su.
Har ƙauyuka suna shiga su wayarda kai, abun yanxu yayi gaba har nijar da sudan ghana sukan leƙa wani lokacin domin halartar taron ƙarawa juna sani ko kuma na ƙungiyoyin duniya qani lokacin ma.har.
Ta tattara rayuwar aure ta aje gefe, duk kuwa da irin tayin da Alhaji bashir da kuma wasu mazan suke mata, bata son abunda zai sake ɗaga mata hankali a yanzu, shiyasa bata kawowa kanta zancen aure a kusa.
A duk lokacin da ta tuna da Kalsoom ce take riƙe da ƴaƴanta sai ta yi ma Allah godiya, domin bata san Kalsoon ƴar'uwa ba ce sai a yanzu, tana ƙoƙari gurin ganin ta bawa yaranta tarbiya, basa mata complain ɗin sun rasa wani abu ko an musu wani abun sai ɗan abunda rai ba zai rasa ba, sai yanzu ta tabbatar good people are still exist, ba ko wace abokiyar zama ce kishiyaba wata kan ƴar'uwa ce.
Bata da matsala ta ko ina a yanzu, sai dai tana nadamar abunda duk ta tuna sai baƙinciki ya rufeta, wato sanadin wannan ciwon nata, a duk lokacin da aka tambaye ta dalilin wannan ciwon nata ta kan ce ta same shi ne ta hanyar ƙarin jini da aka mata, domin kawai ta kare kanta.
Shekara biyar da shiga ƙungiyar zuwa yau rayuwarta ta zama abar kwatance, rayuwarta darasi ce ga duk mace mai irin rayuwarta, ko kuma halinta, ita kanta yanzu ta koyi abubuwa da yawa na rayuwar duniya da kuma zama da mutane.
Ko da aka yi birthday ɗin Izzah tana Abuja gurin wani taro, washe garin ranar da ta dawo taje gidan ta kai musu tsarabarsu da kuma birthday gift ta bawa Izzah.
Ta jidaɗin yadda ta same su, baka iya banbance tsakanin Ƴaƴan Kalsoom da nata a gurin Kalsoom wato Amal da Rafiq da Husna, sam mutum ba zai iya cewa su ne ƴaƴan Kalsoom ba, sau da dama zata bawa su Izza abu ta hana ƴaƴanta.
Bata daɗe a gidan ba duk da ƴaran sun so haka, amman ta ƙi a duk lokacin da taje gidan haka take bata daɗewa take fitowa.
Ko da iso gidanta uku da rabi yayi, dan haka tana shiga bathroom ɗinta ta yi alwalar la'asar ta fito ta shimfiɗa sallaya ta saka hijab taja carbi tana la'zimi kamin lokacin tada sallah yayi.
Wayarta ce tayi ƙara daman ta ji tsayawar mota a harabar gidanta, sai kawai ta miƙe tsaye ta nufi falo ta buɗe masa ƙofa.
“Hajiya...”
“Alhaji Bashir”
Shigowa yayi yana faɗin
“Aiko na taki sa'ah dan ban tsamaci kina garin ba”
“Jiya na dawo”
“Mashallah ya Abujar?”
Ya tambaya yayinda yake ƙoƙarin zaunawa.
“Abuja sai hamdallah, ya aikin naku”
“Aiki da godiya, iv na zo na kawo miki”
“Ba dai na aurenka ba ko?”
“Shi mana ba kin ƙi ni ba”
“Dana ƙi ka ya hana dubu su soka ne?”
“Cikin dubun ai na ƙawo ƙoƙon barata a gareki amman kika ƙi yarda, kuma ni wallahi ko a yanzu kika yarda zan aure ki”
Ruwan tsanyi ta dire masa tana dariya tare da kai hannu ta karɓi iv ɗin.
“Lallai mutumen da gaske kake, budurwa ce ko bazawara”
“Budurwa ce yarinya ce ba zaki sha wahala gurin kishi da ita ba”
“Ai ni na yafe kishi da kowa, sai dai ina fatar tasan halin da kake ciki”
“Ta sani kan, sai dai bayan ke da ita da kuma Asmee babu wanda ya san da wannan maganar”
“To ita mai cutar ce kenan”
“Ai kema kin sani baƙya buƙatar na faɗa miki”
“Amman Asmee ta ji?”
“Ta ji mana, to me zata yi?”
“Ba komai kawai ina tuna lokacin da take cewa ba zaka taɓa aure ba ne”
“Ni kaina ina tuna wancan lokacin da ina son aure amman sai na kasa yi sanadin hakan muka faɗa hallaka ni da ke, sai dai kin san komai lokaci ne da shi, ko magani kika yi kika ga ya kama to daman can Allah ya rubuta zai kama ɗin”
“Na yarda da hakan ai ni sai dai na faɗawa wani, kuma ina fatar idan ka yi wannan auren zaka ɗaga min ƙafa, saboda mutane suna ta zargin muna tare ne, kuma zaka iya tonawa kanka asiri indan kana cigaba da ziyarta na, saboda kai ma za a iya gano kana ɗauke da cutar, abu na uku kuma kasan ance idan mace da namiji suka kasance su biyu sheiɗan ne na ukunsu, dan haka bana son wata alaƙa ta saɓon Allah ta sake shiga tsakanina da kowa”
“Nima bana nufin wani abun makamancin wannan saboda i realized that duk abunda ka yi wa ɗan wani sai an yi ma naka, tun bamu je ko ina ba a scul wani malami yayi raped ƴata, ban taɓa faɗa miki ba ne saboda ba labari ne mai daɗi ba, amman a lokacin na samu kai na a wani irin kalar mutum, abun da ciwo sosai Rashida, sai na dinga jin kamar na kama duka familynshi nayi musu yankan rago, but a dole na rufe magana domin idan na buɗe yanzu ne zata shiga duniya kowa yasan abunda ya samu ƴata bayan kuma nine sila saboda ban tsare kaina ba, kuma zan jawa ƴata abun faɗi ne kawai”
Ya share guntun ƙwalla da suka zubo masa.
