Itama wanka tayi sabo da shi a toilet ta shirya ta canja wata Yar doguwar rigarta ta gwanjo me gajeren hannu pink duk ta ji jiki sai dai tana Mata kyau,da wani kofin Silver ta shigo da Dan karamin flask a Hannunta da spoon da sugar,a gabansa ta Ajiye ta bude Koko fari tas da kosai manya,yasan Kosai Amma Bai taba ganin Koko ba,Yace sunan this? Yana Nuna kokon da yatsa,tunawa yayi ai da sauri yace No..no I knew,na sani ya wayance,Manal Tace Wai Kai da baka iya hausa ba a Ina asalinka ka taso? Kawai yace Wani Kauye ne a Niger mana, French na iya,Manal Tace Oh Allah sarki,a Haka ta zuba sugar a kokon itama ta sa spoon dinta ta fara Sha,shima Haka da nasa Spoon din da kyar yake Sha yafi cin kosan, har Suka Gama sannan Tace an kone maka kayan sai dai ka zauna da wannan na jikinka kafin Nan gaba,Bai Gane ba yace meaning what? Manal Baki ta turo tare da furta Kai Farooq Ni na gaji da halinka na rashin iya hausarka kasan dai ba Jin turanci nake Yi ba,a Niger din a wanne yankin kake da har zaka kasa Jin hausa,Nima daka ganni Hausar Nan ba Isa ta tayi ba da kyar nake yinta tashi muje Asibiti wajen Dan uwanka Ni ai cin Fuska kake min Dan kaga ban iya turanci ba ta karasa da shagwaba,Dariya ta bashi yayi ta a ransa kawai.
Wannan Maganar da tayi ya fahimta sai ya Mike da tarin sumarsa da gemu da saje me uban yawa,mayafinta wani tsoho tukuf Baki ta yafa tare da saka slifas dinta local, kallon takalmin nata yayi a ransa shi ko a toilet bazai iya amfani da wannan local takalmin ba,Fitowa sukayi a tare da Takalminsa flat me Dan kyau Wanda da abinsa yazo dama,Suna Fitowa Hajiya da Farida suna tsakar gida Farida Ta kalle shi ta fetsar da Yawu gefe Yana kallonta a ransa Yana mamakin me ya Mata ta tsane shi haka Bai San Farida ita Bata kaunar talaka ba ita da uwarta tanadin shiga daula suke Yi, gashi Kuma ya Mata laifi sunyi sanadin da Bata ga masoyinta ba Fuzail Dan sarki.
Farida tana yatsina Fuska tace dama ance Yan Fulani ba abinda Suka sani sai sex always sex..sex...a daji ma babu komai sai sex,ance Haka ma kuke bin yan uwa da sex da juna wannan tabi Mijin wannan,har Yan uwanku binsu kuke Yi,to wallahi Bari Yaya Yazed ya dawo sai mun fada Masa kin kawo katon gardi Kuna Sex kullum Baku da Aiki sai Zina,Manal kalleki 17yrs kin San Namiji,kin San bin maza,Fuzail ya Gane duk abinda take nufi sabo da Farida tana hadawa da turanci,Yaji Haushi a ransa sosai shi a rayuwa ma in Banda Manal babu wata mace a duniya da ya taba yiwa kallon kwaf.
Shuru ya musu,Manal tace muje Farooq Haka Suka fice tare suna tafiya zuwa gefen Titi,Manal sai surutu take Masa shi Kuma wani ya Gane wani baya ganewa,Tace a gidanku kuwa Kun taba kwana da yunwa Baku ci ba? What? Ya sake tambaya tace babu abinci har kwana Daya ta Masa zancen tana nuna Masa da hannu,Ohhh ya furta Yana murmushi yace Yes Uku kwana,Dariya ta dinga Yi Tace Dan Niger Kawai kwana Uku ake cewa ba Uku kwana ba,No Uku kwana,Kwana Uku Haka yes,murmushi yayi suna tafiya sun jera yace na gani,Na Gane zaka ce fa, alright na gane ya furta da kyar ,Manal tace Zan koya maka hausa Kai Kuma ka koya min yaren faransanci da turanci,Okay ya furta yasan Bai iya french ba Amma zai mata yaren Brazil Kawai ya barta a French,Tace Ina jinka har kwana Uku Kuna Yi ba abinci? Kai ya daga Mata kawai,Manal Tace Ni fa ban Gane ba sai kace wani Dan sarauta kayi ta yanga gaka da Izza da Gadara Naga Alama talaucin da kuke ciki Bai koya maka darasi ba,ita duniya a Sannu ake binta,kana Dan talaka futuk ka dinga wannan Gadara wallahi ka canja hali,gaba Daya ka faffake Hanya sabo da Izza Haka ake lamarin duniya ga Gadara ga rashin kudi to wallahi Dole ka daina wannan halin ba tsabiyar kirki bace,kace zaka zauna Dani har sati Daya kafin ku samu wajen Zama to Dole ka daina wannan mummunar Dabi'ar taka,shi dai abinda ya tsinta ya gane Yana ji kuma,da kyar yace Haka nikai,Haka nake zaka ce,Okay Haka nake ya furta Yana dariya.
