ma baki ga rai suke kashewa ba? Ai daga baya sai ki ranka ki nemi yafiyar ubangijinki Allah fa gafurun rahimun ne, kin ga sai ma ki daina kwata kwata”
Shiru tayi tana nazari, tasan idan har ta aikata wannan abun ta yi, babban saɓo, ta yi fashin salla saboda biyan buƙatar da bata da tabbacin zata biya? Ajiyar zuciya ta sauke ta cigaba da tuƙin.
“Zan yi tunani akai Teema, amman ina jin tsoro sosai”
“Ai da tsoro zaki cuci kan ki, kawai ki cire wannan tsoron ki yaƙi zuciyarki”
“Zan yi ƙoƙarin yin hakan”
Daga nan Teema ta ɗauko mata firar ƙawarsu, ita mai bin bokaye marar tsoro, wance ta mallake miji da uwarsa.
Duk tana yi ne dan kawai ta ƙara tunzira Rashida ta aikata, so that ita ma ta samu abokin shiga wuta, dan mugu be son ace shi kaɗai yake aikata abu.
Sai da ta fara biyawa ta sauke Teema a gidansu, sannan ta wuce na su gidan dan ta yi shirin zuwa gurin aiki, ganin karfe ɗaya ma bata yi ba.
Tun da tayi parking a harabar gidansu ta fara saƙe-saƙen abunda zata faɗa gurin aikin, dan gaba ɗaya kashe wayarta tayi. Tana shiga falo sai ga Momy ta fito daga ɗakinta jiki na rawa, Rashida na ganinta ta gane hankalinta a tashe yake.
“Momy lafiya?”
“Lafiya ba lau ba, tun ɗazu nake cikin zullumi Rashida”
“Me ya faru?”
Momy ta tsaya tunanin ta inda zata soma, dan tana jin faɗin kalamar kai tsaye.
“Safiya tace min ta ga ƙawarki Asma'u a... Hiv unit....”
Yadda kasan cida haka gaban Rashida ya riƙa faɗuwa, zuciyarta na zillo kamar ta fito, a take yawun bakinta ya tsarƙe ta har sai da ta soma tari. Tasan Momy ba Asmee take nufi ba, idan kuma har da gaske Asmee take nufi to Safiya ce ta faɗa, kuma taya Safiya zata ga Asmee ita ce ta gani.
“Safiya ce ta faɗa?”
Momy ta ɗaga mata kai tana hawaye.
“Ni ta ce ta gani ko?”
Nan ma kai Momy ta ɗaga mata.
“I tell not once not twice several times, naje nemanta ne a asibitin amman ta ƙi ta yarda gani take kamar ni ce naje a karan kai na...”
Maganar take tana nuna da gaske take, amman bata son kallon Momy. Kai Momy ta girgiza na tausayin ƴarta da kuma ganin wautarta akan abunda take ta ƙoƙarin ɓoyewa.
“What about the results?”
Da sauri ta kalli Momy, tana mamakin kalamanta. Kenan bincike suka mata lokacin da bata nan! Ita da tayi ma results ɗin mugun ɓoyo taya aka yi suka gani?
Durƙushewa tayi a gurin ta fashe da kuka mai ƙarfin gaske. Momy bata san lokacin data ƙarasa gaban ƴarta ta rumgume suka soma kukan tare.
“Taya haka ya faru Rashida ta ya? Miyasa kika yi ƙoƙarin ɓoyewa?”
Cikin kuka Momy take tambayarta, tana jinjigata. Da sauri Rashida ta zame jikinta daga na Momy ta tashi da sauri ta shige ɗakinta ta kulle da maƙulli. Jinginawa tayi jikin ƙofar tana kuka, irin kuka mai sa kaji kamar ka cire ranka ka huta.
Momy ma kuka take sosai, dan yanzu ne ta ƙara tabbatar da zancen Safiya. Daman tun Safe Safiya ta shiga ɗakin Rashida tana mata bincike har Momy ta same ta a ciki, anan takr faɗawa Momy haɗuwarsu da Rashida a asibiti. Da kuma maganin da abokan aikinta suke bawa ƙawarta Asmee, a wacan Asibitin ta su.
Babu irin bugun ƙofar da Momy bata yi ba, amman Rashida ta ƙi ta buɗe, kuma ta ƙi tayi magana, sai kuka take. Waya Momy ta ɗauka ta kira Dady ta faɗa masa, cikin ƴan'mintuna sai gashi ya dawo gida hankali a tashe, ɗan har gumi ke keto masa ta ko'ina.
Kai tsaye ɗakin Momy ya nufo, sai ya same ta itama tana kuka.
“Ya aka yi haka ta faru? Amman an tabbatar?”
Kallonsa Momy tayi idonta na zubar da ƙwalla.
“Safiya ce ta faɗa, nima ban yarda ba har dai yanzu dana nuna mata na ga takardun, bayan kuma ban gansu ba nace ne kawai dan na gano gaskiyarta, kuma the way she act ya nuna tana da shi”
Jiki a sanyaye Dady ya zauna idonsa sun rine sun yi wani ja sosai, irin na ɓacin rai da damuwa sun sauka ga mutum. Can kuma ya sauke ajiyar zuciya yana ta nazarin inda Rashida zata samo hiv da tsakar rana.
“Amman ƙara dai a bincika, ba lallai ba ne tana ɗauke da ciwon to ina ma zata kwaso wannan ciwon?”
