ko asiri ya Mata ne? Suna kallo Manal ta fito da wata Leda Viva da kayan Fuzail da komai na bukata sai da ta dakko,Farooq Yana tsaye a jike sharkaf da ruwa yayi mutuwar tsaye,ransa Bai taba baci ba irin yau,wani zazzabi ma yake ji,Manal tana Fitowa da hawayenta sai kace Kanin ubanta ta Furta muje Suka juya da komai nasa har kayan gwanjo Dake Leda ta dauki musu komai suka fice.
Direct wani layi Suka nufa me nisa da layinsu Wanda shi layin ma sabuwar Unguwa ce babu gidaje da yawa,Wajen wani Dattijo Wanda take cefane a Wajensa ta karasa,Baba ya washe Baki Yana 'yata Ina zuwa Haka? Manal ta fashe da kuka tace Baba wannan Mijina ne yazo daga rugar mu,kasan Yan Fulani mu da wuri ake Mana aure,nazo birni wajen Yaya na,to yayi tafiya kishiyar Mamata ta Hana Mijina Zama kalli yanda ta kwara Masa ruwa,Kuma bashi da lafiya kalli bayansa Manal ta kwaye rigar Farooq Tace kalli Baba a hanyarsa ta tahowa sukayi hatsari,ka taimaka ka Bamu wajen Zama zuwa kwana Uku ko hudu zasu tafi kauye,Baba ganin Manal Bata da Wasa sai ya yarda da zancenta ya tausaya yace na yarda dake Yata,akwai gidan babban Dana Daya Gina sabo ne Amma ba a Gama ginin ba zaiyi aure amma baya Nan ya Yi tafiya sai watan gaba zai dawo ki Shiga Ciki ku zauna kafin ya dawo,Amma fa Kamar kango yake, sannan nayi alkawari kullum kizo gidana ki daukar masa abinci safe,rana da dare,Manal ta dinga godiya,Fuzail ma Haka harda Addua,Dattijon yace muje na nuna muku gidan,Yana gaba suna binsa.
Suna zuwa Suka ga gida an Gama komai har plasta an sa kofofi ma Amma duk ba a sa wasu abin ba babu paint,Baba yasa key tare da Bude musu gidan,Suka Shiga Ciki har tiles anyi ga pampo da ruwa toilet ma an Gama komai me kyau da ita,Baba yace har toilet gata Nan Ana amfani da ita,Fuzail yaji Dadi dama Bai kaunar ta gidan su Manal ko kadan suna ta godiya Baba yace da zuciya Daya na Baku da Kuma yakinin cewar mijinki ne,idan har ba mijinki bane wani Abu ya Shiga tsakaninku kin cuci kanki,kuji tsoron Allah mace da Namiji basa kebewa face na ukunsu Shedan ne,bazan tsananta Bincike ba amma aji tsoron Allah, karki biyewa zuciya, Manal tace Inshaallah ai ba kwana zanyi tare da shi ba abinci Kawai Zan dinga Kai Masa Ina Taya shi Hira amma kafin Magriba ma Ina gidanmu, to Madalla Me kayan Miya ya furta.
Baba Yana tafiya Manal ta fito da kayan gwanjo da sauri ta gansu da kyansu ba laifi kala Daya ta bashi dogon wando arsh da Riga me gajeren hannu red,Daya dakin ta koma Wanda ba komai a ciki sai tiles,Shima inda yake ba komai sai tiles,toilet din ya Shiga da Sabulun data dakko yayi wanka komai Yana Yi na toilet din gata sabuwa gal fes,yau sai da ya Dade kafin ya fito fes cikin sabon kayan gwanjonsa yayi kyau sosai,Abincin ya dauka ya fita dakinta zai kirata yaji itama a toilet dake room dinta tana wanka,mamaki yayi tana wanka Kuma ita da zata koma gida,Bai San Manal sabo da tana period tayi staining shi yasa tayi wankan Dole Kar ta fita a Haka.