Suna bakin Titi Tace to sai mun tsallaka Titi,yace cross titi? Okay Tsalka na Gane,Dariya Manal tayi Tace Niger ta cuceka wallah Wai tsalka,muje ba mota Hannunta ya rike sosai Yana kallon Titi Suka tsallaka,Napep ta tare suka shiga duk Bai iya Hawa ba Amma Haka ya daure ya nuna ya Saba ai,Har cikin Hospital ya kaisu sannan Manal Tace me Nape Nawa? Fuzail yayi Dariya yace Napep not Nape Haka Ana ce a Nigeria,Manal Tace to anji Dan gwani nace Napep,Me Napep kallon Farooq yayi Wanda Fuzail kenan Jin yanda yayi Hausar,Itama Manal gaba Daya harshenta na Yar Fulani sai kace fulatanci take Yi,Me Napep yace dari biyu Manal tace aradu baka Isha ba,dari nika baka aggarin mahaukata mukkai,Fuzail yace how much? Me Napep yace two Hundred Naira,Fuzail ya daura hannu a Kai Wai yayi tsada da yawa yace ba mafiya muke Yi ba fa?Manal sabo da dariya harda rike ciki Farooq yaji hausa harda dogon sentence,Me Napep yace ku kawo dari na tafi Kuna Bata min lokaci,Manal yanda Suka Saba a Kauye ajiye kudi a cikin Bra,Hannu ta zura ta zaro wata dukunkunanniyar naira dari,Fuzail ya zaro Ido da mamaki,me Napep ta mikawa Naira darin kafin ya karba Fuzail ya kwace kudin ya ja Manal gefe yace akwai cuta jikin kudi ....no....no...fasa turancin yayi yace ba'a sawa a bra noooo....really bad,Manal tace na daina naji Farooq bashi kudin mu tafi,Fuzail yace no....ya taba nono naki,Me Napep zai taba laushin a jikin kudin,Manal tayi Dariya tace laushin ba makalewa zaiyi ba a jiki ka bashi mu tafi,Fuzail fafur yaki bada Naira dari yace me Napep yazo su shiga hospital ya karbi wani kudin wajen Ameer,Me Napep da masifa yace Amma wannan Mijin naki ya cika kishin bala'i in Banda hauka a jikin kudin kirjin zai makale da zai Hana kudin aikin banza,shi kadai ne me Mata,ya kalli Fuzail yace har Mata biyu gareni banza Dan akan wannan Yar kauyen ma ance maka Dan Iska ne ni? na yafe muku wallahi kuje Ni baza ku Bata min lokaci ba,Manal ta dinga Murna Tace da gaske ka yafe? Yace ae wallahi Yaja Napep yayi gaba,Farooq ya boye kudin a aljihunsa.
Suna shiga Suka Iske Yaron Ameer Yana kula da shi Amma Manal Bata sani ba,ita dai ance a Asibitin yake taimako yakeyi Kawai,Manal tace Wai ku Kira danginku Mana ko a waya ne ganin wata karamar kwakurar waya Vivo a Hannun Ameer,Shi Kuma Fuzail Wanda ta sani da Farooq tasa Wayar Tecno ce pop 3 ta talaka dai dai gwargwado sabo da matasa yanzu suna kokarin rike Yar babbar waya,Ameer Yana kwance Fuzail ya kyafta Masa Ido,Ameer yace ai kin San duk Dangin namu mun fada Miki suna kauyen Niger,mu Nan zuwa Mukayi Neman wajen Zama kafin mu samu sana'a akwai Wanda yake Dan garin namu anan Baya Nan sai Nan da sati biyu zai dawo shi zai mana komai,Manal Tace Haka Farooq ya fada min Allah sarki Allah ya baka lafiya Sannu, Inshaallah kana warkewa zaku samu gidan zama.
Allah yasa Kinga bawan Allah din Nan ma Yana kawo min abinci Sadaka Ina ci gashi Yana kula dani cewar Ameer ,Manal tana murna Tace da mutumin mun gode Allah ya saka da Alkhairi,mutumin yace Ameen ai yiwa Kaine ko ba komai Zan samu lada sabo da Allah nayi,Manal Tace kai Ameer gashi Kana Jin hausa sosai ya akayi Farooq shi Bai Jin hausa? Ameer yace ai ni kusan a Kano state Muka Yi karatu shi yasa muka ji hausa sosai,shi Kuma a kauyenmu yayi primary da secondary school,sannan University ma wata yayi wacce a Kauye take ma Kuma ba a hausa a yankin,Manal Tace ayya shi yasa ashe to shike nan.
Ameer yace yanzu matsalarmu kayan sawa Amma wannan bawan Allah yace zai siyo Mana kayan gwanjo kala biyu Sadaka sabo da Allah,Manal tana murna Tace har Ina tunani wanne Aiki zanyi na samo kudin da Zan siyo muku ko gwanjo ne ku samu amma bawan Allah mun gode,Fuzail dai Manal yake ta kallo da tsananin mamaki sai murna takeyi kamar wasu Yan uwanta.
Ameer Yana kallon irin kallon da Fuzail kewa Manal Yana mamaki mutumin da Mata ma hadaddu Basu isheshi kallo ba sai wannan ga kauyenci ga talauci duk da yasan karyar mutum ya kalli Manal Bai sake kallonta ba sai dai hassada amma Manal abar kallo ce,Manal tace Farooq ka zauna a Nan Bari naje gida nayi Mana abinci sai nazo na tafi da Kai gida,bani naira darin Nan sai na hau Napep da ita ta furta tana Mika Masa Hannu,Fuzail ya kyaftawa mutumin Dake kula da Ameer ido Nan take yace kanwata kema ga Sadakar dubu Daya kiyi amfani da ita,Manal ta Bude Baki Tace Malam kudin sunyi yawa ka bani duka Sadaka Haka? Yace karbi Allah ya bamu Lada kema ai kin taimaka.
