Kasa tashi Kalsoom ta yi har sai da Momi ta zo ta riƙa ta suka bar falon tare. Daddy Hilal ya kalli Daddyn Kalsoom yana faɗin
“Wato abun ne da ɗaure kai, kasan kuma zuciya wani lokacin bata da ƙashi, ni kai na abun ya ɗan ɗaure min kai da farko, amman ganin soyayyar dake tsakanin dole a ɗaga musu ƙafa, kuma koma minene shi uban ɗa be yarda ba, kai miye na ka a ciki har ka raba musu aure ƙaramar ƙwaƙwalce kawai ta mata”
Murmushi Dadyn Kalsoom ya yi ya girgiza kai
“Allah dai ya kyauta ya bayyana gaskiya”
Dukasu suka amsa da Amin har Hilal dake ƙoƙarin miƙewa tsaye.
YASMEEN POV.
A gajiye ta aje hakar hannunta ta karɓi Babynta daga hannun mai mata reno tana murmushi.
“Sorry Dear i'm back”
Uzair ya aika mata wani kallo mai cike da jin haushi.
“Ni fa wannan aikin na ki ya ishe ni, ace har kana jego ma sai kaje, yau kwana biyu da suna har kin fara fita”
Kallonsa ta yi fuskarta da annuri.
“Am sorry dear, daga yau ba zan sake fita ba sai next week”
Wani tsakin haushi yayi
“Ai kaji fa fitan ya fara kenan, ai ba aure lawyer ba, zamanta a gida ma aiki ne”
Dariya tayi tana gyara sunan da take ba ƴarta, tare da kallon Adnan dake wata tafiya a wahalce.
“Kai me ya same ka?”
Bude baki yayi zai yi magana sai Uzair ya karɓe.
“Da...”
“Ina jin Basir ne yake damunsa, ko kuma ya zauna wani abu ne, ɗazu ma na duba gurin ya masa ja sosai, i will take him to hospital”
Yana gama faɗar hakan ya miƙe tsaye ya riƙa hannu Adnan da sauri suka fice, ita kuma bata wani ɗauke abun serious ba, ta maida hankalinta gurin Mai mata reno.
“Me aka girka?”
“Wake aka yi, shi yace na girka ta daya ga Namra na ta kuka”
“Ayyah Namra na, i'm sorry ba zan sake fita ba dake ba, i love you”
Ta aikawa babyn kiss tana murmushi. Sannan ta tashi ta nufi ɗakinta tana cire ɗankwalin kanta, ɗayan hannunta kuma na ɗauke da new babynta Namra.
ASIM POV.
Be farka ba, sai bakwai da rabi, yana yin sallah asuba ya sake komawa baci,ba shi ya tashi ba sai sha ɗaya na safe, wayarsa dake kusa da shi ya ɗauka ya lalubo number Mardiya dan yau a bachinsa na safe ita yayi mafarki, be wani daɗe sosai yana waya da ita ba, ya miƙe ya shiga wanka.
Sha biyu saura ya shirya ya fita, kai tsaye gidan Hajiya Sadiya ya zuwa, tun kamin ya taso ya tanadi ƙarya da zai mata akan Namra, sai ya tarar bata gidan, mai gadi ya labarta masa tun jiya da dare ta bar gidan wai taje birnin kebi.
Ko kaɗan Asim be jidaɗin hakan da Hajiya tayi masa ba, sai ya zuciyarsa ta soma nuna masa ko dai Hajiya ta yi fushi da shi ne, shiyasa har taje Kebi bata faɗa masa ba, duk da ta faɗa masa zata bashi hutu saboda baƙi zata yi ai bata ce masa zata bar garin ba. Har ya ciro wayarsa ya kirata sai kuma wata zuciyarta ta hanasa, a ganinsa yanzu ba zata sauraresa ba tun da tana cikin fushi ƙara ya bari har sai an kwana biyu sannan ya kira ta, idan bata dawo ba.
Ƴar ƙara wayarsa ta yi, yana duba ya ga alert daga diamond bank saƙon miliyan biyar ya shiga asusun ajiyarsa.
“Wow”
Ya faɗa yana karanta sunan wanda ya aiko masa da kuɗin.
“Yayi Kyau Alhajina”
Ya faɗa cike da tsananin farinciki, kaminɓya ɗora da saƙon daya biyo baya.
“Na aiƙo maka da kuɗi, kazo gobe sokoto ina son ganinka, kuma ka zama mai riƙe sirri”
“Zan zo gobe tun da safe inshallah”
Haka ya mayar masa da amsa, sannan ya rumgume wayar a ƙirjinsa yana dariya har ta fitar hankali. Komawa yayi motarsa ya shiga, yana cigaba da dariya har da jijjiga jiki.
Yana yi ma motar ki kiran Nably ya shigo wayarsa, cikin sauri ya ɗauka yana dariya.
“Hello my second wife”
“Au ba ma nice ta farko ba kenan?”
“Yes karki sa ma ranki zaki zauna ke kaɗai a gidan Asim”
“Ashe kai ba Saurayi ba ne?”
“Saurayi ne kuwa sabo hul, amman bayan ke wata zan ƙara, ko kuma ma akai ku ku biyu a tare”
“Kai da bakinka kake faɗin haka, lallai na yi fushi, na bar mata”
Da sauri ya haɗe hannayensa kamar tana gabansa.
“Sorry my nurul khalbi, wasa nake miki just to get your angry, yanzu dai ya hanya?”
