dan baka san ta rai ba. 😀
Ina roƙon duk wanda na ɓatawa rai sanadin canjin nan ko kuma littafin nan, dan Allah ku yafe min, nima ban za ci sauyin zai zo ba, sai daga baya, da tun farko na faɗa. Ina roƙon alfarma dan Allah kar wanda ya mai da min da Littafi document.
Na gode da shawarwari da ƙauna, Allah ya sakawa kowa da Alheri. I love you all
BEST REGARDS 💖🌺
KHADEEJA CANDY 😘
*🌺🌺🌺 ZAGON ƘASA 🌺🌺🌺*
_Write by_
*Khadeeja Candy*
*PAGE - 36*
NOT EDITED ⚠
Nitsa kai suka yi tayi cikin unguwar, sun yi tafiyar mintina goma zuwa sha uku, sannan suka isa ƙarshen unguwar, a bakin wani makeken gate black color.
Tsoron dake cikin zuciyar Rashida ya kasa ɓoyuwa har sai da ya nuna a jikinta, gani take kamar wani abun zasu mata har ta buɗe baki tayi magana, sai ta tuna da abunda ya kawo ta gurin, kuma ta san bata da wata mafita sai wannan.
Sai kawai tayi shiru da bakinta ta sakar musu na mujiya har suka faka bakin wata babbar ƙofa. Amira ce ta fara fita tana faɗin
“Fito muje”
Buɗewa Rashida tayi ta fito, sai mutun ya ja motar ya nufi wani ɓangare na gidan da ita.
Amira tayi gaba, Rashida ta rufa mata baya sai kalle-kallen gidan take.
Cikin wani ƙaton falo suka shiga, wanda aka ƙawata da kayan alatu, kallon falon tayi sosai ba dan ya birge ta ba, sai dan ɗaukar rahoto ta karanci wane irin gida ne aka a kawo ta.
Kamar daga sama ta ji Amira na mata magana.
“Idan baki yarda da gidan ba, miyasa kika shigo? Ko kina tunanin za mu miki wanin abun ne?”
Kasa cewa komai, tayi har Amira ta gaji da tsayi a gurin, ta isa gaban wata babbar kujera ta zauna tana cire gyalen abayarta.
“Guy Son!”
Ta ƙwala mishi kira, tana nuna ma Rashida kujera.
“Zauna idan zaki iya”
Rashida ta zauna zuciyarta na ɗar-ɗar, wani tunanin ne ya zo mata. What if tafa mutumen data sani? Ko kuma gidan yana tare da Dr Sabo fa?
Fitowarsa yayi dai-dai da sauke ajiyar zuciyar da Rashida ta yi, a yanayin shigarsa da kamalarsa, bata zace shine Guy Son ɗin ba har sai da ya zauna kusa da Amira, jikinsa yana Gugar na Amira.
“Wa kike son ayi miki garkuwa?”
Ya tambaya, fuska babu alamar murmushi balle wasa.
“Wani mutun ne, sunan shi Doc Sabo a asibin Alex yake aiki sashen jini”
“Cire Niƙab ɗin fuskarki kiyi mana bayanin komai”
Tasa hannu ta cire Niƙabin ta gyara zamanta sannan tace
“Mijina ne ya ɗibi jinina dana yara na ya kai masa akan yayi mana gwaji, bana da tabbaci amman ina jin kamar ina ɗauke da cutar hiv kuma ina tunanin mijina da kishiyata basa da shi, na karɓi numbersa gurin abokin aikina na kira mun yi magana akan zai faɗa min idan mijina ya kawo jinin, har na tura masa dubu ɗari, sai gashi ya yaudare ya faɗawa mijina na bashi kuɗi”
Ya kai hannunshi ya riƙa hannun Amira yasa yatsunsa cikin nata.
“So kina son ayi forcing ɗinsa ya canja result ɗin ko?”
“Haka nake so, matuƙar ya faɗi gaskiya, mijina zai rabu da ni, kuma duniya zata ƙyamace ni, zan ba ku ko nawa kake so, dan Allah ku taimaki rayuwata”
Amira ta ɗan yi murmushi.
“Ba shi kike son ayi a ɗauke miki ba, ƴaƴansa za'ayi kidnapped sai asa shi dole ya faɗi abunda kike so”
“Koma yaya ne ni dai yi min zan biya ko nawa kuke so”
Ta faɗa tana karyar da murya irin tausayin nan. Wayar dake hannu ya karɓa, ya saka wata number ya kira, ana picking yace
“Zo nan ina neman ka”
Be fi mintuna uku da aje wayar ba, sai ga mutumen ya shigo cikin ƙaƙanan tufafi, yazo dai-dai shi ya tsaya, Rashida na kallonsa gabanta ya faɗi saboda jan idonsa.
“Ka bincika min addireshin Doc Sabo yana aiki a Alex hospital sashen jini”
“Okay Boss”
Sai ya juya ya fice. Guy son ya kalli Rashida ya ce
“Bani addireshin ki, kuma karki kuskura ba ni na ƙarya dan zan gano ki”
Gabanta ya faɗi sosai, kuma ta tsorata, bata son bashi na ƙarya tun da har ya gargaɗeta, sai dai kuma idan har ta ba shi adireshin na gaskiya, bata san abunda zai faru ba.
