karatu a nan ba, a lokacin govnati na ɗaukar nauyin karatun saboda ana ƙyamar bokon ne, so duk wanda ke da ilmi za a ɗauki nauyinsa zuwa ƙasar waje karatu, Zuwaira da Murja da Sadiq su aka saka a ƙarƙashin govnati ni kuma shi ya biya min a cikin aljihunsa. Dukan mu mun yi karatu, duk da ba ƙasa ɗaya aka kai mu ba, dan ni na zaɓi London ne, su kuma Egypt aka kaisu suka yi karatun lafiya.
Na fi sawa shashanci gaba, saboda farar fatar da nake tare da su, na kan rakasu gurare daban-daban hakan yasa muka shaƙu da su sosai. Su san burina saboda ina yawan faɗa cewar nafi son nafi kowa ɗaukaka a makarantar nan, ranar sai wata take ce mun zata faɗa min wani sirri, zata kai ni inda za'a taimaka min na samu ilmin da ya fi na kowa, kuma na fi kowa ɗaukaka a makarantar. Ban yi musu ba, na biyeta ta sani a cikin wata ƙungiya, ashe ƙungiyar asirice, buƙatata ta biya tabbas, saboda a wannan shekarar ni nayi ta ɗaya a duk faɗin makarantar, daga haka sai abubuwa suka buɗe, duk abunda nake da bukata zan je ne kawai na faɗa kuma sai buƙata ta biya, a lokacin muna meet duk ƙarshen wata, amman lokacin dana ƙare karatun na dawo nan sai suka haɗi ni da manyan da suke abuja, a nan naga manyan mutane, maza da mata a cikin har da manyan ƙasar nan. Duk lokacin da za'ayi meeting ɗin, na kan bar Katsina na je abuja da sunan ganin wata Sister mu ƴar sarki, sai naje meeting idan an gama da kwana biyu na sai na dawo.
Na samu babban aiki a lokacin, nama fi kowa kuɗi a gidan mu, da haka na haɗu da baban su Nabila. Bayan mun yi aure yace baya son aiki, sai na haƙura, a nan su kuma suka soma saka min ƙa'idojin da ban san da su ba a wacan lokacin.
Sun ce min dole ne na riƙa neman mata ƴan'uwana, idan ba haka ba, ba su yarda na fitar da zakka ba. A dole na ɗauki ka'idar mu'amala da mata ƴan'uwana, tun ban saba ba har abun ya zame min jiki, ya koma bana jin daɗi mu'amala da mijina sai mata. Daga baya kuma suka ce suna son a riƙa kawo musu sabbin membobi saboda tsofin ciki suna mutuwa ne, kuma ina son a riƙa yaɗa abun.
A abuja nake zaune da mijina, ɗan haka duk lokacin da naso zuwa kawai nake gurin meeting ɗin ba tare da ya sani ba, wata rana da muka yi meeting sai suka ce suna da buƙatar na Sadaukar musu wani daga cikin iyalaina, ba ni da zaɓi dole na bada mijina, sai ya samu haɗarin mota ya mutu, daga nan kuma sai babban ɗa na, sai mai binsa, sannu-sannu suka cinye min duka ƴaƴana, Nabila ce kawai ta rage min. Shekaran jiya da nace maka zanje birnin keebi ba can naje ba, Abuja na je, gurin meeting ɗin. Yanzu kuma Nabila suke so, ko ɗanta. Ni ko da na bada ita ƙara na bayarda kai na, shiyasa nake son ka taimake ni, ka ceci rayuwata da ta ƴata saboda ita kaɗai ta rage min”
Asim ya sake miƙewa tsaye a karo na biyu.
“Wallahi Allah yana so na, wato da yanzu sai dai ki bada ni? Dan nasan zasu ma iya cewa ki kawo yaron gidanki, ko kuma idan mun yi aure ace ko bada surikin ƴar ki, ai ni duk sun kuɗi na be kai na iya rayuwata ba kuma ni daga yau na barki har a bada wallahi”
“Kar kayi saurin yanke hukuncin Asim kaje ka yi tunani”
“Ba wani tunani da zan yi, salon ki sani cikin mugun hali”
“Da ina da niyar saka ka da na saka tun farkon dana saka tun farko dana fahimci kana da son kuɗi, amman ba kai nake target ba matarka, saboda nasan idan na sata cikin ƙungiyar zasu biya kuɗi mai yawa wata ƙila ma ya iya zama fansar ƴata, amman sai gashi ka saki matarka, da yanzu ace zaka iya kawo min matarka zasu iya ɗaga min ƙafa”
Tsayawa yayi kallonta.
“Indai har Namra zata iya zana fansar ƴarki to zan iya kawo miki ita, bisa sharaɗin zaki bani naira billion uku”
“Wallahi zan baka, kuɗi ba matsala ta bace idan na faɗa maka abunda na tara sai ka haukace, kuma Namra ba kasheta zamu yi ba Wallahi, cikin ƙungiyar kawai za mu sakata”
“Amman taya zan kawo miki ita?”