Manal har kasa ta durkusa tare da sa Hannu biyu ta karbi kudin tana uban godiya da Addua sabo da Bata da ko sisi dama so take taje ta nemi aikin wanke wanke da shara a gidan masu Saida abinci tayi ko na yini Daya ne a biyata ta samu ta dafa musu abinci da kudin sai gashi ta samu Amma duk da Haka tasan a tsadar abin duniya a yau dubu zata Kare gwara ta nemi kudin tun yau gobe ta samu su Kara kawai.
Da murna ta kalli Farooq tare da cewa Zan wuce sai nazo daukanka,Murmushi yayi ta tsira Masa Ido yanda yake da mugun kyau duk da shigar Daya canja tare da kasumba da uban gashi Bai Hana kyawunsa bayyana ba musamman idan yayi Murmushi kyawawan hakoransa suka bayyana ga wani lips dinsa red masu kyau,Hancinsa kadai ya Isa a kalli Farooq,ga kirar surar jikinsa musamman skin dinsa abin Yana birge Manal ita Kam ta Gama ganin kyau wajen Farooq inama zaiyi Aski da yafi Haka kyau ta furta a ranta,tana gama tunaninta tace na tafi ta juya tana waigowa tana kallon Farooq,Hannu ya daga mata har ta bar asibitin.
Tana tafiya wajen wata me siyar da Abinci a Tasha ta tsaya,suna mutunci da Dattijuwar Manal tasan Yaya Yazed ya hanata irin wannan Neman kudin Amma Dan kudin Daya bar Mata su Farooq sun cinye su Dole ta nemi wasu,Ladidi Tace Manal yau ko aikin kika Zo Yi ne? Da sauri Manal Tace ae Ladidi,okay Zo dama ga wanke wanke ya taru bana so customers su fara yawa ba a wanke ba,ai Kuwa Manal ta shiga wanke plates da spoons tana ta faman Yi ana siyen abinci Ana cinyewa za a kwaso wasu a kawo ta wanke,tunda ta fara aikin Hannunta Bai huta ba har 3pm tun safe,lokacin ta tuna da bakinta da suke wuyanta, Nan take tace tafiya zata Yi ta Gama aikin yau,Ladidi taji Dadi sabo da Manal ta Iya Aiki sai tace Manal akwai shinkafa da Miya,fried rice,sakwara da miyar Egusi,ga tuwo ma ki zaba a ciki me Zaki iya ci na zuba Miki ki tafi da shi gida ai kin Sha aiki,Farin ciki ya Kama Manal ba sai tayi girki ba da dare sai ta dafa musu Indomie kawai.
Manal Tace Frit race (Fried rice) za a bani da sakwara,Ladidi da yaranta suka dinga dariya tare da cewa Fried rice ake cewa sai da Manal ta iya fada sannan Ladidi ta Mata take away harda nama yanka biyu a kowanne girki,Ledoji biyu Manal ta karba tana godiya sannan Ladidi ta Bata dari uku.
Ameer Kuwa take away aka musu lafiyayye amma ga mamakinsa sai Fuzail yaki ci,juyin duniya yace na gidan mu zanci,Dariya Ameer yayi yace au har gidansu ma ya Zama gidanku? na talaucin? Kuma wannan Yarinyar in Banda jagwalgwalo me zata yi,Fuzail Cikin Harshen turanci yace yarinyar data taimaki rayuwarka kake fadawa Haka?Yarinyar data kawoka Hospital da kudinta,Yarinyar da zata iya aikin kaskanci ta ciyar da wani,yarinya karama with Good heart,wannan Yarinyar tana da wasu Good Qualities da ba ko wacce mace ke da irinsu ba,Ameer kallon Abokin Nasa Kawai yake Yi da mamaki wannan Yar Yarinyar Yar Kauye yasan tana da Hali me kyau,Ameer yace yanzu prince baza kaci Abinci me kyau ba na waccen yarinyar zaka ci? Idan cuta ta Kamaka fa? Fuzail Baki ya tabe sannan ya bawa Ameer Labarin gidan su Manal da abinda Yan uwanta su Farida suka Masa,Ameer ya dinga dariya yace wlh sunyi dai dai,Fuzail Dan hauka ka shiga dakin yarinya idan da sun Tara maka mutane fa? Yarinya Haka ku kwana tare mahaukaci ne kai? Ban San tayi bacci bafa,Hmm Ni Dadi ma naji tun ranar da yarinyar Nan ta rike Hannuna na Gane Ni Namiji ne Fuzail ya furta Yana murmushin Jin Dadi, Ameer ko magana baiyi ba Likita ya shugo tare da wanke Masa rauninsa yana canja plasta Manal ta shigo da fara'a tayi Sallama,Ameer ta kalla ta Iske Yana cin abinci tace jiki yayi kyau Sannu,karka damu kaji an kusa sallamarka ta furta tana lallashinsa,ta Bawa Ameer Dariya yarinya karama sai iya tattali Amma tana birge shi murmushi yayi tare da furta me kika kawo Mana,Yana magana amma surar Fuzail take kallo yanda ya tube rigarsa taga Namiji iya Namiji ga skin me kyau sai sheki yake yi,surarsa take karewa kallo,Ameer yace Ina magana Yan mata,Firgit ta saki murmushi tace ahm...Uhmm....Fried rice da sakwara.