“Hilal mana, ai shi kaɗai ne mutunen da take taraiya da shi”
Cewar Momy tana kuka, zuciyarta na ayyana mata shi ɗin ne tun da shine kaɗai mijin Rashida. Da sauri Dady ya kalleta
“Wallahi idan kuwa shi ne ya saka mata shi, sai na ɗaure shi gidan yari har ƙarshen rayuwarsa, marar mutumci marar taddako wanda be san halin girma ba, Allah ya usar mana, wallahi ya cuce mu, shiyasa ya sako ta. Ina Rashida take ne?”
“Tsna ɗakinta, ta ƙi ts buɗe tun ɗazu sai kuka take, ta ƙi tayi magana ma”
Tashi yayi yana cire ƴar saman suit ɗinsa, yana sassauta necktie ɗinsa, ya nufi ɗakinta jikinsa har rawa yake kamar mazari.
Sai da ya soma kiran sunanta, jin bata amsa ba yasa ya soma ƙwanƙwasa ƙofar ɗakin.
“Rashida ni ne buɗe mana... Ba wani abun za mu miki ba kawai magana za mu yi, kuma ba zamu faɗawa kowa ba”
Tana jinsa amman ta kasa amsa masa dan bata da abinda zata faɗa masa, tasani matuƙar suka gano gaskiyar dalilin cutar nata ba zasu zauna da ita ba, who else kuma zai zauna da ita bayan iyayenta, lallai ko a haka rayuwa ta tsaya mata ta san ta kai karshenta.
Babu irin maganar da Dady be mata na rarrashi da tausasa zuciya ba, amman ta ƙi ta amsa masa balle ma har ta buɗe ƙofar.
Dawowa yayi ɗakin Momy ya tsaya daga jikin ƙofa fuskarsa da damuwa ya ce
“Ko dai za mu kira shi ne mu tambaye shi?”
“Idan shine taya zai amsa cewar shi ne? Zai yi ƙoƙarin kare kansa ne, kuma kasan babu wanda Rashida take mu'amala da shi sai Hilal dan shin mijinta kuma ni ƴata ba ƴar iska ba ce, ta bakinta ya kamata aji komai”
“Ta ƙi tayi magana, ɗakin ma ta ƙi ta buɗe”
“Zata yi magana, dole zata buɗe kabarta hankalinta ya kwanta kawai, ka koma gurin aikin ka”
“Ba zan iya wani aiki ba ko naje, jikina ya riga da ya mutu, Wallahi Hilal ya cuce mu, amman miyasa Rashida ta yi ƙoƙarin ɓoye irin wannan babban al'amari?”
“Allah kaɗai ya sani, amman rufawa irin wannan mutumen asiri ai ba abun yi ba ne, wallahi sai na sashi yayi nadama sai ya ƙwammace kiɗa da karatu”
A bakin ƙofar Dady ya zauna irin zaman nan na baka san ka yi ba, hankalinsa baya jikinsa, natsuwarta ta gudu ta barsa.
*NAMRA POV.*
Maganganun Asim sun tsaya mata a zuciya, duk bayan dogon numfashinta sai kalmar rabuwa da yayi mata ya maimata kanta a kunnenta. Da zancen ta kwana a ranta, tana mamakin Asim, yadda yayi tsaye yana faɗa mata magangu kamar wani ɗan shaye-shaye. Bw ɗauke a matarsa ta sunna ba be riƙe ta da muhimmaci ba, shiyasa har ya zaɓi aikin da yake sama da ita, yanzu kuma yake neman rayuwa da ita saboda tana da ciki. Sai yanzu take nadamar rashin bin Anty, dan tasan babu makawa Asim rabuwa zai yi da ita, matuƙar bata zubar da cikin ba, dan ta ga gaskiyar maganarsa a idonsa, sai dai ita kuma bata jin zata iya zubar da cikin ko da kuwa shege ne balle na Sunna.
Sai dai idan Asim ya sake ta ina zata je? Ta koma gida da ciki ta faɗawa Abbah Asim ya sake ta? Ta bi sawon Anty bayan ta nemi taje gidan ta ƙi yarda sai yanzu da Asim ya sake ta kuma take ɗauke da cikinsa.?
Tashi ta yi zaune, sai ta nemi kuka da take ta rasa, washe ƙaramin abun ake yi ma kuka, tashin hankalin dake tare da ita baya barin hawayenta zuba.
“Kaico na ni Namra, Ina zan sa kai na sanyi? Ina zan sa rayuwar na samu sassauci? Haƙiƙa wanda duk ya so abinda iyaye suka ƙi yayi hasara, da nasan haka aurena da Asim zai kasance da ban aure shi ba, Allah ka yi min gata Allah”
Hannayenta ta ɗaga sama, tana roƙon Ubanjiginta, zuciyarta cike da yaƙinin lallai Allah zai ƙarɓa mata.
“Ya Allah ka tsare min mutunci na, ka tsare min lafiyata,
Allah ka yi min gata ka tsare min imani na da hankalina,
Allah ka yi min sutura ka kwantar min da hankali
Allah ka kyautata min rayuwa ta, Allah idan aure da Asim Alheri ne Allah ka tabbatar da shi, idan rabuwa da shi ne samuwar jindaɗina Allah ka zaɓa min abunda yafi zama Alheri a gare ni,
Allah ka shirya tsakani na da iyaye na, Allag ka gafarta min kurakurai na
Allah ka tabbarda duga duga-dugaina akan addinin ka”
Bayan ta shafa ta koma ta kwanta, ta kai hannu ta shafa cikinta, tana mai jin tsantsan ƙaunar abinda yake kwance a mararta.
*ABDOOL POV.*
Misalin ƙarfe biyu da rabi na rana jirginsa max air ya sauka a tashar sauka da kuma tashin jirage da ke katsina.
Be sanar da Ummi zuwansa ba, dan haka be tsamaci ta tarbe shi ba, ko ta aiko da motar da zata ɗauke shi. Sai dai hakan be a aiko masa da motar da zata ɗauki daga headquarter ba dan sun san da zuwansa.
