yinsa da ke amman ke baki ga, ina kula da abun nan da Namra ta yi kamar daɗi yayi miki, ba zan ɗauka ba kar bakin ki ya sake furta mummun kalma akan ƴaƴana!”

Ta riƙe baki.

“Alhaji kai kake faɗa min wannan maganar akan Namra? Daga na faɗa maka gaskiya har kace wai bana son ta ita da uwarta? Kuma ka ce baka da so na saboda ƴarka? Anya banza matar nan ta barka Alhaji”

“Ba banza ta bar ni ba, ta kula da ni fiye da yadda kike tsammani, dan tana son ki ke da ƴaƴanki, ba kamar yadda kike nuna mata ba, kuma daga yau sai yau, kar wani munafurci da wata magana marar daɗi ta sake fitowa bakinki akan Ƴaƴa ko wannan matar tau a bakin auren ki! Kar wacce ta aake tadarmin fitina yadda na ga dama haka zan yi a gidana”

Mutuwar tsaye Hajiya Barau ta yi a gurin, tana mamakin Abbah ta ya juye kamar ba shi ba, wai yau shi yake faɗa mata wannan maganar, har yake cewa bakin aurenta. Uffan bata yarda ta sake cewa ba, ta nufi ƙofa cike da nauyin jiki fice sun-sun-sun, hannayenta a baya tana jin kamar an ɗora mata dutse saman kai.

NAMRA POV.

Cikin falo suka riƙa hugging ɗin juna ita da ƴan'uwanta, suna jin kamar su haɗe juna ita da su, sai faman kuka suke. Anty Amarya ta fito daga bedroom ɗinta fuskarta da dariya ta ce

“To ko haɗe ta zaku yi?”

“Anty Faɗa mana yadda aka yi ta yarda ta biyo ku kuma har Abbah ya amince”

Aisha ta faɗa tana laƙƙame da wuyan Namra.

“To ku sake ta taje ta yi wanka ta shirya zan baku labarin komai”

Aisha da Hindatu ne suka saketa yayinda Maryam ta laƙƙame hannunta suka nufi bedroom tare. Bayan sun tashi Zinatu ma ta tashi ta nufi part ɗin Mahaifiyarta. A sannan ne Anty take tambayarsu yaushe Zinatu ta zo.

“Tun ranar da kuka tafi, wai faɗa tayi da mijinta ya ce taje gida, shi ne wai ta baro masa yaransa”

“Subhallahi, miya haɗa su haka?”

“Wallahi bata faɗa ba, ai kin san Hajiya ba zata bari ta faɗi gaskiya ba, dan ita Hajiya ma ce mana ta yi bikin Maryam ta zo”

“Tau Allah ya sauwaƙe yayi mata mafita, ku tashi ku girka mana abinci dan ni dai ba zan ci taliya ba”

Hindatu ta mike tsaye tana dariya.

“Komai kuke so za a muku, sai ku ba mu labarin abunda ya faru”


A ɗaki da suka shiga Namra take labartawa Maryam irin abunda Asim yayi mata, da yadda ta yi rayuwa gidansu Lamido da kuma haɗuwarta da Abdool ya yadda ya haɗa ta da su Anty.

“Ke ni wallahi na jidaɗin da auren ya mutu kuma cikin ya zube, dan zai iya cewa ya maida ki ko dan ɗansa ko kuma ya ce zai maida ki kamin ki cika idda amman yanzu ba ciki ba goyo dole ya ƙyale ki dan ubansa, tsinan nen banza”

“Ba laifinsa ba ne Maryam, laifina ne a gareni ya ga wannan damar kuma ni na zaɓe shi sama da iyayena. Amman yanzu Alhamdulillahi tun da Abbah ya ƙarɓe ni”

“Gaskiya nima na jidadin hakan ciwon Anty zai warke, kuma za'ayi biki da ke, amman dai wannan yaron son ki yake ko?”

“A'a ba so a tsakanin mu, bikin wa za'ayi?”

“Bikina mana ni da Hindatu sati mai zuwa za'a ɗaura aure, Wednesday za'a fara biki”

“Amman shinw ba a faɗa min ba?”

“To ba kin zaɓi wasu family sama da mu ba”

“Haba Maryam, ai komai na zama ni ƴar'uwarku ce jininku, be kamata ku min haka ba”

Maryam ta laƙƙamo kafaɗarta tana dariya.

