lura da yadda yanayinsa ya canja, hakan yasa ta tashi ta nufi da jimmar shiga ɗaki. Sai yayi sauri riƙe hannunta.
“Ina zaki je?”
“Ɗa... Ɗaki”
“Okay”
Sai ya tashi tsaye yayi mata side hug suka nufi ɗakin tare, har suka isa ɗakin mazaunanta yake shafawa, tana zaunawa sai ya kwanto mata saman jikin ta yadda breast ɗinta zasu shafi ƙirjinsa, ya kai ɗayan hannunsa yana shafa ta.
Lumshe ido tayi ta buɗe tana murmushi, sai ta haɗe bakinta da nashi, duk yadda tayi ƙoƙarin abandoned na ƙin yarda sauri yarda da shi sai ta kasa, saboda yadda ya kashe mata jiki, ga kuma irin kayan mata data sha tun jiya suke damunta, a take ta shiga mayar masa da martanin irin saƙon da yake aiko mata.
Basu samu kansu ba sai kusan asuba. Basu yi bachi daya kai minti ashiriba aka kira sallah asuba, shi ne ya riga ta tashi ya shiga bathroom yayi wanka tsarki sannan ya zuba wasu ruwan yayi alwala. Sai da ya canja ya saka jallabiya sannan ya tashe ta dan tayi sallah.
Daker ta unƙura ta tashi zaune, har ta samu ta ɗauki zanenta ta ɗaura sannan ta tashi tana wata tafiya kamar wanda aka ɓarewa kafafu ta nufi banɗaki.
Shi dai da kallo ya bita zuciyarsa cike da zarge zarge, sam shi be ga alamun budurci a tare da itaba, jinin da aka ce ana ganin idan anyi sex da virgin shi be gan shi ba, an faɗa musu wasu har kasa tafiya suke amman ita gashi har ta kai kanta banɗaki.
Kuma the way da take mayar masa da kiss da yadda take romance ɗinsa ya nuna ta taɓa sanin wani namiji kamin shi, daman yasan za'a rina, zargin mahaifiyarsa ya zama gaskiya.
A take wani ƙololon baƙinciki ya taso masa, yana ayyana irin cin amanar da Namra tayi masa, zuciyarsa na nuna masa tayi masa zagon ƙasa, shi take son ta yaudara.
Har sukayi sallah suka gama be kalli inda take ba, har sai da ta gama addu'o'inta sannan ta gaishe shi cikin kunya. Duk wani abu da yake ji a zuciyarsa sai ya dannesa ya ƙirƙiro far'ah da murmushi ya yaɓa a fuskarsa.
“Lafiya ƙalau Amarya, ya gajiyar jiya?”
Tayi saurin sauke kanta, tana mai jin kunya, shi kuma ya watsa mata wani kallo ƙasa-ƙasa, zuciyarsa na ayyana masa abubuwa ƙala-ƙala.
Tashi yayi ya je ya siyo musu kayan tea, ita kuma ta hau gadon ta kwanta saboda ta gaji da yawa. Shi ya haɗa musu tea kamar jiya, har yayi ya gama tana bachi abunta.
Bayan ya kawo kayan tea falo wayarsa tayi ringing, ganin number mahaifiyarsa yasa ta fita daga harabar falo gaba ɗaya, ya nufi can bayan kitchen sannan ya ɗaga wayar.
“Mama ina kwana”
“Lafiya ƙalau Ibrahim ya gida?”
“Lafiya ƙalau”
“Kina lafiya dai ko?”
“Lafiya ƙalau muke, ina su Amma?”
“Kowa lafiya ƙalau, nace ba a aiko da komai ba ko?”
“Eh kin san ai yau kwana biyu da auren a ɗan jira tukuna kuma ko zasu aiko a nan gida zasu kawo sai ku aiko mana ko?”
“Eh toh haka ne, kasan dashen da aka shiga ne jiya ta aiko mana”
“A ɗan jira dai Mama na san suna kan hanya”
“Toh Allah ya taimaka, amman dai karka yi wasa da kuɗin nan ana kawo su ka samu wata sana'ah babba ka riƙa”
“Haka zan yi ai, ko abokaina haka suke cewa”
“Toh Allah ya taimaka, ina Namra ɗin take ne?”
“Bachi take”
“Toh idan ta tashi a gaishe ta”
Daga haka suka yi sallama, sai ya dawo falon ya cigaba da haɗa tea, sannan ya shiga ya tashe ta.
