gabansa yayi, a take gumi ya fara zubo masa, a take launin idanuwansa suka canja.

“Inshaallah ba zan sake ba, dan Allah ki yi haƙuri ban san kina da aure ba”

Sai a sannan ya janye ya bata hanya, ta raɓa gefensa ta wuce, shi kuma ya juya jiki a sanyaye ya nufi hanyar fita, kallonsa ake tayi a gurin saboda wasu sun san Namra tana da aure, wasu kuma suna masa kallon sani tun da akan nunasa a tv akan matsalar tsaro, kuma sun san ɗan sarki ne, tun da ga fuskar Mai-matarba nan a fuskarsa.
Sam be ji maganar da wani likita ke masa ba har sai da likitan ya cira ƙafa ya cin masa ya dafa shi.

“Manjor ina magana fa”

Ya ɗan kalleshi yana murmushin ƙarfin hali

“Doc Husaini ya aiki?”

“Lafiya ƙalau, ka zo ganin wani ne?”

“No... Eh.. Oh.. Yeah.. Yeah.. Naga wani Cousin na mu ne”

“Allah sarki, tau ya aiki ya kwana biyu? Kun yi kuɗi kun ɓoya”

“Kai ina wani kuɗi aiki ya samu gaba ba sauƙi”

Haka suka jera suna tafiya, suna ɗan taɓa fira har Abdool ya isa gurin motarsa. Jikin sashin kuzari ya buɗe motar ya shiga yana yima Doc Sallama.

“Tau ni kan zan wuce”

“Yanzu kan ganin ka sai manya, tun da baka ma zama garin”

“To ya muka iya, aikin ne a haka ko ina jefa mu ake”

“Allah ya taimaka, sai mun yi waya”

Daga haka ya rufe motarsa, shi kuma ya juya ya koma cikin asibitin. Ribas yayi ya juya hanyar gidan daya baro.
Tuƙin kawai yake jikinsa ba kuzari, kansa yayi zafi sosai, sai hannu yake sawa yana murza goshinsa, lokaci zuwa lokaci yake sauke ajiyar zuciya har ya isa gida.

Ya daɗe zaune cikin motar, sannan ya buɗe ya fito, yayi yaƙi sosai da ƙafafunsa kamin ya ci galaba akansu har su samu ƙarasawa da shi falon Ummi.
Be damu da farar shaddar dake jikinsa ya zube saman carpet, ya lumshe ido yana sauraren bugun zuciyarsa. Ya samu minti ashirin zuwa ashirin da biyar a haka, sannan Ummi ta fito cikin wata bugaggar shada ya nufo inda yake hankalinta a tashe.

Saman carpet ɗin itama ta zauna kusa da shi ta kai hannu ta riƙa kansa.

“Son tell me what happen? Larai tace min ba lafiya ba, talk to your Mom please”

Sai a lokacin ya buɗe manyan golden eyes nasa ya kalleta.

“Mom i saw her today”

“Who?”

“The woman i have been dreaming of, i finally saw her in a hospital”

“And...”

“Ummi matar aure ce”

Wani dogon numfashi Ummi taja ta sauke, tana tunanin ta inda zata fara kwantar masa da hankali.

“Abdallah, be patient one day your princess will surely come, miji baya aure sai matarsa, mace ma bata aure sai mijinta”

“I know, but what i don't understand is duk mace da na gani bata kwanta min, sai wannan ita kuma yanzu matar wani ce, zuciyata tana son wahalar da ni”

“Karka damu, komai zai wuce, i will talk to Mai Martaba, zan faɗa masa ya baƙa time, har Allah ya baka wacca kake so, bana son ka auri wace baka so ina son ganin farincikin ka”

“Thank you”

“Anything for you”

Ya ɗan kwanto jikinta, babu abunda yake gani a idonsa sai Namra.

“Allah ka shiga tsakani na da zuciyata, Allah ka min tsari da sherin zuciya”

Be ankaro da fili yayi maganar ba har sai da yaji Ummi ta amsa masa ta Ameen, dan shi duk a tunaninsa a zuci yayi wannan addu'ar.
Ummi tana son ɗan ta sosai, ta kan damu da damu damuwarsa, ta fi kowa son farincikinsa, saboda ta san zafinsa.