“Ai yanzu kin dawo ma hanya, komai da ke za'ayi Maman su Babanmu”

Ɗan Murmushi Namra ta yi ta miƙe ta shiga wanka. A wunin ranar haka suka riƙa treat ɗin Namra kamar wata sarauniya, sai faman dare-dare suke suna rumgume ta. Suna cikin haka sai kawai ta fashe musu da kuka da kuma dariya lokaci ɗaya.

“Ban taɓa tunanin rayuwa zata dawo haka ba, i miss my family a lot”

Hannu Aisha tasa ta share mata hawayenta, sannan ta miƙa mata wayarta da ke ringing.
Namra na karɓa ta zaro ido.

“Asim ne”

“Asim”

Maryam ta amsa da ƙarfi, kana ta ce.

“Ba ni shi”

Anty ta ɗaga mata hannu

“No barta ta yi picking mu ji me zai ce”

Sai da ta yi ajiyar zuciya sannan ta danna picking ta kara a kunne.

“Hajiya Namra kenan! Ina kika shiga na yi nemanki cikin garin Katsina da kewaye baki ciki”

“Ina kake tsammanin zan kasance bayan gidan Ubana”

“bakya giɗan ubanki kam dan na bincika aka ce min baki can, faɗa min inda kike je? Karki damu da tambayar da nake miki ina son naji lafiyar Baby na ne”

“Bka da wani Baby Asim saboda ka zaɓi rabuwa da ni ne saboda shi”

“Yanzu kuma ina son abuna sai yaya?”

“Amman babu kaskantacce wulaƙantacce wawa kamar ka Asim, yanzu da baka da kunya zaka kira ni ka ce min wai lafiyar cikin ka zaka ji?”

“Bana da damar hakan ne? Ai Allah ya ɗora min haƙƙin kula da ke har sai kin haihu, kuma dole ne na bincika ko da kina da buƙatar wani abun sai a kawo miki”

“Kai har kana ganin ka yi arzikin da zaka iya ɗaukar nauyin cikin ka, ka daina wahalar da kan ka dan ni yanzu babu ciki a jikina kuma karka sake kirana”

Tana kaiwa nan ta kashe wayarta tana huci. Anty bata muƙatar ta faɗa mata dalilin kiran nasa dan ta fahimci komai. Ko minti biyu ba tayi ba ya aiko mata sako.

_Wallahi duk kika zubar min da ciki sai mun shiga kotu da ke_

Namra na gama karanta ta nunawa Anty.

“Karki sake ɗaga wayarsa karki sake ce masa komai, har sai mun ji abunda Abbah ki zai ce”

Maryam ta yi ƙwafa.

“Wallahi samun family masu haƙuri irin wannan yana da wahala, wlh da wani guri ne da sai an wulaƙanshi kam uban nan...!”

Anty ta nuna ta yatsa.

“Maryam ki cire wannan zafin ran da kike da shi, aure zaki yi kuma mace kike, abunda duk haƙuri be baka ba rashinka be baka shi, duk wanda ya ci amana kin taɓa ganin ya ƙare da kyau, kar dai karka yarda ka ci amanar wani barshi shi ya ci amanar ka, ki zuba masa ido ki gani ba zai ga da kyau ba”

“Amman wani lokacin mutun yana buƙatar gargaɗi kai, da wannan haƙuri kike ta cutar da mu da kan ki, gashi nan a gida kullum mine ba mu da gata, komai na gidan nan Hajiya ce take da iko da shi, da an yi magana sai ki ce ayi hakuri, fisabilliah har na waje kuma sai a riƙa bari suna takamu”

Ta ƙarasa tare da miƙewa tsaye ta nufi bedroom ɗinta.

“Ke kan Maryam Allah ya shiryaki, da wannan rayuwar babu inda zata kai ki, ni ban san inda kika ɗauko wannan baƙin hali ba, ni dai ba haka na ke ba”

Bayan sun yi Sallah magariba, Anty ta shiga part ɗin Abbah da abinci a hannunta ta tsakura masa labarin abunda ya faru.
Washe gari Namra ta daɗe tana bachin safe saboda gajiya da kuma kwanciyar hankalin yau tana gida bata da wata matsala. Maryam ce ta shigo ita da Aisha suka tashe ta wai zasu je siyen wasu kayan kitchen, kuma ta fito da Yasmin a falo tana jiranta. Mulmula ta riƙa yi saman gadon sai da suka fice, sannan ta miƙe tsaye tana miƙa ta shiga bathroom, bakinta ta wanke, a nan take kallon kanta a madubi ita kanta ta san ta chanja kamar ba ita gaba ɗaya ta fita daga kamamninta, ta yi baƙi sosai idonta sun ƙara fitowa.

