Yace da yaron babu alamar wasa a maganarsa, haka ma a yanayinsa. Da gudu yaron ya koma, ko minti biyu ba'ayi ba sai ga Namra ta fito cikin farin Hijabi ta doso inda yake. Yana kallonta dukan natsuwarsa taje gareta, kalaman daya tara zai watsa mata marar daɗi sai duk ya neme su ya rasa har ta ƙaraso kusa da shi ta tsaya.
“Ban ce kar ka sake zuwa nan ba? Jiya jiya ban maimaita maka wannan maganar ba? Ka ɓace ka bar ƙofar gidan nan”
Ta faɗa a tsawace, fuskarta babu annuri. lumshe ido Abdool yayi ya buɗe ya kalleta.
“Kina burge ni idan kina ba ni Umarni, da ma ace bakin ki be iya faɗar ƙarya ba, kin ce ba ki da aure bayan kina da shi”
“Idan na maka ƙarya nawa zaka ba ni? Miye ribata idan na maka ƙarya bayan ka tambaye tsakani da Allah?”
“Amman ƴan gidanku sun tabbatar mana da kina da aure, Asim be sake ki”
Wani irin kallon ta jefa mata mai cike da tashin hankali da mamaki.
“Ina ka san ƴan gidan mu? Waya faɗa naka sunan mijina? Waye kai? Me kake nema a gare ni”
“Naje har gidanku ne neman auren ki, kuma sun tabbatar min da kina da aure, auren ki be mutu ba”
Ta ɗora hannu saman kai.
“Na shiga uku na lalace, ka ɓata komai yanzu shikenan ba za su karɓe ni ba, miyasa baka bari na faɗa musu mutuwar aurena da kai na ba? Kaico na ni Namra, duk inda na dafa taɓen mi yake yi, ka cuce ni shiyasa ka tambaye ɗan ka ƙara jefani a halin baƙinciki da damuwa? Wayyo ni Allah na”
Ta juya da sauri ta koma ciki tana kuka. Shi dai kallonta kawai yake har ta gama faɗa masa abunda zata faɗa masa ta juya ta shige. Jikinsa yayi sanyi sosai, ko bata faɗa masa ba yasan there's something behind those words and tears da ya ga suna zuba a idonta. Juyawa yayi zai buɗe motar ya shiga sai ga Mustafa ya iso.
“Ranka ya daɗe naje kai maka kayan aka hanani shiga, kuma aka ƙi karɓa wai baka nan”
Ko kallonsa Abdool be yi ba ya ɗaga masa hannu.
“Na bar maka”
Ya shige motar, cikin rashin jindaɗin rai. Tun kamin su bar unguwar kalaman Namra suka riƙa dawo masa, idan ya tuna hawayen da ya ga suna zuba a idonta sai yaji wani abu ya tsaya masa a zuciya marar daɗi.
“Ranka ya daɗe ina za muje?”
Ya tambaya ganin har sun hau titi amman Abdool be ce da shi komai ba.
“Masaukin Mai Martaba”
Ya faɗa cikin sanyayiyar murya mai nuna mutun yana cikin damuwa.
-----------------------------------------------------------------
Ku yi haƙuri da wannan.
*72*
Da kuka Namra ta shiga gidan, bata kula su Neina da ke tsakar gidan suna gyaran giɗa ba ta wuce ɗakin Uwani, saman katifa ta faɗa tana cigaba da rera kuka.
Duk mamakine ya kama su, daman tun jiya ba su gane ma kanta ba.
“Uwani je ki gani mana”
Lamido ya faɗa yana kallon Uwani, duk ya ji babu daɗi ganin tana hawaye.
Da sauri Uwani ta tashi ta shiga ɗakin, hannu ta kai ta ɗago Namra tana tambayar
“Lafiya miya same ki?”
Sai kawai Namra ta faɗa jikinta ta cigaba da kukan. Jin kukan nata ya ƙaru yasa Neina shigowa ɗakin.
“Ke lafiya miya same ta?”
“Wallahi nima ta kasa min magana, sai kuka take”
“Toh Allah dai ya sa lafiya, ko wani ne ya mutu?”
Sai a lokacin Namra ta samu ta girgiza musu kai, tasa hannunta ta share hawayenta.
“Mutumen da ya zo yanzu, shi ne mutumen da ya zo jiya, kuma shine mutumen da ya kaɗe Lamido”
Ba shiri Neina ta zauna sake da baki dan shan labari, Uwani kuma ta yi ma Namra kallon Mamaki.
“To miyasa kawo shi? Miya ce miki”
A nan Namra ta kwashe labarin abunda ya faru, ta faɗa musu, sai dai bata yarda ta faɗa musu sanin da ta yi masa a Katsina ba.
Dukansun cika da tsananin mamaki, bama kamar Neina da take ganin kamar lokacin da ya zo gidan ba su yi ido biyu da Namra ba.
“Amman Namra in ban da abin ki miye abun kuka a ciki? Ke da Allah ya kawo miki ɗauki? Yanzu ko abunda tsohon mijin nan na ki ya yi miki ai wannan idan kika duba sakamako ne Allah zai miki”
Uwani na kai aya. Namra ta yi mata kallon baki fahimce ni ba.