A yadda suka tarbi shi ya burge kowa a gurin, mota uku suka faka. Already sun buɗe motar suna hangosa tafe sai suka duk suka fito wajen motar suka tsaya, a jikin kayan gida yake amman hakan be hana dukansu su tsara masa ba, babu wanda yayi motsi a cikin su har sai da ya shiga motar sannan suka rufe masa suka shiga.
“Gurin Mai Martaba zamu je”
Yanda yayi maganar ba ka ce shi ne ba, dan hankalinsa gaba ɗaya yana kan wayarsa sai faman duba shafukan yana gizo yake dan sanin abinda ƙasa take ciki.
Har aka isa Ahmad Mai-doki road, Abdool be ɗago ya kalli mai driving ɗinsa ba, balle ti-ti. Yana jin motar ta tsaya ya buɗe ya fito ƙamshin gidan ne yasa shi murmushi, dan ƙanshim gidansu daban yake, ko'ina ya ke zai iya gane ƙanshin gidan Mai-martaba.
Sai da ya shiga cikin gidan ya gaishe da mahaifansa, matan sarki sannan ya wuce faɗar mai-martaba. Be same shi a faɗar ba, hakan ya tabbatar masa da yana can turakarsa yana hutawa, tun da yaga motocinsa a waje balle yayi tunanin ko ya fita. Ta faɗar ya bi ya shiga turakar Mai-Martaba, a falon farko ya same shi zaune yana duba air conditioner da ake kan saka masa. Faɗawan na ganin Abdool duk suka faɗi suna ɗiban gaisuwa, shi dai hannu kawai ya ɗaga musu dan baya son irin gaisuwar nan da suke masa, ya fi gane a tsara masa ko a maƙe idan an ganshi. Da murmushi ya zube gaban mahaifinsa yana ɗiban gaisuwa.
Kallonsa Mai-Martaba yake da mamakin zuwan ba zata ta, sai kuma ya kai mafeshin Peacock dake hannunsa ya shafi ka ɗansa da shi. He didn't say a word dan baya son magana da Abdool a gaban faɗawansa ko baboro, yafi son sai ya keɓance yadda zai dake da shi kamar ba ɗansa ba.
Ko ba komai nuna tsantsar ƙaunar da kake wani daga cikin ƴaƴansa babban laifi ne kuma ya kan haddasa ƙiyayah, sai dai hakan be hana familynsa depending ya fi son Abdool da kowa ba, dan abu ne da ko ya ɓoye sai dai ya ɓoye mai yawan ka buɗe kaɗan.
Yana unƙurawa zai miƙe tsaye sai faɗawansa suka zo da sauri suka tara rigunansu, suna masa kirari har ya miƙe tsaye sannan suka rufa masa baya suna masa fita.
Hannu kawai ya ɗaga musu suka fahimci baya buƙatar su raka shi har can, sai kawai suka juyo gurin Abdool suna masa nasa kirarin. Be tsaya jinsun ba ma balle ya nuna masu jindaɗin abunda suke masa sai kawai ya bi bayan Mai-Martaba hannayensa laƙƙame a baya yana tafi guda-guda kamar mai takewa President baya.
Sai da suka wuce falon biyu da na uku, suka wuce garden ɗin Mai-martaba sannan Mai Martaba ya ƙarasa a wata ƴar ƙaramar rumfa mai kyau da ɗaukar hankali ya zauna, shi kuma Abdool ya zauna ƙasa complain ɗin kiraren da suke masa.
Ɗan murmushi Mai-Martaba yayi irin na na manyan sarakuna, yana kallon ɗan nasa cikin farinciki da jindaɗi.
“Wata rana kai Sarki Abdool, irin wannan kalaman be kamata yana fita daga bakin ka ba”
“Haba Mai -Martaba ta ya zan zama sarki bayan Ina da yaya? Kuma ni wannan sarautar sam ba burgeni take ba”
Mai-martaba ya ɗauki ƙafarsa ɗaya ya ɗora akan ɗayar yana murmushin ƙasaita.
“Har gobe Babana baka san Sarauta ba, saboda ka guje mu a lokacin daya kamata acr ka zauna ka karanci komai na gidan nan, baka san jidaɗin sarauta ba, shiyasa kake wannan furuci, na kan lura da yanayin ka sam baka sakin jiki a harkokin sarautar gidan nan, balle na wani gurin, abu kake kamar ba ɗan sarki ba, ai yanzu kuɗi da milki su ake ɗubi abawa mutum sarauta balle kuma kai da ka cancanta dan kana da natsuwa da hankali ga tarbiya”
“Mai martaba wannan sarautar fa dai ku. Ina fatar na samu sarki cikin ƙoshin lafiya”
“Yareema ya samu Mai Martaba cikin ƙoshin lafiya da walwala, ya aka yi ka yi mana zuwan ba zata? Gashi ba ko wane abinci kake so ba balle na ce a ɗibo maka”
“Na samu hutu ne jiya, shiyasa na dawo gida as surprise kasan turawa sun ce surprise is better than disappointed”
“Aiko kayi tsara kan gaɓa, daman akwai ɗaurin auren Abubakar Saturday, daman kai na ke son ka walkice ni, kuma daman can Abubakar ɗin nan abokin ka ne”
Abdool ya shafa kai
“Wai har auren ya tashi ne ? Kwanaki wani friend na mu yake ce min an kai masa kaya”
“Kai ma ai naka yana kusa, mun soma duba maka na dangi kamin mu fita waje, tun ka bamu zaɓi”
Ko be tambaya ba yasan Ummi ce tayi wannan maganar, on behalf of him. Ɗan murmushi yayi ya ce
“Ba wai zaka je ɗin ba, ka tabbatar an ganka, zan haɗa tawagar da za kuje daga nan, kuma zaka je ne cikin shigar sarauta, sadauki zai naɗa maka rawani idan kunje can”
Ƙure yayi ma Mai martaba da ido yana kallonsa. Mai martaba yasan waye ɗansa kuma ya san kallon da yake masa.