“Ki dubi Family Hilal ki gani da yake ya tsare kansa, sai Allah ya tsallakar da shi, duk da kina a cikin gidanshi Allah ya tsare ƴaƴansa da matarsa da shi kansa mu kaɗai muka kwashi abun, dubi rayuwar gidansa ki gani gwanin sha'awa, ni ko rayuwa baƙinciki ne da kuka, saboda halin da muke ciki, ko wannan ciwon da ke jikinmu tawace gashi kullum muna cikin kafakafa kar ƴaranmu su ɗauka, muka tsoron mu kai su wani gurin riƙo asirinmu ya tonu”
Rashida ta girgiza kai cike da tausayawa.
“Ba ku kyautawa rayuwar ƴaƴanku ba, ku ɗauke su ku kaisu gurin ƙaƙaninsu mana, ko karka yi sake yaranka suma su kwasa su girma suna nadamar da kasancewar ƴaƴanka, karka ɓata rayuwar ƴaran ka tun suna da ƙurciya, ka taimaki future ɗin su, kai taka ta ƙare su kuma ka yi tattalinsu...”
Ajiyar zuciya ya sauke yafi sau goma sannan ya miƙe tsaye jiki a mace ya fice ba tare da ya ce da ita komai ba.
Rayuwa kenan sau da yawa Allah yake maka talala kayi ta iskancin da zarar ya tashi kama ka ba zaka ga da kyau ba, kuma matuƙar be yafe maka ba, zaka je lahira ka tararda abunda ka aikata. Duk magane-magane da Asmee ke yi tana ganin kamar ta ci riba wajen hana mijinta aure ashe ba riba bace lokacin auren ne be yi ba sai yanzu, tun da gashi yanzu zai yi auren,garin neman gira an rasa ido ta kwaso musu cuta tana nadamar da babu ranar daina kukanta. Ita kanta Rashida dake yi wa Kalsoom magani a dole ai yanzu ta saka mata ido ta ɗauke ta ƴar'uwa tun da taga addu'ah da tsarin Allah yana tare da wanda duk ya nemi taimakon Allah, tayi iya yinta amman bata raba Kalsoom da gidan mijinta ba saboda Allah ya riga ya rubuta ita ɗin ce dai.
Mata da yawa suna shiga haƙƙin mazajensu wajen ganin sun hanasu aure ko kuma sun mallake miji da kishiya, bayan kuma sun san Allah zai tsayar da su a gabanshi yayi masu shari'ah ranar da baki baya iya magana.
Jiki a mace ta miƙe ta yi nafila wato ƙabli asri sannan ta ɗora da la'asar ɗin, tasbihi da hailala da hamdala ne suka biyo baya tana gode Allah da ya nuna mata kuskurenta tun a nan duniya da ake karɓar tuba, kuma ya bata ikon tuban, kana ya tsare mata yaranta kuma ya basu uwar da zata riƙesu ta tarbiyantar da su, tabbas yanzu ta tabbatar Ubangijinta yafi kowa sonta, shi ta tsaɓawa kuma ya yafe mata har ya musanya mata ta wani ɓangare.
[7/31, 9:26 PM] Khadeeja Candy♥: *93*
Lafewa ta yi a ƙirjinsa tana sauraren yadda zuciyarsa ke bugawa, sai ƙara shigar da kanta take tana shaƙar ƙamshin turarenshi.
Hannu yasa yana shafa bayanta, idanuwansa a lumshe. Wani abu yaji yana sauko masa marar misaltuwa, be taɓa hugging wata mace kamar yadda yayi a yanzu ba, wata mace kuma bata taɓa kwantawa a ƙirjinsa kamar haka ba, ɗayan hannunta dake cikin hannunshi ya soma matsawa a hankali yana lume baki.
Jin shafar da yake mata ne ya sauya salo ne yasa ta ɗago kanta ta kalleshi, idonsa har yanzu kulle yake, hakan yasa ta ɗaga daga jikinsa gaba ɗaya ta zare hannunta daga nashi.
Sai ya buɗe idonsa yana kallonta, fararen idonsa sun fara rinewa zuwa ja ga wani ruwan hawaye da ya kwanta masa. Hannyensa yasa ya riƙa fuskarta.
“I Love you so much Abnam”
Kallonshi take kamar yadda shi ma yake kallonta, sai hawaye suka zubo mata.
“Ban san mi Asim yake nufi da ni ba, ban san miyasa ya ɓullo ta wannan hanyar ba, na masa iya hallacin da zan iya, saboda shi na rabu da iyayena, na bishi na zauna da shi a inda ban taɓa mafarkin zan zauna ba, lokacin da arziki ya zo masa sai ya guje ni, yace min baya son haihuwa, da cikin ya kure na je garin kaduna ba tare da na san kowa ba, Lamido yayi min masauki a gidansu, a gidan cikina ya zube.
Wallahi tallahi ya sake ni Abdallah, ban san miyasa ya canja min ba, har yana tambayar ɗan sa”
Hawaye na bin fuskarta take maganar zuciyarta cike da rauni. Fuskarta ya saki ya kama hannayenta ya riƙe gam.