“Zaka maida aurenka, sannan duk abunda zai biyo baya ya biyo, kuma idan kana so zaka iya auren Nabila”
“Ƴarki kam na yafe, amman Namra zaki sameta kamar yadda kike buƙata”
Ta miƙe tsaye ta shiga ɗakinta bata jima.ba ta fito riƙe da amt ta miƙa masa.
“Akwai milion talatin a ciki kayi amfani da su”
Ya miƙa hannu ya karɓa sannan ya juya ya fice.
TEEMA POV.
Tana kwance saman jikinsa, shi kuma sai faman dannar waya yake yana murmushi. Azatonta dan tana shafa jikinsa yake murmushi, shi kam hankalinsa gaba ɗaya ya tafi kan waya sai faman chating yake da Kalsoom.
Ƙyalƙyalewa yayi da dariya sannan ya kashe datarsa ya kalleta.
“Bari na leƙa office”
“Okay Allah ya tsare min kai”
“Amin dear. Amm anjima Hajiya tace zata aiko da su Ezzah”
Sam bata ji daɗi ba, duk da tasan dalilinsu aka auro ta, amman bata yarda ta nuna masa ba.
“Kai Amman ko na jidaɗi daman ina ta jiran su zo, Allah kawo su lafiya”
“Amin”
Ya faɗa yana ɗaukar hulal dake saman hannu kujera ya saka a kai.
“Okay I love you”
“Love you too”
Da kallo ta bishi sai da ya fice sannan ta miƙe tsaye.
“Sati uku da aure ace za a ɗauko yara a kawo maka, nifa ba bautarsu na zo yi ba, ko amarci ban gama ci ba za'a haɗa ni da ala ƙai ƙai, yara zaggan-zaggan da su, su riƙa sa maka ido idan ka yi ma miji wani abu, mtsssss”
Taja wani uban tsaki ta wuce bedroom ɗinta. Bata jima ba ta fito ta nufi kitchen, girki ta ɗora sai mita take ranta duk a ɓace, dan har ga Allah bata so a kawo su yanzu ba.
“Daman fa ance wasu uwayen miji ba son suruka suke ba, in banda sheri kin san ina Amarya ɗan Amarcin ma ba za'a bari na yi ba, kai kayi naka lokacin sai kace wani ba zai yi ba, nasan dan su aka auro ni amman ai a bari na ci lokacina, tun da can ba saman ƙaya suke ba, daga zuwanka da ƙurciya zaka fara aikin ƴaƴan kishiya”
Kamar mai faɗa da wani haka ta riƙa zuba surutanta har ta yi girkin ta gama mita take, sai da tasa komai a muhallinsa sannan ta shiga ciki ta yi wanka. Tana fitowa ta shirya cikin yellow atamfa, ta kashe ɗauri ta feshe jikinta da turare sannan ta fito falo ta zauna.
Tana jin tsayawar mota ta ƙara gyara ɗaurin ɗankwalinta, tana zaton ko Hilal sai kawai ta ji mota ta tashi, su Ezzah sun turo ƙofa sun shigo fuskarsu da far'ah bakinsu kuma ƙumshe da sallama.
Ciki-ciki ta amsa musu tana murmushin da be kai zuci ba.
“Maraba da ƴaƴana”
“Momi ina wuni? Momi ina wuni?”
“Lafiya ƙalau”
Sai suka zauna saman kujera. Daga nan bata sake bi ta kansu ba, sai da ta ji motar Hilal sannan ta tashi ta koma tsakiyarsu ta zauna ta jasu jikinta ta rumgume tana murmushi.
“Ku bani labarin Hajiya...”
ABDOOL POV.
Around ten ya sauka Katsina, sai da ya fara biyawa Mai Martaba ya ganshi sannan ya wuce gurin Ummi. Da murmushi ya shiga part ɗin Ummi, kamar yasan ita kaɗaice a falon, dan duk ƙannensa sun tafi makaranta.
“Ummi barka da safe”
Ya taɓe baki tana kallonsa.
“Ni ban ga amfanin wannan hutu naka ba, kullum kai ne yawo ba zama gida, yanzu da aure kake yi wace mace ce zata ɗauki wannan rayuwar”
Kusa da ita ya zauna yana dariya.
“To ai gurin matar na je, yau zan baki labarin komai saboda na samu mafitar matsala ta, amman fa nasha wuya but at the end yau tace min Thank you”
“Kana nan kana wahalar da ƴar mutane ai dole wata ta saka cin kwakwa, tun da ka tagi Amirar nan kuka take, na rasa gane kanta idan kuma na tambaye ta sai tace babu komai, yau ma ce min tayi gida zata je daker na hana ta”
“Ina take?”
“Tana ɗakinta”
Ya miƙe tsaye ya nufi ɗakin Amal. Yana tura ƙofar ɗakin ta ɗago ta kalleshi sai kuma ta juya,
“Amira can we talk?”
“Maybe Later i need some space”
Ta faɗa da muryarta ta kuka.
“Okay but i just want you to know that i care for you, if you need someone to talk to, i'm downstairs”
Daga haka ya juya ya fice. Ita kuma. Ta fashe da kuka.
*78*
Kusa da Ummi ya sake zama yana kallon tv.