“Namra ko har yanzu baki tashi ba”

Jin muryar Yasmin yasa ta yi saurin barin gaban madubi ta nufo ƙofar fita tana zumuɗin haɗuwa da Yasmin.

“Anty”

Ta faɗa jikin Yasmin suka rumgume juna.

“Ashe kin ji na dawo”

“Eh Gwaggo ce ta faɗa min komai. Ban jidaɗin abunda ya faru ba Namra sai dai dawowarki ta min daɗi, saboda Uzair, ko da baki zo ni zan je har inda kike”

Gaban Namra ya faɗi ta mata wani kallo mai cike da mamaki.

“Uzair kuma, miya faru?”

Yasmin ta kama hannayen Namra ta riƙe.

“Ina son ki faɗa min tsakani da Allah, da gaske kin taɓa kama Uzair yana luwaɗi?”

“Dan Girman Allah Anty ki rufa in asiri na dawo yanzu cikin family na kuma saki sake tayar min da wannan maganar? Ko so kike Abbah ya sake kora ta ne?”

“Ko kaɗan, Namra kawai ina nema miki justice”

“Justice for what...?”

“For what Uzair did to you, shi ya ɗauke ki ranar da aka ce kin gudu kin je gurin Asim”

Idon Namra ya cika da ƙwalla.

“Waya faɗa miki?”

“Shi ya faɗa min da kansa, kuma yayi rape ɗinsa da kansa Namra, na rasa yadda zan yi abun yana ta ci na a rai, na kasa faɗawa kowa, amman na yi ma kai na alƙawari sai na shigar da ƙarar Uzair kotu da kai na, akan ki sai na nema miki haƙƙinki, saboda ɓacin suna da yayi miki kuma yasa duniya ta zargi kin gudu da saurayinki”

Kai Namra ta girgiza masa.

“Na yafe masa, dan Allah dan Annabi ki taimaka min ki bar wannan maganar”

“Kin tuna lokacin da Amira ta gudu? Shine sila saboda ke aka yi ma maganin sai ya koma kan Amira saboda ta ci amanar ki, Namra you deserve justice”

“Ke da kan ki zaki shiga kotu ki ƙalubalanci mijin ki?”

Cikin kuka Yasmin ta ce

“Yes Goyon bayan ki kawai na ke nema”

Namra ta yi saurin miƙewa tsaye fuskarta da hawaye.

“Zan yi tunani a kai, just go please”

Bata mata musu ba, ta share hawayenta ta mike tsaye ta fice. Tana fitowa falo ta karɓi Little Namra hannun Anty ta fice, ko sallama bata yi ma Anty ba. Anty na ganin hakan ta san ba lafiya dan haka ta tashi ta nufi ɗakinta inda Namra take.



ASIM POV.

Yana fita gidan Hajiya Sadiya, ya kira Matdiya ya faɗa mata ta faɗawa mamanta yau da dare zai zo ya gaishe ta. Haka kuwa aka yi, dare na yi yaje yayi wanka ya shirya cikin tufafi na alfarma, ya shiga motarsa da ya sa aka wanke masa, ya nufi wani boutique ya haɗu mata sabulai da mai da turaruka masu ɗan karen tsaɗa sai da ya kusa ciki bayan motarsa sannan ya shiga ɓangaren kayan ciye-ciye yayi leda uku, bayan ya biya ya kama hanyar gidansu.

Tass ya samu ƙofar gidan yau kam an share ba kamar kullum ba, zamansa yayi cikin mota ya kira ta a waya, ya shaida mata yana nan waje. Yau kan ta fi masa kyau fiye da kullum dan ta chaɓa ado da sari kamar wata amaryar india. Sama-sama suka gaisa yana mata wani kallo mai cike da alamar tambaya, ita kuma sai wani noƙe kai take ita ala dole tana jin kunya. Sannan ta yi masa iso, suka shiga cikin gidan tare. Ya raina gidansu sosai dan shi gani yake yanzu ya wuce irin wannan rayuwar. Bayan ya gama gaisawa da mahaifiyarta ya aje mata dubu hansi, sannan shiga ko wane ɗaki na gidan yana gaisawa da su sannan ya aje musu dubu goma. Su kan sai murna suke suna yabawa Mardiya kan ta yi miji, masu jin zafi suna ji, dan wasu har sun soma maganar ai yadda yayi ma Namra ita sakinta zai yi da ana kwana biyu.