“Au kasan da tafiya na, amman baka kira ka tambaye ni ba”
“i'm sorry dear i'm just kind of busy, In fatar kin sauka Lafiya”
“Na sauka ƙalau idona sai ƙaiƙayin ganinka suke yi ”
“Gani na kan hanya nan da mintuna talati”
“I can't wai to see you”
“The same here”
Yana aje wayar ya ƙara ma motarsa jiya ya nufi wani boutique, dan siyen kaya mai kyau da tsana wanda zai sa yaje gurin gimbiya Nabila.
ABDOOL POV.
Ƙarfe goma sha ɗaya da rabi jirginsa ya sauka Katsina, yana sauka ya kira Ummi ya faɗa mata ya sauka, amman ta ƙi ɗaukar wayarsa, har sai da ya aika mata da saƙo, Sannan ta aiko masa da direba.
Daga filin jirgi zuwa gida tafiyar minti goma sha biyar ce, amman sai yaga ta yi masa tsayi kamar na awa ɗaya saboda zumuɗin da yake na bawa Ummi labarin dake cikin ransa.
Suna shiga harabar gidan farincikin fuskarsa ya ɗaɗa ƙaruwa, ko fakin ɗin kirki direban be yi Abdool ya buɗe ya fito, sai duk sojojin da suke gidan suka maƙe guri ɗaya suna sara masa, hannu kawai ya ɗaga musu ya nufi Babbar ƙofar gidan.
Amira da Haleema na tsaye dinning suna jera abinci Abdool ya shigo da sallama.
Da gudu Amal taje ta rumgume shi.
“Dude i miss you”
“I miss you more”
Kaɗan kaɗan Amira take satar kallonsa tana murmushi, Haleema ma kallonta take tana murmushi dan tasan abunda yake zuciyarta. Fitowar Ummi ne ya ɗago da duka hankalinsu har Amira ta samu damar kallon Abdool da kyau tana auna irin missing ɗinsa da ta yi.
“Ka kuru da baka dawo yau ba ko”
Dariya yayi yana wasa da hannun Amal.
“Ummi ina da labari mai daɗi da zan ba ki, duk da kin katse min uzuri na”
Zaunawa tayi saman kujera tana murmushi.
Sai shi ma ya zauna yana tambayar Amal abunda ya hana ta zuwa makaranta. Lemu Amira ta ɗauko ta kawo masa a gabansa ta dire masa, tana masa sannu da zuwa.
“Yauwa Thank you so much”
Ta jidaɗin kalma nan da yayi mata, bama kamar murmushin da ta gani shimfiɗe a fuskarsa. Cikin natsuwa ta tashi ta nufi dinning dan zuba masa abinci.
Kallon Ummi yayi fuskarsa ɗauke da abunda ke zuciyarsa.
“Ummi kin yi suruka, matar da na taɓa baki labari ina so na samo ta, finally mafarki na zai zama gaskiya...”
Tartsatsa... Suka ji ƙarar fashewar plate mai ɗauke da abinci, wanda Amira ta sake saboda maganarsa da ta soki gadon bayanta, da sauri ta ɗuka tana kwashewa, kamar wacce ta ruɗe, a take hawaye ya fara bin fuskarta, sai dai su basu gani ba kasancewar ta basu bayana ne.
“Ba ki ji ciwo ba?”
Ummi ta faɗa tana ɗan leƙen ta. Sai Haleema ta yi saurin amsawa.
“A'a plate ɗin ne kawai ya fashe”
Ummi ta maida hankalinta gurin ɗan ta.
“Im happy for you Son, na daɗe ina jiran wannan ranar, you have no idea how happy you make me, sai dai ban gane wacce kake magana ba akai kam ba”
“Ye... ”
Ringing ɗin da wayarsa ta yi ne ya hana shi ƙarasa maganar sai yayi saurin tashi ya nufi wani ɓangare na falon yana amsa wayar.
“Salim”
“Sir mun bincika, Manjo Usman Zamau yana sokoto da zama a unguwar clapperto, yana da mata biyu da ƴaƴa goma sha uku Namra ita ce ta goma, kuma ainahin sunan ta shi ne Khadija, ta yi makaranta a dan fodio tana level 300 aka yi mata aure, kuma har yanzu tana gidan aurenta zaune, facebook username ɗin ta Khadija Usman Zamau instagram kuma Namra's, haka yake a twitter da snapchat”
“Amman ba ku bincika zaman auren ta ba? Har yanzu tana da aure?”
“Binciken mu ya nuna har yanzu tana da aure kuma tana a garin katsina da zama, sunan mijin da take aure Ibrahim amman anfi kiransa da Asim”
“Thank you”
“Your Welcome Sir”
Wayar ya ƙurawa ido yana mamakin yadda Namra zata masa ƙarya, bayan ya tambaye tsakaninta da Allah, taya aurenta zai mutu kowa bai sani ba, hakan yana mufin ƙarya ta masa kenan ko kuma akwai abunda take ɓoyewa.
Juyowa yayi yana ƙoƙarin ɓatar da mamakin dake fuskarsa ya kalli Ummi yana tahowa ya ce.
“Wani aiki ya tashi Ummi Ana nema na a Kaduna yanzu yanzu nan”
“What?”
Ummi ta faɗa da mugun mamaki. Shi kuma ya ɗan ɗaga gira yana kallon Amal.dake zumuɗin labarin daya fara badawa.
Hello habibaties nasan kuna haƙuri da ni dan Allah ku ƙara haƙurin. Wallahi abubuwa ne suke min yawa, ga kuma rashin wutar nepa a gusau, yau four days babu wuta, sai an tashi engine ne muke samu mu saka. Idan kuma ka matsa za'a ce sai ka biya na Mai 😂 you know how our grandma's are, sai haƙuri 😂
Love you all fisabilliah ♥️🌹🌺❤
[7/18, 8:12 PM] Khadeeja Candy♥: *71*
Ɗauke kansa yayi daga kallon da yake ma Amal ya kalli Ummi, irin babu zacen wasa a kalamansa.