Abdallah Ahmad Mai-doki. Ɗa ɗaya namiji gurin Hajiya Zuwaira. Kuma ɗa na uku a jerin ƴaƴanyen Mai Martaba sarkin katsina na uku III, wato Alhaji Ahmad Abdallahi Mai-doki, jiki gurin Isma'il Mai-doki sarkin Katsina na farko.
Shine ya gaji sarautar kakansa, tun bayan da sarautar ta bar gidansu, sanadin rasuwar kakansa. Bayan rasuwar Sarkin Katsina na biyu, sai aka ɗauko sarautar aka bawa mahaifin Abdallah, wato Ahmad Abdallah Mai-doki.

Matan sa biyu a yanzu, bayan fitar Ummi ya auro Hajiya Salamatu, wace ta kasance ita ta biyu a yanzu. Hajiya Zuwaira (Ummi) Ta sha gwargwarmaya da uwar gidansa Hajiya Shafa, dan zame mata tayi muguwar kaza, mai hana shiga akurki. Hajiya Shafa ta haifa masa ƴaƴa bakwai, Mashkur ne na farko, sannan Salwee wace ita ce ta biyu, sannan Ummi ta Haifi Abdallah, wanda mai martaba ya saka masa sunan babansa, hakan yasa bata taɓa faɗar sunansa sai dai ya kira sa da Yarima ko Babana.
Mar martaba yana matuƙar son Ummi ganin ita ce ƴar'uwarsa kuma itace tafi kula da shi sama da Hajiya Shafa, hakan yasa zaman gidan ya gagareta, saboda irin son da yake nuna mata.
Babu inda Hajiya Shafa bata shiga ta fita ba, har sai da taga ta raba aurensu da Mar matarba, ba tare daya sani ba yayi mata saki uku lokaci ɗaya, kuma ya karɓe ɗansa, Abdallah a lokacin yana ɗan shekara biyu da wata uku. Son duniya nan Mai Martaba ya ɗauka ya ɗora masa, saboda son da yake ma uwarsa, sai kuma akayi sa'ah ya zama ɗa na gari gurin iyayensa, duk kuwa da faɗi tashin da yasha kamin ya kawo inda yake yanzu. Mai martaba ya so ya kaishi waje karatu amman Hajiya shafa ta hana, tasa aka kai ɗanta.

Haka tasa aka riƙa tura masa kuɗi da sunan karatu ashe yana can yana holewa da ƴan matansa, har yayi karatun ya gama be dawo gida da kyakkyawan results ba. Abdallah da yayi karatu a Nigeria sai ya fishi ƙoƙari da basira, sosai hakan ya ƙarawa Mai matarba ƙaunarsa, bayan ya gama degree a nan sai ya turawa waje yayi Master's. Hakan yasa Hajiya Uwani ma da tazo daga baya ta ɗauki ƙiyayyah ta ɗora masa, kowa cewa yake Mai Martaba yafi son sa da kowa.

Bayan fitar Ummi a gidan Mai Martaba, sai auri Alhaji Dahiru, mahaifin Haleema da Meesha da Fauza, tana da goyon ƴar autar ta, Amal ya rasu. Tun daga lokacin bata sake aure ba, sai tayi zamanta a gidan da take ita da yaranta, daman ba guri ɗaya suke da abokiyar zamanta ba. Da aka raba musu gado sai ta riƙa juya dukiyar tana business da ita har abun ya bunƙasa.

Abdallah mutum ne mai tsantsan da kai, da kuma taka tsantsan da duniya, duk da irin tarin dukiyar mahaifinsa da ta mahaifiyarsa da kuma sarautar da suke da ita, be taɓa sa yayi unƙurin wulaƙanta kowa akan hakan ba.
Yana yawan samun matsala da Ƴan'uwansa a lokacin da yake gurin mai martaba, ganin irin son da yake masa, da kuma irin rufin asirin da Allah yayi masa, ga kuma aikin da shine sillar ɗaukaka a duniya.
Baya son fitina ko tashin hankali, hakan yasa ya tattara ya dawo gurin Mahaifiyarsa, sai ya warewa kansa part ɗaya a gidan, daman can ya zuba musu securities. Ko kaɗan Mai Martaba be so hakan ba, amman dole ya haƙura ganin hakan shine mafita a garesu gaba ɗaya.
Kuma hakan be rage ƙaunarsa a zuciyar Mai martaba sai ma ƙaruwa da tayi, dan a yanzu ne Abdallah yake nuna masa kulawa da biyayyar fiye da da. Ga kuma zumuncin daya ƙaru tsakanin Mai Martaba da Ummi, kasancewar Kakansu ɗaya, daman can auren gida ne aka yi. Idan har zai cilasta Abdallah yin abu to sai dai ya kira Ummi ya faɗa mata, dan baya tun karar Abdallah kai tsaye da abunda ya san zai iya sosa zuciyarsa.