“Ya ƙara ɓata min komai Uwani, yanzu iyaye na sun ji aure na ya mutu, kuma za su yi tunanin ko nice na tura sa neman aure na, idan yanzu na koma gida ban san mi zan ce musu ba”
Neina ta ɗaga kai ta kalleta
“A yadda na fahimta, idan har yana son ki da gaske ne, hakan ba zai sa ya ƙi ki ba”
“Ya so ni, ko ya ƙi i, ni duka ɗaya ne a guri na, ban shirya mutuwa sau biyu ba, ban shiryawa yaudara Namiji ba, wani na Namiji ba zai sake ɗiga min baƙinciki a rayuwata ba, na rufe shafin Namiji a rayuwata, dan haka ni ba shi nake ji ba, iyayena na ke ji da makomata”
Duk shiru suka yi, suna sauraren kukan da take rerawa. Kamin hankalinsu ya koma kan sallamar da Mustafa yake yi. Neina ce ta tashi ta fita Uwani kuma ta tsaya yana bawa Namra haƙuri.
“Maraba da Mustafa, yau an dawo shago da wuri?”
Ya zauna saman kujerar tsakar gida ta mata, yana faɗin
“Wallahi yau ban ma je ba, ya mai jiki?”
“Jiki yayi sauƙi Alhamdulillahi”
Lamido ya amsa da kansa yana miƙa masa hannu su gaisa.
“Allah ya ƙara sauƙi, naga kun yi wani babban baƙo ne a waje, amman kamar be shigo cikin gidan ba”
“Eh gurin Namra ya zo ɗan'uwanta ne”
Cewar Lamido, kamin Neina ta amsa da
“Wai Ɗan Sarki nan ne da ya kaɗe ka, shine ya zo wai yana son ta, kuma har yaje can gida ita bata ma sani ba”
Da sauri Lamido ya kalli Neina, wani irin abu ya daki ƙirjinsa, be ji daɗin maganar ba, kuma be ji rashin daɗinta ba, sai ya samu kansa cikin wani kalar yanayi na dabam.
“Me ta ce masa? Ai na ga ta dawo da kuka”
Ya tambaya kamar ba komai, sai a baɗini yana jin zuciyarsa kamar ta rabe biyu. A nan Neina ta kwashe labarin da Namra ta faɗa musu ta faɗa ma Lamido.
“Ba duka maza ne ƴan iska ba, ba duka maza ne mayaudara ba, ba a taru aka zama ɗaya ba, yadda wani yake da kwaɗayi ba haka wani yake da shi ba, ba a taru a zama ɗaya”
Ya faɗa a hankali yana kallon wani gurin kamar mai nazari. Har Neina ta buɗe baki zata yi magana, sai Mustafa ya jinjina kai ya ce.
“Amman abun da ya ba ni mamaki, wannan mutumen yayi min kama da wanda na sani, kuma shine mutumen da ya aiko yaronsa ya kira nia ka bani wanki, ya ɗauki dubu goma sha ɗaya ya ba ni wai na wanki ne, har yake labarta min wai shi ɗan'uwan ku ne, kuma yana zuwa gidan, da neje kai masa wankin sai aka ce baya nan, ina nan kuma zaune sai na gansa, ina masa magana wai ya ba ni tufafin”
Lamido ya riƙe baki.
“Wallahi ba mu da wani alaƙa da shi, ai baka nan lokacin daya kaɗe ne da ka gani, anya ba yana da wata muguwar manufa ba ce akan yarinyar nan da mu ma?”
Neina ta yi saurin rufe masa baki.
“Dan Allah ka rufa mana asiri, ɗan Sarki ne”
“Dan yana Ɗan Sarki fa? So what? Ba a da ikon faɗar gaskiya, ku kuke tsoron sa”
Mustafa ma ya saka baki.
“Kai da ka rufa ma kan ka asiri. Ko ma minene iya karka ka yi addu'ah ka zura na mujiya”
“Wallahi ba zan yi ba, ba zan zuba ido wani ya cutar da yarinyar nan ba, iya wahalar da tasha ta ishe ta haka”
Ya faɗa cike da ɓacin rai. Mustafa ya miƙe tsaye bakinsa cike da maganganun da be samu furtawa ba, yana musu Allah ya sauwaƙe.
“Amin an gode Mustafa”
Neina ce ta amsa da haka, Lamido kan hankalinsa na can wani gurin.
ABDOOL POV.
Samun kansa yayi da damuwar abunda be kamata ace ya dame shi ba, ya sara sukuninsa tun hawayen da ya gani suna zuba a idon Namra.
“Na ɓata komai? Na ƙara ruguza mata rayuwa? Mi take nufin da hakan?”
Magana yake yi da kansa yana kallon tv, babu abunda kunnuwansa suke da buƙata a yanzu kamar jin labarin Namra.
“Allah kai ka san ina son yarinyar nan, kuma Allah kai ka saka min son ta, ya Rabb help me, wallahi daga gani sai ta yi taurin kai”
Ya shafa fuskarsa yana busar da iskar bakinsa. Can kuma ya kai dubansa ga wayar dake gefensa ya ɗauka ya danna number Ummi. Bugu ɗaya Amal ta ɗauka.
“Dude zaka cigaba da ba ni labarin matar ka ko?”
Murmushi yayi marar sauti kamar tana gabansa.
“Ina Ummi?”
“Tana falo, ni ina game da wayarta”
“Tau ki ce mata na isa lafiya ƙalau kin ji”
Be jira abunda zata ce ba ya kashe wayar, yana sauke ajiyar zuciya. Sam be jin yau zan iya haƙura be ji labarin Namra ba, dare kawai yake jira yayi masa ya koma unguwar, sai dai me idan tace ba zata faɗa ba fa?
“Tau ya zan yi? Ni Wallahi tsoro ma yarinyar nan take ba ni”
Ya sake magana a fili kamar mai magana da wani. miƙewa yayi tsaye ya nufi bedroom ɗinsa yana ware hannayensa.