“Na yarda da ke Abnam, Asim yana son shiga tsakaninmu ne, saboda yana tunanin zamu fara sabuwar rayuwa mai kyau, karki saka ranki cikin matsala nasara bata zuwa ba tare da wahala ba”
Ƙofar da Hajiya Kilishi ta buga ne yasa shi kallon ƙofar sannan ya kai hannu ya share mata hawayenta. Sannan ya miƙe tsaye ya buɗe ƙofar.
“Hajiya...”
“Na'am, Abdallah ya mai jikin”
“Ta ji sauƙi”
“Ga breakfast nan Hajiya ta aiko su Amal su kawo ance wayarka na kashe”
“Oh Okay bari na kunna”
“Okay ka gaishe da ita”
Ta juya shi kuma ya rufe ƙofar ya dawo yana ciro wayarsa da ke aljihu ya kunna, sai ya kira Ummi.
“Abdallah na kira wayarka kashe”
“Na kasheta ne saboda Doc yace min ana bukatar ta samu bachi, barka da safiya”
“An tashi lafiya ya jikinta? Miya same ta? Meesha tace min kawai sun ga ka fito da ita a sume”
“Ummi labari ne mai tsawo da rikitarwa zan zo anjima”
“Okay ga abinci nan na aiko muku nasan zata buƙaci abincin a yanzu, amman dai ka faɗa min ko minene”
A nan ya soma labarta mata abunda ya faru. Ta kiɗima sosai abun ya zo mata kamar almara, sai dai ta kwantarda hankalinta saboda kar hankalin ɗanta ya tashi.
“Allah zai muku mafita Abdallah”
“Na gode Ummi I love you”
“Allah ya maka albarka”
Yana sauke kiran wayar Mai Martaba ta shigo, cike da ladabi yayi picking.
“Assalamu Alaikum Mai Martaba”
“Wa'alaikassalam, Babana ya mai jiki”
“Alhamdullillah ta ji sauƙi fatar ka tashi lafiya”
“Alhamdullah, Babana bana son ka tashi hankalinka na san kana sonta sosai, sai dai bana son da kake mata ya iya rufe maka ido ka tsallake gaskiya, kai ɗana ne nafi son komai za'ayi ka tsaya kan gaskiyarka”
“Mai Martaba kafi kowa sani na, ba zan taɓa aikata abun assha ba, kuma zan saurareshi matuƙar yana da hujja”
“Allah ya maka albarka”
“Amin Mai Martaba Allah yaja kwananka”
Daga haka ya sauke wayar sai ga kiran sisters ɗinsa ya shigo sai kuma na Maryam, sai dai be ɗaga ba sai kawai ya kashe wayar. Ya miƙe tsaye ya fita. Sojojin da ke gurin da dogarai ya sallama sai dogara ɗaya ya bari, sannan ya dawo ɗakin.
Wannan karon jikin windo ya same ta tsaye fuskarta na kallon ƙasa kasancewar inda suke gidan sama ne. Ƙarasawa yayi ya riƙe kunkurunta ya ɗora kansa saman wuyanta.
“Jiya ya kamata ace na tare, amman hargitsin da ya faru jiya ya hana hakan, dare biyu kenan na amarci ina kwana ba cikin daɗi ba, a wacan daren fargaba da tunanin halin da na bar mahaifina da kuma tunanin makomar aurena, yanzu kuma wannan hargitsin ya taso, Ina roƙon Allah ya tsayar a nan kar wannan abun ya shafi rayuwar auren da zanyi nan gaba”
Ɗayan hannunshi yasa ya zagaye cikinta.
“Wannan rigimar ma na ɗan lokaci ne, kar zuciyarki ta sake irin wacan tunanin, ko kaɗan Abdallah be yi kama da Asim ba, a halitta balle kuma a hali da ɗabiyu da halaiya, Wannan karon da Abdalla aka ɗaura miki aure ba Asim ba, kar ki sake irin wacan mafarkin”
Juyowa tayi ta riƙa fuskarsa tana hawaye.
“Zuciya bata iya tantance gaskiya da ƙarya a yanzu, shi ma haka yayin ya yaudare ni da daɗaɗan kalamai, da su ya siye ni har na rufta a duniyarsa mai cike da duhu da kuma hayaƙi”
Jin an buga ƙofa yasa tayi saurin janye hannunta daga fuskarsa ta zauna saman gadon tana share hawaye. Haleema ce da Fauza sai Shukura mai aikin Ummi.
Sai da suka fara gaisawa da Abdool sannan ta ƙaraso kusa da Namra tana mata ya jiki.
“Senu senu Ajiya, Allah kew wo sauƙi, Allah baka lafiya get well soon”
“Thank you, ya Mama?”
“Lafiya ƙalau yace a agaise ki”
Haleema ta matsa tana ƙare mata kallon tare da yi mata ya jiki.
“Sannu adda Namra Allah baki lafiya”
Sai Fauza ta ɗora da nata
“Ummi tace a gaishe ki, Allah ƙara sauƙi”
“Amin amin na gode”
Bayan sun dire mata kulolin abinci suka tafi. Da kanshi ya ɗauki plate ya zuba mata abincin da aka kawo ya soma bata da kanshi sai da ya tabbatar ta koshi sannan aje plate ɗin ya ɗauki ruwa ya bata, yana dire kofin sai ga Sisters nashi sun shigo tare da Maryam sun kawo abincin cikin manyan kuloli na alfarma masu mugun tsada.
Da sauri Maryam ta zauna kusa da ita tana mata ya jiki cike da tausayin ƴar'uwarta.
“Na ji sauƙi kin yi waya da Anty?”