“Sunana Rashida Abdullahi Kardam ina aiki a Stanbic Ibtc Bank, mijina babban likita ne, yana aiki a Kaduna special hospital, muna nan GRA magaji road”
“You can go, zaki ga motar data kawo ki zata maida ke inda kike”
“Thank you”
Ta saka niƙabinta ta saka sannan ta ɗauki jakarta ta fice. Amira ta tashi ta nufi gurin window falon ta tsaya, tana kallon harabar gidan. Tana sinkayar motar har suka fice, sannan ta sauke ajiyar zuciya, ta jingina da gurin ta rufe ido.
Hannunshi yasa cikin jikinta yana murza fatar jikinta, ya fara shinshinar gefen wuyanta. Buɗe idon ta yi ta ture shi da dukan ƙarfinta.
Kallon da zai yi sai hawaye ya gani sun silalo daga idonta. Yarfarda hannu yayi ya cije fuska.
“So nawa zan faɗa miki bana son hawayen nan”
“Ka bar ni nayi kuka na, ai ina da dalilin kuka”
Hannu ya kai ya riƙe fuskarta iya ƙarfinsa ya matse ta.
“Ba dalili bane, idan har kina son iyayen ki dole ne ki koma gare su, amman kin kasa kuma kin ƙi ki faɗa min gaskiya, saboda kin san mugun abun da kika aikata”
Yana kaiwa nan ya wurgar mata da fuska gefe, ya wuce ciki. Da kallo kawai ta bishi idonta na hawaye, wani irin zafi zuciyarta ke mata, ita kaɗai tasan irin abunda take ji.
Bata ganin laifin kowa sai Uzair da Namra, dan sune suka rusa mafarkinta, suka gurɓata duniyarta, suka canja tunaninta, sun salwantar da farincikinta, sune sanadin barin gidan iyayenta, sune suka sa duniya ta zage ta, sun yi nasarar sauyata daga mutum zuwa mutum mutumen da kowa ke kallonta.
Lallai bata da maƙiya kamar su, bata da wani buri illa na ganin bayan su. Har yanzu zuciyarta bata lurar da ita illar abunda ta aikatawa Namra ba, bata ganin asirin ne ya koma mata, gani take kamar da haɗin bakin Namra Uzair ya cuce ta.
Tana son komawa gida amman hakan sai ya gagareta, idan ta tuna yadda ta bar kowa nata, ta watsar da karatun ta, ta dawo nan ta zauna, sai taji kamar ta haɗiye zuciya ta mutu.
Rayuwarta ta zame mata kamar mafarki, yadda sauyin yazo mata, sai yayi mata kamar a shirin fim ko littafi, silar su ne take a cikin halin da take ciki. A yanzu kan bata da mafarki sai na Namra da Uzair bata da buri sai na su.
Ƙarar buɗe ƙofar gidansu da tayi ta fita ne ya dawo mata sabo, yadda ta kai kanta har tasa ta bar garin sokoto ne ya riƙa mata yawo a ƙwaƙwalwa.
Durƙushewa tayi a gurin ta fashe da wani irin mahaukacin kuka, tana yagar fuskarta. Da sauri Guy son ya fito daga ɗakin daya shiga yazo ya rumgume ta yana rarrashinta.
“Shiiiiiiiiiii, I'm sorry Amira, I'm so sorry”
Ya ɗora kansa saman na ta yana girgizata, alamar lallashi, har cikin kansa yake jin kukanta, son ta na masa yawa a ko ina na gaɓoɓinsa.
RASHIDA POV.
A inda suka ɗauke ta ɗazu, mutumen ya sauke ta, sai ta tari Napep ya kai ta unguwar da iyayenta suke. A nesa da gurin tasa ya sauke ta ta sallame shi, sannan ta taka da ƙafa ta ƙarasa cikin gidan.
Sai da ta buɗe motarta ta saka jakarta sannan ta, ta shiga cikin gidan, bakinta ƙumshe da sallama. Da far'ah Momy ta amsa mata.
“Ma'aikatan kuɗi yau a gidan na mu?”
“Wallahi kuwa, yau kin san babu aiki”
“Yau kuma har da hijabi! Aiko kin ga yadda ya fitar da ke, mashallah”
Zaunawa tayi tana murmushi.
“Momy kenan, shi saka Hijabi har wani abun ne?”
“Wani abun ne mana, shiyasa abokiyar zaman ki take burgeni saboda ta san kanta sosai, duk inda zaka ganta da hijabi zaka ganta, kin ga irin wannan matar? Da wahala wani namiji yayi mata maganar banza, Hijabi ne abu ne mai muhimmanci Rashida tun da har ki ga musulunci ya koyar da mu saka shi ai kinsan yana da kyau”
Ta ɗanyi murmushi, wanda be kai ciki ba murmushin rashin jindaɗin maganar da Momy tayi na Kalsoom.
“Nikan bana burge ki ko Momy?”
“Ba haka nake nufi ba, yadda ɗabi'unta da halayenta yake haka na so naki ya kasance, amman sai ki ari wata rayuwar ta daban kika ratayawa kanki, kika ɗauki wani hali wanda ban san inda kika samo shi ba kika laƙabawa kan ki”
“Uhmm Momy ban yi breakfast, yunwa nake ji sosai”
Ta faɗa da nufin kawar da wacan maganar ta Momy, shiyasa bata cikin son zuwa gidan ba, duk lokacin da tazo sai ance tayi wani abu ba dai-dai ba, yanzu ma abun ya wuce guri har abokiyar zamanta Momy take yabo, ita kam bata taɓa ganin uwar dake yabon kishiyar ɗiyarta ba sai nata uwar.