“Kar ma ka soma, kai shikenan baka son shiga mutane? Ƴaƴan saraku irinka amman baka son shiga cikin su? Rabon ka da rawani tun a hawan salla, ni wannan rayuwar ta ka bata min Yareema, wasu ma basu kao darajarka ba basu kai muƙamin ka ba, sannan sarautar ta su ƙarama ce amman su yi ta tinƙaho suna nuna isa balle ka!”
Yayi tsuntsun da kai, yana murmushi, dan yasan Mai Martaba ya kamo tasharsa.
“Ai ban ce komai ba Mai martaba”
“Na san zaka ce ɗin ne. Tashi ga ruwa can ɗauko ka sha, kar kaje ka ce wa uwarka baka ci komai gidan Mai Martaba ba”
Ya tashi yana murmushi ya nufi wani ɓangare na gurin da aka jera freezer biyar a gurin dan shan ruwa kawai da lemu.
Be bar gidan ba sai da Mai- Martaba yasa aka daba masa wani abu ya ci. Bayan yayi la'asar, yayi ma Mai Martaba sallama sannan ya nufo gida gurin Umminsa.
Gaisuwar ban girma da tadabi sojojin gida suka masa suna masa maraba da zuwa.
Har zai wuce part ɗinsa sai kuma yaji ba zai iya ba har sai ya saka mahaifiyarsa a ido. Da far'ah da zumuɗi ya nufi part ɗinta.
Tun daga yanayin yadda yaga falon zuciyarsa ta raya masa Ummi bata cikin gidan. Sai ya ɗauki remote ya kashe plasma ɗake falon sannan ya nufi ɗakin Ummi dan tabbatarwa. Haleema ya gani kwance saman gado Amira kuma na gurin tufafinta tana gyarawa.
“What nonsense is this?”
Ya faɗa a tsawaci. Daga Haleema har Amira zuyowa suka yi suka kalleshi dan babu wanda yasan da shigowarsa. Da sauri Amira ta zube ƙasa tana miƙa masa gaisuwa zuciya na bugawa da ƙarfi, haka kawai ta samu kanta tana mai tsantsar kunyarsa.
Be amsa gaisuwar ba sai kawai ya watsawa Haleema harara, ita kaɗai tasan abunda Hararar tasa take nufi sai ta sauka saman gadon da sauri ta kama hannu Amira suka fice.
Sai ya ƙofar ɗakin ya rufe da key, ya cire keys ɗin ya nufi part ɗinsa da shi. Yana shiga ya cire tufafin jikinsa ya ɗaura tawul ya shiga Bathroom.
Ya ɗauki kusan mintuna arba'in a banɗakin yana cuɗa jikinsa kamar wanda zai canja fatarsa. Bayan ya gama wanka ya ƙarasa gaban madubi yana ƙara gyara gemensa da babu komai a gurin.
Sallamar da yaji ana ta dokawa ne yasa ya wanke fuskarsa ya fito. Ya nufo falonsa. Amira ya samu tsaye a gurin hannunta riƙe da cup ɗayan hannun kuma riƙe da wasu dinner set an rufe su da ɗayansu.
Tana kallonsa gabanta yayi mummunan faɗuwa, bodybuilding ɗinsa ne ya tashi hankalinta, yadda aka tsara jikinsa da faffanɗan ƙirjinsa, ga fararen idon nan kamar an watsa masa madara tabbas shine irin mijin da take so.
“How may i help you?”
Ya tambaya ganin yadda take kallonsa kamar bata san da shi a gurin ba. Sai da ta gyara tsayuwarta gudun faɗuwa sannan ta miƙa masa duka abunda yake hannunsa.
“Coffee and fruits, tuwo ne aka yi kuma Haleema tace ba ka son tuwo, shine na haɗa maka wannan”
“Thanks i'm not a coffee drinker”
Fruits ɗin kawai ya karɓa ya aje saman kujera ya bar mata coffee. Har ya juya sai kuma ya juyo ya kalleta
“By the way bana son texts ɗin nan da kike tura min, ki daina please”
Kai ta ɗaga masa idonta na son cika da hawaye.
“Note”
“You may go”
“Thank you”
Jikin sanyi jiki ta juya ta fice, hawaye na bin fuskarta. A yadda ta fahimta kamar bata burge Abdool kwata-kwata irin ɗan sakewar nan ma baya mata shi.
Haleema na gani hawayenta tasan ba lafiya ba, daman kuma tasan za'a rina indai Abdool ne.
“Wani abun ya ce miki ne?”
“A'a kawai
Showing 153001 words to 156000 words out of 280121 words
Shiru tayi tana nazari, tasan idan har ta aikata wannan abun ta yi, babban saɓo, ta yi fashin salla saboda biyan buƙatar da bata da tabbacin zata biya? Ajiyar zuciya ta sauke ta cigaba da tuƙin.
“Zan yi tunani akai Teema, amman ina jin tsoro sosai”
“Ai da tsoro zaki cuci kan ki, kawai ki cire wannan tsoron ki yaƙi zuciyarki”
“Zan yi ƙoƙarin yin hakan”
Daga nan Teema ta ɗauko mata firar ƙawarsu, ita mai bin bokaye marar tsoro, wance ta mallake miji da uwarsa.