“Ina ta ƙoƙarin zama mahaukaci akan wannan yarinyar, Allah ka da ka jarrabe ni ta wannan hanyar”
RASHIDA POV.
Da taimakon Teema suka kwashe duk wani abu na amfaninta suka mayar a gidan da Mahaifinta ya bata. Ɗan madaidaicin gida ne mai ɗauke da ɗakuna biyar, da kuma madaidacin tsakar gida.
Gidan yayi datti sosai duk da kasancewar ba a taɓa zama a cikinsa, sai dai daɗewa da aka yi ba a buɗe shi ba yasa ya koma kamar anyi yaƙi a cikinsa. Tare da teema suka jera komai, sam bata yarda ta nunawa Teema damuwarta akan komawarta gidan ba, hasali ma tana yawan maimaita ita hakan ya fi mata daɗi kuma ita ce ta nemi Dady ta bata gidan alhalin ba haka ba ne, duk yadda hawaye suka yi ƙoƙarin zubar mata sai ta yi kamar abu ya faɗa mata a ido.
Sai dai abunda Teema ta saka samun natsuwa da shi, ganin babu ɗan'uwanta ko ɗaya daya zo rakata a gidan, ko kuma su tausasata akan karta bar wacan gidan ta dawo nan ita kaɗai. Bata nuna mata komai ba har suka gama tsara komai suka share iya inda za su iya, sauran ta ce almajiri zai gyara mata, daf da za su fita Momi ta iso gidan da kukanta kamar wance aka cirewa rai. Duk dauriyar da Rashida ta ke sai da ta fasa na ta kukan, sai ita da Momi aka rasa mai bawa wani haƙuri.
“Ni Wallahi sam ban ga amfanin wannan kukan ba, miye na barin gida Rashida in ban da abun ki? Ai ƙara ki zauna cikin danginki, ko danuwa ai kya rage”
Rashida ta share hawayenta, tana jan majina.
“Ni na zaɓi zama a nan, na fi son na zauna ni kaɗai”
Momi kan bata iya cewa komai ba, sai kawai ta miƙe tsaye tana faɗin.
“Dadyn ki ya ce zai aiko da furniture da abinci, da kuɗi kuma duk abunda kike so ki riƙa faɗa mana”
Daga haka ta fice hawaye na cigaba da mata zuba. Bayan fitarta da minti goma shabiyar Rashida ta tashi ta shiga bathroom ta yi wanke fuskarta ta fito suka ɗauki hanyar dutsen Malam.
Rashida ce take driving, Teema kuma na zaune front seat, sai kallon Rashida ta ke yi ƙasa-ƙasa. Ɗan ƙauye ne da yake can waje gari sai dai kuma ba sosai ba. Shi wannan malamin da alama aikinsa ba yayi ko kuma sabon farawa, dan babu ƙowa a ƙofar gidansa. Matan biyu masu far'ah da son mutane, suna shiga suka ɗauko musu tabarma suka shimfiɗa musu da zimmar za su aika a kira Malam wai yana gona.
Sai ga shi ya iso cikin ƙanƙanen lokaci, jikinsa har ɓari yake, bakin nan cike da goro. Bayan ya gaisa da su yayi musu iso zuwa ɗakin da yake aikin nasa.
“Bismillah”
Ya nuna musu gurin zama yana ɗauko farra ƙasarsa dake cikin ɗan ƙaramin windi. Sai da Teema ta fara gabatar masa da Rashida sannan ta fara faɗa masa matsalolinta da kuma abunda ke tafe da ita. Kai ya girgiza ya sake girgizawa sannan ya shiga duba ƙasar, can ya ɗago ya kalli Rashida ya ce.
“Wato ni bana ɓoye komai, magana ta gaskiya ƙasa ta bada bayanin ba zaki taɓa komawa gidan mijin ki ba”
Rashida ta daki ƙirji.
“Innalillahi wa'inna ilaihi raji'un”
Sai hawaye ya fara bin fuskarta. Teema ta nuna damuwa sosai.
“Malam ko dai ƙasar bata ba da bayani dai-dai ba ne? Dan Allah a sake bincikawa”
“Ai babu wani bincike, ni ba zan cuce ku ba, kun ga idan wani ne sai ya nuna muku kamar aiki zai ci ya riƙa cin kuɗin ku”
Miƙewa Rashida ta yi tsaye tana hawaye
“Teema tashi mu je”
Kamin Teema ta tashi har Rashida ta kai ƙofar gida.
“Zan kira ka Malam”
Teema ta faɗa tana aje mishi kuɗi masu ɗan dama gabansa. A tsakar gidan ma Teema ce ta yi musu sallama da godiya, ko da ta fito waje har Rashida ta yi ma motar key ita kawai take jira.
Wani mahaukacin gudu Rashida ta fara, kamar marar hankali, har sai da Teema ta riƙa ta.
“Idan har kw baki son kan ki ni ai ina son ki, be kamata kina wannan gudun ba, yawancin bokayen nan ƙarya suke faɗa fa, ki bari zamu je wani gurin”
Uffan Rashida bata ce cewa Teema ba har suka isa ƙofar gidansu Teema.
“Idan Hankalin ki ya kwanta ki kira ni zan kai ki wani gurin”
Sai ta buɗe motar ta fita. Rashida ta fi ƙarfin minti goma a gurin tana kukan sannan ta kaɗa motarta ta yi gaba.
ASIM POV.
“Nice House”
Ya faɗa yana ƙarewa gidan kallo, hannu Nably tasa taja hancinsa.
“Gida zaka yaba ba ni ba?”
“Ke ai babu kalmomin da zan iya amfani da su na ya be ki da su, amman gida ko akwai kalmomi da zan yabe shi da shi”
Ɗan murmushi ta yi, tana ƙara kallon harabar gidan.