6ana ɗaya daga cikin dalilin dayasa Kalsoom ta zame mata ƙashin wuya, amman wannan matsalar da take ciki yasa ta ma manta da ita sai yanzu da Momy take tsokaro mata tsatsar ƙiyayyar da tayi mata katutu a zuciya.
A gidan da wuni, duk irin tambayar da Momy tayi mata na barin motar ta da tayi taje wani gurin, ƙin faɗar inda taje tayi, balle ma har ta faɗawa Momy dalilin zuwan nata.
Tasan bayan sallah magariba Hilal baya gida, dan a masallaci yake sallah magariba kuma baya shigowa gida sai anyi isha'i, hakan yasa ta dawo gida a lokacin, dan bata son ta dawo lokacin da yake nan.
Ta jidaɗin rashin ganin ɗaya daga cikin motocinsa hakan ya tabbatar mata da baya ma unguwar kenan, sai da ta cire hijabin ta bar a mota sannan ta fito, ta nufi hanyar falo.
Ɗora ƙafarta da zatayi sai gabanta ya faɗi, maido ƙafar tayi tayi baya-baya tana sauraren bugun zuciyarta.
Ta kusan minti biyar a haka, sannan ta kai hannu ta tura ƙofar ta shiga, bata ga alamun motsin kowa a gidan ba, hakan ya tabbatar mata da dukansu basa nan. Sai da ta leƙa ɗakin yaranta, taga babu kowa sannan ta nufi ɗakinta.
Jakarta ta fara ajewa tana sauke gajiya, sannan ta cire tufafin jikinta, ta shiga banɗaki tayi wanka, ta fito.
Dressing mirror ta nufa, ta shafa mai da turare sannan ta zauna tana nazarin duniyarta, idan har ta aikata abunda take da niya, to asirinta ya rufu, sai ɗayan kuma tana tunanin makomarta, akan abunda take ƙoƙarin aikatawa. Wani dogon numfashi taja ta sauke. Sam bata lura da takardun dake saman gadonta ba har sai da ta unƙura zata tashi.
Gabanta ya faɗi, a iya tunaninta bata san ta bar komai a saman gadonta da zata fita ba, sannan yanayin takardar be yi kama da documment ko file ba. Matsawa tayi kusa da gando ta kai hannu cikinn rawar jiki ta ɗauki takardaun.
Tana fara karantawa ta ji kamar an mata shocking, wani abu yazo mata tsam tun daga saman kanta har zuwa cikin ƙafafunta, bata ankaro da duniyar da take ciki ba, har sai da jini ya fara bin ƙafafunta.
NAMRA POV.
Sai da yamma sosai ƴan gidan suka dawo, abun walima ɗaya Inna ta bawa Mardiya tace su raba ita da Namra. A tare suka ci, lemun da yake ciki Namra tacw ba zata sha, ta bar ma Mardiya.
Bayan sallah magariba, ɗaya daga cikin matan gidan ta kawo ma, Namra tuwon masara da miyar ganye, haka Namra tayi ta tura abincin ba dan tana so ba, abun ka da wanda be saba ba.
Kaɗan kawai ta ci ta bar ma ƙannen Mardiya saura, ta wanke hannunta, sai ta koma kusa da Maman Mardiya ta zauna tana labarta mata zasu koma BQ, Inna tayi mata murna sosai, har tana cewa zata ƙara mata da wani abun.
A daren sun sha hira, ita da Inna sai labarin rayuwa take bata, irin gwargwarmayar da ta sha kamin ta kawo yanzu, da kuma labarin ƙurciyarsu ta ƙauye, wani abun na dariya wani na ban haushi, wani kuma na ɗaukar darasi.
Sai kusan goman dare Namra ta kwanta, har kuma lokacin Mardiya bata gidan, kuma sam hankalin Inna be tashi ba, bata ma nuna damuwarta akan rashin sanin inda Ƴarta take ba. Sai kusan shabiyun dare ta dawo gidan, tana ta wani ƙunshen-ƙunshe, suna sun-sun ita da Inna a tunaninsu Namra tayi bachi.
Sai kawai ta warware Mardiya da ta zo da shi. Har suka ci suka cinye Namra bata motsa ba balle ta nuna musu idonta ba, sun tana bachin ƙarya har na gasken yayi gaba da ita.
*WASHE GARI*
Inna ta bada aka siyo musu koko da ƙosai, sai ta siyo ma Namra waina, dan ta lura sam bata son koko, tun farkon kwananta gidan. Sai da ta ci ta ƙoshi, sannan ta nufi akwatin Mardiya dan ɗauko kuɗinta, da zimmar ta siya ma Asim abinci ta kai musu.
Bata ga jakar a inda ta aje ta ba, sai ta sa hannunta tana ta lalabawa, wayan bata ji komai ba, wale akwatin tayi tana duba sama-sama ko zata ganta, amman bata ganta ba.
Zata canye hannunta kenan sai taji abu ya zargi hannunta kamar an soke ta da allura, da sauri ta janye hannun tana raki.
“Waisss Ina jakar nan ta shiga ne”
Sai ta soma ɗaga tufafin ɗaya bayan ɗaya, tana dubata, ganin tayi kamar be dace ta ya mutsa mata kaya ba, saboda neman jaka wata ƙila ma ta ɓoye mata a wani gurin, ƙara kawai ta tambaye ta.
Har zata mai da kayan sai abu ya faɗo daga cikin ɗankwalin atamfar Mardiya, dubawar da Namra zata yi sai ta ga wayarta, da sauri ta kai hannu ta ɗauka.
No it can't be her phone, ta duba wayar gaba da baya.