“Eh tun ɗazu take son ta yi magana da ke wayarki na hannuna shi kuma wayarsa a kashe, tace mun ma sun kamo hanya ita da Abbah da asubar nan”
“Kin faɗa musu abunda ya faru”
“Eh Abbah ma yace Mai Martaba ya kira shi, Namra karki saka ranki a damuwa Asim yana son ya saka ki cikin matsala ne kawai kuma yana son ganin zubar hawayenki saboda yasan a yanzu ba zaki taɓa dawowa gareshi ba”
Abdool ne yayi saurin katse musu fira saboda baya son sisters ɗinshi su gane inda matsalar take, duk da bashi da tabbacin ko Mai Martaba ya faɗa a masarauta.
“Maryam ku zo ku tafi Doc yace ana buƙatar ta huta sosai”
“Okay Allah ya baki Lafiya”
Maryam ta faɗa idonta cike da ƙwalla ganin hawayen da ke zuba a idanuwan ƴar uwarta. Tare da Sisters ɗinsa suka fita sai ya sake buɗe kulolin ya zuba mata abincin da aka kawo amman bata ci ba shi ma kuma baya jin cin abincin sai kawai ya aje. Yana kallon Likitan da ya turo ƙofar ɗakin ya shigo, murmushi suka yi ma juna shi da da Abdool kamin ya miƙa masa hannu su gaisa.
“Ango Ango daya tare a asibiti, ina fatar dai ba ƙarfin amaryar mu ka ci ba har ka kawo mana ita asibiti, kasan baƙauye be iya sintar agogo ba”
Abdool yayi murmushin ƙasaita Hafiz abokinsa ne tare suka yi karatu a waje.
“Ni dai duba min matata please bana son ƙananan magana”
“Ai yanzu kana da baki jiya da na tsaya iya bayani ai ko kallon inda nake baka yi ba”
“Ai ban ma san da kai ba”
“Ai ba zaka sani ba, hankalinka yana tashe”
Ya shiga duba hannun Namra da Abdool ya cire mata drip. Sannan ya tambayi Namra abunda take ji.
Magani ya rubuta mata sannan ya faɗi yadda za a bata shi ya kuma rubuta musu takardar sallama, daman ba wani ciwon ba ne sai gajiya da kuma iɗima a lokaci ɗaya.
Sai basu bar asibitin ba sai da an gidansu Abdool ta ɓangaren Mai Martaba suka cika motoci suka zo ganin Namra, hakan kuma ba ƙaramin faranta ran Namra yayi ba, at least tasan ta shigo familyn da ake marhabun da ita kuma ake sonta da ɗaukinta ta ko wane ɓangare.
Sai ƙarfe goma sha ɗaya har da rabi sannan suka bar asibitin, Abdool be nufi gida da ita ba kasancewar shi ne yake tuƙin motar sai Sis ɗinsa ɗaya da ke gaban mota yayinda Namra da wasu ƴan gidansu suke baya su uku.
Ya tararda gidan cike da mutane kasancewar har yanzu ƴan biki basu gama watsewa ba, balle ma yau Ummi take da niyar yin nata walimar sai dai wannan abun daya faru ya kashe mata jiki, ganin hakan yasa be shigo ba, sai su Meesha da Ƴan Gidansu wato Maryam da Raihanatu da Gwaggo Ramatu, ba laifi tana iya tafiya dan ta samu ƙwarin jiki sosai tsaɓanin jiya da bata da wani kuzari sosai.
Da kanta take takawa har suka isa bacony ɗin, sannu mutanen da ke cikin falon suka riƙa mata har aka nufi ɗaƙin Ummi da ita saboda Ummi tace a shigo da ita cikin.
Kanta a ƙasa ta shiga ɗakin, dan haka bata iya gane mutanen dake cikin bathroom ɗin sai dai taɓa jin ba Ummi bace kaɗai a ɗakin.
Da ɗai-ɗaya Ummi ta riƙa nuna mata su tan gaishesu a nan Namra take ɗan ɗaga ido ta kallesu saboda ta tantancesu.
Sai sannu suke mata suna tsinewa Asim Albarka duk da basu san shi ba, domin Ummi ta faɗa musu komai, ganin ƴan'uwanta babu abunda zata ɓoye musu.
“Tashi ki zauna saman gadi magana zamu yi”
Ummi ta faɗa fuskarta da murmushi kamar babu damuwa cikin ranta. Sai duk suka tashi suna dariya tare da cewa basu su bata guri, daman ana ta kiransu su zo su duba Donuts ɗin da ake haɗawa idan yayi. Namra na zaunawa saman gado Hajiya Sadiya ta buɗo ƙofar Bathroom ta fito ta fito.
Suka haɗa ido da Namra sai ta yi tsaye jikin ƙofar kamar marar gaskiya, Namra kan saurin kawar da idonta tayi saboda bata gama yarda ita ɗince ba ko a'a idan ɗince miya kawo ta nan? Anya ma itace wannan ta rame sosai kamar ba ita ba, duk jikinta nan ya zube ta koma siririya sosai.
“Hajiya Ƙaraso ku gaisa da ƴar ta ki”
Ummi ta faɗa ba tare
Showing 261001 words to 264000 words out of 280121 words
Har ƙauyuka suna shiga su wayarda kai, abun yanxu yayi gaba har nijar da sudan ghana sukan leƙa wani lokacin domin halartar taron ƙarawa juna sani ko kuma na ƙungiyoyin duniya qani lokacin ma.har.
Ta tattara rayuwar aure ta aje gefe, duk kuwa da irin tayin da Alhaji bashir da kuma wasu mazan suke mata, bata son abunda zai sake ɗaga mata hankali a yanzu, shiyasa bata kawowa kanta zancen aure a kusa.