Ya kan zauna yayi fira da shi kamar abokinsa, shine yafi kowa sanin sirrin Mai martaba, gashi ya karanci mahaifinsa sosai, da ido kaɗai zai oya gane abunda Mai martaba yake so ko ƙi.
A duk lokacin da suke tare baka taɓa ganin danuwa a fuskar Mai matarba, idan ba su yi labarin zamanin baya ba, tun Abdallah zai ɗauko masa firar matsalar tsaro da kuma sauran matsalolin da suke damun ƴan negeriya, ko kuma na siyasa.

Wani lokacin kuma idan ya shiga faɗar Mai martaba, zai zauna a kusa da shi ya riƙa karatun alƙur'ane, Mai martaba na sauraro, hakan kuma ba ƙaramin daɗi yake masa ba. Ga shi kuma Major abunda Mai martaba ya daɗe yana mafarki Allah be ƙaddari zai yi ba, ɗansa yayi.
Major General Abdullah Ahmad Mai-doki, an officer of very high rank in the army. Sunan ma kawai idan an faɗa daɗi yake ma Mai maraba.

*Back to Story*

****
Sai da ya bar cikin asibitin gaba ɗaya sannan Mama ta koma ta zauna, sai taɓe baki take, ita dai bata san ko waye ba amman zuciyarta na nasalta masa babban mutum ne, sai dai alaƙar dake tsakaninsa da Namra ne ya tsaya mata a rai.
Bata jiyo abunda suke cewa ba, amman dai ta ga Namra ta tsaya ta yi magana da shi, rai ta ya sosu tana jin kamar tana taya ɗanta kishi, sai yanzu take jin rashin natsuwa a lamarin Namra ya saukar mata.

‘To idan bata san shi ba, ya za'ayi tayi magana da shi? Miye ma na wani biyota har asibiti? Ko ƙe tsakanin su Allah masa ni’

A baɗini take zancen, a zahiri kuma sai taja tsaki, ta gyara zamanta, tana kalle-kalle kamar baƙuwar asibitin.


NAMRA POV.

Tsaye ta tararda shi jikin window, yana kallon wani ɓangare na asibitin.
Har Sallamarta daya amsa be sa ya juyo ba, jar sai da aje abincin ta ƙarasa inda yake tana murmushi.

“Haka ake so Allah ya ƙara lafiya”

Ya kalleta a karkace, yana mai jindaɗi har cikin ransa, shi kansa ya san yana daf da komawa dai-dai, dan yana jin kuzari a jikinsa sosai, ga kumburin kansa nan duk a cire.
Shi kan sa ya san he has to fight for his life, just to achieve his goal, he needs so many things and many things need him, so there's no point of giving up.

“I'm just trying na ga samu sauki sun sallame mu Next week”

“Inshallah indai har kana takawa haka zasu sallame mu da wuri”

Ta faɗa tana shafa bayansa, daɗi har fal har cikin ranta. Bayan ya ci abincin ta zuba masa ruwa ya sha, sannan ya ɗauko masa zancen gyara gida.

“Har yanzu Mama bata je kasuwa ba”

“Eh wai cewa tayi tun da ga wannan kuɗin Anty ta turo miki, ta ce a bar wacan a siye magani da shi, kin ga daman rantuwa tayi abunda yayi saura sai ta mai da mata”

“Kuɗin da Anty ta tura min har na biya bashin gado da su, sauran zan siye tufafi ne da wasu abubuwan kuma Anty tace na siye waya”

“Amman ai kin ci kin ga zinarin ki? Da kin siyar sai a ƙara ayi lalura, idan Allah yasa na warke sai na siya miki wani, wanda ya fishi ma zan siya miki”

Ta ɓata fuska tana kallonsa.