“Wayata ce wannan this is my phone, how... ”
Sai kuma tayi shiru, tana nazari. Da sauri ta barkata kayan ta kai har ƙasan akwati, sai ga sarƙarta, da wasu manyan ƴan kunne nata, da agogon ta. Da sauri ta ɗauki ta miƙe tsaye tana mamaki.
Cikin wani irin bachin rai ta fito waje ta isa har inda Mardiya take zaune suka fira da Matan gida, ta ɗauke ta mari. Namra bata damu da matan da suke cikin gidan ba haka ta shararawa mardiya mari har huɗu tana hawaye.
*🌺🌺🌺 ZAGON ƘASA 🌺🌺🌺*
_Write by_
*Khadeeja Candy*
*PAGE - 37*
NOT EDITED ⚠
Sare saren jini ne ya fara zubar mata, amman hankalinta gaba ɗaya ya tattara ya koma gurin takardar.
‘Ga result ɗin da kike nema nan, da kuma wanda Doc Sabo ya bani jiya, ranar Monday, na biyun zai fito, idan har baki tsallake ba, za'a sake miki na uku, bana son kowa ya san sirrin mu, na yi alƙawarin rufa miki asiri saboda ƴaƴanmu, amman ba zan zauna dake ba Rashida idan har hakan ya tabbata, kar ki kuskura canja komai kar kiyi unƙurin yin komai, har sai gaskiya ta bayyana kuma na baki damar zuwa gida idan kina da buƙata, bana son wata alaƙa ta sake shiga tsakanin ki da su Ezzah a yanzu’
Taya zai mata katanga da yaranta? Taya asirinta zai tono tun yanzu, ba zata iya jure rashin Hilal ba ta shirya sadaukar da rayuwarta a gareshi, tana son mijinta, miyasa zata farka daga bachi tun yanzu? Baya mafarkinta be ƙare ba?
Wani irin ihu ta saka ta silale a gurin.
NAMRA POV.
Faɗuwa Mardiya tayi ƙasa daga kan turmin da take zaune, tana kallon Namra da mugun razana a fuskarta.
Gaba ɗaya matan gida sai hankalinsu ya tattara ya ya koma kan Mardiya da Namra. Babu wanda yace uffan har Inna da take Mahaifiyar Mardiya, dan tasan Namra ba zata mari Mari Mardiya haka kawai kawai ba.
“Ashe baki da zuciyar Imani? Duk zaman amanar da nake dake Zagon ƙasa kike min? Kina ganin yadda na yi ta neman wayar nan, ashe tana gareki kika ƙi faɗa min? Taya kika ɗauki sarƙa ta da ƴan kunne na? Faɗa!”
Namra ta faɗa a tsawace tana mai jin kamar ta kama Mardiya ta ɓanlata gida-gida, ta watsar. A nan matan gidan kowa ya fara sun-sun da kai suna kallon-kallon ma junansu, daman sun daɗe suna jiran zuwan wannan ranar, tun da sun san Mardiya ta na ɗan ɗauke-ɗauke kuma sun san ba zata rasa yi ma Namra ba, tun da halinta ne.
Murje ido Mardiya tayi, ta mayarda hawayen da suke son zuba mata, wani dakewar zuciya ta samu kanta da ita, na mayarda ƙaryarta ta zama gaskiya.
“Namra ya kamata ace kina bincike kamin ki aikata abu, kuɗin ki na canja musu muhalline, sannan ni ban ɗaukar ka miki waya ba balle kuma sarƙa, sai idan wani sherin zaki min”
Tassss Namra ta sake marinta ta turata can baya har ta faɗi.
“Munafuna mai siffar ƴan wuta, nayi farinciki da Allah ya nuna min ko wacece ke tun a yanzu, na yi nadamar sanin ki a rayuwarta, baki da imani ba ki da tausayi Mardiya, duk irin halin da nake ciki sai da kika ƙafe zuciya kika min sata? Ɗaukar haƙƙin wani? kuma ki jira sakamakon ki”
Wannan karon Mardiya hawaye take. Mahaifiyarta ta matso tana hantarar Namra, magangannunta sun ɓata mata rai sosai, tana ganin dan me Namra zata musu haka.
“Amma ke kam ba ƴa bace sam baki da mutunci, ai komai Mardiya tayi miki ya kamata ace kin taushe zuciyarki kin ɗaga mata ƙafa, balle ma bayi ba dan ban haifi ɓarauniya ba”
Namra ta kalleta da jajayen idanuwanta, ta yarfe ta da hannu.
“Kin ji kunya Wallahi, tirr da uwa irin ki mai ɗaurewa ƴarta gindi tana abunda take so, uwar da ƴarta zata sa ƙafa ta fita ba zata dawo sai taga dama kuma hankalin ki kwance, sai murna kike tana kawo miki abunda
Showing 78001 words to 81000 words out of 280121 words
Ina roƙon duk wanda na ɓatawa rai sanadin canjin nan ko kuma littafin nan, dan Allah ku yafe min, nima ban za ci sauyin zai zo ba, sai daga baya, da tun farko na faɗa. Ina roƙon alfarma dan Allah kar wanda ya mai da min da Littafi document.
Na gode da shawarwari da ƙauna, Allah ya sakawa kowa da Alheri. I love you all
BEST REGARDS 💖🌺
KHADEEJA CANDY 😘
*🌺🌺🌺 ZAGON ƘASA 🌺🌺🌺*
_Write by_
*Khadeeja Candy*
*PAGE - 36*
NOT EDITED ⚠
Nitsa kai suka yi tayi cikin unguwar, sun yi tafiyar mintina goma zuwa sha uku, sannan suka isa ƙarshen unguwar, a bakin wani makeken gate black color.