A duk lokacin da ta tuna da Kalsoom ce take riƙe da ƴaƴanta sai ta yi ma Allah godiya, domin bata san Kalsoon ƴar'uwa ba ce sai a yanzu, tana ƙoƙari gurin ganin ta bawa yaranta tarbiya, basa mata complain ɗin sun rasa wani abu ko an musu wani abun sai ɗan abunda rai ba zai rasa ba, sai yanzu ta tabbatar good people are still exist, ba ko wace abokiyar zama ce kishiyaba wata kan ƴar'uwa ce.
Bata da matsala ta ko ina a yanzu, sai dai tana nadamar abunda duk ta tuna sai baƙinciki ya rufeta, wato sanadin wannan ciwon nata, a duk lokacin da aka tambaye ta dalilin wannan ciwon nata ta kan ce ta same shi ne ta hanyar ƙarin jini da aka mata, domin kawai ta kare kanta.
Shekara biyar da shiga ƙungiyar zuwa yau rayuwarta ta zama abar kwatance, rayuwarta darasi ce ga duk mace mai irin rayuwarta, ko kuma halinta, ita kanta yanzu ta koyi abubuwa da yawa na rayuwar duniya da kuma zama da mutane.
Ko da aka yi birthday ɗin Izzah tana Abuja gurin wani taro, washe garin ranar da ta dawo taje gidan ta kai musu tsarabarsu da kuma birthday gift ta bawa Izzah.
Ta jidaɗin yadda ta same su, baka iya banbance tsakanin Ƴaƴan Kalsoom da nata a gurin Kalsoom wato Amal da Rafiq da Husna, sam mutum ba zai iya cewa su ne ƴaƴan Kalsoom ba, sau da dama zata bawa su Izza abu ta hana ƴaƴanta.
Bata daɗe a gidan ba duk da ƴaran sun so haka, amman ta ƙi a duk lokacin da taje gidan haka take bata daɗewa take fitowa.
Ko da iso gidanta uku da rabi yayi, dan haka tana shiga bathroom ɗinta ta yi alwalar la'asar ta fito ta shimfiɗa sallaya ta saka hijab taja carbi tana la'zimi kamin lokacin tada sallah yayi.
Wayarta ce tayi ƙara daman ta ji tsayawar mota a harabar gidanta, sai kawai ta miƙe tsaye ta nufi falo ta buɗe masa ƙofa.
“Hajiya...”
“Alhaji Bashir”
Shigowa yayi yana faɗin
“Aiko na taki sa'ah dan ban tsamaci kina garin ba”
“Jiya na dawo”
“Mashallah ya Abujar?”
Ya tambaya yayinda yake ƙoƙarin zaunawa.
“Abuja sai hamdallah, ya aikin naku”
“Aiki da godiya, iv na zo na kawo miki”
“Ba dai na aurenka ba ko?”
“Shi mana ba kin ƙi ni ba”
“Dana ƙi ka ya hana dubu su soka ne?”
“Cikin dubun ai na ƙawo ƙoƙon barata a gareki amman kika ƙi yarda, kuma ni wallahi ko a yanzu kika yarda zan aure ki”
Ruwan tsanyi ta dire masa tana dariya tare da kai hannu ta karɓi iv ɗin.
“Lallai mutumen da gaske kake, budurwa ce ko bazawara”
“Budurwa ce yarinya ce ba zaki sha wahala gurin kishi da ita ba”
“Ai ni na yafe kishi da kowa, sai dai ina fatar tasan halin da kake ciki”
“Ta sani kan, sai dai bayan ke da ita da kuma Asmee babu wanda ya san da wannan maganar”
“To ita mai cutar ce kenan”
“Ai kema kin sani baƙya buƙatar na faɗa miki”
“Amman Asmee ta ji?”
“Ta ji mana, to me zata yi?”
“Ba komai kawai ina tuna lokacin da take cewa ba zaka taɓa aure ba ne”
“Ni kaina ina tuna wancan lokacin da ina son aure amman sai na kasa yi sanadin hakan muka faɗa hallaka ni da ke, sai dai kin san komai lokaci ne da shi, ko magani kika yi kika ga ya kama to daman can Allah ya rubuta zai kama ɗin”
“Na yarda da hakan ai ni sai dai na faɗawa wani, kuma ina fatar idan ka yi wannan auren zaka ɗaga min ƙafa, saboda mutane suna ta zargin muna tare ne, kuma zaka iya tonawa kanka asiri indan kana cigaba da ziyarta na, saboda kai ma za a iya gano kana ɗauke da cutar, abu na uku kuma kasan ance idan mace da namiji suka kasance su biyu sheiɗan ne na ukunsu, dan haka bana son wata alaƙa ta saɓon Allah ta sake shiga tsakanina da kowa”
“Nima bana nufin wani abun makamancin wannan saboda i realized that duk abunda ka yi wa ɗan wani sai an yi ma naka, tun bamu je ko ina ba a scul wani malami yayi raped ƴata, ban taɓa faɗa miki ba ne saboda ba labari ne mai daɗi ba, amman a lokacin na samu kai na a wani irin kalar mutum, abun da ciwo sosai Rashida, sai na dinga jin kamar na kama duka familynshi nayi musu yankan rago, but a dole na rufe magana domin idan na buɗe yanzu ne zata shiga duniya kowa yasan abunda ya samu ƴata bayan kuma nine sila saboda ban tsare kaina ba, kuma zan jawa ƴata abun faɗi ne kawai”
Ya share guntun ƙwalla da suka zubo masa.