“Tana son ta saka kanta cikin matsala ne kawai Ummi amman tasan ba zan taɓa son ta ba”
“Nasan tana son ka har zuciyarta, amman sam ban yarda da yarinyar nan ba, mutanen da sukayi ƙoƙarin su kashe ka, waya sani ko plan ne aka yi ta yadda idan ta aure ka zata fin jindaɗin kashe ka”
Yayi murmushin gefen baki.
“Ko babu plan Ummi bana son ta, ko da kuwa tun can farko ita mai tarbiya ce, because if i love someone i mean it no matter what she did or whoever she is, and if i said i do i do, so i don't love Amira, i only fell in love once because i have never been in that kind of situation, but when it comes to Namra i take it so serious, and i love with all my heart and blood and mind and soul i love her more than you think Ummi”
Ajiyar zuciya Ummi ta sauke, ta kalli ɗanta fuskarta da alamun damuwa.
“Tell me more about her”
Miƙewa ya yi tsaye ya nufi freezer.
“She's so simple and kind, but difficult to handle. You know when we first meet, she slap me and insult me in front of my boys, but i can't slap her back”
Ya ƙarasa yana bulbula ruwan da ya fiddo a cup. Ummi ta yi murmushi.
“I know how my son is ba ya faɗa da mata”
“Yap bana faɗa da mata because we are not in the same level, strength, brain, heart, soul and lot. Ban taɓa jin ina son wata mace ba, but lokacin da na ji ina son Namra, nasan our souls mean to be, duk da a lokacin na san tana da aure, amman zuciya ta kasa haƙura, and now what! Her husband divorce her ta je wani gida ta zauna, kuma ƙaddara ta sake haɗa mu kaduna na kaɗe yaron gidan ina zuwa sai gata a gidan, hmm' mmm funny, and now ni ne silar shiryawa da iyayenta, i hope you love her too?”
“Of course i love her ai dole naso matar da ɗa na yake so, but i'm just worried about Mai Martba, ba lalle ne shi ya so ta”
“Why”
“Saboda Bazawara ce! And i hear that Mai Martaba and Hajiya Shafa sun maka mata”
“What...!”
Ya aje cup ɗin ruwa dake hannunsa saman dinning yana kallonta fuskarsa cike da tashin hankali.
“How true it's?”
“Mai Martaba ya kira ni da kan shi, yana neman shawara akan zai ɗoraka a Sarautar Katsina, da na nuna masa be dace ba sai ya nuna ɓacin ransa, the following day ya sake kira a waya ya faɗa min Hajiya Shafa tace be kamata a ɗoraka a Saurata baka tare da iyalaiba, dan haka ta maka mata, zata aura maka Zaliha ƙanwarta, idan anyi auren da watanni sai a baka Sarautar, kuma Mai Martaba yayi na'am da hakan”
“Miyasa baki faɗa musu ina da wacce nake so ba?”
“Idan na faɗa zai ga kamar ina kare ka ne, amman ina son ka min wani abu Abdallah, duk yadda Mai Martaba zai yi karka yarda ka karɓi Sarautar nan, kai ne ɗa na uku a gurin shi, be kamata ya tsallake su ba, ya ɗauki Sarauta ya baka, nasan yana son ka, amman hakan ba zai jawo maka komai ba sai ƙiyayya da ganin laifi, kai kuma ka yi ƙanƙanta da irin rayuwar nan, kuma idan har ka yarda ka auri Zaliha, to ka jefa rayuwarka da ta mu cikin matsala, tun da ƙanwar Hajiya Shafa ce, kuma kasan wacece Hajiya Shafa a gareni da gare ka. Ka da ka amince da duka biyu idan har ya yi maka magana”
“Ai ba zan amince ba, ina son aiki na kuma ina alfahari da shi, ni ba Sarauta ba ce a gabana, kuma Namra ce kaɗai matar da nake so”
“And be careful with her love too, kar ya rufe maka ido ka saɓawa Mahaifin ka”
“My Dad is...”
Ummi ta miƙe tsaye tana tarar numfashinsa.
“I know who your Dad is, he's my ex-husband the Father of my own male son”
Ta nufi bedroom ɗinta. Shi kuma ya faɗa zaune saman kujerar dinning yana bugashi da ƙarfi.
“Damn it! miyasa abubuwa zasu zo min haka kuma yanzu? Shine surprise ɗin da Mai Martaba yake ta faɗi? Ya Salam...!”
Ya miƙe tsaye, sai ya nufi kitchen duk da ya san babu abunda zai ɗauka a gurin. He need some fresh air, sai ya buɗe ƙofar baya ya fita, jin ya gaba ɗaya gidan ya masa wani irin, kai tsaye ya nufi Garden, ko ba komai yana son kukan tsuntsaye maybe zai sashi relaxing ya sama ma kan shi mafita.
Gaban icen guava ya zo ya tsaya yana kallon pool, motsin mutum ya ji a bayansa, yasan cikin biyu ba za'a rasa ɗaya ba, Maybe Amira ce tun da ita kaɗai take gidan ko kuma barewa, dan tana masa haka a duk lokacin da ya shigo Garden ɗin. Juyowa yayi sai yayi ido huɗu da Amira fuskarta shakaf da hawaye.
“What do you want?”