Itama cikin shiri ta fito ta ganshi a dakin da ta shige bayinsa a tsaye gashinta ya kalla me uban tsayi Wanda yasha ruwa Bai bushe ba Amma ta tsane shi,sai tayi Masa kyau ya Shiga kallonta itama Kallonsa takeyi yayi kyau sosai,sai da suka dauki lokaci me tsawo a Haka sannan Ya dawo Hayyacinsa tare da Furta Abincin?Yana Nuna Mata ledojin hannunsa,Zama tayi a saman tiles Tace kayi Sallar la'asar? Yace ae nayi yanzu abincin ta Bude Masa Tace wanne zaka ci a ciki? Ya kalleta Kawai sannan ya nuna yace all duka, Tace to muci ta Mika Masa spoon na Roba itama da nata duk a take away din aka Sako Mata, pounded Yam Suka Fara cinyewa sannan Fried rice din,Nama daya ne ya rage a karshe ya dauka ya saka Rabi a tsakanin hakoransa Rabi Yana daga waje ya nunawa Manal Wai ta gutsira,Manal Bata san mene hakan ba,Tace cinye na barmaka tana kallonsa a kunyace,cinyewa yayi sannan yasha pure water tare da kuskure bakinsa.
Paracetamol ta bashi ya Sha da sauran Magungunansa sannan ya fara lumshe Ido zaiyi bacci,dakin da yake a matsayin nasa ta Shiga tare da shimfida Masa wani zaninta kasancewar babu ko Tabarma a ciki,Tace jeka kwanta,ba musu sabo da bacci yake ji Haka ya kwanta a saman zaninta ta lulluba Masa wani zaninta .
Itama Manal dakinta ta koma ba ko Shimfida ta kwanta sai bacci suka dinga bacci sai Magriba Suka tashi,Sallah ya Gabatar Manal Kuwa ta zauna tayi Shuru a dakinta tana ta mamakin kanta me yasa taji wannan bawan Allah ya kwanta Mata ne,me yasa Idan tana tare da shi take jinta ta Zama safe,me yasa Idan tana tare da shi ta Kan tsinci kanta cikin tsananin farin ciki marar misaltuwa bayan tasan bashi da komai Bai da kowa Bai da wajen ajiyeta,jinsa takeyi har jininta.
Har bayan Sallar Isha tana wannan tunani shi har yayi Sallah ma tuni,Fitowa Manal tayi tare da lekawa dakinsa Tace muje gidan Baba me kayan Miya Nan ne kusa na karbo abinci,Fuzail Wanda Manal ta sani da Farooq mikewa yayi suka fita tare Yana me murmushi,a Kofar gidan ya tsaya Yana jiranta Baba Yana gida Manal ta shiga Bayan sun gaisa da matar Baba da shi Baban,Baba yace laraba zubo Mata Tuwon ta tafi da shi,Laraba ta Mike ta dakko flasks shake da Tuwon shinkafa Miyar kubewa Danya da kifi ta bawa Manal,Manal tayi godiya ta tafi.
Can suka koma gidan Fuzail yace yunwa yake ji sannan Suka ci Tuwon tare a kwano Daya,suna Dan Hira Sama sama har Manal tare da Yi Masa Sallama tace Zan tafi gida to dare yanayi,Kamar zaiyi kuka shi Bai so ta tafi gashi Bai Saba ba tsoro ma yake ji shi,har Kofar gida ya rakota yace Good Night,Murmushi tayi tare da furta ka kulle ko Ina kaji gobe da wuri zanzo,da sauri yace karfe Nawa? Dariya ya Bata duk ya damu tace karfe Tara na safe,No 8am please, Kallonsa take Yi Kawai yace I mean Takwar,Dariya Manal tayi ba shiri tare da gyara Masa takwas ba takwar ba, Allah ya kaimu Kuma ta juya ta tafi gidansu.
Hajiya Khausar
Uktee
Fulani gal ce
Bamalli ce
Jiddah
Hajiya Abou
Hafsat Bako Maibeza
Teema's collection
Mmn Waheeda
Aisha Fulani Gal
Hadiza Mukhtar
Meerah
Rahmatu Kunde
Rukayyatu
Bilkisu
Lokacin da Manal ta koma gida su Hajiya ko kallonta basuyi ba Itama Bata kulasu ba ta shige dakinta tayi kwanciyarta da Niyyar bacci Amma ya gagareta Kamar yanda ya gagari Fuzail,ga kwanciya a kasa ga Kuma tunanin Manal.