Duk tana yi ne dan kawai ta ƙara tunzira Rashida ta aikata, so that ita ma ta samu abokin shiga wuta, dan mugu be son ace shi kaɗai yake aikata abu.
Sai da ta fara biyawa ta sauke Teema a gidansu, sannan ta wuce na su gidan dan ta yi shirin zuwa gurin aiki, ganin karfe ɗaya ma bata yi ba.
Tun da tayi parking a harabar gidansu ta fara saƙe-saƙen abunda zata faɗa gurin aikin, dan gaba ɗaya kashe wayarta tayi. Tana shiga falo sai ga Momy ta fito daga ɗakinta jiki na rawa, Rashida na ganinta ta gane hankalinta a tashe yake.
“Momy lafiya?”
“Lafiya ba lau ba, tun ɗazu nake cikin zullumi Rashida”
“Me ya faru?”
Momy ta tsaya tunanin ta inda zata soma, dan tana jin faɗin kalamar kai tsaye.
“Safiya tace min ta ga ƙawarki Asma'u a... Hiv unit....”
Yadda kasan cida haka gaban Rashida ya riƙa faɗuwa, zuciyarta na zillo kamar ta fito, a take yawun bakinta ya tsarƙe ta har sai da ta soma tari. Tasan Momy ba Asmee take nufi ba, idan kuma har da gaske Asmee take nufi to Safiya ce ta faɗa, kuma taya Safiya zata ga Asmee ita ce ta gani.
“Safiya ce ta faɗa?”
Momy ta ɗaga mata kai tana hawaye.
“Ni ta ce ta gani ko?”
Nan ma kai Momy ta ɗaga mata.
“I tell not once not twice several times, naje nemanta ne a asibitin amman ta ƙi ta yarda gani take kamar ni ce naje a karan kai na...”
Maganar take tana nuna da gaske take, amman bata son kallon Momy. Kai Momy ta girgiza na tausayin ƴarta da kuma ganin wautarta akan abunda take ta ƙoƙarin ɓoyewa.
“What about the results?”
Da sauri ta kalli Momy, tana mamakin kalamanta. Kenan bincike suka mata lokacin da bata nan! Ita da tayi ma results ɗin mugun ɓoyo taya aka yi suka gani?
Durƙushewa tayi a gurin ta fashe da kuka mai ƙarfin gaske. Momy bata san lokacin data ƙarasa gaban ƴarta ta rumgume suka soma kukan tare.
“Taya haka ya faru Rashida ta ya? Miyasa kika yi ƙoƙarin ɓoyewa?”
Cikin kuka Momy take tambayarta, tana jinjigata. Da sauri Rashida ta zame jikinta daga na Momy ta tashi da sauri ta shige ɗakinta ta kulle da maƙulli. Jinginawa tayi jikin ƙofar tana kuka, irin kuka mai sa kaji kamar ka cire ranka ka huta.
Momy ma kuka take sosai, dan yanzu ne ta ƙara tabbatar da zancen Safiya. Daman tun Safe Safiya ta shiga ɗakin Rashida tana mata bincike har Momy ta same ta a ciki, anan takr faɗawa Momy haɗuwarsu da Rashida a asibiti. Da kuma maganin da abokan aikinta suke bawa ƙawarta Asmee, a wacan Asibitin ta su.
Babu irin bugun ƙofar da Momy bata yi ba, amman Rashida ta ƙi ta buɗe, kuma ta ƙi tayi magana, sai kuka take. Waya Momy ta ɗauka ta kira Dady ta faɗa masa, cikin ƴan'mintuna sai gashi ya dawo gida hankali a tashe, ɗan har gumi ke keto masa ta ko'ina.
Kai tsaye ɗakin Momy ya nufo, sai ya same ta itama tana kuka.
“Ya aka yi haka ta faru? Amman an tabbatar?”
Kallonsa Momy tayi idonta na zubar da ƙwalla.
“Safiya ce ta faɗa, nima ban yarda ba har dai yanzu dana nuna mata na ga takardun, bayan kuma ban gansu ba nace ne kawai dan na gano gaskiyarta, kuma the way she act ya nuna tana da shi”
Jiki a sanyaye Dady ya zauna idonsa sun rine sun yi wani ja sosai, irin na ɓacin rai da damuwa sun sauka ga mutum. Can kuma ya sauke ajiyar zuciya yana ta nazarin inda Rashida zata samo hiv da tsakar rana.
“Amman ƙara dai a bincika, ba lallai ba ne tana ɗauke da ciwon to ina ma zata kwaso wannan ciwon?”
“Hilal mana, ai shi kaɗai ne mutunen da take taraiya da shi”
Cewar Momy tana kuka, zuciyarta na ayyana mata shi ɗin ne tun da shine kaɗai mijin Rashida. Da sauri Dady ya kalleta
“Wallahi idan kuwa shi ne ya saka mata shi, sai na ɗaure shi gidan yari har ƙarshen rayuwarsa, marar mutumci marar taddako wanda be san halin girma ba, Allah ya usar mana, wallahi ya cuce mu, shiyasa ya sako ta. Ina Rashida take ne?”
“Tsna ɗakinta, ta ƙi ts buɗe tun ɗazu sai kuka take, ta ƙi tayi magana ma”
Tashi yayi yana cire ƴar saman suit ɗinsa, yana sassauta necktie ɗinsa, ya nufi ɗakinta jikinsa har rawa yake kamar mazari.
Sai da ya soma kiran sunanta, jin bata amsa ba yasa ya soma ƙwanƙwasa ƙofar ɗakin.