Bayan sun fito yasa yara suka kashe kayan da ke bayan motarta suka shigar ma Mahaifiyar Mardiya da su cikin gida. Ita Mardiya ji tayi kamar ta ɗauke shi ta haɗe saboda ƙaunarsa dake ƙara mamaye mata zuciya, ko a mafarki bata zaci mutum mai kuɗi kamar Asim zai so ta ba, balle ma har ya ce zai aureta. Sun sha fira sosai sai kusan ƙarfe goma sha ɗayan dare sannan suka yi sallama.

A daren da farinciki suka kwana daga ita har Asim, har yana jin ba zai iya bari ta jima sosai ba. Sai dai abunda ya tsaya masa a rai miyasa bata nuna masa dangin ubanta ba? Ko lokacin da ya ce zai turo cewa ta yi bari ta faɗawa Uncle ɗinta.

“Idan ma bata da uba miye ruwana tun da ita nake so ba ubanta ba”

Ya faɗa yana fesa turare a jikinsa. Sannan ya ɗauki glass ya saka ya ɗauki makullin motarsa ya fice. Kai tsaye gidan ƙanen Babansa ya nufa, daman yasan a irin wannan lokacin yana gida kamin yaje gurin da yake aikin ƙira. Har ciki gidan ya shiga, sai qani ƙyaƙƙyami yake da ginin ƙasa, ya gaisa da matansa sannan suka fito waje suna tattauna maganar auren da Asim yake labarta masa na Mardiya akan maganar tura magaba, a nan suka kitse maganar sati mai zuwa sai nemi sauran ƴan'uwa suke je su nema masa aurenta, sannan kuma ya ɗora masa da maganar gidan da aka ce masa akwai amman milinya takwas ne.

Gidan ba shi da nisa sosai da unguwar hakan yasa suka ƙarasa da mota aka kira Mai gidan ya shiga da Asim ciki ya ga komai. Ya yaba da gidan sosai, komai na cikin gidan sabo ne ga sabo fenti ga fulawowi daman irin gidan nan ne da ake ginawa sababbin a saida. Ko tayawa Asim be yi ba, suka kutse magana akan idan ya dawo daga sokoto zai zo tare da shedu a bashi makulin gida takardu shi kuma ya bada kuɗi. Mutunen sai godiya yake ganin Asim be taya ba ya amince zai ba shi kuɗin. Bayan sun dawo ya aje Ƙanen Baban nasa ya miƙa masa dubu ashiri, sannan ya kama hanyar gidan Hajiya Sadiya yana aikawa Namra kira.....


Tsaki yaja bayan ya kashe wayar, lallai ma yarinyar nan ta raina masa hankali, shi zata yi ma ɓoyun ɗansa? Allah yasa ma da gaske ta zubar da cikin nan ta ga yadda zai yi da ita ƙut! ya yi ƙwafa.

Yayi mamakin ganin Hajiya Sadiya a gidan nata, bayan yasan a wacan take zama saboda ƴarta. Bayan sun gaisa ya zauna saman kujera yana kallonta.

“Mun yi waya da Alhaji yace na same shi sokoto, kuma na samu labarin Namra tana sokoto har ma na yi waya da ita, amman kin san ba lallai ba ne ta amince ta dawo gidana ba ko?”

“Nasan da hakan shiyasa ka ga na dawo nan gidan ai, nasan zaka zo nema na, abunda nake so da kai ka yi ta try har sai kaga ta aminci, idan kuma hakan be samu ba, to zan baka abunda zaka bata, kuma ka tabbatar ya kai ga bakinta, ma'ana ta ci”

“Mi zaki ba ni?”

“Ina zuwa”

Ta miƙw tsaye ta nufi wani bedroom. Shi kuma ya ƙurawa pop ido kamar yau ya fara ganinsa.