Ameer yace ashe abin Dadi ne Yar Fulani an iya turanci Ashe,da sauri Manal ta zauna a gefensa tare da furta kaji tsiya wata ce Tace sai na koya yanda ake fada da turanci sai Dana kwashe Rabin awa ban iya fada ba sai da kyar kasan kaina kindirmo ne a ciki ya daskare,Dariya Ameer ya dinga Yi yace Baki da dama,Manal tana Dariya Tace wlh Ni wata Kindirmo ce ka ganni to ya za muyi talauci ne ya jaja mana,Da ace da kudi yaushe zaka ganni haka yanda nazo birni ai da tuni na dauki Hanyar wayewa dodar.
Ana Gama dressing Masa Farooq ya maida rigarsa sannan ya mike tare da daukan kayansa na gwanjo kala biyu da aka siyo musu Suka ce mutumin Nan ne ya Basu Sadaka, Manal tace muje ko? Kai ya daga da Izza,Suna Fitowa Manal tace tsaya,cak ya tsaya Tace masifa Zan maka to na fada maka ka daina wannan Izzar, murmushi yayi kadan idan baka kula ba baza ka Gane murmushi yayi ba,Oh ba Haka ake murmushi ba yaye bakinka zaka Yi sosai kalla Haka ta gwada Masa tare da washe bakinta Tace Haka fa,Yi na gani Dariya ce ta kamashi ai Kuwa ya washe Dan karamin bakin sa,Manal tace kaga Baki Kamar kurtun Limamin rugar mu da yake dura kakin majina a ciki,yaji abinda tace yace zagina ko?Da sauri Manal ta furta no Ina nufin bakin me kyau, kyau? Ya tambaya tace ae,Okay yace Suka tafi,Napep Suka shiga zuwa gida,Ana zuwa Ta biya kudin sannan Suka shiga gidan.
Suna shiga gidan Farida da Hajiya sun tanaji ruwa botiki Guda ai Kawai sai ruwan Suka juye shi a jikin Farooq gaba Daya,Hajiya tazo ta zuba Masa Rankwashi a Uwar sumarsa me yawa,sabo da tarin Sumar Bai ma San ta rankwashe shi ba,yaga dai gilmawar Hannunta ta saman Kansa, kunnensa Zaki murde Dan matsiyata kwarto cewar Farida,Hajiya ta Kama Kunnen Farooq ta murde da karfi ya saki kara,Manal ta fashe da kuka tayi kukan Kura ta Kama fatar gadon bayan Hajiya tare da gartsa Mata uban cizo,ai Hajiya ihu ta saki ba shiri ta saki Farooq,kunnensa yayi wani ja,Manal ta kalle su Tace wallahi wulakanta Dan Adam babu Dadi a rayuwa Ina ruwanku da shi? Farida ta kalli Farooq Ido da Ido ta shiga dura Masa ashar ta uwa ta uba,Dan Bur....Dan bura..gidan Ubanka ne? Ai na tsaneka tunda har kayi sanadin da na kasa ganin masoyina har yayi tafiya sai ka bar gidan Nan tsinannen banza,Hajiya tace wallahi yau bazai kwana a gidan Nan ba,idan wani kwarton Zaki kawo Manal ki kawo kuyi ta kwana wallahi mu zamu rufa Miki asiri Amma Banda wannan algungumin Yana yawo da shegiyar Suma ga kasumba Kamar liman,me ci da addini Kawai Allah ya tsine maka Albarka tunda ka Hana yarinya ta haduwa da arzikinta Dan Iska mazinacin banza.
Wallahi Manal bazai kwana a gidan Nan ba wannan in Banda wari ma me zaiyi ke ko kunya bakya ji kalleki kyakyawa ai kinfi karfin talaka Manal,ke matar manya ce,kina so ki jefa rayuwarki a wani sabon talaucin cewar Farida,Hajiya Tace in Banda masifa gamu talakawa ki kwaso wani talakan again.
Hajiya tabarya ta dakko tace gidan Nan ba asibiti bane ya bar gidan Nan ko na rushe Masa Kai ko Kuma wallahi yau na Tara muku mutane a watsaku a Internet,Manal tasan Hajiya zata iya aikata komai tace ba sai kinyi Haka ba zamu tafi Zan bishi sai Sanda Suka samu wajen Zama kullum zan dinga zuwa inda suke Ina kula da su,idan Yaya ya dawo ki fada Masa nasan abinda zaku ce Kenan,ai dai baza ku Hana nayi musu girki na Kai musu ba,taimako ne sai nayi,Hajiya tace munji Amma ba a gidan Nan ba,ya Gama cutar mu zaizo ya tare Mana a gida bazai yuwu ba,Manal tace muje Farooq.