Tsoron dake cikin zuciyar Rashida ya kasa ɓoyuwa har sai da ya nuna a jikinta, gani take kamar wani abun zasu mata har ta buɗe baki tayi magana, sai ta tuna da abunda ya kawo ta gurin, kuma ta san bata da wata mafita sai wannan.
Sai kawai tayi shiru da bakinta ta sakar musu na mujiya har suka faka bakin wata babbar ƙofa. Amira ce ta fara fita tana faɗin
“Fito muje”
Buɗewa Rashida tayi ta fito, sai mutun ya ja motar ya nufi wani ɓangare na gidan da ita.
Amira tayi gaba, Rashida ta rufa mata baya sai kalle-kallen gidan take.
Cikin wani ƙaton falo suka shiga, wanda aka ƙawata da kayan alatu, kallon falon tayi sosai ba dan ya birge ta ba, sai dan ɗaukar rahoto ta karanci wane irin gida ne aka a kawo ta.
Kamar daga sama ta ji Amira na mata magana.
“Idan baki yarda da gidan ba, miyasa kika shigo? Ko kina tunanin za mu miki wanin abun ne?”
Kasa cewa komai, tayi har Amira ta gaji da tsayi a gurin, ta isa gaban wata babbar kujera ta zauna tana cire gyalen abayarta.
“Guy Son!”
Ta ƙwala mishi kira, tana nuna ma Rashida kujera.
“Zauna idan zaki iya”
Rashida ta zauna zuciyarta na ɗar-ɗar, wani tunanin ne ya zo mata. What if tafa mutumen data sani? Ko kuma gidan yana tare da Dr Sabo fa?
Fitowarsa yayi dai-dai da sauke ajiyar zuciyar da Rashida ta yi, a yanayin shigarsa da kamalarsa, bata zace shine Guy Son ɗin ba har sai da ya zauna kusa da Amira, jikinsa yana Gugar na Amira.
“Wa kike son ayi miki garkuwa?”
Ya tambaya, fuska babu alamar murmushi balle wasa.
“Wani mutun ne, sunan shi Doc Sabo a asibin Alex yake aiki sashen jini”
“Cire Niƙab ɗin fuskarki kiyi mana bayanin komai”
Tasa hannu ta cire Niƙabin ta gyara zamanta sannan tace
“Mijina ne ya ɗibi jinina dana yara na ya kai masa akan yayi mana gwaji, bana da tabbaci amman ina jin kamar ina ɗauke da cutar hiv kuma ina tunanin mijina da kishiyata basa da shi, na karɓi numbersa gurin abokin aikina na kira mun yi magana akan zai faɗa min idan mijina ya kawo jinin, har na tura masa dubu ɗari, sai gashi ya yaudare ya faɗawa mijina na bashi kuɗi”
Ya kai hannunshi ya riƙa hannun Amira yasa yatsunsa cikin nata.
“So kina son ayi forcing ɗinsa ya canja result ɗin ko?”
“Haka nake so, matuƙar ya faɗi gaskiya, mijina zai rabu da ni, kuma duniya zata ƙyamace ni, zan ba ku ko nawa kake so, dan Allah ku taimaki rayuwata”
Amira ta ɗan yi murmushi.
“Ba shi kike son ayi a ɗauke miki ba, ƴaƴansa za'ayi kidnapped sai asa shi dole ya faɗi abunda kike so”
“Koma yaya ne ni dai yi min zan biya ko nawa kuke so”
Ta faɗa tana karyar da murya irin tausayin nan. Wayar dake hannu ya karɓa, ya saka wata number ya kira, ana picking yace
“Zo nan ina neman ka”
Be fi mintuna uku da aje wayar ba, sai ga mutumen ya shigo cikin ƙaƙanan tufafi, yazo dai-dai shi ya tsaya, Rashida na kallonsa gabanta ya faɗi saboda jan idonsa.
“Ka bincika min addireshin Doc Sabo yana aiki a Alex hospital sashen jini”
“Okay Boss”
Sai ya juya ya fice. Guy son ya kalli Rashida ya ce
“Bani addireshin ki, kuma karki kuskura ba ni na ƙarya dan zan gano ki”
Gabanta ya faɗi sosai, kuma ta tsorata, bata son bashi na ƙarya tun da har ya gargaɗeta, sai dai kuma idan har ta ba shi adireshin na gaskiya, bata san abunda zai faru ba.
“Sunana Rashida Abdullahi Kardam ina aiki a Stanbic Ibtc Bank, mijina babban likita ne, yana aiki a Kaduna special hospital, muna nan GRA magaji road”
“You can go, zaki ga motar data kawo ki zata maida ke inda kike”
“Thank you”
Ta saka niƙabinta ta saka sannan ta ɗauki jakarta ta fice. Amira ta tashi ta nufi gurin window falon ta tsaya, tana kallon harabar gidan. Tana sinkayar motar har suka fice, sannan ta sauke ajiyar zuciya, ta jingina da gurin ta rufe ido.
Hannunshi yasa cikin jikinta yana murza fatar jikinta, ya fara shinshinar gefen wuyanta. Buɗe idon ta yi ta ture shi da dukan ƙarfinta.
Kallon da zai yi sai hawaye ya gani sun silalo daga idonta. Yarfarda hannu yayi ya cije fuska.