“You told me if i need someone to talk to”
“It Abdool who told you that, and now i'm someone else, and my words could hurt you, i'm not in the mood”
Cikin muryar kuka ta ce.
“You already hurt me because i learn the truth, i know you upset because of what Ummi told you, we share the same pain, i'm in love with you while you're in love with someone else”
Ta share hawayenta da haɓar rigarta.
“Maybe i will have peace of mind if you tell me that you never love me, maybe i will back to my senses, think about my future and....”
Kuka ya ci ƙarfinta. Taku biyu yayi ya matso kusa da ita.
“Do you know what is best for you, ki koma gida cikin iyayenki, ki manta da ni a rayuwarki, and i promise you zan rufa miki asiri ba zan faɗawa kowa abunda kika aikata ba”
“Zan koma gurin iyayena, nima a yanzu babu abunda na ke so sai su, but forgetting you is the hardest thing ever, thank you so for letting me staying with your family and know you better, can you take me home now please, am eager to see my parents”
“Yeah... Zan ma direba magana, ki shirya kayan ki”
“Ban zo da komai ba a nan”
Har ta juya sai kuma ta juyo.
“Ina matar da kake so take?”
“Why?”
“Saboda ta fi kowa sa'ah a duniya, ina son na ganta ne kawai”
“I can't tell you Amira, i'm sorry to say this, i don't trust you”
“I know i shouldn't...”
Ta juya ta shiga ciki da kuka. Da kallo ya bita sai da ta fice sannan ya haka hannunsa aljihu ya ciro handkerchief yana shinshinawa.
“I loved you so much”
Ya ɗauki tsawo lokaci a gurin sannan ya nufi part ɗinsa. Be daɗe ba ya fito da takarda hannunsa ya kira ɗaya daga cikin direban gidan ya miƙa masa.
“Zaka kai Amira a wannan addireshin, karka yarda ka sauketa ko ina sai nan”
“Toh Ranka ya daɗe”
Ya nufi part ɗin Ummi. Su biyu ya samu a falon Amira ta yi kneel down tana riƙe da hannun Ummi tana kuka, Ummi kuma na hawaye.
“Ki min hallaci Ummi kin riƙe ni kamar ƴar cikin ki, baki taɓa nuna min banbanci da ƴaran ki ba, na yi fatar wata rana zata zo da zan saka miki abunda kika min, Na gode da karamcin ina fatar zaki yafe min duk abunda na miki”
“Ba ki min komai ba Amira sai alheri, Allah ya miki albarka”
Kuka ta yi sosai sannan ta saki Ummi ta nufi ƙofar fita kamar zata faɗi. Kai Ummi ta girgiza ta kalli Abdool ta ce
“Is not fair ya kamata ace mu muka kai ta gida”
Ya ɗago daga jikin ƙofar da yake jingine ya nufo Ummi
“No hakan zai fi mata, dole ta tanadi abunda zata faɗawa iyayenta, idan suka gan mu kawo ta za suyi zaton ko ina son ta ne, kuma dole zasu tambayi inda na haɗu da ita, ni ko kin san gaskiya zan faɗa musu, beside irin waɗannan mutane ba a yawo da su it risk baki san abunda suka tana da ba”
Kai ta kaɗa masa cike da gamsuwar bayanin da yayi mata. Sannan ya juya suka fita tare gurin mota suke je suka tsaya, ita kuma tana daga ciki sai faman kuka take. Hannu Abdool yasa a aljihu ya ciro takardar kuɗi ya miƙa mata.
“Maybe you will need this”
“No i don't”
Ta kawar da fuskarta tare da cewa direba su tafi. Daga Ummi har Abdool tsaye suka yi suna kallonta har aka buɗe musu gate ɗin farko, bayan sun fice aka rufe gate ɗin sannan suka daina hango motar ta.
“Ina jin kamar ba mu kyauta mata ba, kuma bata jidaɗi ba ta ƙi ya tsaya har su Fauza su dawo”
“Zamu iya mata alheri daga baya idan mun fahimci da gaske ta shiryu, ai ƙara haka idan suna nan ai zasu ta kuka suma”
“Allah yasa ta shiryun, but wata rana zamu yi visiting na ta”
Ya miƙa hannunsa yana miƙa.
“Bari na shirya na koma gurin Mai Martaba”
“Okay”
Ummi ta juya. Shi kuma ya nufi part ɗinsa. Cikin rashin jundaɗi ya nufi part ɗinsa, dan bana jin kamar be kyautawa Amira, but he has no choice but to let her go. Cikin mintuna shirin ya watsa ruwa ya shirya cikin manyan kaya dan cox he know how Mai Martaba hate ƙananan kaya, yana fitowa part ɗinsa sai ƙamshin turare ke tashi.