“Momi na ta so ta gaisa da kai, sai dai tafiyar gaggauwa ta kama ta yau, amman gobe dole ne ka dawo, dan momi ta ga wanda nake yawan bata labari”
Ya kai hannunsa ya riƙo nata.
“Wato gulma na kike?”
“Ba wani gulma, ba kai ba ne ka sace mata zuciyar ƴa ba”
“Ko kuma ƴarta ta sace zuciyar wani ba”
Cikin wasa ta kai masa duka, shi kuma ya goce yana mata wani kallo, tuni idonsa har sun soma canjawa. Yar yar daya fara jin jikinsa na yi ne yasa ya saki hannunta yana faɗin
“Bari ma zo ma tafi na wuni a gidan na ku ai”
“Wato har ka gaji da gani na kenan?”
“Kai ni har na isa, kawai dai naga magariba tana gabatowa ne, ai kin ga dole jibi naje na kai ki birthday ɗin friend ɗin ta ki, kuma mu zaga gari”
“Ai gobe ne”
Ya buɗe ido.
“Tab aiko dai gobe tafiya za mu yi da oga na, ban da haka kan wallahi babu abunda zai hana ni kai ki ko ina ne a faɗin duniyar nan”
Ta wara ido.
“Kar ka damu, nima ai ban cika son kaje ba gudun kar wata ƙwace min kai”
Sai da aka soma kiran sallah, sannan ya tashi, ta rakoshi har gurin motarsa, ta buɗe masa, har zai shiga sai kuma a juyo ya kalleta ya ce
“Haka zan je ba good bye?”
Murmushi ta yi ta juya ta juyo, kamar mai nuna masa mazaunanta, daman jikinta babu mayafi, sai kawai ta kai masa kiss a baki.
“Shikenan?”
Ya ɗaga mata kai yana wani shegen murmushi. Sannan ya shiga motarsa tana ɗaga masa hannu har ya bar gidan.
“Wow wayayiyace sosai, i'm so lucky”
Abunda ya furta kenan yana ƙarawa motarsa giya. Be tsaya ko ina ba sai da isa unguwarsu, a lokacin har an sauko daga sallar magariba, sai da ya shiga gida yayi wanka sannan ya fito a masallacin unguwar yaje ya yi alwala ya yi sallah, sannan ya koma cikin gidan ya ɗauki motarsa ya ƙarasa ƙofar gidansu Mardiya.
Ko da ya kirata yace yana kofar gidansu, bata cikin gidan, dan haka sai da ya jirata har na tsawon mintuna talati sannan ya ta iso gurin da saurinta. Ta kanta ta buɗe motar ta shiga tana masa sallama.
“Ya gida ya su Mama?”
“Wallahi lafiya ƙalau, ya naka gidan?”
“Gida na babu daɗi fa”
“Subhannalla miya same ka?”
“Kin san na zama gwauro yanzu, tun da kin kore min Namra”
Mardiya ta riƙe baki kamar gaske.
“Wai da gaske ne da ake cewa Namra ta fita?”
“Ba ki sani ba? Kuma saboda ke ta bar gidan?”
“Saboda ni kuma?”
“Eh dan ta gano ina son ki, shine ta so na sake ta ni kuma na ƙi na sake ta, shine sai ta tafiyarta”
“Kai amman ban jidaɗi ba, kaje ka dawo da ita dan Allah”
“Ni yanzu ba ta ita nake ba ta ki na ke”
“Ni kuma?”
“Eh mana, ni fa tsakani da Allah na ke son ki, kuma auren ki zan yi, shine abunda ya kawo ni yanzu, na baki kwana biyu ki je ki yi shawara”
“Amman Namra ba zata ce komai ba?”
“Ke kike ta kanta, ga wannan ni zan wuce, dan gobe zan yi tafiya yau nake son na fara shiri na”
Ya miƙa mata dubu goma, ƴan ɗari biyar-biyar. Ƙin karɓa ta yi har sai da ya matsa mata sannan ta karɓa tana masa godiya, ta buɗe mota ta fita.
KALSOOM POV.
Be barta ta yi aikin komai ba, shi ya haɗa musu abun kari, kuma ya haɗa musu ruwan wanka. Daman ita ta gaji sosai, tun da ta yi sallah asuba ta koma bachi, shi kuma ganin hakan yasa be tashe ba, ya barta ta yi bachinta, har ta gaji ta tashi dan kanta, sannan ya shigo ɗakin fuskarsa da Annuri.
“Tun ɗazu breakfast yake jiran ki”
Ya faɗa yana zama kusa da ita. Agogon ɗakin ta kalla ta ga sha ɗaya har da kwata.
“Kai ya aka yi nayi bachi haka?”
“Kin gaji ne, shiyasa ban tashe ki ba”
“Amman kai ka karya ko?”
A maimakon
Showing 189001 words to 192000 words out of 280121 words
Yace da yaron babu alamar wasa a maganarsa, haka ma a yanayinsa. Da gudu yaron ya koma, ko minti biyu ba'ayi ba sai ga Namra ta fito cikin farin Hijabi ta doso inda yake. Yana kallonta dukan natsuwarsa taje gareta, kalaman daya tara zai watsa mata marar daɗi sai duk ya neme su ya rasa har ta ƙaraso kusa da shi ta tsaya.
“Ban ce kar ka sake zuwa nan ba? Jiya jiya ban maimaita maka wannan maganar ba? Ka ɓace ka bar ƙofar gidan nan”
Ta faɗa a tsawace, fuskarta babu annuri. lumshe ido Abdool yayi ya buɗe ya kalleta.