“So nawa zan faɗa miki bana son hawayen nan”
“Ka bar ni nayi kuka na, ai ina da dalilin kuka”
Hannu ya kai ya riƙe fuskarta iya ƙarfinsa ya matse ta.
“Ba dalili bane, idan har kina son iyayen ki dole ne ki koma gare su, amman kin kasa kuma kin ƙi ki faɗa min gaskiya, saboda kin san mugun abun da kika aikata”
Yana kaiwa nan ya wurgar mata da fuska gefe, ya wuce ciki. Da kallo kawai ta bishi idonta na hawaye, wani irin zafi zuciyarta ke mata, ita kaɗai tasan irin abunda take ji.
Bata ganin laifin kowa sai Uzair da Namra, dan sune suka rusa mafarkinta, suka gurɓata duniyarta, suka canja tunaninta, sun salwantar da farincikinta, sune sanadin barin gidan iyayenta, sune suka sa duniya ta zage ta, sun yi nasarar sauyata daga mutum zuwa mutum mutumen da kowa ke kallonta.
Lallai bata da maƙiya kamar su, bata da wani buri illa na ganin bayan su. Har yanzu zuciyarta bata lurar da ita illar abunda ta aikatawa Namra ba, bata ganin asirin ne ya koma mata, gani take kamar da haɗin bakin Namra Uzair ya cuce ta.
Tana son komawa gida amman hakan sai ya gagareta, idan ta tuna yadda ta bar kowa nata, ta watsar da karatun ta, ta dawo nan ta zauna, sai taji kamar ta haɗiye zuciya ta mutu.
Rayuwarta ta zame mata kamar mafarki, yadda sauyin yazo mata, sai yayi mata kamar a shirin fim ko littafi, silar su ne take a cikin halin da take ciki. A yanzu kan bata da mafarki sai na Namra da Uzair bata da buri sai na su.
Ƙarar buɗe ƙofar gidansu da tayi ta fita ne ya dawo mata sabo, yadda ta kai kanta har tasa ta bar garin sokoto ne ya riƙa mata yawo a ƙwaƙwalwa.
Durƙushewa tayi a gurin ta fashe da wani irin mahaukacin kuka, tana yagar fuskarta. Da sauri Guy son ya fito daga ɗakin daya shiga yazo ya rumgume ta yana rarrashinta.
“Shiiiiiiiiiii, I'm sorry Amira, I'm so sorry”
Ya ɗora kansa saman na ta yana girgizata, alamar lallashi, har cikin kansa yake jin kukanta, son ta na masa yawa a ko ina na gaɓoɓinsa.
RASHIDA POV.
A inda suka ɗauke ta ɗazu, mutumen ya sauke ta, sai ta tari Napep ya kai ta unguwar da iyayenta suke. A nesa da gurin tasa ya sauke ta ta sallame shi, sannan ta taka da ƙafa ta ƙarasa cikin gidan.
Sai da ta buɗe motarta ta saka jakarta sannan ta, ta shiga cikin gidan, bakinta ƙumshe da sallama. Da far'ah Momy ta amsa mata.
“Ma'aikatan kuɗi yau a gidan na mu?”
“Wallahi kuwa, yau kin san babu aiki”
“Yau kuma har da hijabi! Aiko kin ga yadda ya fitar da ke, mashallah”
Zaunawa tayi tana murmushi.
“Momy kenan, shi saka Hijabi har wani abun ne?”
“Wani abun ne mana, shiyasa abokiyar zaman ki take burgeni saboda ta san kanta sosai, duk inda zaka ganta da hijabi zaka ganta, kin ga irin wannan matar? Da wahala wani namiji yayi mata maganar banza, Hijabi ne abu ne mai muhimmanci Rashida tun da har ki ga musulunci ya koyar da mu saka shi ai kinsan yana da kyau”
Ta ɗanyi murmushi, wanda be kai ciki ba murmushin rashin jindaɗin maganar da Momy tayi na Kalsoom.
“Nikan bana burge ki ko Momy?”
“Ba haka nake nufi ba, yadda ɗabi'unta da halayenta yake haka na so naki ya kasance, amman sai ki ari wata rayuwar ta daban kika ratayawa kanki, kika ɗauki wani hali wanda ban san inda kika samo shi ba kika laƙabawa kan ki”
“Uhmm Momy ban yi breakfast, yunwa nake ji sosai”
Ta faɗa da nufin kawar da wacan maganar ta Momy, shiyasa bata cikin son zuwa gidan ba, duk lokacin da tazo sai ance tayi wani abu ba dai-dai ba, yanzu ma abun ya wuce guri har abokiyar zamanta Momy take yabo, ita kam bata taɓa ganin uwar dake yabon kishiyar ɗiyarta ba sai nata uwar.
6ana ɗaya daga cikin dalilin dayasa Kalsoom ta zame mata ƙashin wuya, amman wannan matsalar da take ciki yasa ta ma manta da ita sai yanzu da Momy take tsokaro mata tsatsar ƙiyayyar da tayi mata katutu a zuciya.
A gidan da wuni, duk irin tambayar da Momy tayi mata na barin motar ta da tayi taje wani gurin, ƙin faɗar inda taje tayi, balle ma har ta faɗawa Momy dalilin zuwan nata.
Tasan bayan sallah magariba Hilal baya gida, dan a masallaci yake sallah magariba kuma baya shigowa gida sai anyi isha'i, hakan yasa ta dawo gida a lokacin, dan bata son ta dawo lokacin da yake nan.