Gaba dayansu kasa bacci suka Yi sai dai Juyi kawai,Manal baccinsu na Jiya take tunani da yanda suke Muamula cikin Dan lokaci ya shiga ranta Bata son kasancewa sai kusa da shi,Shima bangarensa saman shimfidar zaninta yayi juyi tare da Jan Tsaki Yana mamakin Kansa daga Fitowa ganin rayuwar talakawa ko zai tsinci wani darasi a rayuwa Kawai ya hadu da yarinya mistakenly yarinya karama wacce Bata ma da ilmi,Yar Kauye amma gaba Daya tunda ya daura ido a kanta yaji duk duniya ba wacce yake so kamarta,Ji yake bazai iya rayuwa ba sai da Manal,Yana wannan tunanin ya Mike zaune abinsa gashi wayarsa Saura kadan ta mutu ba charge.
Kasancewar gidan yayi wajen Unguwa sosai ba gidaje kusa sai kukan wasu tsuntsu yake ji da wani jifa tassss a saman kwano,Tsoro ya Kama Fuzail ya Mike tsaye da sauri,kunne ya kasa yaji Shuru sannan ya koma ya kwanta,da kyar bacci ya kwashe shi.
Itama Manal Haka baccin tayi sabo da gajiya,Washe gari Sassafe ta farka,ai da sauri tayi wanka dama Bata sallah,Yau Harda saka wata Atamfarta me kyau Riga da skert sun kamata sosai sabo da ta Kara girma sun janye,Hijab ta saka Kawai yau Harda Shafa powder da lipgloss,Fitowa tayi tsakar gidansu duk su Sa'iha sun lalata shi,Farida da Hajiya tare da sauran Yaran sun zuba tagumi sunyi jungum jungum sabo da Basu da ko sisi yau ko na Koko Basu da kudin Siya,Hajiya a hankali ta furta tashin hankali baka da shi me baka ma babu, Farida ta zumbura baki tace Manal Sanda tana sana'a duk tsiya Muna ci yanzu ta rasa mun rasa.
Manal tana kallonsu sabo da suji haushi ta zaro dubu Daya da dari biyar ta karkade su tare da dagasu sama tare da furta Allah yasa ku isheni yau madarar gongoni Uku Zan juye a cikina yau Ni da Bawan Allah na bako na, Ta kalli Farida tare da furta Yar kurkura karfe nawa? Farida tana so a Basu ko dari biyu ce su karya da sauri Tace 7:30am,Manal ta kalli Yaran su Falaqi sunyi malaho sai Suka Bata tausayi ta zare dari biyar a ciki Tace Falaqi Zo ka karba ka siyo muku kayan shayi Allah bazai hana bawa abin kaiwa Baki ba,Allah sarki Masatura ta Mike tare da Furta an gode Manal Kai Falaqi tsaya na rakaka karka Yi shirme,Hajiya Kuwa da Farida tsabar ki Fadi ganin an Basu sai ma tabe Baki da sukayi Farida Tace mu Muna da kudin karyawarmu,ai ba ku na bawa ba kunji nace Hajiya ko Farida? Kanne na na bawa idan kune ai ko takardar littafi bazan Baku ba bare kudi na,ta juya tayi tafiyarta ta barsu Nan suna hassada.
Direct Gidan da Farooq yake ta karasa tana ta sauri,a lokacin Fuzail ya fito Kofar gida yafi sau goma Yana jiran ganin ta inda zata bullo sabo da Haka Manal ta samu Kofar gidan a bude ya gaji da jira ya koma dakinsa ya kwanta,a hankali Manal ta lallaba ta shigo gidan tare da wucewa dakin data Yi wanka a toilet din ciki, Lallabawa tayi zata fito
Itama wajen Farooq sai ya rigata shigowa dakinta da zanin shimfidar a hannunsa gaba daya.