“Ki dubi Family Hilal ki gani da yake ya tsare kansa, sai Allah ya tsallakar da shi, duk da kina a cikin gidanshi Allah ya tsare ƴaƴansa da matarsa da shi kansa mu kaɗai muka kwashi abun, dubi rayuwar gidansa ki gani gwanin sha'awa, ni ko rayuwa baƙinciki ne da kuka, saboda halin da muke ciki, ko wannan ciwon da ke jikinmu tawace gashi kullum muna cikin kafakafa kar ƴaranmu su ɗauka, muka tsoron mu kai su wani gurin riƙo asirinmu ya tonu”
Rashida ta girgiza kai cike da tausayawa.
“Ba ku kyautawa rayuwar ƴaƴanku ba, ku ɗauke su ku kaisu gurin ƙaƙaninsu mana, ko karka yi sake yaranka suma su kwasa su girma suna nadamar da kasancewar ƴaƴanka, karka ɓata rayuwar ƴaran ka tun suna da ƙurciya, ka taimaki future ɗin su, kai taka ta ƙare su kuma ka yi tattalinsu...”
Ajiyar zuciya ya sauke yafi sau goma sannan ya miƙe tsaye jiki a mace ya fice ba tare da ya ce da ita komai ba.
Rayuwa kenan sau da yawa Allah yake maka talala kayi ta iskancin da zarar ya tashi kama ka ba zaka ga da kyau ba, kuma matuƙar be yafe maka ba, zaka je lahira ka tararda abunda ka aikata. Duk magane-magane da Asmee ke yi tana ganin kamar ta ci riba wajen hana mijinta aure ashe ba riba bace lokacin auren ne be yi ba sai yanzu, tun da gashi yanzu zai yi auren,garin neman gira an rasa ido ta kwaso musu cuta tana nadamar da babu ranar daina kukanta. Ita kanta Rashida dake yi wa Kalsoom magani a dole ai yanzu ta saka mata ido ta ɗauke ta ƴar'uwa tun da taga addu'ah da tsarin Allah yana tare da wanda duk ya nemi taimakon Allah, tayi iya yinta amman bata raba Kalsoom da gidan mijinta ba saboda Allah ya riga ya rubuta ita ɗin ce dai.
Mata da yawa suna shiga haƙƙin mazajensu wajen ganin sun hanasu aure ko kuma sun mallake miji da kishiya, bayan kuma sun san Allah zai tsayar da su a gabanshi yayi masu shari'ah ranar da baki baya iya magana.
Jiki a mace ta miƙe ta yi nafila wato ƙabli asri sannan ta ɗora da la'asar ɗin, tasbihi da hailala da hamdala ne suka biyo baya tana gode Allah da ya nuna mata kuskurenta tun a nan duniya da ake karɓar tuba, kuma ya bata ikon tuban, kana ya tsare mata yaranta kuma ya basu uwar da zata riƙesu ta tarbiyantar da su, tabbas yanzu ta tabbatar Ubangijinta yafi kowa sonta, shi ta tsaɓawa kuma ya yafe mata har ya musanya mata ta wani ɓangare.
[7/31, 9:26 PM] Khadeeja Candy♥: *93*
Lafewa ta yi a ƙirjinsa tana sauraren yadda zuciyarsa ke bugawa, sai ƙara shigar da kanta take tana shaƙar ƙamshin turarenshi.
Hannu yasa yana shafa bayanta, idanuwansa a lumshe. Wani abu yaji yana sauko masa marar misaltuwa, be taɓa hugging wata mace kamar yadda yayi a yanzu ba, wata mace kuma bata taɓa kwantawa a ƙirjinsa kamar haka ba, ɗayan hannunta dake cikin hannunshi ya soma matsawa a hankali yana lume baki.
Jin shafar da yake mata ne ya sauya salo ne yasa ta ɗago kanta ta kalleshi, idonsa har yanzu kulle yake, hakan yasa ta ɗaga daga jikinsa gaba ɗaya ta zare hannunta daga nashi.
Sai ya buɗe idonsa yana kallonta, fararen idonsa sun fara rinewa zuwa ja ga wani ruwan hawaye da ya kwanta masa. Hannyensa yasa ya riƙa fuskarta.
“I Love you so much Abnam”
Kallonshi take kamar yadda shi ma yake kallonta, sai hawaye suka zubo mata.
“Ban san mi Asim yake nufi da ni ba, ban san miyasa ya ɓullo ta wannan hanyar ba, na masa iya hallacin da zan iya, saboda shi na rabu da iyayena, na bishi na zauna da shi a inda ban taɓa mafarkin zan zauna ba, lokacin da arziki ya zo masa sai ya guje ni, yace min baya son haihuwa, da cikin ya kure na je garin kaduna ba tare da na san kowa ba, Lamido yayi min masauki a gidansu, a gidan cikina ya zube.
Wallahi tallahi ya sake ni Abdallah, ban san miyasa ya canja min ba, har yana tambayar ɗan sa”
Hawaye na bin fuskarta take maganar zuciyarta cike da rauni. Fuskarta ya saki ya kama hannayenta ya riƙe gam.
“Na yarda da ke Abnam, Asim yana son shiga tsakaninmu ne, saboda yana tunanin zamu fara sabuwar rayuwa mai kyau, karki saka ranki cikin matsala nasara bata zuwa ba tare da wahala ba”
Ƙofar da Hajiya Kilishi ta buga ne yasa shi kallon ƙofar sannan ya kai hannu ya share mata hawayenta. Sannan ya miƙe tsaye ya buɗe ƙofar.
“Hajiya...”
“Na'am, Abdallah ya mai jikin”
“Ta ji sauƙi”
“Ga breakfast nan Hajiya ta aiko su Amal su kawo ance wayarka na kashe”
“Oh Okay bari na kunna”
“Okay ka gaishe da ita”
Ta juya shi kuma ya rufe ƙofar ya dawo yana ciro wayarsa da ke aljihu ya kunna, sai ya kira Ummi.