Hajiya da Farida tare da su Sa'iha suka rike Baki da mamakin Manal su duk abinda suke Mata hange talaka ta kula,Masatura Tace tab
Showing 24001 words to 27000 words out of 153479 words
Itama wanka tayi sabo da shi a toilet ta shirya ta canja wata Yar doguwar rigarta ta gwanjo me gajeren hannu pink duk ta ji jiki sai dai tana Mata kyau,da wani kofin Silver ta shigo da Dan karamin flask a Hannunta da spoon da sugar,a gabansa ta Ajiye ta bude Koko fari tas da kosai manya,yasan Kosai Amma Bai taba ganin Koko ba,Yace sunan this? Yana Nuna kokon da yatsa,tunawa yayi ai da sauri yace No..no I knew,na sani ya wayance,Manal Tace Wai Kai da baka iya hausa ba a Ina asalinka ka taso? Kawai yace Wani Kauye ne a Niger mana, French na iya,Manal Tace Oh Allah sarki,a Haka ta zuba sugar a kokon itama ta sa spoon dinta ta fara Sha,shima Haka da nasa Spoon din da kyar yake Sha yafi cin kosan, har Suka Gama sannan Tace an kone maka kayan sai dai ka zauna da wannan na jikinka kafin Nan gaba,Bai Gane ba yace meaning what? Manal Baki ta turo tare da furta Kai Farooq Ni na gaji da halinka na rashin iya hausarka kasan dai ba Jin turanci nake Yi ba,a Niger din a wanne yankin kake da har zaka kasa Jin hausa,Nima daka ganni Hausar Nan ba Isa ta tayi ba da kyar nake yinta tashi muje Asibiti wajen Dan uwanka Ni ai cin Fuska kake min Dan kaga ban iya turanci ba ta karasa da shagwaba,Dariya ta bashi yayi ta a ransa kawai.
Wannan Maganar da tayi ya fahimta sai ya Mike da tarin sumarsa da gemu da saje me uban yawa,mayafinta wani tsoho tukuf Baki ta yafa tare da saka slifas dinta local, kallon takalmin nata yayi a ransa shi ko a toilet bazai iya amfani da wannan local takalmin ba,Fitowa sukayi a tare da Takalminsa flat me Dan kyau Wanda da abinsa yazo dama,Suna Fitowa Hajiya da Farida suna tsakar gida Farida Ta kalle shi ta fetsar da Yawu gefe Yana kallonta a ransa Yana mamakin me ya Mata ta tsane shi haka Bai San Farida ita Bata kaunar talaka ba ita da uwarta tanadin shiga daula suke Yi, gashi Kuma ya Mata laifi sunyi sanadin da Bata ga masoyinta ba Fuzail Dan sarki.
Farida tana yatsina Fuska tace dama ance Yan Fulani ba abinda Suka sani sai sex always sex..sex...a daji ma babu komai sai sex,ance Haka ma kuke bin yan uwa da sex da juna wannan tabi Mijin wannan,har Yan uwanku binsu kuke Yi,to wallahi Bari Yaya Yazed ya dawo sai mun fada Masa kin kawo katon gardi Kuna Sex kullum Baku da Aiki sai Zina,Manal kalleki 17yrs kin San Namiji,kin San bin maza,Fuzail ya Gane duk abinda take nufi sabo da Farida tana hadawa da turanci,Yaji Haushi a ransa sosai shi a rayuwa ma in Banda Manal babu wata mace a duniya da ya taba yiwa kallon kwaf.
Shuru ya musu,Manal tace muje Farooq Haka Suka fice tare suna tafiya zuwa gefen Titi,Manal sai surutu take Masa shi Kuma wani ya Gane wani baya ganewa,Tace a gidanku kuwa Kun taba kwana da yunwa Baku ci ba? What? Ya sake tambaya tace babu abinci har kwana Daya ta Masa zancen tana nuna Masa da hannu,Ohhh ya furta Yana murmushi yace Yes Uku kwana,Dariya ta dinga Yi Tace Dan Niger Kawai kwana Uku ake cewa ba Uku kwana ba,No Uku kwana,Kwana Uku Haka yes,murmushi yayi suna tafiya sun jera yace na gani,Na Gane zaka ce fa, alright na gane ya furta da kyar ,Manal tace Zan koya maka hausa Kai Kuma ka koya min yaren faransanci da turanci,Okay ya furta yasan Bai iya french ba Amma zai mata yaren Brazil Kawai ya barta a French,Tace Ina jinka har kwana Uku Kuna Yi ba abinci? Kai ya daga Mata kawai,Manal Tace Ni fa ban Gane ba sai kace wani Dan sarauta kayi ta yanga gaka da Izza da Gadara Naga Alama talaucin da kuke ciki Bai koya maka darasi ba,ita duniya a Sannu ake binta,kana Dan talaka futuk ka dinga wannan Gadara wallahi ka canja hali,gaba Daya ka faffake Hanya sabo da Izza Haka ake lamarin duniya ga Gadara ga rashin kudi to wallahi Dole ka daina wannan halin ba tsabiyar kirki bace,kace zaka zauna Dani har sati Daya kafin ku samu wajen Zama to Dole ka daina wannan mummunar Dabi'ar taka,shi dai abinda ya tsinta ya gane Yana ji kuma,da kyar yace Haka nikai,Haka nake zaka ce,Okay Haka nake ya furta Yana dariya.