Showing 213001 words to 216000 words out of 280121 words
Na fi sawa shashanci gaba, saboda farar fatar da nake tare da su, na kan rakasu gurare daban-daban hakan yasa muka shaƙu da su sosai. Su san burina saboda ina yawan faɗa cewar nafi son nafi kowa ɗaukaka a makarantar nan, ranar sai wata take ce mun zata faɗa min wani sirri, zata kai ni inda za'a taimaka min na samu ilmin da ya fi na kowa, kuma na fi kowa ɗaukaka a makarantar. Ban yi musu ba, na biyeta ta sani a cikin wata ƙungiya, ashe ƙungiyar asirice, buƙatata ta biya tabbas, saboda a wannan shekarar ni nayi ta ɗaya a duk faɗin makarantar, daga haka sai abubuwa suka buɗe, duk abunda nake da bukata zan je ne kawai na faɗa kuma sai buƙata ta biya, a lokacin muna meet duk ƙarshen wata, amman lokacin dana ƙare karatun na dawo nan sai suka haɗi ni da manyan da suke abuja, a nan naga manyan mutane, maza da mata a cikin har da manyan ƙasar nan. Duk lokacin da za'ayi meeting ɗin, na kan bar Katsina na je abuja da sunan ganin wata Sister mu ƴar sarki, sai naje meeting idan an gama da kwana biyu na sai na dawo.
Na samu babban aiki a lokacin, nama fi kowa kuɗi a gidan mu, da haka na haɗu da baban su Nabila. Bayan mun yi aure yace baya son aiki, sai na haƙura, a nan su kuma suka soma saka min ƙa'idojin da ban san da su ba a wacan lokacin.
Sun ce min dole ne na riƙa neman mata ƴan'uwana, idan ba haka ba, ba su yarda na fitar da zakka ba. A dole na ɗauki ka'idar mu'amala da mata ƴan'uwana, tun ban saba ba har abun ya zame min jiki, ya koma bana jin daɗi mu'amala da mijina sai mata. Daga baya kuma suka ce suna son a riƙa kawo musu sabbin membobi saboda tsofin ciki suna mutuwa ne, kuma ina son a riƙa yaɗa abun.
A abuja nake zaune da mijina, ɗan haka duk lokacin da naso zuwa kawai nake gurin meeting ɗin ba tare da ya sani ba, wata rana da muka yi meeting sai suka ce suna da buƙatar na Sadaukar musu wani daga cikin iyalaina, ba ni da zaɓi dole na bada mijina, sai ya samu haɗarin mota ya mutu, daga nan kuma sai babban ɗa na, sai mai binsa, sannu-sannu suka cinye min duka ƴaƴana, Nabila ce kawai ta rage min. Shekaran jiya da nace maka zanje birnin keebi ba can naje ba, Abuja na je, gurin meeting ɗin. Yanzu kuma Nabila suke so, ko ɗanta. Ni ko da na bada ita ƙara na bayarda kai na, shiyasa nake son ka taimake ni, ka ceci rayuwata da ta ƴata saboda ita kaɗai ta rage min”
Asim ya sake miƙewa tsaye a karo na biyu.
“Wallahi Allah yana so na, wato da yanzu sai dai ki bada ni? Dan nasan zasu ma iya cewa ki kawo yaron gidanki, ko kuma idan mun yi aure ace ko bada surikin ƴar ki, ai ni duk sun kuɗi na be kai na iya rayuwata ba kuma ni daga yau na barki har a bada wallahi”
“Kar kayi saurin yanke hukuncin Asim kaje ka yi tunani”
“Ba wani tunani da zan yi, salon ki sani cikin mugun hali”
“Da ina da niyar saka ka da na saka tun farkon dana saka tun farko dana fahimci kana da son kuɗi, amman ba kai nake target ba matarka, saboda nasan idan na sata cikin ƙungiyar zasu biya kuɗi mai yawa wata ƙila ma ya iya zama fansar ƴata, amman sai gashi ka saki matarka, da yanzu ace zaka iya kawo min matarka zasu iya ɗaga min ƙafa”
Tsayawa yayi kallonta.
“Indai har Namra zata iya zana fansar ƴarki to zan iya kawo miki ita, bisa sharaɗin zaki bani naira billion uku”
“Wallahi zan baka, kuɗi ba matsala ta bace idan na faɗa maka abunda na tara sai ka haukace, kuma Namra ba kasheta zamu yi ba Wallahi, cikin ƙungiyar kawai za mu sakata”
“Amman taya zan kawo miki ita?”
“Zaka maida aurenka, sannan duk abunda zai biyo baya ya biyo, kuma idan kana so zaka iya auren Nabila”
“Ƴarki kam na yafe, amman Namra zaki sameta kamar yadda kike buƙata”
Ta miƙe tsaye ta shiga ɗakinta bata jima.ba ta fito riƙe da amt ta miƙa masa.
“Akwai milion talatin a ciki kayi amfani da su”
Ya miƙa hannu ya karɓa sannan ya juya ya fice.
TEEMA POV.
Tana kwance saman jikinsa, shi kuma sai faman dannar waya yake yana murmushi. Azatonta dan tana shafa jikinsa yake murmushi, shi kam hankalinsa gaba ɗaya ya tafi kan waya sai faman chating yake da Kalsoom.
Ƙyalƙyalewa yayi da dariya sannan ya kashe datarsa ya kalleta.
“Bari na leƙa office”
“Okay Allah ya tsare min kai”
“Amin dear. Amm anjima Hajiya tace zata aiko da su Ezzah”
Sam bata ji daɗi ba, duk da tasan dalilinsu aka auro ta, amman bata yarda ta nuna masa ba.