Sai da ya tsorata da farko Bai San ta shigo ba,Karfa kaji tsoro nice yanzu nazo,Murmushi ya saki tare da Mata wani kallo,Manal ta Kare Masa kallo taga yayi wanka ya Sa Daya kayan nasa na gwanjo,Shuru tayi sannan ta gaisar da shi tare da furta Ina zuwa,da sauri ya furta no Ina Zaki tafi Kuma? Minti Biyar Zan dawo,Okay ya furta tayi waje ta bar gidan sai wajen me shayi ta siyo cup biyu Hadi me kauri sai Bread harda kwai Bata je gidan Baba Me kayan Miya karba ba, tana dawowa ya karbi kayan Hannunta Yana murmushi,Farooq yace wow kin San a Kauye na taso ban Saba da Zama da yunwa ba,Manal ta kyalkyale da dariya Tace Nima wallahi haka ai bakwai na safe tuni na karya,Farooq ya furta me too Yana Bude tea din, yace to Ina karamin cup? Manal tace Sha ka rage min sai na Sha,Yana kallonta da mamaki Haka ya Sha ya rage Mata komai itama ta Sha ta koshi sannan Suka zauna basa wata Hira sosai.
Yace bani labarin kauyenku,Manal kanta a kasa tace Ni me zance to sai dai in kana son labarin tinkiyata da Sanuwa ta da kaji na,Ina so bani labarinsu ya furta,Manal tace Tinkiyata ce dai-Tinkiyata ce dai Watarana tana da ciki cin abincinta ya karu ta dameni sai na Bata abinci,Rannan Ina bacci ban sani ba tazo garin Neman abinci ta taka min bakina da kafarta kallo ka gani inda ya fashe ya Zama tabo,Fuzail Ya kalli inda take nuna Masa kusa da lips dinta babu Wanda zaice wani tabo ne ma,Fuzail yace Very Bad wannan akuya ba kyau,Manal da sauri Tace Kai kyakyawa ce Dan baka taba ganinta bane.
Dariya ta sake Yi Tace baka San Sanuwa ta ba ko? Fuzail ya fara Dariya shi Ina zai San wani Saniyarta yace no ban sani ba,Manal Tace Kallo ya barka ai baka gani ba da aka Mata ciki Manal ta rufe Ido da kunya tana ta dariya Tace Allah sabo da Yan Iskan Shanayen bana zuwa garkensu kunya suke bani,Saurayin Saniyata na Uku yaga Saurayinta na farko yaje wajen Budurwarsa ai Kuwa kishinsa ya tashi naje Zan tatsi Madara akan kishinsa na jaraba ya samu ya min Wata Masga sai Dana fadi,Fuzail ya Kama Dariya yace Saniyoyi suna Yin Budurwa Suma? Manal tana ta faman Dariya da nishadi Ana zancen Saniyarta sabo da Murna ta manta ma Fuzail Namiji ne tayi zaton kawarta ce Khaltum ta dage ta dada Masa duka a cinya tana Dariyarta Tace nayi Mafarki Jiya Tinkiyata ta Haifi Yan Biyar, Fuzail ya saki Kara sabo da iya karfinta ta dake shi,cinyarsa ya duba da sauri ya janye Wandonsa yaga wajen yayi ja,Manal Baki ta rufe tare da tsayawa cak da dariyar kunya ta lullubeta tayi Shuru kamar ruwa ya cinye su,Fuzail Murmushin me tsada ya saki tare da Matsawa can nesa da ita yace Ina jinki daga Nan kar dadin Tinkiyarki ya kwashe ki kizo kina Balla min cinya Nan gaba.
Manal tayi murmushi sannan ta dinga bashi labari wani abin baya ganewa sam,Sun Dade a Haka sai da Rana Manal ta karbo Masa Wake da shinkafa gidan Baba me kayan Miya,kasa ci yayi yace yaji. Haka ta Masa Sallama ta koma gida sai Yamma likis ta taho Masa da doya da kwai da yawa a leda.
Zata tafi ya hanata tafiya tare da kulle gidan yanda baza ta iya budewa ba,ta dinga rokonsa amma yace sai anjima zata tafi Dole ta hakura ta zauna har bayan Sallar Isha yaki Bari ta tafi karshe ma yace sai dai ta kwana a Daya dakin.