“Wallahi duk kika zubar min da ciki ko? Hmmm, Allah yasa ma Ubanki ne ya zubar da shi ta yadda zan fi jindaɗin shari'ah da shi...”

Fitowar Hajiya Sadiya ce tasa ya mai da dubansa gareta yana kallon farin ƙyalen da ke hannunta. Tana ƙarasowa ta warware ƙyalen ta miƙa masa apple ja.

“Ka tabbatar ta ci wannan apple ɗin ko da kaɗan ne, amman sai idan ta ƙi yarda ta koma ɗakinta”

Ya ƙurawa Apple ɗin ido

“Kar fa wani abu ya same ta, i mean kar ta mutu, akwai baby na a jikinta”

“Babu abunda zai same ta, ka yi yadda na ce kawai”

“Okay”

Ya miƙe tsaye tare da saka apple ɗin a aljihu, ya fice. Be yi nisa da barin gidan ba Nably ta kira shi, amman sai ya samu kansa da ƙin ɗauka shi kwata-kwata yanzu ta fita ransa, Mardiya ce on top.





KU YI HAƘURI DA WANNAN🙏

*Ku yi ta yaudarar kan ku da sunan wata ta siya ta ara muku ku karanta, idan mun je can inda baki be magana zamu tsaya gaban Allah ni da ku ya mana hukunci.*

HILAL POV.

SIX MONTHS LATER...
Suna jin ƙarar tsayawar Motar Dadynsu suka fita da gudu suna masa oyoyo. Zaune suka same shi cikin motar yana waya, hakan yasa Ezzah zagayawa a front seat ta zauna tana jiran ya gama wayar ta fara masa complain.

“Dady muna dawowa daga makaranta Mama Teema tasa mu wanki”

Yana sauke wayar daga kunnensa kenan, ta soma labarto masa abinda ya faru yau. Wani kallo yake mata, irin kallon nan na ɗa da ƴa, kamin ya kai hannunsa ya kama fuskarta ya riƙe.

“Ezzah kin yi ƙanƙanta da irin abubuwan nan, kullum sai kin ce Teema ta miki kaza bla bla bla, wannan sam be dace da ke ba, babu abunda Teema zata muku sai tarbiya, ƴar'uwarki bata taɓa faɗar an mata wani abu ba sai ke”

Ta turo baki zata masa magana da kuka a lokaci ɗaya.

“Dady ni bana son ta, a kawo mana Mummie mu”

“Ba za'a kawo ba, kuma kar bakin ki ya ƙara furta kalmar ƙi ga matata, ke kowa ai baki so, har Kalsoom ba haka kika mata ba? Saboda ku Hajiya tasa na auri Teema yanzu kuma ki bijiro min da wannan maganar! Kar na sake ji”

Ya fita daga motar ya kama hannun Ulfah, sannan Ezzah ta fito ita ma tana share hawaye ta rufe masa motarsa, ta rufa musu baya.

Teema na tsinkayarsu dan tana tsaye jikin window ne, sai dai ba zata iya jin me suke cewa ba. Tana ganin ya doso ƙofar falon sai ta bar gurin da sauri ta shige bedroom ɗinta ta zauna bakin gado ta soma ƙirƙiro kuka. Tun da ya saka kafarsa a falon ya ji be ji motsin Amaryarsa ba ya saki hannu Ulfah ya doshi bedroom.
Zaune ya same ta bakin gado tana rusar kuka, zama yayi kusa da ita cikin damuwa, dan yasan dalilin kukan nata baya buƙatar tambayarta.

“Sau nawa zan faɗa miki ki yi haƙuri Teema? Wasu ma sai da suka shekara ashiri a gidan miji sannan Allah ya ba su haihuwa, balle ke da baki yi shekara ɗaya ba ma?”

Ta ɗago kai ta dube shi.

“Hilal ina tsoron kar a'ce ba zan haihu ba ne gaba ɗaya, tun da na zo gidan nan ko ɓari ban taɓa yi ba”

“Idan Allah ya ga dama zai baki just be patient, wani lokacin abun mutum nesa yake, na shigo da farinciki kuma kin rusa min shi”

“Ka yi haƙuri rai na ne yake ɓaci”

Ta share hawayenta, har ga Allah wannan matsalar tana damunta, sai dai ta kan yawaita yi ma
Showing 222001 words to 225000 words out of 280121 words