“Kai Amman ko na jidaɗi daman ina ta jiran su zo, Allah kawo su lafiya”
“Amin”
Ya faɗa yana ɗaukar hulal dake saman hannu kujera ya saka a kai.
“Okay I love you”
“Love you too”
Da kallo ta bishi sai da ya fice sannan ta miƙe tsaye.
“Sati uku da aure ace za a ɗauko yara a kawo maka, nifa ba bautarsu na zo yi ba, ko amarci ban gama ci ba za'a haɗa ni da ala ƙai ƙai, yara zaggan-zaggan da su, su riƙa sa maka ido idan ka yi ma miji wani abu, mtsssss”
Taja wani uban tsaki ta wuce bedroom ɗinta. Bata jima ba ta fito ta nufi kitchen, girki ta ɗora sai mita take ranta duk a ɓace, dan har ga Allah bata so a kawo su yanzu ba.
“Daman fa ance wasu uwayen miji ba son suruka suke ba, in banda sheri kin san ina Amarya ɗan Amarcin ma ba za'a bari na yi ba, kai kayi naka lokacin sai kace wani ba zai yi ba, nasan dan su aka auro ni amman ai a bari na ci lokacina, tun da can ba saman ƙaya suke ba, daga zuwanka da ƙurciya zaka fara aikin ƴaƴan kishiya”
Kamar mai faɗa da wani haka ta riƙa zuba surutanta har ta yi girkin ta gama mita take, sai da tasa komai a muhallinsa sannan ta shiga ciki ta yi wanka. Tana fitowa ta shirya cikin yellow atamfa, ta kashe ɗauri ta feshe jikinta da turare sannan ta fito falo ta zauna.
Tana jin tsayawar mota ta ƙara gyara ɗaurin ɗankwalinta, tana zaton ko Hilal sai kawai ta ji mota ta tashi, su Ezzah sun turo ƙofa sun shigo fuskarsu da far'ah bakinsu kuma ƙumshe da sallama.
Ciki-ciki ta amsa musu tana murmushin da be kai zuci ba.
“Maraba da ƴaƴana”
“Momi ina wuni? Momi ina wuni?”
“Lafiya ƙalau”
Sai suka zauna saman kujera. Daga nan bata sake bi ta kansu ba, sai da ta ji motar Hilal sannan ta tashi ta koma tsakiyarsu ta zauna ta jasu jikinta ta rumgume tana murmushi.
“Ku bani labarin Hajiya...”
ABDOOL POV.
Around ten ya sauka Katsina, sai da ya fara biyawa Mai Martaba ya ganshi sannan ya wuce gurin Ummi. Da murmushi ya shiga part ɗin Ummi, kamar yasan ita kaɗaice a falon, dan duk ƙannensa sun tafi makaranta.
“Ummi barka da safe”
Ya taɓe baki tana kallonsa.
“Ni ban ga amfanin wannan hutu naka ba, kullum kai ne yawo ba zama gida, yanzu da aure kake yi wace mace ce zata ɗauki wannan rayuwar”
Kusa da ita ya zauna yana dariya.
“To ai gurin matar na je, yau zan baki labarin komai saboda na samu mafitar matsala ta, amman fa nasha wuya but at the end yau tace min Thank you”
“Kana nan kana wahalar da ƴar mutane ai dole wata ta saka cin kwakwa, tun da ka tagi Amirar nan kuka take, na rasa gane kanta idan kuma na tambaye ta sai tace babu komai, yau ma ce min tayi gida zata je daker na hana ta”
“Ina take?”
“Tana ɗakinta”
Ya miƙe tsaye ya nufi ɗakin Amal. Yana tura ƙofar ɗakin ta ɗago ta kalleshi sai kuma ta juya,
“Amira can we talk?”
“Maybe Later i need some space”
Ta faɗa da muryarta ta kuka.
“Okay but i just want you to know that i care for you, if you need someone to talk to, i'm downstairs”
Daga haka ya juya ya fice. Ita kuma. Ta fashe da kuka.
*78*
Kusa da Ummi ya sake zama yana kallon tv.
“Tana son ta saka kanta cikin matsala ne kawai Ummi amman tasan ba zan taɓa son ta ba”
“Nasan tana son ka har zuciyarta, amman sam ban yarda da yarinyar nan ba, mutanen da sukayi ƙoƙarin su kashe ka, waya sani ko plan ne aka yi ta yadda idan ta aure ka zata fin jindaɗin kashe ka”
Yayi murmushin gefen baki.
“Ko babu plan Ummi bana son ta, ko da kuwa tun can farko ita mai tarbiya ce, because if i love someone i mean it no matter what she did or whoever she is, and if i said i do i do, so i don't love Amira, i only fell in love once because i have never been in that kind of situation, but when it comes to Namra i take it so serious, and i love with all my heart and blood and mind and soul i love her more than you think Ummi”
Ajiyar zuciya Ummi ta sauke, ta kalli ɗanta fuskarta da alamun damuwa.
“Tell me more about her”
Miƙewa ya yi tsaye ya nufi freezer.