“Rashida ni ne buɗe mana... Ba wani abun za mu miki ba kawai magana za mu yi, kuma ba zamu faɗawa kowa ba”
Tana jinsa amman ta kasa amsa masa dan bata da abinda zata faɗa masa, tasani matuƙar suka gano gaskiyar dalilin cutar nata ba zasu zauna da ita ba, who else kuma zai zauna da ita bayan iyayenta, lallai ko a haka rayuwa ta tsaya mata ta san ta kai karshenta.
Babu irin maganar da Dady be mata na rarrashi da tausasa zuciya ba, amman ta ƙi ta amsa masa balle ma har ta buɗe ƙofar.
Dawowa yayi ɗakin Momy ya tsaya daga jikin ƙofa fuskarsa da damuwa ya ce
“Ko dai za mu kira shi ne mu tambaye shi?”
“Idan shine taya zai amsa cewar shi ne? Zai yi ƙoƙarin kare kansa ne, kuma kasan babu wanda Rashida take mu'amala da shi sai Hilal dan shin mijinta kuma ni ƴata ba ƴar iska ba ce, ta bakinta ya kamata aji komai”
“Ta ƙi tayi magana, ɗakin ma ta ƙi ta buɗe”
“Zata yi magana, dole zata buɗe kabarta hankalinta ya kwanta kawai, ka koma gurin aikin ka”
“Ba zan iya wani aiki ba ko naje, jikina ya riga da ya mutu, Wallahi Hilal ya cuce mu, amman miyasa Rashida ta yi ƙoƙarin ɓoye irin wannan babban al'amari?”
“Allah kaɗai ya sani, amman rufawa irin wannan mutumen asiri ai ba abun yi ba ne, wallahi sai na sashi yayi nadama sai ya ƙwammace kiɗa da karatu”
A bakin ƙofar Dady ya zauna irin zaman nan na baka san ka yi ba, hankalinsa baya jikinsa, natsuwarta ta gudu ta barsa.
*NAMRA POV.*
Maganganun Asim sun tsaya mata a zuciya, duk bayan dogon numfashinta sai kalmar rabuwa da yayi mata ya maimata kanta a kunnenta. Da zancen ta kwana a ranta, tana mamakin Asim, yadda yayi tsaye yana faɗa mata magangu kamar wani ɗan shaye-shaye. Bw ɗauke a matarsa ta sunna ba be riƙe ta da muhimmaci ba, shiyasa har ya zaɓi aikin da yake sama da ita, yanzu kuma yake neman rayuwa da ita saboda tana da ciki. Sai yanzu take nadamar rashin bin Anty, dan tasan babu makawa Asim rabuwa zai yi da ita, matuƙar bata zubar da cikin ba, dan ta ga gaskiyar maganarsa a idonsa, sai dai ita kuma bata jin zata iya zubar da cikin ko da kuwa shege ne balle na Sunna.
Sai dai idan Asim ya sake ta ina zata je? Ta koma gida da ciki ta faɗawa Abbah Asim ya sake ta? Ta bi sawon Anty bayan ta nemi taje gidan ta ƙi yarda sai yanzu da Asim ya sake ta kuma take ɗauke da cikinsa.?
Tashi ta yi zaune, sai ta nemi kuka da take ta rasa, washe ƙaramin abun ake yi ma kuka, tashin hankalin dake tare da ita baya barin hawayenta zuba.
“Kaico na ni Namra, Ina zan sa kai na sanyi? Ina zan sa rayuwar na samu sassauci? Haƙiƙa wanda duk ya so abinda iyaye suka ƙi yayi hasara, da nasan haka aurena da Asim zai kasance da ban aure shi ba, Allah ka yi min gata Allah”
Hannayenta ta ɗaga sama, tana roƙon Ubanjiginta, zuciyarta cike da yaƙinin lallai Allah zai ƙarɓa mata.
“Ya Allah ka tsare min mutunci na, ka tsare min lafiyata,
Allah ka yi min gata ka tsare min imani na da hankalina,
Allah ka yi min sutura ka kwantar min da hankali
Allah ka kyautata min rayuwa ta, Allah idan aure da Asim Alheri ne Allah ka tabbatar da shi, idan rabuwa da shi ne samuwar jindaɗina Allah ka zaɓa min abunda yafi zama Alheri a gare ni,
Allah ka shirya tsakani na da iyaye na, Allag ka gafarta min kurakurai na
Allah ka tabbarda duga duga-dugaina akan addinin ka”
Bayan ta shafa ta koma ta kwanta, ta kai hannu ta shafa cikinta, tana mai jin tsantsan ƙaunar abinda yake kwance a mararta.
*ABDOOL POV.*
Misalin ƙarfe biyu da rabi na rana jirginsa max air ya sauka a tashar sauka da kuma tashin jirage da ke katsina.
Be sanar da Ummi zuwansa ba, dan haka be tsamaci ta tarbe shi ba, ko ta aiko da motar da zata ɗauke shi. Sai dai hakan be a aiko masa da motar da zata ɗauki daga headquarter ba dan sun san da zuwansa.
A yadda suka tarbi shi ya burge kowa a gurin, mota uku suka faka. Already sun buɗe motar suna hangosa tafe sai suka duk suka fito wajen motar suka tsaya, a jikin kayan gida yake amman hakan be hana dukansu su tsara masa ba, babu wanda yayi motsi a cikin su har sai da ya shiga motar sannan suka rufe masa suka shiga.
“Gurin Mai Martaba zamu je”
Yanda yayi maganar ba ka ce shi ne ba, dan hankalinsa gaba ɗaya yana kan wayarsa sai faman duba shafukan yana gizo yake dan sanin abinda ƙasa take ciki.