“Kina burge ni idan kina ba ni Umarni, da ma ace bakin ki be iya faɗar ƙarya ba, kin ce ba ki da aure bayan kina da shi”
“Idan na maka ƙarya nawa zaka ba ni? Miye ribata idan na maka ƙarya bayan ka tambaye tsakani da Allah?”
“Amman ƴan gidanku sun tabbatar mana da kina da aure, Asim be sake ki”
Wani irin kallon ta jefa mata mai cike da tashin hankali da mamaki.
“Ina ka san ƴan gidan mu? Waya faɗa naka sunan mijina? Waye kai? Me kake nema a gare ni”
“Naje har gidanku ne neman auren ki, kuma sun tabbatar min da kina da aure, auren ki be mutu ba”
Ta ɗora hannu saman kai.
“Na shiga uku na lalace, ka ɓata komai yanzu shikenan ba za su karɓe ni ba, miyasa baka bari na faɗa musu mutuwar aurena da kai na ba? Kaico na ni Namra, duk inda na dafa taɓen mi yake yi, ka cuce ni shiyasa ka tambaye ɗan ka ƙara jefani a halin baƙinciki da damuwa? Wayyo ni Allah na”
Ta juya da sauri ta koma ciki tana kuka. Shi dai kallonta kawai yake har ta gama faɗa masa abunda zata faɗa masa ta juya ta shige. Jikinsa yayi sanyi sosai, ko bata faɗa masa ba yasan there's something behind those words and tears da ya ga suna zuba a idonta. Juyawa yayi zai buɗe motar ya shiga sai ga Mustafa ya iso.
“Ranka ya daɗe naje kai maka kayan aka hanani shiga, kuma aka ƙi karɓa wai baka nan”
Ko kallonsa Abdool be yi ba ya ɗaga masa hannu.
“Na bar maka”
Ya shige motar, cikin rashin jindaɗin rai. Tun kamin su bar unguwar kalaman Namra suka riƙa dawo masa, idan ya tuna hawayen da ya ga suna zuba a idonta sai yaji wani abu ya tsaya masa a zuciya marar daɗi.
“Ranka ya daɗe ina za muje?”
Ya tambaya ganin har sun hau titi amman Abdool be ce da shi komai ba.
“Masaukin Mai Martaba”
Ya faɗa cikin sanyayiyar murya mai nuna mutun yana cikin damuwa.
-----------------------------------------------------------------
Ku yi haƙuri da wannan.
*72*
Da kuka Namra ta shiga gidan, bata kula su Neina da ke tsakar gidan suna gyaran giɗa ba ta wuce ɗakin Uwani, saman katifa ta faɗa tana cigaba da rera kuka.
Duk mamakine ya kama su, daman tun jiya ba su gane ma kanta ba.
“Uwani je ki gani mana”
Lamido ya faɗa yana kallon Uwani, duk ya ji babu daɗi ganin tana hawaye.
Da sauri Uwani ta tashi ta shiga ɗakin, hannu ta kai ta ɗago Namra tana tambayar
“Lafiya miya same ki?”
Sai kawai Namra ta faɗa jikinta ta cigaba da kukan. Jin kukan nata ya ƙaru yasa Neina shigowa ɗakin.
“Ke lafiya miya same ta?”
“Wallahi nima ta kasa min magana, sai kuka take”
“Toh Allah dai ya sa lafiya, ko wani ne ya mutu?”
Sai a lokacin Namra ta samu ta girgiza musu kai, tasa hannunta ta share hawayenta.
“Mutumen da ya zo yanzu, shi ne mutumen da ya zo jiya, kuma shine mutumen da ya kaɗe Lamido”
Ba shiri Neina ta zauna sake da baki dan shan labari, Uwani kuma ta yi ma Namra kallon Mamaki.
“To miyasa kawo shi? Miya ce miki”
A nan Namra ta kwashe labarin abunda ya faru, ta faɗa musu, sai dai bata yarda ta faɗa musu sanin da ta yi masa a Katsina ba.
Dukansun cika da tsananin mamaki, bama kamar Neina da take ganin kamar lokacin da ya zo gidan ba su yi ido biyu da Namra ba.
“Amman Namra in ban da abin ki miye abun kuka a ciki? Ke da Allah ya kawo miki ɗauki? Yanzu ko abunda tsohon mijin nan na ki ya yi miki ai wannan idan kika duba sakamako ne Allah zai miki”
Uwani na kai aya. Namra ta yi mata kallon baki fahimce ni ba.
“Ya ƙara ɓata min komai Uwani, yanzu iyaye na sun ji aure na ya mutu, kuma za su yi tunanin ko nice na tura sa neman aure na, idan yanzu na koma gida ban san mi zan ce musu ba”
Neina ta ɗaga kai ta kalleta
“A yadda na fahimta, idan har yana son ki da gaske ne, hakan ba zai sa ya ƙi ki ba”
“Ya so ni, ko ya ƙi i, ni duka ɗaya ne a guri na, ban shirya mutuwa sau biyu ba, ban shiryawa yaudara Namiji ba, wani na Namiji ba zai sake ɗiga min baƙinciki a rayuwata ba, na rufe shafin Namiji a rayuwata, dan haka ni ba shi nake ji ba, iyayena na ke ji da makomata”
Duk shiru suka yi, suna sauraren kukan da take rerawa. Kamin hankalinsu ya koma kan sallamar da Mustafa yake yi. Neina ce ta tashi ta fita Uwani kuma ta tsaya yana bawa Namra haƙuri.
“Maraba da Mustafa, yau an dawo shago da wuri?”