Manal tayi kawaici duk da cewa tana tsoro amma ta yarda da shi ta Kuma yarda da kanta,Zama tayi har yayi shimfidarsa a dakin da take ya kwanta,zata tashi ta bar Masa dakin yace tsaya na fada Miki gaskiya I'm serious tsoro nake ji jiya da kyar na iya kwana Ni Daya,ya kamata a sallami Ameer Haka ya dawo Ni tsoro nake ji ya karasa da shagwaba,Manal tace Ah ta fara sheka Dariya tace Namiji da shagwaba sai kace wata ni lallai Ina shagwabaka Dole kayi min shagwaba.
Ita Bata da zanin lulluba bare na shimfida ma ga uban sanyin tiles shimfida Mata nasa yayi yace kwanta ke yarinya,dama I knew kin tsorata to babu komai calm down and Relax okay? Manal dai ita Bata San ya fita Jin tsoro ba Amma ta Gane nufinsa sai tace to tare da kwanciya saman zanin,Dayan ya shimfida shima can nesa da ita ya kwanta abinsa.
Manal Dadi ya kumeta sai taji ta samu nutsuwa,Shima Haka yaji,babu wuta a gidan bare ya saka charge sai uban duhu da kyar yake haska wuri da wayarsa,Kowa ya kwanta yayi Shuru can taji Muryarsa me Dadi,muryar Dake sata nutsuwa ya furta Baki da phone waya?
Manal da tausayi tace Dan Uwa tayani jaje mutumin namu ya hana Ni mallakar ko ta dubu biyu ce,Farooq yayi Murmushi tare da tambaya waye mutumin mu? Talauci Mana cewar Manal,yanda ka bani labarin talaucin da kake ciki,gaka Maraya baka da kowa sai Yan tsirarin dangi a Kauye,gashi Dan kudin daka Nema da guminka ka Tara ka taho Nigeria zaka Yi Business ka nemi kudi Wannan marasa kirkin Suka cuceka Suka maku fashi da makami ai wallahi kaga rayuwa ka fini ganin ta duniya shi yasa Idan na kalle ka sai naji masifar tausayinka,sai naji Hawaye Yana Neman zubo min,Haka Kawai nake Jin tausayinka a rayuwa,ai gaba Daya kayi a rayuwa wallahi Dole ma na tsaya na taimakeka sai ka samu wajen Zama.
Farooq Yana Jin Manal Yana ta dariya a duhu yanda take da surutu Wai,Zafi ne ya dameshi sai zufa ya hada sabo da ba ac,wayarsa ya haska dakin da ita Manal ita sanyi ma take ji harda dukunkunewa a cikin Hijab,Fuzail ya dinga ta mamaki Yana kallonta,tana kallonsa taga yanda ya jike da gumi Tace Kai Kai a wannan sanyi sai kace Wanda kayi rayuwa a iskimo,Dariya yayi ta dakko Plate din Robar da Suka ci doya a ciki dama ta wanke shi tas gabansa ta koma ta fara Masa fifita da plate din Robar Yana ta Jin Dadi tana Masa tana wani Waka Fi.... Fi.... fi....a hankali ya kalleta cikin hasken yace Manalll.....wani Dadi sunan ya Mata dake shi ya fada,ta washe Baki Tace Dan Kara fada naji Yasin baka taba Kiran Sunana ba sai yau Fadi naji,Yana murmushi sosai ya sake cewa Manalll....Plate din ta ajiye gefe tace wayyo Allah ka iya fada,duk Hausar da Manal takeyi a Gaban Fuzail ya Gama haddacewa shi Bai ma San ta mutanen Kauye bace Hausar duk kalolin rantsuwar da Manal ke Yi ya iya tas.