“Nima sai da na ce miyasa ba su bar ni nayi aikin ba acan ba sai yanzu da na dawo”
“Abdallah ka ce min kun samu hutu fa? Aikin me zaka je yi yanzu?”
“Wai General ne zai zo daga Abuja zuwa Kaduna gobe, kuma dole ne muje. Bari naje ya canja kaya gobe da safe ai zan dawo”
Be jira abunda Ummi zata ce ba, ya nufi ƙofar fita yana lalabar number Salim dan ya sama masa jirgin da zai koma Kaduna yanzu ko da Yammar nan.
Ummi dai da kallo Mamaki ta bishi, ta fi kowa sanin ɗanta dan haka ta san ba aiki ne zai maida shi Kaduna ba, sai dai wani abun na daban, kai ta girgiza tana kallon Amal data wani turo baki.
“Be ma ƙarasa mana labarin ba”
Ummi ta miƙe tsaye ta nufi kitchen tana faɗin
“Uhnm kya ji da shi”
AMIRA POV.
Tana gama kwashe plate ɗin da ya fashe ta zuba a shara, sai ta nufi ɗakinta cikin wani irin kuka marar misaltuwa.
Saman gadon Amal ta faɗa ta kife tana rera kukanta a hankali yadda wani ba zai ji.
“Shikenan na rasa komai, wata yake so ba ni ba, shi ma na rasa shi”
Tausayin kanta take da kanta tana tunanin irin rayuwar da zata yi nan gaba. Bayan ta rasa duk wani abun da zai iya saka ta farinciki. A hankali Haleema ta turo ƙofar ta shigo fuskarta ɗauke da tausayin Amira,wanda har zuciyarta haka ne. Kusa da ita ta zauna ta kai hannu ta taɓa ta.
“Ki yi haƙuri Amira, ni kai na ban san haka zai faru ba...”
Da sauri Amira ta ɗago ta kalleta da idonta da suka gana canja kala saboda kuka.
“Ke ma kin yarda na rasa ɗan uwanki ko? Babu wani abun da za kiyi? Dan Allah ki taimaka min Haleema kema mecece zaki iya shiga a halin dana shiga, kin san irin abunda nake ji, Wallahi ina son Yaya kuma tsakani da Allah zan zauna da shi, idan har na ci amanarsa na yarda amanar Allah ta ci ni, na rantse da Allah ba zan cutar da shi ba”
Kuka take sosai zuciyarta a narke, ta kama hannayen Haleema ta riƙa tana mai jin kamar Haleema ta yi mata maganin damuwarta.
Cikin kuka Haleem ta ce.
“Babu wani taimako da zan iya yi miki Amira, Big Bro babu mai saka shi dole idan ba Ummi ba, kuma idan har ya nuna baya so ita ma bata so, babu abunda ya cutar da ke kamar zama ba a gurin iyayen ki ba”
“Ba zan iya komawa ba, ban san yadda zan yi na koma ba”
Ya zube ƙasa zaune tana rushewa da sabon kuka. Haleema ta riƙa ta tana bata haƙuri. Kamin ta tashi cikin ɓacin rai ta nufi hanyar fita, Amal ta samu tsaye jikin ƙofar ta yi wani wuƙi-wuƙi da ido.
“Ummi tan kiran ki”
Ta faɗa a sagarce, sannan ta falfala da gudu ta nufi ɗakin Ummi ɗin. Haleema ta rufa mata baya tana share hawayenta. Ƙusƙus ta tarar Amal na yi gurin Ummi, hakan ya tabbatar ma da Haleema Amal ta ji abunda suke cewa.
Meesha na gaban maduba Ummi tana ɗanɗasa kwaliya ita da Fauza, dan su basu ma san Abdool ya dawo ba.
“Ummi ga ni”
Ta faɗa yayinda take ƙoƙarin zama kusa da ita.
“Gulma ta kuke yi?”
Da sauri Haleema ta sake kallon Ummi baki sake, kamin ta maida dubanta gurin Amal.
“Amman yarinyar nan munafuka ce Wallahi, gulamar ta kika ce na yi, aiko sai na miki ɗan banzan duka a gidan nan”
Ummi ta katsa mata tsawa.
“A'a akan me? Maganar me kuke ke da ita har kuke kuka?”
“Walahi akan big bro ne, dan ta ji ya samu mata shine take kuka ina bata haƙuri”
“Dan ya samu mata sai aka yi me?”
“Kin san son shi take sosai wallahi”
“Amman dai Haleema baki da hankali, ke ko a mafarki aka ce yayanki zai aureta idan kika farka ai kya nemi tsarin Allah, macen data zauna da yan fashi? Kika san ciki nawa ta zubar? Baki san zaman ta a nan ma it very risk ba”
“Haba Ummi ciwo ƴa mace na ƴa mace ne, yanzu idan nice a wannan hali zaki jidaɗi? Ba ita ta ƙaddaro ma kanta ba, kuma ta yi sadaukarwa ma Big Bro ita ta cancanci ya so ta wallahi”
Ummi kasa magana ta yi saboda mamakin furucin Haleema. Meesha ta taso daga gaban madubi da take zaune tana faɗin.
“Kin san me Ummi zata iya saka mana guba duka mu mutu idan har ta ji Big Bro ba zai aureta ba, ƙila ma turo ta aka yi, ta ina ma.taji Yaya ya samu mata? Kodai ta ga alamun ba zai so ta ba ne”
Fauza ta amsa.