“She's so simple and kind, but difficult to handle. You know when we first meet, she slap me and insult me in front of my boys, but i can't slap her back”
Ya ƙarasa yana bulbula ruwan da ya fiddo a cup. Ummi ta yi murmushi.
“I know how my son is ba ya faɗa da mata”
“Yap bana faɗa da mata because we are not in the same level, strength, brain, heart, soul and lot. Ban taɓa jin ina son wata mace ba, but lokacin da na ji ina son Namra, nasan our souls mean to be, duk da a lokacin na san tana da aure, amman zuciya ta kasa haƙura, and now what! Her husband divorce her ta je wani gida ta zauna, kuma ƙaddara ta sake haɗa mu kaduna na kaɗe yaron gidan ina zuwa sai gata a gidan, hmm' mmm funny, and now ni ne silar shiryawa da iyayenta, i hope you love her too?”
“Of course i love her ai dole naso matar da ɗa na yake so, but i'm just worried about Mai Martba, ba lalle ne shi ya so ta”
“Why”
“Saboda Bazawara ce! And i hear that Mai Martaba and Hajiya Shafa sun maka mata”
“What...!”
Ya aje cup ɗin ruwa dake hannunsa saman dinning yana kallonta fuskarsa cike da tashin hankali.
“How true it's?”
“Mai Martaba ya kira ni da kan shi, yana neman shawara akan zai ɗoraka a Sarautar Katsina, da na nuna masa be dace ba sai ya nuna ɓacin ransa, the following day ya sake kira a waya ya faɗa min Hajiya Shafa tace be kamata a ɗoraka a Saurata baka tare da iyalaiba, dan haka ta maka mata, zata aura maka Zaliha ƙanwarta, idan anyi auren da watanni sai a baka Sarautar, kuma Mai Martaba yayi na'am da hakan”
“Miyasa baki faɗa musu ina da wacce nake so ba?”
“Idan na faɗa zai ga kamar ina kare ka ne, amman ina son ka min wani abu Abdallah, duk yadda Mai Martaba zai yi karka yarda ka karɓi Sarautar nan, kai ne ɗa na uku a gurin shi, be kamata ya tsallake su ba, ya ɗauki Sarauta ya baka, nasan yana son ka, amman hakan ba zai jawo maka komai ba sai ƙiyayya da ganin laifi, kai kuma ka yi ƙanƙanta da irin rayuwar nan, kuma idan har ka yarda ka auri Zaliha, to ka jefa rayuwarka da ta mu cikin matsala, tun da ƙanwar Hajiya Shafa ce, kuma kasan wacece Hajiya Shafa a gareni da gare ka. Ka da ka amince da duka biyu idan har ya yi maka magana”
“Ai ba zan amince ba, ina son aiki na kuma ina alfahari da shi, ni ba Sarauta ba ce a gabana, kuma Namra ce kaɗai matar da nake so”
“And be careful with her love too, kar ya rufe maka ido ka saɓawa Mahaifin ka”
“My Dad is...”
Ummi ta miƙe tsaye tana tarar numfashinsa.
“I know who your Dad is, he's my ex-husband the Father of my own male son”
Ta nufi bedroom ɗinta. Shi kuma ya faɗa zaune saman kujerar dinning yana bugashi da ƙarfi.
“Damn it! miyasa abubuwa zasu zo min haka kuma yanzu? Shine surprise ɗin da Mai Martaba yake ta faɗi? Ya Salam...!”
Ya miƙe tsaye, sai ya nufi kitchen duk da ya san babu abunda zai ɗauka a gurin. He need some fresh air, sai ya buɗe ƙofar baya ya fita, jin ya gaba ɗaya gidan ya masa wani irin, kai tsaye ya nufi Garden, ko ba komai yana son kukan tsuntsaye maybe zai sashi relaxing ya sama ma kan shi mafita.
Gaban icen guava ya zo ya tsaya yana kallon pool, motsin mutum ya ji a bayansa, yasan cikin biyu ba za'a rasa ɗaya ba, Maybe Amira ce tun da ita kaɗai take gidan ko kuma barewa, dan tana masa haka a duk lokacin da ya shigo Garden ɗin. Juyowa yayi sai yayi ido huɗu da Amira fuskarta shakaf da hawaye.
“What do you want?”
“You told me if i need someone to talk to”
“It Abdool who told you that, and now i'm someone else, and my words could hurt you, i'm not in the mood”
Cikin muryar kuka ta ce.
“You already hurt me because i learn the truth, i know you upset because of what Ummi told you, we share the same pain, i'm in love with you while you're in love with someone else”
Ta share hawayenta da haɓar rigarta.
“Maybe i will have peace of mind if you tell me that you never love me, maybe i will back to my senses, think about my future and....”
Kuka ya ci ƙarfinta. Taku biyu yayi ya matso kusa da ita.
“Do you know what is best for you, ki koma gida cikin iyayenki, ki manta da ni a rayuwarki, and i promise you zan rufa miki asiri ba zan faɗawa kowa abunda kika aikata ba”
“Zan koma gurin iyayena, nima a yanzu babu abunda na ke so sai su, but forgetting you is the hardest thing ever, thank you so for letting me staying with your family and know you better, can you take me home now please, am eager to see my parents”
“Yeah... Zan ma direba magana, ki shirya kayan ki”
“Ban zo da komai ba a nan”
Har ta juya sai kuma ta juyo.