Sai da tayi brush shima yayi sannan suka dawo falo suka karya. Bayan sun gama ya kwashe kayan ya kai kitchen, ita kuma ta shiga kiran wayar Anty Amarya suka gaisa.
Kowa dai da ta kira a gida har Hajiya Barau, sannan ta kira Abbah, kira biyu tayi masa be ɗauka ba saboda sabon layi ne, sai a na uku yayi picking, be wani sake sosai ba sama sama suka gaisa, sannan ta kashe wayar.
Duk tsawon lokacin data ɗauka tana gaisawa da ƴan'gidan su Asim na kusa da ita yana lalabenta, tana aje wayar ya shiga saka mata hannu ƙasanta. Sanin abunda yake nufi da ita yasa ta unƙura ta tana tureshi, cikin yanayin damuwa take masa magana tana son ya fahimceta
“Asim, not now please, Wallahi na gaji kuma har yanzu zafi nake ji”
Kallonta kawai yayi ba dan yana da niyar fasa abunda yake yi ba, idonsa sun rikiɗe sun canja sosai, sai wani numfashi yake.
Ita kanta tasan a yanzu ko da wane yare tayi masa magana ba ganewa zai yi ba, a dole ta ƙyaleshi ya riƙa wasa da ɓangare jikinta, kamin ya jata su koma ɗaki.
Har yayi abunda zai yi gama, be ji ya gamsu ba, ita kuma duk ta ƙosa ya fita ma ya bata ɗakin, da ita kaɗai tasan irin azabar da take ji. Daker ta samu ya rabu da ita, ta tashi a wahale tayi wanka dan ta karanta ta gani kuma ta sha ji a wa'azi ana faɗar cewa ba kyau ka kwanta bachi da janaba a jikinka, ko yaya ne ƙara dai kayi wankan. Ta gasa jikinta sosai da sosai sannan ta fito kamar da rarrafe ta dawo bedroom ɗin. Ko tufafi bata tsaya sawa ba ta hau saman gado, sai bachi.
KALSOOM POV.
A cikin ƴan kwanakin nan kwata-kwata ta rasa gane kan mijinta, duk yabi ya birkice mata kamar ba shi ba, abu kaɗan sai ya hauta da faɗa, ko kuma yayi ta haɗe mata fuska yana nuna baya son tana zama kusa da shi. Sai dai a ɗayan ɓangaren ta samu sassauci gurin Rashida yanzu kan zamansu babu laifi tana ɗan sakewa da ita, har ma tayi mata godiya a wani lokacin.
Yau ta kama weekend Rashida bata da aiki, kuma Doc yau a ɗakinta yake. Sai ta tashi tun da asuba ta haɗa musu breakfast, sai ta gama shirya komai sannan yaje ta tasheshi, ta shiga ɗakin Kalsoom ita ta taso ta.
Da gangan Rashida ta ɗauki dinner set mai plantain da kuma mai kifi ta aza gaban kujerar Kalsoom.
Sannan ta shiga haɗa masa tea dan tuni ya iso gurin yana duba chat ɗinsa na whatsapp. Har Kalsoom ta iso gurin ta
Book Chapters
Chapter 1Chapter 2Chapter 3Chapter 4Chapter 5Chapter 6Chapter 7Chapter 8Chapter 9Chapter 10Chapter 11Chapter 12Chapter 13Chapter 14Chapter 15 Chapter 16Chapter 17Chapter 18Chapter 19Chapter 20Chapter 21Chapter 22Chapter 23Chapter 24Chapter 25Chapter 26Chapter 27Chapter 28Chapter 29Chapter 30Chapter 31Chapter 32Chapter 33Chapter 34Chapter 35Chapter 36Chapter 37Chapter 38Chapter 39Chapter 40Chapter 41Chapter 42Chapter 43Chapter 44Chapter 45Chapter 46Chapter 47Chapter 48Chapter 49Chapter 50Chapter 51Chapter 52Chapter 53Chapter 54Chapter 55Chapter 56Chapter 57Chapter 58Chapter 59Chapter 60Chapter 61Chapter 62Chapter 63Chapter 64Chapter 65Chapter 66Chapter 67Chapter 68Chapter 69Chapter 70Chapter 71Chapter 72Chapter 73Chapter 74Chapter 75Chapter 76Chapter 77Chapter 78Chapter 79Chapter 80Chapter 81Chapter 82Chapter 83Chapter 84Chapter 85Chapter 86Chapter 87Chapter 88Chapter 89Chapter 90Chapter 91Chapter 92Chapter 93Chapter 94