“Abdallah na kira wayarka kashe”
“Na kasheta ne saboda Doc yace min ana bukatar ta samu bachi, barka da safiya”
“An tashi lafiya ya jikinta? Miya same ta? Meesha tace min kawai sun ga ka fito da ita a sume”
“Ummi labari ne mai tsawo da rikitarwa zan zo anjima”
“Okay ga abinci nan na aiko muku nasan zata buƙaci abincin a yanzu, amman dai ka faɗa min ko minene”
A nan ya soma labarta mata abunda ya faru. Ta kiɗima sosai abun ya zo mata kamar almara, sai dai ta kwantarda hankalinta saboda kar hankalin ɗanta ya tashi.
“Allah zai muku mafita Abdallah”
“Na gode Ummi I love you”
“Allah ya maka albarka”
Yana sauke kiran wayar Mai Martaba ta shigo, cike da ladabi yayi picking.
“Assalamu Alaikum Mai Martaba”
“Wa'alaikassalam, Babana ya mai jiki”
“Alhamdullillah ta ji sauƙi fatar ka tashi lafiya”
“Alhamdullah, Babana bana son ka tashi hankalinka na san kana sonta sosai, sai dai bana son da kake mata ya iya rufe maka ido ka tsallake gaskiya, kai ɗana ne nafi son komai za'ayi ka tsaya kan gaskiyarka”
“Mai Martaba kafi kowa sani na, ba zan taɓa aikata abun assha ba, kuma zan saurareshi matuƙar yana da hujja”
“Allah ya maka albarka”
“Amin Mai Martaba Allah yaja kwananka”
Daga haka ya sauke wayar sai ga kiran sisters ɗinsa ya shigo sai kuma na Maryam, sai dai be ɗaga ba sai kawai ya kashe wayar. Ya miƙe tsaye ya fita. Sojojin da ke gurin da dogarai ya sallama sai dogara ɗaya ya bari, sannan ya dawo ɗakin.
Wannan karon jikin windo ya same ta tsaye fuskarta na kallon ƙasa kasancewar inda suke gidan sama ne. Ƙarasawa yayi ya riƙe kunkurunta ya ɗora kansa saman wuyanta.
“Jiya ya kamata ace na tare, amman hargitsin da ya faru jiya ya hana hakan, dare biyu kenan na amarci ina kwana ba cikin daɗi ba, a wacan daren fargaba da tunanin halin da na bar mahaifina da kuma tunanin makomar aurena, yanzu kuma wannan hargitsin ya taso, Ina roƙon Allah ya tsayar a nan kar wannan abun ya shafi rayuwar auren da zanyi nan gaba”
Ɗayan hannunshi yasa ya zagaye cikinta.
“Wannan rigimar ma na ɗan lokaci ne, kar zuciyarki ta sake irin wacan tunanin, ko kaɗan Abdallah be yi kama da Asim ba, a halitta balle kuma a hali da ɗabiyu da halaiya, Wannan karon da Abdalla aka ɗaura miki aure ba Asim ba, kar ki sake irin wacan mafarkin”
Juyowa tayi ta riƙa fuskarsa tana hawaye.
“Zuciya bata iya tantance gaskiya da ƙarya a yanzu, shi ma haka yayin ya yaudare ni da daɗaɗan kalamai, da su ya siye ni har na rufta a duniyarsa mai cike da duhu da kuma hayaƙi”
Jin an buga ƙofa yasa tayi saurin janye hannunta daga fuskarsa ta zauna saman gadon tana share hawaye. Haleema ce da Fauza sai Shukura mai aikin Ummi.
Sai da suka fara gaisawa da Abdool sannan ta ƙaraso kusa da Namra tana mata ya jiki.
“Senu senu Ajiya, Allah kew wo sauƙi, Allah baka lafiya get well soon”
“Thank you, ya Mama?”
“Lafiya ƙalau yace a agaise ki”
Haleema ta matsa tana ƙare mata kallon tare da yi mata ya jiki.
“Sannu adda Namra Allah baki lafiya”
Sai Fauza ta ɗora da nata
“Ummi tace a gaishe ki, Allah ƙara sauƙi”
“Amin amin na gode”
Bayan sun dire mata kulolin abinci suka tafi. Da kanshi ya ɗauki plate ya zuba mata abincin da aka kawo ya soma bata da kanshi sai da ya tabbatar ta koshi sannan aje plate ɗin ya ɗauki ruwa ya bata, yana dire kofin sai ga Sisters nashi sun shigo tare da Maryam sun kawo abincin cikin manyan kuloli na alfarma masu mugun tsada.
Da sauri Maryam ta zauna kusa da ita tana mata ya jiki cike da tausayin ƴar'uwarta.
“Na ji sauƙi kin yi waya da Anty?”
“Eh tun ɗazu take son ta yi magana da ke wayarki na hannuna shi kuma wayarsa a kashe, tace mun ma sun kamo hanya ita da Abbah da asubar nan”
“Kin faɗa musu abunda ya faru”
“Eh Abbah ma yace Mai Martaba ya kira shi, Namra karki saka ranki a damuwa Asim yana son ya saka ki cikin matsala ne kawai kuma yana son ganin zubar hawayenki saboda yasan a yanzu ba zaki taɓa dawowa gareshi ba”
Abdool ne yayi saurin katse musu fira saboda baya son sisters ɗinshi su gane inda matsalar take, duk da bashi da tabbacin ko Mai Martaba ya faɗa a masarauta.