Manalll...ya sake furtawa Karo na Uku Manal harda rufe Fuska da hijab sabo da Murna da dadin sunan fuskarta boye a hijab tace Allah wallahi Yaya Yazed ya iya sa min suna Ashe Yana da Dadi Haka yau naji matsayin Yaya Yazed ya karu a zuciyata,Fuzail yana ta murmushi yace rigar jikina susar min ciwo takeyi,to cire Mana,Bai dace ka zauna da Abu ya dameka ba,rigar ya cire Manal taga Kira iya Kira Tace huuu tare da rufe idonta da sauri Wai kunya, Juya muga ciwon ko ya fara warkewa Tace Idonta a rufe sai da ya juya Mata baya sannan ta Bude idonta ta kafe bayan da kallo ko ta ciwon ma Bata Yi sai da ta Dade a Haka har ya gaji zai juyo tace tsaya na gani sosai kamar wani waje zai kwabe,Tsayawa yayi ya juya Mata baya Manal a ranta tace Wannan Allah ya bashi sura da fata me kyau,Sai da ta Gama tunaninta sannan tace Alhmdllh kallon Musulunci nayiwa bayanka wikil nayi
Showing 27001 words to 30000 words out of 153479 words
Direct wani layi Suka nufa me nisa da layinsu Wanda shi layin ma sabuwar Unguwa ce babu gidaje da yawa,Wajen wani Dattijo Wanda take cefane a Wajensa ta karasa,Baba ya washe Baki Yana 'yata Ina zuwa Haka? Manal ta fashe da kuka tace Baba wannan Mijina ne yazo daga rugar mu,kasan Yan Fulani mu da wuri ake Mana aure,nazo birni wajen Yaya na,to yayi tafiya kishiyar Mamata ta Hana Mijina Zama kalli yanda ta kwara Masa ruwa,Kuma bashi da lafiya kalli bayansa Manal ta kwaye rigar Farooq Tace kalli Baba a hanyarsa ta tahowa sukayi hatsari,ka taimaka ka Bamu wajen Zama zuwa kwana Uku ko hudu zasu tafi kauye,Baba ganin Manal Bata da Wasa sai ya yarda da zancenta ya tausaya yace na yarda dake Yata,akwai gidan babban Dana Daya Gina sabo ne Amma ba a Gama ginin ba zaiyi aure amma baya Nan ya Yi tafiya sai watan gaba zai dawo ki Shiga Ciki ku zauna kafin ya dawo,Amma fa Kamar kango yake, sannan nayi alkawari kullum kizo gidana ki daukar masa abinci safe,rana da dare,Manal ta dinga godiya,Fuzail ma Haka harda Addua,Dattijon yace muje na nuna muku gidan,Yana gaba suna binsa.
Suna zuwa Suka ga gida an Gama komai har plasta an sa kofofi ma Amma duk ba a sa wasu abin ba babu paint,Baba yasa key tare da Bude musu gidan,Suka Shiga Ciki har tiles anyi ga pampo da ruwa toilet ma an Gama komai me kyau da ita,Baba yace har toilet gata Nan Ana amfani da ita,Fuzail yaji Dadi dama Bai kaunar ta gidan su Manal ko kadan suna ta godiya Baba yace da zuciya Daya na Baku da Kuma yakinin cewar mijinki ne,idan har ba mijinki bane wani Abu ya Shiga tsakaninku kin cuci kanki,kuji tsoron Allah mace da Namiji basa kebewa face na ukunsu Shedan ne,bazan tsananta Bincike ba amma aji tsoron Allah, karki biyewa zuciya, Manal tace Inshaallah ai ba kwana zanyi tare da shi ba abinci Kawai Zan dinga Kai Masa Ina Taya shi Hira amma kafin Magriba ma Ina gidanmu, to Madalla Me kayan Miya ya furta.
Baba Yana tafiya Manal ta fito da kayan gwanjo da sauri ta gansu da kyansu ba laifi kala Daya ta bashi dogon wando arsh da Riga me gajeren hannu red,Daya dakin ta koma Wanda ba komai a ciki sai tiles,Shima inda yake ba komai sai tiles,toilet din ya Shiga da Sabulun data dakko yayi wanka komai Yana Yi na toilet din gata sabuwa gal fes,yau sai da ya Dade kafin ya fito fes cikin sabon kayan gwanjonsa yayi kyau sosai,Abincin ya dauka ya fita dakinta zai kirata yaji itama a toilet dake room dinta tana wanka,mamaki yayi tana wanka Kuma ita da zata koma gida,Bai San Manal sabo da tana period tayi staining shi yasa tayi wankan Dole Kar ta fita a Haka.