“Kuma Wallahi irin waɗan nan ba tsoron kisan kai suke ba, tun da sun saba”
Ran Haleema ya ɓace sosai.
“Ku daina judge mutane ne, hakan be da kyau, Allah ma yana karɓar tubar bayinsa balle kuma mu....”
Shigowar Abdool ne yasa duk suka warsar da maganar, Fauza da Meesha suka fara ɗaukin shigowarsa tare da masa sannu da zuwa.
“Ai kune ba ku san ya dawo ba, mu tuni muka sani har ya ba mu labarin matarsa da zai aura”
Ya ɗaga gira ɗaya yana kallon Amal, ita kuna ta shigar da kai jikin Ummi dake dariya, ita ala dole ga auta.
“My girls ku fita za mu yi magana”
Ya faɗa yana ƙoƙarin zama a kujerar dake fuskantar gadon Ummi. Ba musu duk suka fita har Amal uwar son zancen dan bata ga alamun wasa a fuskarsa ba balle ta tsaya.
“Maganar gaskiya Ummi ba aiki zani ba, gurin yarinyar nan zan koma, kawai ki min addu'ah, gobe da safe zan dawo”
“Na gama karantar ka sarau Lamiɗo kallon ka kawai na ke yi. Allah ya kai ka lafiya, kuma a gaishe min ita sosai da sosai”
‘Ai ba gaisuwa ba, ni kaina ban san makomata ba’
Zance daa ya faɗo masa kenan a rai kamin ya ɗago ya saurari zancen da Ummi ta ɗora da shi.
“Dan Allah ka nemo iyayen yarinyar nan, idan ba zata iya zuwa ba, su suzo su tafi da ita”
“Ummi laifin wa? Idan na yi magana ai cewa kike na ɗaga mata ƙafa”
“Ai ba ƙafa ba komai ma.an ɗaga mata, yanzu kam ya kamata ace tana gaban iyayenta”
Miƙewa yayi tsaye yana faɗin
“Don't worry Ummi, if she planning something evil, za a sanar da ni, ai akwai mai kula da cctv camera. A min addu'ah jirgin mu zai tashi nan da ten minutes”
“Allah ya kiyaye ya kai ku lafiya”
Tasowa ta yi ta suka fito tare da shi yana labarta mata maganar da suka yi da Mai Martaba.
Ko da ya isa airport sauran minti uku jirgin ya tashi, abun ka da manya a take aka masa checking ya wuce.
Be da sukuni har sai da jirginsu ya sauka garin Kaduna, yana sauka airport yayi waya daga Abuja, suka kuma suka yi waya a kaduna, cikin minti ashiri sai ga direba in military uniform sun zo ɗaukarsa.
A cikin motar ya sha ruwa, kamin ya buɗe biscuit ya ɗan ci kaɗan yana faɗa musu inda zasu kai shi. A masallaci unguwar ya ce a aje shi, suna yin parking da sauri wani ya fito daga cikin motar yazo ya buɗe masa yana sare masa, umarni ya basu na suje sai ya nemesu. Ba musu suka sake tsara masa suka koma cikin motar suka juya. Yi yayi kamar be kula da mutanen da suke kallonsa ba, yayi alwalarsa ya bi jam'i, har aka gama sallar kowa da abunda yake faɗa, wasu wai ya zo bincike ne, wasu kuma wai akwai wanda zai kama, shi dai yana gama sallah la'asar ya kanyar kwanar da zata sadashi da gidansu Lamido,daman daga masalacin zuwa cikin gidan babu wani nisa sosai. Hango mustafa da yayi yasa shi sauri juyawo ya ciro wayarsa a aljihu ya neman number direban Mai Martaba da yake gidansa da suka sauka da ke Kaduna.
Cikin mintuna da basu bi goma sha ɗaya ba sai ga direba ya iso, be faka ko'ina ba sai gaban Abdool da sauri Abdool ya buɗe ya shiga, yana nuna masa inda zaije.
Mustafa na zaune gindin wani icce yana kallon motar har suka faka ta dai-dai ƙofar gidan su Lamido. Ya maida hankali sosai da son ganin wanda zai fito daga motar, sai kawai yaga baƙuwar fuska ta fito daga gidan gaba mazaunin direba yana buga ƙofar giɗansu Lamido.
“Waye...”
Suka amsa daga can ciki kamin ɗan uwani ya fito waje ganin mai buga ƙofar.
“Shiga ciki ka ce Abdallahi daga Katsina yana sallama da Namra”
“Toh ya juya da gudu ya koma”
Shi kuma direba ya juyo dan mayarma da Lamido saƙo.
“Wai Ance bata nan”
Yaron ya faɗa yana tsaye jikin ƙofar gidan. Abdool ya buɗe motar da kansa ya fito.
“Kije ka ce idan bata
Showing 186001 words to 189000 words out of 280121 words
Kasa tashi Kalsoom ta yi har sai da Momi ta zo ta riƙa ta suka bar falon tare. Daddy Hilal ya kalli Daddyn Kalsoom yana faɗin
“Wato abun ne da ɗaure kai, kasan kuma zuciya wani lokacin bata da ƙashi, ni kai na abun ya ɗan ɗaure min kai da farko, amman ganin soyayyar dake tsakanin dole a ɗaga musu ƙafa, kuma koma minene shi uban ɗa be yarda ba, kai miye na ka a ciki har ka raba musu aure ƙaramar ƙwaƙwalce kawai ta mata”
Murmushi Dadyn Kalsoom ya yi ya girgiza kai
“Allah dai ya kyauta ya bayyana gaskiya”
Dukasu suka amsa da Amin har Hilal dake ƙoƙarin miƙewa tsaye.