Suna bakin Titi Tace to sai mun tsallaka Titi,yace cross titi? Okay Tsalka na Gane,Dariya Manal tayi Tace Niger ta cuceka wallah Wai tsalka,muje ba mota Hannunta ya rike sosai Yana kallon Titi Suka tsallaka,Napep ta tare suka shiga duk Bai iya Hawa ba Amma Haka ya daure ya nuna ya Saba ai,Har cikin Hospital ya kaisu sannan Manal Tace me Nape Nawa? Fuzail yayi Dariya yace Napep not Nape Haka Ana ce a Nigeria,Manal Tace to anji Dan gwani nace Napep,Me Napep kallon Farooq yayi Wanda Fuzail kenan Jin yanda yayi Hausar,Itama Manal gaba Daya harshenta na Yar Fulani sai kace fulatanci take Yi,Me Napep yace dari biyu Manal tace aradu baka Isha ba,dari nika baka aggarin mahaukata mukkai,Fuzail yace how much? Me Napep yace two Hundred Naira,Fuzail ya daura hannu a Kai Wai yayi tsada da yawa yace ba mafiya muke Yi ba fa?Manal sabo da dariya harda rike ciki Farooq yaji hausa harda dogon sentence,Me Napep yace ku kawo dari na tafi Kuna Bata min lokaci,Manal yanda Suka Saba a Kauye ajiye kudi a cikin Bra,Hannu ta zura ta zaro wata dukunkunanniyar naira dari,Fuzail ya zaro Ido da mamaki,me Napep ta mikawa Naira darin kafin ya karba Fuzail ya kwace kudin ya ja Manal gefe yace akwai cuta jikin kudi ....no....no...fasa turancin yayi yace ba'a sawa a bra noooo....really bad,Manal tace na daina naji Farooq bashi kudin mu tafi,Fuzail yace no....ya taba nono naki,Me Napep zai taba laushin a jikin kudin,Manal tayi Dariya tace laushin ba makalewa zaiyi ba a jiki ka bashi mu tafi,Fuzail fafur yaki bada Naira dari yace me Napep yazo su shiga hospital ya karbi wani kudin wajen Ameer,Me Napep da masifa yace Amma wannan Mijin naki ya cika kishin bala'i in Banda hauka a jikin kudin kirjin zai makale da zai Hana kudin aikin banza,shi kadai ne me Mata,ya kalli Fuzail yace har Mata biyu gareni banza Dan akan wannan Yar kauyen ma ance maka Dan Iska ne ni? na yafe muku wallahi kuje Ni baza ku Bata min lokaci ba,Manal ta dinga Murna Tace da gaske ka yafe? Yace ae wallahi Yaja Napep yayi gaba,Farooq ya boye kudin a aljihunsa.
Suna shiga Suka Iske Yaron Ameer Yana kula da shi Amma Manal Bata sani ba,ita dai ance a Asibitin yake taimako yakeyi Kawai,Manal tace Wai ku Kira danginku Mana ko a waya ne ganin wata karamar kwakurar waya Vivo a Hannun Ameer,Shi Kuma Fuzail Wanda ta sani da Farooq tasa Wayar Tecno ce pop 3 ta talaka dai dai gwargwado sabo da matasa yanzu suna kokarin rike Yar babbar waya,Ameer Yana kwance Fuzail ya kyafta Masa Ido,Ameer yace ai kin San duk Dangin namu mun fada Miki suna kauyen Niger,mu Nan zuwa Mukayi Neman wajen Zama kafin mu samu sana'a akwai Wanda yake Dan garin namu anan Baya Nan sai Nan da sati biyu zai dawo shi zai mana komai,Manal Tace Haka Farooq ya fada min Allah sarki Allah ya baka lafiya Sannu, Inshaallah kana warkewa zaku samu gidan zama.
Allah yasa Kinga bawan Allah din Nan ma Yana kawo min abinci Sadaka Ina ci gashi Yana kula dani cewar Ameer ,Manal tana murna Tace da mutumin mun gode Allah ya saka da Alkhairi,mutumin yace Ameen ai yiwa Kaine ko ba komai Zan samu lada sabo da Allah nayi,Manal Tace kai Ameer gashi Kana Jin hausa sosai ya akayi Farooq shi Bai Jin hausa? Ameer yace ai ni kusan a Kano state Muka Yi karatu shi yasa muka ji hausa sosai,shi Kuma a kauyenmu yayi primary da secondary school,sannan University ma wata yayi wacce a Kauye take ma Kuma ba a hausa a yankin,Manal Tace ayya shi yasa ashe to shike nan.
Ameer yace yanzu matsalarmu kayan sawa Amma wannan bawan Allah yace zai siyo Mana kayan gwanjo kala biyu Sadaka sabo da Allah,Manal tana murna Tace har Ina tunani wanne Aiki zanyi na samo kudin da Zan siyo muku ko gwanjo ne ku samu amma bawan Allah mun gode,Fuzail dai Manal yake ta kallo da tsananin mamaki sai murna takeyi kamar wasu Yan uwanta.
Ameer Yana kallon irin kallon da Fuzail kewa Manal Yana mamaki mutumin da Mata ma hadaddu Basu isheshi kallo ba sai wannan ga kauyenci ga talauci duk da yasan karyar mutum ya kalli Manal Bai sake kallonta ba sai dai hassada amma Manal abar kallo ce,Manal tace Farooq ka zauna a Nan Bari naje gida nayi Mana abinci sai nazo na tafi da Kai gida,bani naira darin Nan sai na hau Napep da ita ta furta tana Mika Masa Hannu,Fuzail ya kyaftawa mutumin Dake kula da Ameer ido Nan take yace kanwata kema ga Sadakar dubu Daya kiyi amfani da ita,Manal ta Bude Baki Tace Malam kudin sunyi yawa ka bani duka Sadaka Haka? Yace karbi Allah ya bamu Lada kema ai kin taimaka.