Ya zauna saman kujerar tsakar gida ta mata, yana faɗin
“Wallahi yau ban ma je ba, ya mai jiki?”
“Jiki yayi sauƙi Alhamdulillahi”
Lamido ya amsa da kansa yana miƙa masa hannu su gaisa.
“Allah ya ƙara sauƙi, naga kun yi wani babban baƙo ne a waje, amman kamar be shigo cikin gidan ba”
“Eh gurin Namra ya zo ɗan'uwanta ne”
Cewar Lamido, kamin Neina ta amsa da
“Wai Ɗan Sarki nan ne da ya kaɗe ka, shine ya zo wai yana son ta, kuma har yaje can gida ita bata ma sani ba”
Da sauri Lamido ya kalli Neina, wani irin abu ya daki ƙirjinsa, be ji daɗin maganar ba, kuma be ji rashin daɗinta ba, sai ya samu kansa cikin wani kalar yanayi na dabam.
“Me ta ce masa? Ai na ga ta dawo da kuka”
Ya tambaya kamar ba komai, sai a baɗini yana jin zuciyarsa kamar ta rabe biyu. A nan Neina ta kwashe labarin da Namra ta faɗa musu ta faɗa ma Lamido.
“Ba duka maza ne ƴan iska ba, ba duka maza ne mayaudara ba, ba a taru aka zama ɗaya ba, yadda wani yake da kwaɗayi ba haka wani yake da shi ba, ba a taru a zama ɗaya”
Ya faɗa a hankali yana kallon wani gurin kamar mai nazari. Har Neina ta buɗe baki zata yi magana, sai Mustafa ya jinjina kai ya ce.
“Amman abun da ya ba ni mamaki, wannan mutumen yayi min kama da wanda na sani, kuma shine mutumen da ya aiko yaronsa ya kira nia ka bani wanki, ya ɗauki dubu goma sha ɗaya ya ba ni wai na wanki ne, har yake labarta min wai shi ɗan'uwan ku ne, kuma yana zuwa gidan, da neje kai masa wankin sai aka ce baya nan, ina nan kuma zaune sai na gansa, ina masa magana wai ya ba ni tufafin”
Lamido ya riƙe baki.
“Wallahi ba mu da wani alaƙa da shi, ai baka nan lokacin daya kaɗe ne da ka gani, anya ba yana da wata muguwar manufa ba ce akan yarinyar nan da mu ma?”
Neina ta yi saurin rufe masa baki.
“Dan Allah ka rufa mana asiri, ɗan Sarki ne”
“Dan yana Ɗan Sarki fa? So what? Ba a da ikon faɗar gaskiya, ku kuke tsoron sa”
Mustafa ma ya saka baki.
“Kai da ka rufa ma kan ka asiri. Ko ma minene iya karka ka yi addu'ah ka zura na mujiya”
“Wallahi ba zan yi ba, ba zan zuba ido wani ya cutar da yarinyar nan ba, iya wahalar da tasha ta ishe ta haka”
Ya faɗa cike da ɓacin rai. Mustafa ya miƙe tsaye bakinsa cike da maganganun da be samu furtawa ba, yana musu Allah ya sauwaƙe.
“Amin an gode Mustafa”
Neina ce ta amsa da haka, Lamido kan hankalinsa na can wani gurin.
ABDOOL POV.
Samun kansa yayi da damuwar abunda be kamata ace ya dame shi ba, ya sara sukuninsa tun hawayen da ya gani suna zuba a idon Namra.
“Na ɓata komai? Na ƙara ruguza mata rayuwa? Mi take nufin da hakan?”
Magana yake yi da kansa yana kallon tv, babu abunda kunnuwansa suke da buƙata a yanzu kamar jin labarin Namra.
“Allah kai ka san ina son yarinyar nan, kuma Allah kai ka saka min son ta, ya Rabb help me, wallahi daga gani sai ta yi taurin kai”
Ya shafa fuskarsa yana busar da iskar bakinsa. Can kuma ya kai dubansa ga wayar dake gefensa ya ɗauka ya danna number Ummi. Bugu ɗaya Amal ta ɗauka.
“Dude zaka cigaba da ba ni labarin matar ka ko?”
Murmushi yayi marar sauti kamar tana gabansa.
“Ina Ummi?”
“Tana falo, ni ina game da wayarta”
“Tau ki ce mata na isa lafiya ƙalau kin ji”
Be jira abunda zata ce ba ya kashe wayar, yana sauke ajiyar zuciya. Sam be jin yau zan iya haƙura be ji labarin Namra ba, dare kawai yake jira yayi masa ya koma unguwar, sai dai me idan tace ba zata faɗa ba fa?
“Tau ya zan yi? Ni Wallahi tsoro ma yarinyar nan take ba ni”
Ya sake magana a fili kamar mai magana da wani. miƙewa yayi tsaye ya nufi bedroom ɗinsa yana ware hannayensa.
“Ina ta ƙoƙarin zama mahaukaci akan wannan yarinyar, Allah ka da ka jarrabe ni ta wannan hanyar”
RASHIDA POV.
Da taimakon Teema suka kwashe duk wani abu na amfaninta suka mayar a gidan da Mahaifinta ya bata. Ɗan madaidaicin gida ne mai ɗauke da ɗakuna biyar, da kuma madaidacin tsakar gida.
Gidan yayi datti sosai duk da kasancewar ba a taɓa zama a cikinsa, sai dai daɗewa da aka yi ba a buɗe shi ba yasa ya koma kamar anyi yaƙi a cikinsa. Tare da teema suka jera komai, sam bata yarda ta nunawa Teema damuwarta akan komawarta gidan ba, hasali ma tana yawan maimaita ita hakan ya fi mata daɗi kuma ita ce ta nemi Dady ta bata gidan alhalin ba haka ba ne, duk yadda hawaye suka yi ƙoƙarin zubar mata sai ta yi kamar abu ya faɗa mata a ido.