YASMEEN POV.
A gajiye ta aje hakar hannunta ta karɓi Babynta daga hannun mai mata reno tana murmushi.
“Sorry Dear i'm back”
Uzair ya aika mata wani kallo mai cike da jin haushi.
“Ni fa wannan aikin na ki ya ishe ni, ace har kana jego ma sai kaje, yau kwana biyu da suna har kin fara fita”
Kallonsa ta yi fuskarta da annuri.
“Am sorry dear, daga yau ba zan sake fita ba sai next week”
Wani tsakin haushi yayi
“Ai kaji fa fitan ya fara kenan, ai ba aure lawyer ba, zamanta a gida ma aiki ne”
Dariya tayi tana gyara sunan da take ba ƴarta, tare da kallon Adnan dake wata tafiya a wahalce.
“Kai me ya same ka?”
Bude baki yayi zai yi magana sai Uzair ya karɓe.
“Da...”
“Ina jin Basir ne yake damunsa, ko kuma ya zauna wani abu ne, ɗazu ma na duba gurin ya masa ja sosai, i will take him to hospital”
Yana gama faɗar hakan ya miƙe tsaye ya riƙa hannu Adnan da sauri suka fice, ita kuma bata wani ɗauke abun serious ba, ta maida hankalinta gurin Mai mata reno.
“Me aka girka?”
“Wake aka yi, shi yace na girka ta daya ga Namra na ta kuka”
“Ayyah Namra na, i'm sorry ba zan sake fita ba dake ba, i love you”
Ta aikawa babyn kiss tana murmushi. Sannan ta tashi ta nufi ɗakinta tana cire ɗankwalin kanta, ɗayan hannunta kuma na ɗauke da new babynta Namra.
ASIM POV.
Be farka ba, sai bakwai da rabi, yana yin sallah asuba ya sake komawa baci,ba shi ya tashi ba sai sha ɗaya na safe, wayarsa dake kusa da shi ya ɗauka ya lalubo number Mardiya dan yau a bachinsa na safe ita yayi mafarki, be wani daɗe sosai yana waya da ita ba, ya miƙe ya shiga wanka.
Sha biyu saura ya shirya ya fita, kai tsaye gidan Hajiya Sadiya ya zuwa, tun kamin ya taso ya tanadi ƙarya da zai mata akan Namra, sai ya tarar bata gidan, mai gadi ya labarta masa tun jiya da dare ta bar gidan wai taje birnin kebi.
Ko kaɗan Asim be jidaɗin hakan da Hajiya tayi masa ba, sai ya zuciyarsa ta soma nuna masa ko dai Hajiya ta yi fushi da shi ne, shiyasa har taje Kebi bata faɗa masa ba, duk da ta faɗa masa zata bashi hutu saboda baƙi zata yi ai bata ce masa zata bar garin ba. Har ya ciro wayarsa ya kirata sai kuma wata zuciyarta ta hanasa, a ganinsa yanzu ba zata sauraresa ba tun da tana cikin fushi ƙara ya bari har sai an kwana biyu sannan ya kira ta, idan bata dawo ba.
Ƴar ƙara wayarsa ta yi, yana duba ya ga alert daga diamond bank saƙon miliyan biyar ya shiga asusun ajiyarsa.
“Wow”
Ya faɗa yana karanta sunan wanda ya aiko masa da kuɗin.
“Yayi Kyau Alhajina”
Ya faɗa cike da tsananin farinciki, kaminɓya ɗora da saƙon daya biyo baya.
“Na aiƙo maka da kuɗi, kazo gobe sokoto ina son ganinka, kuma ka zama mai riƙe sirri”
“Zan zo gobe tun da safe inshallah”
Haka ya mayar masa da amsa, sannan ya rumgume wayar a ƙirjinsa yana dariya har ta fitar hankali. Komawa yayi motarsa ya shiga, yana cigaba da dariya har da jijjiga jiki.
Yana yi ma motar ki kiran Nably ya shigo wayarsa, cikin sauri ya ɗauka yana dariya.
“Hello my second wife”
“Au ba ma nice ta farko ba kenan?”
“Yes karki sa ma ranki zaki zauna ke kaɗai a gidan Asim”
“Ashe kai ba Saurayi ba ne?”
“Saurayi ne kuwa sabo hul, amman bayan ke wata zan ƙara, ko kuma ma akai ku ku biyu a tare”
“Kai da bakinka kake faɗin haka, lallai na yi fushi, na bar mata”
Da sauri ya haɗe hannayensa kamar tana gabansa.
“Sorry my nurul khalbi, wasa nake miki just to get your angry, yanzu dai ya hanya?”
“Au kasan da tafiya na, amman baka kira ka tambaye ni ba”
“i'm sorry dear i'm just kind of busy, In fatar kin sauka Lafiya”
“Na sauka ƙalau idona sai ƙaiƙayin ganinka suke yi ”
“Gani na kan hanya nan da mintuna talati”
“I can't wai to see you”
“The same here”
Yana aje wayar ya ƙara ma motarsa jiya ya nufi wani boutique, dan siyen kaya mai kyau da tsana wanda zai sa yaje gurin gimbiya Nabila.
ABDOOL POV.
Ƙarfe goma sha ɗaya da rabi jirginsa ya sauka Katsina, yana sauka ya kira Ummi ya faɗa mata ya sauka, amman ta ƙi ɗaukar wayarsa, har sai da ya aika mata da saƙo, Sannan ta aiko masa da direba.