Manal har kasa ta durkusa tare da sa Hannu biyu ta karbi kudin tana uban godiya da Addua sabo da Bata da ko sisi dama so take taje ta nemi aikin wanke wanke da shara a gidan masu Saida abinci tayi ko na yini Daya ne a biyata ta samu ta dafa musu abinci da kudin sai gashi ta samu Amma duk da Haka tasan a tsadar abin duniya a yau dubu zata Kare gwara ta nemi kudin tun yau gobe ta samu su Kara kawai.
Da murna ta kalli Farooq tare da cewa Zan wuce sai nazo daukanka,Murmushi yayi ta tsira Masa Ido yanda yake da mugun kyau duk da shigar Daya canja tare da kasumba da uban gashi Bai Hana kyawunsa bayyana ba musamman idan yayi Murmushi kyawawan hakoransa suka bayyana ga wani lips dinsa red masu kyau,Hancinsa kadai ya Isa a kalli Farooq,ga kirar surar jikinsa musamman skin dinsa abin Yana birge Manal ita Kam ta Gama ganin kyau wajen Farooq inama zaiyi Aski da yafi Haka kyau ta furta a ranta,tana gama tunaninta tace na tafi ta juya tana waigowa tana kallon Farooq,Hannu ya daga mata har ta bar asibitin.
Tana tafiya wajen wata me siyar da Abinci a Tasha ta tsaya,suna mutunci da Dattijuwar Manal tasan Yaya Yazed ya hanata irin wannan Neman kudin Amma Dan kudin Daya bar Mata su Farooq sun cinye su Dole ta nemi wasu,Ladidi Tace Manal yau ko aikin kika Zo Yi ne? Da sauri Manal Tace ae Ladidi,okay Zo dama ga wanke wanke ya taru bana so customers su fara yawa ba a wanke ba,ai Kuwa Manal ta shiga wanke plates da spoons tana ta faman Yi ana siyen abinci Ana cinyewa za a kwaso wasu a kawo ta wanke,tunda ta fara aikin Hannunta Bai huta ba har 3pm tun safe,lokacin ta tuna da bakinta da suke wuyanta, Nan take tace tafiya zata Yi ta Gama aikin yau,Ladidi taji Dadi sabo da Manal ta Iya Aiki sai tace Manal akwai shinkafa da Miya,fried rice,sakwara da miyar Egusi,ga tuwo ma ki zaba a ciki me Zaki iya ci na zuba Miki ki tafi da shi gida ai kin Sha aiki,Farin ciki ya Kama Manal ba sai tayi girki ba da dare sai ta dafa musu Indomie kawai.
Manal Tace Frit race (Fried rice) za a bani da sakwara,Ladidi da yaranta suka dinga dariya tare da cewa Fried rice ake cewa sai da Manal ta iya fada sannan Ladidi ta Mata take away harda nama yanka biyu a kowanne girki,Ledoji biyu Manal ta karba tana godiya sannan Ladidi ta Bata dari uku.
Ameer Kuwa take away aka musu lafiyayye amma ga mamakinsa sai Fuzail yaki ci,juyin duniya yace na gidan mu zanci,Dariya Ameer yayi yace au har gidansu ma ya Zama gidanku? na talaucin? Kuma wannan Yarinyar in Banda jagwalgwalo me zata yi,Fuzail Cikin Harshen turanci yace yarinyar data taimaki rayuwarka kake fadawa Haka?Yarinyar data kawoka Hospital da kudinta,Yarinyar da zata iya aikin kaskanci ta ciyar da wani,yarinya karama with Good heart,wannan Yarinyar tana da wasu Good Qualities da ba ko wacce mace ke da irinsu ba,Ameer kallon Abokin Nasa Kawai yake Yi da mamaki wannan Yar Yarinyar Yar Kauye yasan tana da Hali me kyau,Ameer yace yanzu prince baza kaci Abinci me kyau ba na waccen yarinyar zaka ci? Idan cuta ta Kamaka fa? Fuzail Baki ya tabe sannan ya bawa Ameer Labarin gidan su Manal da abinda Yan uwanta su Farida suka Masa,Ameer ya dinga dariya yace wlh sunyi dai dai,Fuzail Dan hauka ka shiga dakin yarinya idan da sun Tara maka mutane fa? Yarinya Haka ku kwana tare mahaukaci ne kai? Ban San tayi bacci bafa,Hmm Ni Dadi ma naji tun ranar da yarinyar Nan ta rike Hannuna na Gane Ni Namiji ne Fuzail ya furta Yana murmushin Jin Dadi, Ameer ko magana baiyi ba Likita ya shugo tare da wanke Masa rauninsa yana canja plasta Manal ta shigo da fara'a tayi Sallama,Ameer ta kalla ta Iske Yana cin abinci tace jiki yayi kyau Sannu,karka damu kaji an kusa sallamarka ta furta tana lallashinsa,ta Bawa Ameer Dariya yarinya karama sai iya tattali Amma tana birge shi murmushi yayi tare da furta me kika kawo Mana,Yana magana amma surar Fuzail take kallo yanda ya tube rigarsa taga Namiji iya Namiji ga skin me kyau sai sheki yake yi,surarsa take karewa kallo,Ameer yace Ina magana Yan mata,Firgit ta saki murmushi tace ahm...Uhmm....Fried rice da sakwara.