Ta jidaɗin rashin ganin ɗaya daga cikin motocinsa hakan ya tabbatar mata da baya ma unguwar kenan, sai da ta cire hijabin ta bar a mota sannan ta fito, ta nufi hanyar falo.
Ɗora ƙafarta da zatayi sai gabanta ya faɗi, maido ƙafar tayi tayi baya-baya tana sauraren bugun zuciyarta.
Ta kusan minti biyar a haka, sannan ta kai hannu ta tura ƙofar ta shiga, bata ga alamun motsin kowa a gidan ba, hakan ya tabbatar mata da dukansu basa nan. Sai da ta leƙa ɗakin yaranta, taga babu kowa sannan ta nufi ɗakinta.
Jakarta ta fara ajewa tana sauke gajiya, sannan ta cire tufafin jikinta, ta shiga banɗaki tayi wanka, ta fito.
Dressing mirror ta nufa, ta shafa mai da turare sannan ta zauna tana nazarin duniyarta, idan har ta aikata abunda take da niya, to asirinta ya rufu, sai ɗayan kuma tana tunanin makomarta, akan abunda take ƙoƙarin aikatawa. Wani dogon numfashi taja ta sauke. Sam bata lura da takardun dake saman gadonta ba har sai da ta unƙura zata tashi.
Gabanta ya faɗi, a iya tunaninta bata san ta bar komai a saman gadonta da zata fita ba, sannan yanayin takardar be yi kama da documment ko file ba. Matsawa tayi kusa da gando ta kai hannu cikinn rawar jiki ta ɗauki takardaun.
Tana fara karantawa ta ji kamar an mata shocking, wani abu yazo mata tsam tun daga saman kanta har zuwa cikin ƙafafunta, bata ankaro da duniyar da take ciki ba, har sai da jini ya fara bin ƙafafunta.
NAMRA POV.
Sai da yamma sosai ƴan gidan suka dawo, abun walima ɗaya Inna ta bawa Mardiya tace su raba ita da Namra. A tare suka ci, lemun da yake ciki Namra tacw ba zata sha, ta bar ma Mardiya.
Bayan sallah magariba, ɗaya daga cikin matan gidan ta kawo ma, Namra tuwon masara da miyar ganye, haka Namra tayi ta tura abincin ba dan tana so ba, abun ka da wanda be saba ba.
Kaɗan kawai ta ci ta bar ma ƙannen Mardiya saura, ta wanke hannunta, sai ta koma kusa da Maman Mardiya ta zauna tana labarta mata zasu koma BQ, Inna tayi mata murna sosai, har tana cewa zata ƙara mata da wani abun.
A daren sun sha hira, ita da Inna sai labarin rayuwa take bata, irin gwargwarmayar da ta sha kamin ta kawo yanzu, da kuma labarin ƙurciyarsu ta ƙauye, wani abun na dariya wani na ban haushi, wani kuma na ɗaukar darasi.
Sai kusan goman dare Namra ta kwanta, har kuma lokacin Mardiya bata gidan, kuma sam hankalin Inna be tashi ba, bata ma nuna damuwarta akan rashin sanin inda Ƴarta take ba. Sai kusan shabiyun dare ta dawo gidan, tana ta wani ƙunshen-ƙunshe, suna sun-sun ita da Inna a tunaninsu Namra tayi bachi.
Sai kawai ta warware Mardiya da ta zo da shi. Har suka ci suka cinye Namra bata motsa ba balle ta nuna musu idonta ba, sun tana bachin ƙarya har na gasken yayi gaba da ita.
*WASHE GARI*
Inna ta bada aka siyo musu koko da ƙosai, sai ta siyo ma Namra waina, dan ta lura sam bata son koko, tun farkon kwananta gidan. Sai da ta ci ta ƙoshi, sannan ta nufi akwatin Mardiya dan ɗauko kuɗinta, da zimmar ta siya ma Asim abinci ta kai musu.
Bata ga jakar a inda ta aje ta ba, sai ta sa hannunta tana ta lalabawa, wayan bata ji komai ba, wale akwatin tayi tana duba sama-sama ko zata ganta, amman bata ganta ba.
Zata canye hannunta kenan sai taji abu ya zargi hannunta kamar an soke ta da allura, da sauri ta janye hannun tana raki.
“Waisss Ina jakar nan ta shiga ne”
Sai ta soma ɗaga tufafin ɗaya bayan ɗaya, tana dubata, ganin tayi kamar be dace ta ya mutsa mata kaya ba, saboda neman jaka wata ƙila ma ta ɓoye mata a wani gurin, ƙara kawai ta tambaye ta.
Har zata mai da kayan sai abu ya faɗo daga cikin ɗankwalin atamfar Mardiya, dubawar da Namra zata yi sai ta ga wayarta, da sauri ta kai hannu ta ɗauka.
No it can't be her phone, ta duba wayar gaba da baya.
“Wayata ce wannan this is my phone, how... ”
Sai kuma tayi shiru, tana nazari. Da sauri ta barkata kayan ta kai har ƙasan akwati, sai ga sarƙarta, da wasu manyan ƴan kunne nata, da agogon ta. Da sauri ta ɗauki ta miƙe tsaye tana mamaki.
Cikin wani irin bachin rai ta fito waje ta isa har inda Mardiya take zaune suka fira da Matan gida, ta ɗauke ta mari. Namra bata damu da matan da suke cikin gidan ba haka ta shararawa mardiya mari har huɗu tana hawaye.