Har aka isa Ahmad Mai-doki road, Abdool be ɗago ya kalli mai driving ɗinsa ba, balle ti-ti. Yana jin motar ta tsaya ya buɗe ya fito ƙamshin gidan ne yasa shi murmushi, dan ƙanshim gidansu daban yake, ko'ina ya ke zai iya gane ƙanshin gidan Mai-martaba.
Sai da ya shiga cikin gidan ya gaishe da mahaifansa, matan sarki sannan ya wuce faɗar mai-martaba. Be same shi a faɗar ba, hakan ya tabbatar masa da yana can turakarsa yana hutawa, tun da yaga motocinsa a waje balle yayi tunanin ko ya fita. Ta faɗar ya bi ya shiga turakar Mai-Martaba, a falon farko ya same shi zaune yana duba air conditioner da ake kan saka masa. Faɗawan na ganin Abdool duk suka faɗi suna ɗiban gaisuwa, shi dai hannu kawai ya ɗaga musu dan baya son irin gaisuwar nan da suke masa, ya fi gane a tsara masa ko a maƙe idan an ganshi. Da murmushi ya zube gaban mahaifinsa yana ɗiban gaisuwa.
Kallonsa Mai-Martaba yake da mamakin zuwan ba zata ta, sai kuma ya kai mafeshin Peacock dake hannunsa ya shafi ka ɗansa da shi. He didn't say a word dan baya son magana da Abdool a gaban faɗawansa ko baboro, yafi son sai ya keɓance yadda zai dake da shi kamar ba ɗansa ba.
Ko ba komai nuna tsantsar ƙaunar da kake wani daga cikin ƴaƴansa babban laifi ne kuma ya kan haddasa ƙiyayah, sai dai hakan be hana familynsa depending ya fi son Abdool da kowa ba, dan abu ne da ko ya ɓoye sai dai ya ɓoye mai yawan ka buɗe kaɗan.
Yana unƙurawa zai miƙe tsaye sai faɗawansa suka zo da sauri suka tara rigunansu, suna masa kirari har ya miƙe tsaye sannan suka rufa masa baya suna masa fita.
Hannu kawai ya ɗaga musu suka fahimci baya buƙatar su raka shi har can, sai kawai suka juyo gurin Abdool suna masa nasa kirarin. Be tsaya jinsun ba ma balle ya nuna masu jindaɗin abunda suke masa sai kawai ya bi bayan Mai-Martaba hannayensa laƙƙame a baya yana tafi guda-guda kamar mai takewa President baya.
Sai da suka wuce falon biyu da na uku, suka wuce garden ɗin Mai-martaba sannan Mai Martaba ya ƙarasa a wata ƴar ƙaramar rumfa mai kyau da ɗaukar hankali ya zauna, shi kuma Abdool ya zauna ƙasa complain ɗin kiraren da suke masa.
Ɗan murmushi Mai-Martaba yayi irin na na manyan sarakuna, yana kallon ɗan nasa cikin farinciki da jindaɗi.
“Wata rana kai Sarki Abdool, irin wannan kalaman be kamata yana fita daga bakin ka ba”
“Haba Mai -Martaba ta ya zan zama sarki bayan Ina da yaya? Kuma ni wannan sarautar sam ba burgeni take ba”
Mai-martaba ya ɗauki ƙafarsa ɗaya ya ɗora akan ɗayar yana murmushin ƙasaita.
“Har gobe Babana baka san Sarauta ba, saboda ka guje mu a lokacin daya kamata acr ka zauna ka karanci komai na gidan nan, baka san jidaɗin sarauta ba, shiyasa kake wannan furuci, na kan lura da yanayin ka sam baka sakin jiki a harkokin sarautar gidan nan, balle na wani gurin, abu kake kamar ba ɗan sarki ba, ai yanzu kuɗi da milki su ake ɗubi abawa mutum sarauta balle kuma kai da ka cancanta dan kana da natsuwa da hankali ga tarbiya”
“Mai martaba wannan sarautar fa dai ku. Ina fatar na samu sarki cikin ƙoshin lafiya”
“Yareema ya samu Mai Martaba cikin ƙoshin lafiya da walwala, ya aka yi ka yi mana zuwan ba zata? Gashi ba ko wane abinci kake so ba balle na ce a ɗibo maka”
“Na samu hutu ne jiya, shiyasa na dawo gida as surprise kasan turawa sun ce surprise is better than disappointed”
“Aiko kayi tsara kan gaɓa, daman akwai ɗaurin auren Abubakar Saturday, daman kai na ke son ka walkice ni, kuma daman can Abubakar ɗin nan abokin ka ne”
Abdool ya shafa kai
“Wai har auren ya tashi ne ? Kwanaki wani friend na mu yake ce min an kai masa kaya”
“Kai ma ai naka yana kusa, mun soma duba maka na dangi kamin mu fita waje, tun ka bamu zaɓi”
Ko be tambaya ba yasan Ummi ce tayi wannan maganar, on behalf of him. Ɗan murmushi yayi ya ce
“Ina za'ayi ɗaurin auren?”
“Zariya, ƴar sakin Zazzauce zai aura, Saturday nan”
“Okay zan je inshallah”
“Ba wai zaka je ɗin ba, ka tabbatar an ganka, zan haɗa tawagar da za kuje daga nan, kuma zaka je ne cikin shigar sarauta, sadauki zai naɗa maka rawani idan kunje can”
Ƙure yayi ma Mai martaba da ido yana kallonsa. Mai martaba yasan waye ɗansa kuma ya san kallon da yake masa.
“Kar ma ka soma, kai shikenan baka son shiga mutane? Ƴaƴan saraku irinka amman baka son shiga cikin su? Rabon ka da rawani tun a hawan salla, ni wannan rayuwar ta ka bata min Yareema, wasu ma basu kao darajarka ba basu kai muƙamin ka ba, sannan sarautar ta su ƙarama ce amman su yi ta tinƙaho suna nuna isa balle ka!”