Daga filin jirgi zuwa gida tafiyar minti goma sha biyar ce, amman sai yaga ta yi masa tsayi kamar na awa ɗaya saboda zumuɗin da yake na bawa Ummi labarin dake cikin ransa.
Suna shiga harabar gidan farincikin fuskarsa ya ɗaɗa ƙaruwa, ko fakin ɗin kirki direban be yi Abdool ya buɗe ya fito, sai duk sojojin da suke gidan suka maƙe guri ɗaya suna sara masa, hannu kawai ya ɗaga musu ya nufi Babbar ƙofar gidan.
Amira da Haleema na tsaye dinning suna jera abinci Abdool ya shigo da sallama.
Da gudu Amal taje ta rumgume shi.
“Dude i miss you”
“I miss you more”
Kaɗan kaɗan Amira take satar kallonsa tana murmushi, Haleema ma kallonta take tana murmushi dan tasan abunda yake zuciyarta. Fitowar Ummi ne ya ɗago da duka hankalinsu har Amira ta samu damar kallon Abdool da kyau tana auna irin missing ɗinsa da ta yi.
“Ka kuru da baka dawo yau ba ko”
Dariya yayi yana wasa da hannun Amal.
“Ummi ina da labari mai daɗi da zan ba ki, duk da kin katse min uzuri na”
Zaunawa tayi saman kujera tana murmushi.
Sai shi ma ya zauna yana tambayar Amal abunda ya hana ta zuwa makaranta. Lemu Amira ta ɗauko ta kawo masa a gabansa ta dire masa, tana masa sannu da zuwa.
“Yauwa Thank you so much”
Ta jidaɗin kalma nan da yayi mata, bama kamar murmushin da ta gani shimfiɗe a fuskarsa. Cikin natsuwa ta tashi ta nufi dinning dan zuba masa abinci.
Kallon Ummi yayi fuskarsa ɗauke da abunda ke zuciyarsa.
“Ummi kin yi suruka, matar da na taɓa baki labari ina so na samo ta, finally mafarki na zai zama gaskiya...”
Tartsatsa... Suka ji ƙarar fashewar plate mai ɗauke da abinci, wanda Amira ta sake saboda maganarsa da ta soki gadon bayanta, da sauri ta ɗuka tana kwashewa, kamar wacce ta ruɗe, a take hawaye ya fara bin fuskarta, sai dai su basu gani ba kasancewar ta basu bayana ne.
“Ba ki ji ciwo ba?”
Ummi ta faɗa tana ɗan leƙen ta. Sai Haleema ta yi saurin amsawa.
“A'a plate ɗin ne kawai ya fashe”
Ummi ta maida hankalinta gurin ɗan ta.
“Im happy for you Son, na daɗe ina jiran wannan ranar, you have no idea how happy you make me, sai dai ban gane wacce kake magana ba akai kam ba”
“Ye... ”
Ringing ɗin da wayarsa ta yi ne ya hana shi ƙarasa maganar sai yayi saurin tashi ya nufi wani ɓangare na falon yana amsa wayar.
“Salim”
“Sir mun bincika, Manjo Usman Zamau yana sokoto da zama a unguwar clapperto, yana da mata biyu da ƴaƴa goma sha uku Namra ita ce ta goma, kuma ainahin sunan ta shi ne Khadija, ta yi makaranta a dan fodio tana level 300 aka yi mata aure, kuma har yanzu tana gidan aurenta zaune, facebook username ɗin ta Khadija Usman Zamau instagram kuma Namra's, haka yake a twitter da snapchat”
“Amman ba ku bincika zaman auren ta ba? Har yanzu tana da aure?”
“Binciken mu ya nuna har yanzu tana da aure kuma tana a garin katsina da zama, sunan mijin da take aure Ibrahim amman anfi kiransa da Asim”
“Thank you”
“Your Welcome Sir”
Wayar ya ƙurawa ido yana mamakin yadda Namra zata masa ƙarya, bayan ya tambaye tsakaninta da Allah, taya aurenta zai mutu kowa bai sani ba, hakan yana mufin ƙarya ta masa kenan ko kuma akwai abunda take ɓoyewa.
Juyowa yayi yana ƙoƙarin ɓatar da mamakin dake fuskarsa ya kalli Ummi yana tahowa ya ce.
“Wani aiki ya tashi Ummi Ana nema na a Kaduna yanzu yanzu nan”
“What?”
Ummi ta faɗa da mugun mamaki. Shi kuma ya ɗan ɗaga gira yana kallon Amal.dake zumuɗin labarin daya fara badawa.
Hello habibaties nasan kuna haƙuri da ni dan Allah ku ƙara haƙurin. Wallahi abubuwa ne suke min yawa, ga kuma rashin wutar nepa a gusau, yau four days babu wuta, sai an tashi engine ne muke samu mu saka. Idan kuma ka matsa za'a ce sai ka biya na Mai 😂 you know how our grandma's are, sai haƙuri 😂
Love you all fisabilliah ♥️🌹🌺❤
[7/18, 8:12 PM] Khadeeja Candy♥: *71*
Ɗauke kansa yayi daga kallon da yake ma Amal ya kalli Ummi, irin babu zacen wasa a kalamansa.
“Nima sai da na ce miyasa ba su bar ni nayi aikin ba acan ba sai yanzu da na dawo”
“Abdallah ka ce min kun samu hutu fa? Aikin me zaka je yi yanzu?”
“Wai General ne zai zo daga Abuja zuwa Kaduna gobe, kuma dole ne muje. Bari naje ya canja kaya gobe da safe ai zan dawo”
Be jira abunda Ummi zata ce ba, ya nufi ƙofar fita yana lalabar number Salim dan ya sama masa jirgin da zai koma Kaduna yanzu ko da Yammar nan.