“Ni gaskiya ba zan siyar da zinari na ba, shi ƙadai ya rage min na kuɗi, kuma ko na siyar sana'ah zanyi da kuɗin, dan ba zan riƙa zuwa ina roƙon kowa komai ba”

Ya taɓe baki yana mata wani kallon.

“Hmmm Namra kenan, kina min kallon talaka ko? Har zan ce ki ranta min zinarin ki yi min complain, an faɗa miki zan dauwama a talauci ne hala? Kina ganin bana da mafitar da zan biya ki ko? Nima zan yi kuɗi Namra, zan yi arxiki irin kuɗin da baki taɓa mafarkin Asim zai yi ba, akwai buƙatar nayi kuɗi ko dan na rama bikin da aka min”

“Idan nayi magana zaka ga laifi na, haba Asim shikenan sai ace kullum nice zan riƙa biyar dangi ina roƙon su abu? Yau da gobe sai Allah, na rasa komai dana mallaka, sauran kuɗin nan daya rage min da shi nake cefane, kuma siyen abinci ba haƙƙina bane, kai Allah ya ɗorawa amman ka ɗauki kuɗin nan ka bawa Mama, idan nayi magana kace rantowa kayi alhalin kuɗinka ne na adashe!”

Dammm ya wulga mata wani kallo da mugun faɗuwar gaba. Ya akayi ta sani? Ina ta ji?Ko dai Mama ce tayi subul da baka ta faɗa mata. Ƙoƙarin kare kansa yake yana naɗe tabarmar kunya da hauka.

“Allah sarki rayuwa, talauci be yi ba, a yau har ni kike tunanin na ɓoye miki wani abu, yau ni kike yi ma gori akan kin siye abinci, ai ban san ba dan Allah kika aure ni ba sai yau, kina ganin kamar ba zan iya rayuwa babu ke ba ko? Kina ganin kamar da arzikin ki nake ci ko? Kina ganin ke kika min magani ko? Da gaskiyar Mama yanzu cewa za ayi duk ni na ƙarar miki da komai na ki, daman haka kike so ace na auro ki na zo na aje ki ina cin amanarki ko? So that ki samu damar fakewa da na yaudare ki, daman na san ba dan Allah kika aure ni ba”

Tun da ya soma kwarara zantukansa kallonsa kawai take tana mamakin kalamansa, wasu zantukan ma bata san inda suka dosa ba. Yau kam ya fara fito mata a kowaye shi, ya bayyana mata abunda zuciyarta ta soma zargi akansa.

“Na bar jindaɗin gidan mu, na zabe ka. Na watsar da karatuna na bika, saboda kar kace na yaudare ka. Na sadaukarda komai nawa saboda kai, amman duk ban tsira ba? Irin kallon da kake min kenan? Nice ya kamata ace na zarge ka tun lokacin da na ji abunda kuke magana kai da Mama amman na taushe zuciyata ina ƙoƙarin yaƙi da ita akan ka, ka kan nuna son iyayena su taimaka kama amman duk be sa na zarge ka ba, miyasa baka tausayina ne? Yanzu na gano dalilin rashin son da Mama take min, kuna min kallon wawuya wacce bata san ciwon kanta ba.

Son ka ne Asim shine ya rufe min ido na kasa ganin laifin ka, babu irin furucin da ba amin ba akan ka, amman na dage sai na aureka, a tunani na kana min irin son da nake maka ne”

Ta ƙarasa maganar murya ƙasa-ƙasa irin kifi musulmim nama, tana hawaye. Shi kam tsire baki yayi ya kalleta

“Kowa ya sani ba tsakani da Allah kika aure ni ba, sai da wanda zai aureki yace ya fasa sannan aka nemo ni, yanzu kuma kina son yin amfani da damar da kike da ita na rashin lafiya ki kula wasu mazan a waje”

“Me kake nufi?”

“Kin fi kowa sanin abunda nake nufi, waya kawo ki yanzu cikin asibitin nan? Ina kallon yadda ya rako ki ya koma, ko kin maidani mahaukaci ne, talauci ba yin kaina bane Namra, dan ina talaka ba zaki wulaƙanta ni a banza ba”

Ta miƙe tsaye tana masa kallon mamaki, har kofin ruwan dake hannunta ya zube.