Yayi tsuntsun da kai, yana murmushi, dan yasan Mai Martaba ya kamo tasharsa.
“Ai ban ce komai ba Mai martaba”
“Na san zaka ce ɗin ne. Tashi ga ruwa can ɗauko ka sha, kar kaje ka ce wa uwarka baka ci komai gidan Mai Martaba ba”
Ya tashi yana murmushi ya nufi wani ɓangare na gurin da aka jera freezer biyar a gurin dan shan ruwa kawai da lemu.
Be bar gidan ba sai da Mai- Martaba yasa aka daba masa wani abu ya ci. Bayan yayi la'asar, yayi ma Mai Martaba sallama sannan ya nufo gida gurin Umminsa.
Gaisuwar ban girma da tadabi sojojin gida suka masa suna masa maraba da zuwa.
Har zai wuce part ɗinsa sai kuma yaji ba zai iya ba har sai ya saka mahaifiyarsa a ido. Da far'ah da zumuɗi ya nufi part ɗinta.
Tun daga yanayin yadda yaga falon zuciyarsa ta raya masa Ummi bata cikin gidan. Sai ya ɗauki remote ya kashe plasma ɗake falon sannan ya nufi ɗakin Ummi dan tabbatarwa. Haleema ya gani kwance saman gado Amira kuma na gurin tufafinta tana gyarawa.
“What nonsense is this?”
Ya faɗa a tsawaci. Daga Haleema har Amira zuyowa suka yi suka kalleshi dan babu wanda yasan da shigowarsa. Da sauri Amira ta zube ƙasa tana miƙa masa gaisuwa zuciya na bugawa da ƙarfi, haka kawai ta samu kanta tana mai tsantsar kunyarsa.
Be amsa gaisuwar ba sai kawai ya watsawa Haleema harara, ita kaɗai tasan abunda Hararar tasa take nufi sai ta sauka saman gadon da sauri ta kama hannu Amira suka fice.
Sai ya ƙofar ɗakin ya rufe da key, ya cire keys ɗin ya nufi part ɗinsa da shi. Yana shiga ya cire tufafin jikinsa ya ɗaura tawul ya shiga Bathroom.
Ya ɗauki kusan mintuna arba'in a banɗakin yana cuɗa jikinsa kamar wanda zai canja fatarsa. Bayan ya gama wanka ya ƙarasa gaban madubi yana ƙara gyara gemensa da babu komai a gurin.
Sallamar da yaji ana ta dokawa ne yasa ya wanke fuskarsa ya fito. Ya nufo falonsa. Amira ya samu tsaye a gurin hannunta riƙe da cup ɗayan hannun kuma riƙe da wasu dinner set an rufe su da ɗayansu.
Tana kallonsa gabanta yayi mummunan faɗuwa, bodybuilding ɗinsa ne ya tashi hankalinta, yadda aka tsara jikinsa da faffanɗan ƙirjinsa, ga fararen idon nan kamar an watsa masa madara tabbas shine irin mijin da take so.
“How may i help you?”
Ya tambaya ganin yadda take kallonsa kamar bata san da shi a gurin ba. Sai da ta gyara tsayuwarta gudun faɗuwa sannan ta miƙa masa duka abunda yake hannunsa.
“Coffee and fruits, tuwo ne aka yi kuma Haleema tace ba ka son tuwo, shine na haɗa maka wannan”
“Thanks i'm not a coffee drinker”
Fruits ɗin kawai ya karɓa ya aje saman kujera ya bar mata coffee. Har ya juya sai kuma ya juyo ya kalleta
“By the way bana son texts ɗin nan da kike tura min, ki daina please”
Kai ta ɗaga masa idonta na son cika da hawaye.
“Note”
“You may go”
“Thank you”
Jikin sanyi jiki ta juya ta fice, hawaye na bin fuskarta. A yadda ta fahimta kamar bata burge Abdool kwata-kwata irin ɗan sakewar nan ma baya mata shi.
Haleema na gani hawayenta tasan ba lafiya ba, daman kuma tasan za'a rina indai Abdool ne.
“Wani abun ya ce miki ne?”
“A'a kawai
Book Chapters
Chapter 1Chapter 2Chapter 3Chapter 4Chapter 5Chapter 6Chapter 7Chapter 8Chapter 9Chapter 10Chapter 11Chapter 12Chapter 13Chapter 14Chapter 15Chapter 16Chapter 17Chapter 18Chapter 19Chapter 20Chapter 21Chapter 22Chapter 23Chapter 24Chapter 25Chapter 26Chapter 27Chapter 28Chapter 29Chapter 30Chapter 31Chapter 32Chapter 33Chapter 34Chapter 35Chapter 36Chapter 37Chapter 38Chapter 39Chapter 40Chapter 41Chapter 42Chapter 43Chapter 44Chapter 45Chapter 46Chapter 47Chapter 48Chapter 49Chapter 50Chapter 51Chapter 52 Chapter 53Chapter 54Chapter 55Chapter 56Chapter 57Chapter 58Chapter 59Chapter 60Chapter 61Chapter 62Chapter 63Chapter 64Chapter 65Chapter 66Chapter 67Chapter 68Chapter 69Chapter 70Chapter 71Chapter 72Chapter 73Chapter 74Chapter 75Chapter 76Chapter 77Chapter 78Chapter 79Chapter 80Chapter 81Chapter 82Chapter 83Chapter 84Chapter 85Chapter 86Chapter 87Chapter 88Chapter 89Chapter 90Chapter 91Chapter 92Chapter 93Chapter 94