Ummi dai da kallo Mamaki ta bishi, ta fi kowa sanin ɗanta dan haka ta san ba aiki ne zai maida shi Kaduna ba, sai dai wani abun na daban, kai ta girgiza tana kallon Amal data wani turo baki.
“Be ma ƙarasa mana labarin ba”
Ummi ta miƙe tsaye ta nufi kitchen tana faɗin
“Uhnm kya ji da shi”
AMIRA POV.
Tana gama kwashe plate ɗin da ya fashe ta zuba a shara, sai ta nufi ɗakinta cikin wani irin kuka marar misaltuwa.
Saman gadon Amal ta faɗa ta kife tana rera kukanta a hankali yadda wani ba zai ji.
“Shikenan na rasa komai, wata yake so ba ni ba, shi ma na rasa shi”
Tausayin kanta take da kanta tana tunanin irin rayuwar da zata yi nan gaba. Bayan ta rasa duk wani abun da zai iya saka ta farinciki. A hankali Haleema ta turo ƙofar ta shigo fuskarta ɗauke da tausayin Amira,wanda har zuciyarta haka ne. Kusa da ita ta zauna ta kai hannu ta taɓa ta.
“Ki yi haƙuri Amira, ni kai na ban san haka zai faru ba...”
Da sauri Amira ta ɗago ta kalleta da idonta da suka gana canja kala saboda kuka.
“Ke ma kin yarda na rasa ɗan uwanki ko? Babu wani abun da za kiyi? Dan Allah ki taimaka min Haleema kema mecece zaki iya shiga a halin dana shiga, kin san irin abunda nake ji, Wallahi ina son Yaya kuma tsakani da Allah zan zauna da shi, idan har na ci amanarsa na yarda amanar Allah ta ci ni, na rantse da Allah ba zan cutar da shi ba”
Kuka take sosai zuciyarta a narke, ta kama hannayen Haleema ta riƙa tana mai jin kamar Haleema ta yi mata maganin damuwarta.
Cikin kuka Haleem ta ce.
“Babu wani taimako da zan iya yi miki Amira, Big Bro babu mai saka shi dole idan ba Ummi ba, kuma idan har ya nuna baya so ita ma bata so, babu abunda ya cutar da ke kamar zama ba a gurin iyayen ki ba”
“Ba zan iya komawa ba, ban san yadda zan yi na koma ba”
Ya zube ƙasa zaune tana rushewa da sabon kuka. Haleema ta riƙa ta tana bata haƙuri. Kamin ta tashi cikin ɓacin rai ta nufi hanyar fita, Amal ta samu tsaye jikin ƙofar ta yi wani wuƙi-wuƙi da ido.
“Ummi tan kiran ki”
Ta faɗa a sagarce, sannan ta falfala da gudu ta nufi ɗakin Ummi ɗin. Haleema ta rufa mata baya tana share hawayenta. Ƙusƙus ta tarar Amal na yi gurin Ummi, hakan ya tabbatar ma da Haleema Amal ta ji abunda suke cewa.
Meesha na gaban maduba Ummi tana ɗanɗasa kwaliya ita da Fauza, dan su basu ma san Abdool ya dawo ba.
“Ummi ga ni”
Ta faɗa yayinda take ƙoƙarin zama kusa da ita.
“Gulma ta kuke yi?”
Da sauri Haleema ta sake kallon Ummi baki sake, kamin ta maida dubanta gurin Amal.
“Amman yarinyar nan munafuka ce Wallahi, gulamar ta kika ce na yi, aiko sai na miki ɗan banzan duka a gidan nan”
Ummi ta katsa mata tsawa.
“A'a akan me? Maganar me kuke ke da ita har kuke kuka?”
“Walahi akan big bro ne, dan ta ji ya samu mata shine take kuka ina bata haƙuri”
“Dan ya samu mata sai aka yi me?”
“Kin san son shi take sosai wallahi”
“Amman dai Haleema baki da hankali, ke ko a mafarki aka ce yayanki zai aureta idan kika farka ai kya nemi tsarin Allah, macen data zauna da yan fashi? Kika san ciki nawa ta zubar? Baki san zaman ta a nan ma it very risk ba”
“Haba Ummi ciwo ƴa mace na ƴa mace ne, yanzu idan nice a wannan hali zaki jidaɗi? Ba ita ta ƙaddaro ma kanta ba, kuma ta yi sadaukarwa ma Big Bro ita ta cancanci ya so ta wallahi”
Ummi kasa magana ta yi saboda mamakin furucin Haleema. Meesha ta taso daga gaban madubi da take zaune tana faɗin.
“Kin san me Ummi zata iya saka mana guba duka mu mutu idan har ta ji Big Bro ba zai aureta ba, ƙila ma turo ta aka yi, ta ina ma.taji Yaya ya samu mata? Kodai ta ga alamun ba zai so ta ba ne”
Fauza ta amsa.
“Kuma Wallahi irin waɗan nan ba tsoron kisan kai suke ba, tun da sun saba”
Ran Haleema ya ɓace sosai.
“Ku daina judge mutane ne, hakan be da kyau, Allah ma yana karɓar tubar bayinsa balle kuma mu....”
Shigowar Abdool ne yasa duk suka warsar da maganar, Fauza da Meesha suka fara ɗaukin shigowarsa tare da masa sannu da zuwa.
“Ai kune ba ku san ya dawo ba, mu tuni muka sani har ya ba mu labarin matarsa da zai aura”
Ya ɗaga gira ɗaya yana kallon Amal, ita kuna ta shigar da kai jikin Ummi dake dariya, ita ala dole ga auta.