“Ina matar da kake so take?”
“Why?”
“Saboda ta fi kowa sa'ah a duniya, ina son na ganta ne kawai”
“I can't tell you Amira, i'm sorry to say this, i don't trust you”
“I know i shouldn't...”
Ta juya ta shiga ciki da kuka. Da kallo ya bita sai da ta fice sannan ya haka hannunsa aljihu ya ciro handkerchief yana shinshinawa.
“I loved you so much”
Ya ɗauki tsawo lokaci a gurin sannan ya nufi part ɗinsa. Be daɗe ba ya fito da takarda hannunsa ya kira ɗaya daga cikin direban gidan ya miƙa masa.
“Zaka kai Amira a wannan addireshin, karka yarda ka sauketa ko ina sai nan”
“Toh Ranka ya daɗe”
Ya nufi part ɗin Ummi. Su biyu ya samu a falon Amira ta yi kneel down tana riƙe da hannun Ummi tana kuka, Ummi kuma na hawaye.
“Ki min hallaci Ummi kin riƙe ni kamar ƴar cikin ki, baki taɓa nuna min banbanci da ƴaran ki ba, na yi fatar wata rana zata zo da zan saka miki abunda kika min, Na gode da karamcin ina fatar zaki yafe min duk abunda na miki”
“Ba ki min komai ba Amira sai alheri, Allah ya miki albarka”
Kuka ta yi sosai sannan ta saki Ummi ta nufi ƙofar fita kamar zata faɗi. Kai Ummi ta girgiza ta kalli Abdool ta ce
“Is not fair ya kamata ace mu muka kai ta gida”
Ya ɗago daga jikin ƙofar da yake jingine ya nufo Ummi
“No hakan zai fi mata, dole ta tanadi abunda zata faɗawa iyayenta, idan suka gan mu kawo ta za suyi zaton ko ina son ta ne, kuma dole zasu tambayi inda na haɗu da ita, ni ko kin san gaskiya zan faɗa musu, beside irin waɗannan mutane ba a yawo da su it risk baki san abunda suka tana da ba”
Kai ta kaɗa masa cike da gamsuwar bayanin da yayi mata. Sannan ya juya suka fita tare gurin mota suke je suka tsaya, ita kuma tana daga ciki sai faman kuka take. Hannu Abdool yasa a aljihu ya ciro takardar kuɗi ya miƙa mata.
“Maybe you will need this”
“No i don't”
Ta kawar da fuskarta tare da cewa direba su tafi. Daga Ummi har Abdool tsaye suka yi suna kallonta har aka buɗe musu gate ɗin farko, bayan sun fice aka rufe gate ɗin sannan suka daina hango motar ta.
“Ina jin kamar ba mu kyauta mata ba, kuma bata jidaɗi ba ta ƙi ya tsaya har su Fauza su dawo”
“Zamu iya mata alheri daga baya idan mun fahimci da gaske ta shiryu, ai ƙara haka idan suna nan ai zasu ta kuka suma”
“Allah yasa ta shiryun, but wata rana zamu yi visiting na ta”
Ya miƙa hannunsa yana miƙa.
“Bari na shirya na koma gurin Mai Martaba”
“Okay”
Ummi ta juya. Shi kuma ya nufi part ɗinsa. Cikin rashin jundaɗi ya nufi part ɗinsa, dan bana jin kamar be kyautawa Amira, but he has no choice but to let her go. Cikin mintuna shirin ya watsa ruwa ya shirya cikin manyan kaya dan cox he know how Mai Martaba hate ƙananan kaya, yana fitowa part ɗinsa sai ƙamshin turare ke tashi.
Book Chapters
Chapter 1Chapter 2Chapter 3Chapter 4Chapter 5Chapter 6Chapter 7Chapter 8Chapter 9Chapter 10Chapter 11Chapter 12Chapter 13Chapter 14Chapter 15Chapter 16Chapter 17Chapter 18Chapter 19Chapter 20Chapter 21Chapter 22Chapter 23Chapter 24Chapter 25Chapter 26Chapter 27Chapter 28Chapter 29Chapter 30Chapter 31Chapter 32Chapter 33Chapter 34Chapter 35Chapter 36Chapter 37Chapter 38Chapter 39Chapter 40Chapter 41Chapter 42Chapter 43Chapter 44Chapter 45Chapter 46Chapter 47Chapter 48Chapter 49Chapter 50Chapter 51Chapter 52Chapter 53Chapter 54Chapter 55Chapter 56Chapter 57Chapter 58Chapter 59Chapter 60Chapter 61Chapter 62Chapter 63Chapter 64Chapter 65Chapter 66Chapter 67Chapter 68Chapter 69Chapter 70Chapter 71Chapter 72 Chapter 73Chapter 74Chapter 75Chapter 76Chapter 77Chapter 78Chapter 79Chapter 80Chapter 81Chapter 82Chapter 83Chapter 84Chapter 85Chapter 86Chapter 87Chapter 88Chapter 89Chapter 90Chapter 91Chapter 92Chapter 93Chapter 94