“Maryam ku zo ku tafi Doc yace ana buƙatar ta huta sosai”
“Okay Allah ya baki Lafiya”
Maryam ta faɗa idonta cike da ƙwalla ganin hawayen da ke zuba a idanuwan ƴar uwarta. Tare da Sisters ɗinsa suka fita sai ya sake buɗe kulolin ya zuba mata abincin da aka kawo amman bata ci ba shi ma kuma baya jin cin abincin sai kawai ya aje. Yana kallon Likitan da ya turo ƙofar ɗakin ya shigo, murmushi suka yi ma juna shi da da Abdool kamin ya miƙa masa hannu su gaisa.
“Ango Ango daya tare a asibiti, ina fatar dai ba ƙarfin amaryar mu ka ci ba har ka kawo mana ita asibiti, kasan baƙauye be iya sintar agogo ba”
Abdool yayi murmushin ƙasaita Hafiz abokinsa ne tare suka yi karatu a waje.
“Ni dai duba min matata please bana son ƙananan magana”
“Ai yanzu kana da baki jiya da na tsaya iya bayani ai ko kallon inda nake baka yi ba”
“Ai ban ma san da kai ba”
“Ai ba zaka sani ba, hankalinka yana tashe”
Ya shiga duba hannun Namra da Abdool ya cire mata drip. Sannan ya tambayi Namra abunda take ji.
Magani ya rubuta mata sannan ya faɗi yadda za a bata shi ya kuma rubuta musu takardar sallama, daman ba wani ciwon ba ne sai gajiya da kuma iɗima a lokaci ɗaya.
Sai basu bar asibitin ba sai da an gidansu Abdool ta ɓangaren Mai Martaba suka cika motoci suka zo ganin Namra, hakan kuma ba ƙaramin faranta ran Namra yayi ba, at least tasan ta shigo familyn da ake marhabun da ita kuma ake sonta da ɗaukinta ta ko wane ɓangare.
Sai ƙarfe goma sha ɗaya har da rabi sannan suka bar asibitin, Abdool be nufi gida da ita ba kasancewar shi ne yake tuƙin motar sai Sis ɗinsa ɗaya da ke gaban mota yayinda Namra da wasu ƴan gidansu suke baya su uku.
Ya tararda gidan cike da mutane kasancewar har yanzu ƴan biki basu gama watsewa ba, balle ma yau Ummi take da niyar yin nata walimar sai dai wannan abun daya faru ya kashe mata jiki, ganin hakan yasa be shigo ba, sai su Meesha da Ƴan Gidansu wato Maryam da Raihanatu da Gwaggo Ramatu, ba laifi tana iya tafiya dan ta samu ƙwarin jiki sosai tsaɓanin jiya da bata da wani kuzari sosai.
Da kanta take takawa har suka isa bacony ɗin, sannu mutanen da ke cikin falon suka riƙa mata har aka nufi ɗaƙin Ummi da ita saboda Ummi tace a shigo da ita cikin.
Kanta a ƙasa ta shiga ɗakin, dan haka bata iya gane mutanen dake cikin bathroom ɗin sai dai taɓa jin ba Ummi bace kaɗai a ɗakin.
Da ɗai-ɗaya Ummi ta riƙa nuna mata su tan gaishesu a nan Namra take ɗan ɗaga ido ta kallesu saboda ta tantancesu.
Sai sannu suke mata suna tsinewa Asim Albarka duk da basu san shi ba, domin Ummi ta faɗa musu komai, ganin ƴan'uwanta babu abunda zata ɓoye musu.
“Tashi ki zauna saman gadi magana zamu yi”
Ummi ta faɗa fuskarta da murmushi kamar babu damuwa cikin ranta. Sai duk suka tashi suna dariya tare da cewa basu su bata guri, daman ana ta kiransu su zo su duba Donuts ɗin da ake haɗawa idan yayi. Namra na zaunawa saman gado Hajiya Sadiya ta buɗo ƙofar Bathroom ta fito ta fito.
Suka haɗa ido da Namra sai ta yi tsaye jikin ƙofar kamar marar gaskiya, Namra kan saurin kawar da idonta tayi saboda bata gama yarda ita ɗince ba ko a'a idan ɗince miya kawo ta nan? Anya ma itace wannan ta rame sosai kamar ba ita ba, duk jikinta nan ya zube ta koma siririya sosai.
“Hajiya Ƙaraso ku gaisa da ƴar ta ki”
Ummi ta faɗa ba tare
Book Chapters
Chapter 1Chapter 2Chapter 3Chapter 4Chapter 5Chapter 6Chapter 7Chapter 8Chapter 9Chapter 10Chapter 11Chapter 12Chapter 13Chapter 14Chapter 15Chapter 16Chapter 17Chapter 18Chapter 19Chapter 20Chapter 21Chapter 22Chapter 23Chapter 24Chapter 25Chapter 26Chapter 27Chapter 28Chapter 29Chapter 30Chapter 31Chapter 32Chapter 33Chapter 34Chapter 35Chapter 36Chapter 37Chapter 38Chapter 39Chapter 40Chapter 41Chapter 42Chapter 43Chapter 44Chapter 45Chapter 46Chapter 47Chapter 48Chapter 49Chapter 50Chapter 51Chapter 52Chapter 53Chapter 54Chapter 55Chapter 56Chapter 57Chapter 58Chapter 59Chapter 60Chapter 61Chapter 62Chapter 63Chapter 64Chapter 65Chapter 66Chapter 67Chapter 68Chapter 69Chapter 70Chapter 71Chapter 72Chapter 73Chapter 74Chapter 75Chapter 76Chapter 77Chapter 78Chapter 79Chapter 80Chapter 81Chapter 82Chapter 83Chapter 84Chapter 85Chapter 86Chapter 87Chapter 88 Chapter 89Chapter 90Chapter 91Chapter 92Chapter 93Chapter 94