“Ka zarge ni da komai, amman ban da Zina, dan ban sha nono ba, mahaifina be yi da ƴar wasu ba, dan haka ba za'ayi da ni ba, ban aikata zina ina budurwa ba, ba zan aikata da aurena ba. Kai butulu ne Asim wanda be san hallaci ba, ɗan bushiya mai soke uwar goyonsa a baya....”

Tasss ya watsa mata yatsunsa biyar a gefen fuskarsa, a zaune da yake, sai wani zanzana yake kamar ya riƙota yayi ta dukanta.

“Kim fita da ainahin kalar ki Namra, daman kin min duk abunda kika min ne dan wata rana ki min gori? To mina samu a auren naki? In banda baƙar ƙaddara miye ke bi na?”

Dafe kuncinta tayi ta juya a guje tana wani irin kuka mai taɓa zuciya, ta fice ɗaga ɗakin.



RASHIDA POV.

Kukanta ne ya shigo da su Momy a ɗakin. Duk tambayar da suka mata kasa amsawa tayi sai kuka take kamar wace aka cirewa rai.

“Ya sake ni Momy ya sake ni! Na shiga uku na lalace na ba ni Momy mutuwa zan yi, Wayyo Allah na”

“Me kika masa?”

Momy ta tambaya hankali a tashe. Ta kardar kawai ta iya nunawa Momy tana kuka sosai.
Da sauri Momy ta ɗauki takardar ta buɗe.

“Ni Hilal a yau na saki Rashida saki ɗaya”

Momy na gama karantawa ta rufe takardar tana faɗin

“Innalillahi wa'inna ilaihi raji'un”

Sai ta riƙata, ta zaunar saman gado tana girgizata, ganin tana ƙoƙarin fita hayyacinta.

“Ke Rashida kwantar da hankalin ki zan sa ya maida ke kin ji?”

Ta rirriƙe Momy gamgam tana zare ido.

“Da gaske Momy?”

“Da gaske mana, ki kwantar da hankalin ki kinji? Zan yi magana da shi”

“Toh”

Tayi zurun kamar sabuwar mahaukaciya. Sai kallon Ummu Faisak take wace ta shigo yanzu.

“Lafiya miya same ta?”

Ta ƙarasa da sauri tana tambaya. Momy bata iya faɗa mata komai ba ta fita ta kira likita, yayi mata allura, cikin ƙanƙanen lokaci ta samu bachi.
Sai da suka fito sannan Momy take labarta mata abunda ya faru cikin yanayin damuwa.

“Af ai da sauƙi tun da sakinta kawai yayi be kashe ta ba, ai a yanayin yadda ya bar gida na ɗauka yana zuwa zai kashe ne ma, kin ga yadda yake ji da matar nan? Hmmm”

“Aiko idan ka ganta kamar ta ƙwarai, ƙo dai wani abun ne ya haɗa su?”

“Ai haka ƴan matan zamani suke, suyi miki laflaf su kwace miki miji sannan su koreki, ai wannan saki daga gani bana banza bane mace na ciwon zubar ciki kuma asibiti gurin iyayenta? Hmmm”

“Ai yanzu sai an bincika za a ji ko minene, bari na faɗa ma Daddyn”

Cikin yanayin damuwa da ɗaurewar kai Momy take maganar.

Hilal ko da ya koma gida ya tarar yaransa sun dawo, daga gidan Hajiya, ko wanne fuskarsa babu walwala sun saka Kalsoom gaba, kamar su mata kuka.

“Hey kids”

Ya faɗa yana ƙokarin zaunawa sound so cool and funny. Sai duk suka nufo shi suna faɗar.

“Daddy wai Hajiya tace mana Ammyn mu ba lafiya tana asibiti”

Ya ɗan sosa kansa, sam ya manta yace kar Hajiya ta faɗa musu. Kalsoom dake ɗauke Rafiq ta nufo shi tana faɗin

“I try to explain but.. ”

Da ido yayi mata alama da tayi shiru yaja hannunta ya zaunar da ita kusa da shi, ya kalli yaran.

“Listen kids Maman ku ta ji sauƙi sosai, har ma tace na gaishe ku”

“Daddy ina son na ganta”

“Ba zaki ganta yanzu ba, amman ajima zan kira miki ita a waya ku gaisa”

“Tau”

Ulfah ce ta wayance, jin ance taji sauƙi, Ezzah kam ƙin sakewa tayi sai ƙoƙarin
Showing 87001 words to 90000 words out of 280121 words