*🌺🌺🌺 ZAGON ƘASA 🌺🌺🌺*
_Write by_
*Khadeeja Candy*
*PAGE - 37*
NOT EDITED ⚠
Sare saren jini ne ya fara zubar mata, amman hankalinta gaba ɗaya ya tattara ya koma gurin takardar.
‘Ga result ɗin da kike nema nan, da kuma wanda Doc Sabo ya bani jiya, ranar Monday, na biyun zai fito, idan har baki tsallake ba, za'a sake miki na uku, bana son kowa ya san sirrin mu, na yi alƙawarin rufa miki asiri saboda ƴaƴanmu, amman ba zan zauna dake ba Rashida idan har hakan ya tabbata, kar ki kuskura canja komai kar kiyi unƙurin yin komai, har sai gaskiya ta bayyana kuma na baki damar zuwa gida idan kina da buƙata, bana son wata alaƙa ta sake shiga tsakanin ki da su Ezzah a yanzu’
Taya zai mata katanga da yaranta? Taya asirinta zai tono tun yanzu, ba zata iya jure rashin Hilal ba ta shirya sadaukar da rayuwarta a gareshi, tana son mijinta, miyasa zata farka daga bachi tun yanzu? Baya mafarkinta be ƙare ba?
Wani irin ihu ta saka ta silale a gurin.
NAMRA POV.
Faɗuwa Mardiya tayi ƙasa daga kan turmin da take zaune, tana kallon Namra da mugun razana a fuskarta.
Gaba ɗaya matan gida sai hankalinsu ya tattara ya ya koma kan Mardiya da Namra. Babu wanda yace uffan har Inna da take Mahaifiyar Mardiya, dan tasan Namra ba zata mari Mari Mardiya haka kawai kawai ba.
“Ashe baki da zuciyar Imani? Duk zaman amanar da nake dake Zagon ƙasa kike min? Kina ganin yadda na yi ta neman wayar nan, ashe tana gareki kika ƙi faɗa min? Taya kika ɗauki sarƙa ta da ƴan kunne na? Faɗa!”
Namra ta faɗa a tsawace tana mai jin kamar ta kama Mardiya ta ɓanlata gida-gida, ta watsar. A nan matan gidan kowa ya fara sun-sun da kai suna kallon-kallon ma junansu, daman sun daɗe suna jiran zuwan wannan ranar, tun da sun san Mardiya ta na ɗan ɗauke-ɗauke kuma sun san ba zata rasa yi ma Namra ba, tun da halinta ne.
Murje ido Mardiya tayi, ta mayarda hawayen da suke son zuba mata, wani dakewar zuciya ta samu kanta da ita, na mayarda ƙaryarta ta zama gaskiya.
“Namra ya kamata ace kina bincike kamin ki aikata abu, kuɗin ki na canja musu muhalline, sannan ni ban ɗaukar ka miki waya ba balle kuma sarƙa, sai idan wani sherin zaki min”
Tassss Namra ta sake marinta ta turata can baya har ta faɗi.
“Munafuna mai siffar ƴan wuta, nayi farinciki da Allah ya nuna min ko wacece ke tun a yanzu, na yi nadamar sanin ki a rayuwarta, baki da imani ba ki da tausayi Mardiya, duk irin halin da nake ciki sai da kika ƙafe zuciya kika min sata? Ɗaukar haƙƙin wani? kuma ki jira sakamakon ki”
Wannan karon Mardiya hawaye take. Mahaifiyarta ta matso tana hantarar Namra, magangannunta sun ɓata mata rai sosai, tana ganin dan me Namra zata musu haka.
“Amma ke kam ba ƴa bace sam baki da mutunci, ai komai Mardiya tayi miki ya kamata ace kin taushe zuciyarki kin ɗaga mata ƙafa, balle ma bayi ba dan ban haifi ɓarauniya ba”
Namra ta kalleta da jajayen idanuwanta, ta yarfe ta da hannu.
“Kin ji kunya Wallahi, tirr da uwa irin ki mai ɗaurewa ƴarta gindi tana abunda take so, uwar da ƴarta zata sa ƙafa ta fita ba zata dawo sai taga dama kuma hankalin ki kwance, sai murna kike tana kawo miki abunda
Book Chapters
Chapter 1Chapter 2Chapter 3Chapter 4Chapter 5Chapter 6Chapter 7Chapter 8Chapter 9Chapter 10Chapter 11Chapter 12Chapter 13Chapter 14Chapter 15Chapter 16Chapter 17Chapter 18Chapter 19Chapter 20Chapter 21Chapter 22Chapter 23Chapter 24Chapter 25Chapter 26Chapter 27 Chapter 28Chapter 29Chapter 30Chapter 31Chapter 32Chapter 33Chapter 34Chapter 35Chapter 36Chapter 37Chapter 38Chapter 39Chapter 40Chapter 41Chapter 42Chapter 43Chapter 44Chapter 45Chapter 46Chapter 47Chapter 48Chapter 49Chapter 50Chapter 51Chapter 52Chapter 53Chapter 54Chapter 55Chapter 56Chapter 57Chapter 58Chapter 59Chapter 60Chapter 61Chapter 62Chapter 63Chapter 64Chapter 65Chapter 66Chapter 67Chapter 68Chapter 69Chapter 70Chapter 71Chapter 72Chapter 73Chapter 74Chapter 75Chapter 76Chapter 77Chapter 78Chapter 79Chapter 80Chapter 81Chapter 82Chapter 83Chapter 84Chapter 85Chapter 86Chapter 87Chapter 88Chapter 89Chapter 90Chapter 91Chapter 92Chapter 93Chapter 94