Sai dai abunda Teema ta saka samun natsuwa da shi, ganin babu ɗan'uwanta ko ɗaya daya zo rakata a gidan, ko kuma su tausasata akan karta bar wacan gidan ta dawo nan ita kaɗai. Bata nuna mata komai ba har suka gama tsara komai suka share iya inda za su iya, sauran ta ce almajiri zai gyara mata, daf da za su fita Momi ta iso gidan da kukanta kamar wance aka cirewa rai. Duk dauriyar da Rashida ta ke sai da ta fasa na ta kukan, sai ita da Momi aka rasa mai bawa wani haƙuri.
“Ni Wallahi sam ban ga amfanin wannan kukan ba, miye na barin gida Rashida in ban da abun ki? Ai ƙara ki zauna cikin danginki, ko danuwa ai kya rage”
Rashida ta share hawayenta, tana jan majina.
“Ni na zaɓi zama a nan, na fi son na zauna ni kaɗai”
Momi kan bata iya cewa komai ba, sai kawai ta miƙe tsaye tana faɗin.
“Dadyn ki ya ce zai aiko da furniture da abinci, da kuɗi kuma duk abunda kike so ki riƙa faɗa mana”
Daga haka ta fice hawaye na cigaba da mata zuba. Bayan fitarta da minti goma shabiyar Rashida ta tashi ta shiga bathroom ta yi wanke fuskarta ta fito suka ɗauki hanyar dutsen Malam.
Rashida ce take driving, Teema kuma na zaune front seat, sai kallon Rashida ta ke yi ƙasa-ƙasa. Ɗan ƙauye ne da yake can waje gari sai dai kuma ba sosai ba. Shi wannan malamin da alama aikinsa ba yayi ko kuma sabon farawa, dan babu ƙowa a ƙofar gidansa. Matan biyu masu far'ah da son mutane, suna shiga suka ɗauko musu tabarma suka shimfiɗa musu da zimmar za su aika a kira Malam wai yana gona.
Sai ga shi ya iso cikin ƙanƙanen lokaci, jikinsa har ɓari yake, bakin nan cike da goro. Bayan ya gaisa da su yayi musu iso zuwa ɗakin da yake aikin nasa.
“Bismillah”
Ya nuna musu gurin zama yana ɗauko farra ƙasarsa dake cikin ɗan ƙaramin windi. Sai da Teema ta fara gabatar masa da Rashida sannan ta fara faɗa masa matsalolinta da kuma abunda ke tafe da ita. Kai ya girgiza ya sake girgizawa sannan ya shiga duba ƙasar, can ya ɗago ya kalli Rashida ya ce.
“Wato ni bana ɓoye komai, magana ta gaskiya ƙasa ta bada bayanin ba zaki taɓa komawa gidan mijin ki ba”
Rashida ta daki ƙirji.
“Innalillahi wa'inna ilaihi raji'un”
Sai hawaye ya fara bin fuskarta. Teema ta nuna damuwa sosai.
“Malam ko dai ƙasar bata ba da bayani dai-dai ba ne? Dan Allah a sake bincikawa”
“Ai babu wani bincike, ni ba zan cuce ku ba, kun ga idan wani ne sai ya nuna muku kamar aiki zai ci ya riƙa cin kuɗin ku”
Miƙewa Rashida ta yi tsaye tana hawaye
“Teema tashi mu je”
Kamin Teema ta tashi har Rashida ta kai ƙofar gida.
“Zan kira ka Malam”
Teema ta faɗa tana aje mishi kuɗi masu ɗan dama gabansa. A tsakar gidan ma Teema ce ta yi musu sallama da godiya, ko da ta fito waje har Rashida ta yi ma motar key ita kawai take jira.
Wani mahaukacin gudu Rashida ta fara, kamar marar hankali, har sai da Teema ta riƙa ta.
“Idan har kw baki son kan ki ni ai ina son ki, be kamata kina wannan gudun ba, yawancin bokayen nan ƙarya suke faɗa fa, ki bari zamu je wani gurin”
Uffan Rashida bata ce cewa Teema ba har suka isa ƙofar gidansu Teema.
“Idan Hankalin ki ya kwanta ki kira ni zan kai ki wani gurin”
Sai ta buɗe motar ta fita. Rashida ta fi ƙarfin minti goma a gurin tana kukan sannan ta kaɗa motarta ta yi gaba.
ASIM POV.
“Nice House”
Ya faɗa yana ƙarewa gidan kallo, hannu Nably tasa taja hancinsa.
“Gida zaka yaba ba ni ba?”
“Ke ai babu kalmomin da zan iya amfani da su na ya be ki da su, amman gida ko akwai kalmomi da zan yabe shi da shi”
Ɗan murmushi ta yi, tana ƙara kallon harabar gidan.
“Momi na ta so ta gaisa da kai, sai dai tafiyar gaggauwa ta kama ta yau, amman gobe dole ne ka dawo, dan momi ta ga wanda nake yawan bata labari”
Ya kai hannunsa ya riƙo nata.
“Wato gulma na kike?”
“Ba wani gulma, ba kai ba ne ka sace mata zuciyar ƴa ba”
“Ko kuma ƴarta ta sace zuciyar wani ba”
Cikin wasa ta kai masa duka, shi kuma ya goce yana mata wani kallo, tuni idonsa har sun soma canjawa. Yar yar daya fara jin jikinsa na yi ne yasa ya saki hannunta yana faɗin
“Bari ma zo ma tafi na wuni a gidan na ku ai”
“Wato har ka gaji da gani na kenan?”