Ameer yace ashe abin Dadi ne Yar Fulani an iya turanci Ashe,da sauri Manal ta zauna a gefensa tare da furta kaji tsiya wata ce Tace sai na koya yanda ake fada da turanci sai Dana kwashe Rabin awa ban iya fada ba sai da kyar kasan kaina kindirmo ne a ciki ya daskare,Dariya Ameer ya dinga Yi yace Baki da dama,Manal tana Dariya Tace wlh Ni wata Kindirmo ce ka ganni to ya za muyi talauci ne ya jaja mana,Da ace da kudi yaushe zaka ganni haka yanda nazo birni ai da tuni na dauki Hanyar wayewa dodar.
Ana Gama dressing Masa Farooq ya maida rigarsa sannan ya mike tare da daukan kayansa na gwanjo kala biyu da aka siyo musu Suka ce mutumin Nan ne ya Basu Sadaka, Manal tace muje ko? Kai ya daga da Izza,Suna Fitowa Manal tace tsaya,cak ya tsaya Tace masifa Zan maka to na fada maka ka daina wannan Izzar, murmushi yayi kadan idan baka kula ba baza ka Gane murmushi yayi ba,Oh ba Haka ake murmushi ba yaye bakinka zaka Yi sosai kalla Haka ta gwada Masa tare da washe bakinta Tace Haka fa,Yi na gani Dariya ce ta kamashi ai Kuwa ya washe Dan karamin bakin sa,Manal tace kaga Baki Kamar kurtun Limamin rugar mu da yake dura kakin majina a ciki,yaji abinda tace yace zagina ko?Da sauri Manal ta furta no Ina nufin bakin me kyau, kyau? Ya tambaya tace ae,Okay yace Suka tafi,Napep Suka shiga zuwa gida,Ana zuwa Ta biya kudin sannan Suka shiga gidan.
Suna shiga gidan Farida da Hajiya sun tanaji ruwa botiki Guda ai Kawai sai ruwan Suka juye shi a jikin Farooq gaba Daya,Hajiya tazo ta zuba Masa Rankwashi a Uwar sumarsa me yawa,sabo da tarin Sumar Bai ma San ta rankwashe shi ba,yaga dai gilmawar Hannunta ta saman Kansa, kunnensa Zaki murde Dan matsiyata kwarto cewar Farida,Hajiya ta Kama Kunnen Farooq ta murde da karfi ya saki kara,Manal ta fashe da kuka tayi kukan Kura ta Kama fatar gadon bayan Hajiya tare da gartsa Mata uban cizo,ai Hajiya ihu ta saki ba shiri ta saki Farooq,kunnensa yayi wani ja,Manal ta kalle su Tace wallahi wulakanta Dan Adam babu Dadi a rayuwa Ina ruwanku da shi? Farida ta kalli Farooq Ido da Ido ta shiga dura Masa ashar ta uwa ta uba,Dan Bur....Dan bura..gidan Ubanka ne? Ai na tsaneka tunda har kayi sanadin da na kasa ganin masoyina har yayi tafiya sai ka bar gidan Nan tsinannen banza,Hajiya tace wallahi yau bazai kwana a gidan Nan ba,idan wani kwarton Zaki kawo Manal ki kawo kuyi ta kwana wallahi mu zamu rufa Miki asiri Amma Banda wannan algungumin Yana yawo da shegiyar Suma ga kasumba Kamar liman,me ci da addini Kawai Allah ya tsine maka Albarka tunda ka Hana yarinya ta haduwa da arzikinta Dan Iska mazinacin banza.
Wallahi Manal bazai kwana a gidan Nan ba wannan in Banda wari ma me zaiyi ke ko kunya bakya ji kalleki kyakyawa ai kinfi karfin talaka Manal,ke matar manya ce,kina so ki jefa rayuwarki a wani sabon talaucin cewar Farida,Hajiya Tace in Banda masifa gamu talakawa ki kwaso wani talakan again.
Hajiya tabarya ta dakko tace gidan Nan ba asibiti bane ya bar gidan Nan ko na rushe Masa Kai ko Kuma wallahi yau na Tara muku mutane a watsaku a Internet,Manal tasan Hajiya zata iya aikata komai tace ba sai kinyi Haka ba zamu tafi Zan bishi sai Sanda Suka samu wajen Zama kullum zan dinga zuwa inda suke Ina kula da su,idan Yaya ya dawo ki fada Masa nasan abinda zaku ce Kenan,ai dai baza ku Hana nayi musu girki na Kai musu ba,taimako ne sai nayi,Hajiya tace munji Amma ba a gidan Nan ba,ya Gama cutar mu zaizo ya tare Mana a gida bazai yuwu ba,Manal tace muje Farooq.
Hajiya da Farida tare da su Sa'iha suka rike Baki da mamakin Manal su duk abinda suke Mata hange talaka ta kula,Masatura Tace tab
Book Chapters
Chapter 1Chapter 2Chapter 3Chapter 4Chapter 5Chapter 6Chapter 7Chapter 8Chapter 9 Chapter 10Chapter 11Chapter 12Chapter 13Chapter 14Chapter 15Chapter 16Chapter 17Chapter 18Chapter 19Chapter 20Chapter 21Chapter 22Chapter 23Chapter 24Chapter 25Chapter 26Chapter 27Chapter 28Chapter 29Chapter 30Chapter 31Chapter 32Chapter 33Chapter 34Chapter 35Chapter 36Chapter 37Chapter 38Chapter 39Chapter 40Chapter 41Chapter 42Chapter 43Chapter 44Chapter 45Chapter 46Chapter 47Chapter 48Chapter 49Chapter 50Chapter 51Chapter 52