“My girls ku fita za mu yi magana”
Ya faɗa yana ƙoƙarin zama a kujerar dake fuskantar gadon Ummi. Ba musu duk suka fita har Amal uwar son zancen dan bata ga alamun wasa a fuskarsa ba balle ta tsaya.
“Maganar gaskiya Ummi ba aiki zani ba, gurin yarinyar nan zan koma, kawai ki min addu'ah, gobe da safe zan dawo”
“Na gama karantar ka sarau Lamiɗo kallon ka kawai na ke yi. Allah ya kai ka lafiya, kuma a gaishe min ita sosai da sosai”
‘Ai ba gaisuwa ba, ni kaina ban san makomata ba’
Zance daa ya faɗo masa kenan a rai kamin ya ɗago ya saurari zancen da Ummi ta ɗora da shi.
“Dan Allah ka nemo iyayen yarinyar nan, idan ba zata iya zuwa ba, su suzo su tafi da ita”
“Ummi laifin wa? Idan na yi magana ai cewa kike na ɗaga mata ƙafa”
“Ai ba ƙafa ba komai ma.an ɗaga mata, yanzu kam ya kamata ace tana gaban iyayenta”
Miƙewa yayi tsaye yana faɗin
“Don't worry Ummi, if she planning something evil, za a sanar da ni, ai akwai mai kula da cctv camera. A min addu'ah jirgin mu zai tashi nan da ten minutes”
“Allah ya kiyaye ya kai ku lafiya”
Tasowa ta yi ta suka fito tare da shi yana labarta mata maganar da suka yi da Mai Martaba.
Ko da ya isa airport sauran minti uku jirgin ya tashi, abun ka da manya a take aka masa checking ya wuce.
Be da sukuni har sai da jirginsu ya sauka garin Kaduna, yana sauka airport yayi waya daga Abuja, suka kuma suka yi waya a kaduna, cikin minti ashiri sai ga direba in military uniform sun zo ɗaukarsa.
A cikin motar ya sha ruwa, kamin ya buɗe biscuit ya ɗan ci kaɗan yana faɗa musu inda zasu kai shi. A masallaci unguwar ya ce a aje shi, suna yin parking da sauri wani ya fito daga cikin motar yazo ya buɗe masa yana sare masa, umarni ya basu na suje sai ya nemesu. Ba musu suka sake tsara masa suka koma cikin motar suka juya. Yi yayi kamar be kula da mutanen da suke kallonsa ba, yayi alwalarsa ya bi jam'i, har aka gama sallar kowa da abunda yake faɗa, wasu wai ya zo bincike ne, wasu kuma wai akwai wanda zai kama, shi dai yana gama sallah la'asar ya kanyar kwanar da zata sadashi da gidansu Lamido,daman daga masalacin zuwa cikin gidan babu wani nisa sosai. Hango mustafa da yayi yasa shi sauri juyawo ya ciro wayarsa a aljihu ya neman number direban Mai Martaba da yake gidansa da suka sauka da ke Kaduna.
Cikin mintuna da basu bi goma sha ɗaya ba sai ga direba ya iso, be faka ko'ina ba sai gaban Abdool da sauri Abdool ya buɗe ya shiga, yana nuna masa inda zaije.
Mustafa na zaune gindin wani icce yana kallon motar har suka faka ta dai-dai ƙofar gidan su Lamido. Ya maida hankali sosai da son ganin wanda zai fito daga motar, sai kawai yaga baƙuwar fuska ta fito daga gidan gaba mazaunin direba yana buga ƙofar giɗansu Lamido.
“Waye...”
Suka amsa daga can ciki kamin ɗan uwani ya fito waje ganin mai buga ƙofar.
“Shiga ciki ka ce Abdallahi daga Katsina yana sallama da Namra”
“Toh ya juya da gudu ya koma”
Shi kuma direba ya juyo dan mayarma da Lamido saƙo.
“Wai Ance bata nan”
Yaron ya faɗa yana tsaye jikin ƙofar gidan. Abdool ya buɗe motar da kansa ya fito.
“Kije ka ce idan bata
Book Chapters
Chapter 1Chapter 2Chapter 3Chapter 4Chapter 5Chapter 6Chapter 7Chapter 8Chapter 9Chapter 10Chapter 11Chapter 12Chapter 13Chapter 14Chapter 15Chapter 16Chapter 17Chapter 18Chapter 19Chapter 20Chapter 21Chapter 22Chapter 23Chapter 24Chapter 25Chapter 26Chapter 27Chapter 28Chapter 29Chapter 30Chapter 31Chapter 32Chapter 33Chapter 34Chapter 35Chapter 36Chapter 37Chapter 38Chapter 39Chapter 40Chapter 41Chapter 42Chapter 43Chapter 44Chapter 45Chapter 46Chapter 47Chapter 48Chapter 49Chapter 50Chapter 51Chapter 52Chapter 53Chapter 54Chapter 55Chapter 56Chapter 57Chapter 58Chapter 59Chapter 60Chapter 61Chapter 62Chapter 63 Chapter 64Chapter 65Chapter 66Chapter 67Chapter 68Chapter 69Chapter 70Chapter 71Chapter 72Chapter 73Chapter 74Chapter 75Chapter 76Chapter 77Chapter 78Chapter 79Chapter 80Chapter 81Chapter 82Chapter 83Chapter 84Chapter 85Chapter 86Chapter 87Chapter 88Chapter 89Chapter 90Chapter 91Chapter 92Chapter 93Chapter 94