“Kai ni har na isa, kawai dai naga magariba tana gabatowa ne, ai kin ga dole jibi naje na kai ki birthday ɗin friend ɗin ta ki, kuma mu zaga gari”
“Ai gobe ne”
Ya buɗe ido.
“Tab aiko dai gobe tafiya za mu yi da oga na, ban da haka kan wallahi babu abunda zai hana ni kai ki ko ina ne a faɗin duniyar nan”
Ta wara ido.
“Kar ka damu, nima ai ban cika son kaje ba gudun kar wata ƙwace min kai”
Sai da aka soma kiran sallah, sannan ya tashi, ta rakoshi har gurin motarsa, ta buɗe masa, har zai shiga sai kuma a juyo ya kalleta ya ce
“Haka zan je ba good bye?”
Murmushi ta yi ta juya ta juyo, kamar mai nuna masa mazaunanta, daman jikinta babu mayafi, sai kawai ta kai masa kiss a baki.
“Shikenan?”
Ya ɗaga mata kai yana wani shegen murmushi. Sannan ya shiga motarsa tana ɗaga masa hannu har ya bar gidan.
“Wow wayayiyace sosai, i'm so lucky”
Abunda ya furta kenan yana ƙarawa motarsa giya. Be tsaya ko ina ba sai da isa unguwarsu, a lokacin har an sauko daga sallar magariba, sai da ya shiga gida yayi wanka sannan ya fito a masallacin unguwar yaje ya yi alwala ya yi sallah, sannan ya koma cikin gidan ya ɗauki motarsa ya ƙarasa ƙofar gidansu Mardiya.
Ko da ya kirata yace yana kofar gidansu, bata cikin gidan, dan haka sai da ya jirata har na tsawon mintuna talati sannan ya ta iso gurin da saurinta. Ta kanta ta buɗe motar ta shiga tana masa sallama.
“Ya gida ya su Mama?”
“Wallahi lafiya ƙalau, ya naka gidan?”
“Gida na babu daɗi fa”
“Subhannalla miya same ka?”
“Kin san na zama gwauro yanzu, tun da kin kore min Namra”
Mardiya ta riƙe baki kamar gaske.
“Wai da gaske ne da ake cewa Namra ta fita?”
“Ba ki sani ba? Kuma saboda ke ta bar gidan?”
“Saboda ni kuma?”
“Eh dan ta gano ina son ki, shine ta so na sake ta ni kuma na ƙi na sake ta, shine sai ta tafiyarta”
“Kai amman ban jidaɗi ba, kaje ka dawo da ita dan Allah”
“Ni yanzu ba ta ita nake ba ta ki na ke”
“Ni kuma?”
“Eh mana, ni fa tsakani da Allah na ke son ki, kuma auren ki zan yi, shine abunda ya kawo ni yanzu, na baki kwana biyu ki je ki yi shawara”
“Amman Namra ba zata ce komai ba?”
“Ke kike ta kanta, ga wannan ni zan wuce, dan gobe zan yi tafiya yau nake son na fara shiri na”
Ya miƙa mata dubu goma, ƴan ɗari biyar-biyar. Ƙin karɓa ta yi har sai da ya matsa mata sannan ta karɓa tana masa godiya, ta buɗe mota ta fita.
KALSOOM POV.
Be barta ta yi aikin komai ba, shi ya haɗa musu abun kari, kuma ya haɗa musu ruwan wanka. Daman ita ta gaji sosai, tun da ta yi sallah asuba ta koma bachi, shi kuma ganin hakan yasa be tashe ba, ya barta ta yi bachinta, har ta gaji ta tashi dan kanta, sannan ya shigo ɗakin fuskarsa da Annuri.
“Tun ɗazu breakfast yake jiran ki”
Ya faɗa yana zama kusa da ita. Agogon ɗakin ta kalla ta ga sha ɗaya har da kwata.
“Kai ya aka yi nayi bachi haka?”
“Kin gaji ne, shiyasa ban tashe ki ba”
“Amman kai ka karya ko?”
A maimakon
Book Chapters
Chapter 1Chapter 2Chapter 3Chapter 4Chapter 5Chapter 6Chapter 7Chapter 8Chapter 9Chapter 10Chapter 11Chapter 12Chapter 13Chapter 14Chapter 15Chapter 16Chapter 17Chapter 18Chapter 19Chapter 20Chapter 21Chapter 22Chapter 23Chapter 24Chapter 25Chapter 26Chapter 27Chapter 28Chapter 29Chapter 30Chapter 31Chapter 32Chapter 33Chapter 34Chapter 35Chapter 36Chapter 37Chapter 38Chapter 39Chapter 40Chapter 41Chapter 42Chapter 43Chapter 44Chapter 45Chapter 46Chapter 47Chapter 48Chapter 49Chapter 50Chapter 51Chapter 52Chapter 53Chapter 54Chapter 55Chapter 56Chapter 57Chapter 58Chapter 59Chapter 60Chapter 61Chapter 62Chapter 63Chapter 64 Chapter 65Chapter 66Chapter 67Chapter 68Chapter 69Chapter 70Chapter 71Chapter 72Chapter 73Chapter 74Chapter 75Chapter 76Chapter 77Chapter 78Chapter 79Chapter 80Chapter 81Chapter 82Chapter 83Chapter 84Chapter 85Chapter 86Chapter 87Chapter 88Chapter 89Chapter 90Chapter 91Chapter 92Chapter 93Chapter 94