Itama cikin shiri ta fito ta ganshi a dakin da ta shige bayinsa a tsaye gashinta ya kalla me uban tsayi Wanda yasha ruwa Bai bushe ba Amma ta tsane shi,sai tayi Masa kyau ya Shiga kallonta itama Kallonsa takeyi yayi kyau sosai,sai da suka dauki lokaci me tsawo a Haka sannan Ya dawo Hayyacinsa tare da Furta Abincin?Yana Nuna Mata ledojin hannunsa,Zama tayi a saman tiles Tace kayi Sallar la'asar? Yace ae nayi yanzu abincin ta Bude Masa Tace wanne zaka ci a ciki? Ya kalleta Kawai sannan ya nuna yace all duka, Tace to muci ta Mika Masa spoon na Roba itama da nata duk a take away din aka Sako Mata, pounded Yam Suka Fara cinyewa sannan Fried rice din,Nama daya ne ya rage a karshe ya dauka ya saka Rabi a tsakanin hakoransa Rabi Yana daga waje ya nunawa Manal Wai ta gutsira,Manal Bata san mene hakan ba,Tace cinye na barmaka tana kallonsa a kunyace,cinyewa yayi sannan yasha pure water tare da kuskure bakinsa.
Paracetamol ta bashi ya Sha da sauran Magungunansa sannan ya fara lumshe Ido zaiyi bacci,dakin da yake a matsayin nasa ta Shiga tare da shimfida Masa wani zaninta kasancewar babu ko Tabarma a ciki,Tace jeka kwanta,ba musu sabo da bacci yake ji Haka ya kwanta a saman zaninta ta lulluba Masa wani zaninta .
Itama Manal dakinta ta koma ba ko Shimfida ta kwanta sai bacci suka dinga bacci sai Magriba Suka tashi,Sallah ya Gabatar Manal Kuwa ta zauna tayi Shuru a dakinta tana ta mamakin kanta me yasa taji wannan bawan Allah ya kwanta Mata ne,me yasa Idan tana tare da shi take jinta ta Zama safe,me yasa Idan tana tare da shi ta Kan tsinci kanta cikin tsananin farin ciki marar misaltuwa bayan tasan bashi da komai Bai da kowa Bai da wajen ajiyeta,jinsa takeyi har jininta.
Har bayan Sallar Isha tana wannan tunani shi har yayi Sallah ma tuni,Fitowa Manal tayi tare da lekawa dakinsa Tace muje gidan Baba me kayan Miya Nan ne kusa na karbo abinci,Fuzail Wanda Manal ta sani da Farooq mikewa yayi suka fita tare Yana me murmushi,a Kofar gidan ya tsaya Yana jiranta Baba Yana gida Manal ta shiga Bayan sun gaisa da matar Baba da shi Baban,Baba yace laraba zubo Mata Tuwon ta tafi da shi,Laraba ta Mike ta dakko flasks shake da Tuwon shinkafa Miyar kubewa Danya da kifi ta bawa Manal,Manal tayi godiya ta tafi.
Can suka koma gidan Fuzail yace yunwa yake ji sannan Suka ci Tuwon tare a kwano Daya,suna Dan Hira Sama sama har Manal tare da Yi Masa Sallama tace Zan tafi gida to dare yanayi,Kamar zaiyi kuka shi Bai so ta tafi gashi Bai Saba ba tsoro ma yake ji shi,har Kofar gida ya rakota yace Good Night,Murmushi tayi tare da furta ka kulle ko Ina kaji gobe da wuri zanzo,da sauri yace karfe Nawa? Dariya ya Bata duk ya damu tace karfe Tara na safe,No 8am please, Kallonsa take Yi Kawai yace I mean Takwar,Dariya Manal tayi ba shiri tare da gyara Masa takwas ba takwar ba, Allah ya kaimu Kuma ta juya ta tafi gidansu.
Sharhi fans pls
AsmaBaffa
[1/1, 10:24 PM] Sis Asma: 🧭🧭MAFARKIN FARIDA🧭🧭
MAFARKIN FARIDA IS DEDICATED TO
DUNIYATA AAMNA GP
21-25
Official
By
AsmaBaffa
Page naku ne
Hajiya Khausar
Uktee
Fulani gal ce
Bamalli ce
Jiddah
Hajiya Abou
Hafsat Bako Maibeza
Teema's collection
Mmn Waheeda
Aisha Fulani Gal
Hadiza Mukhtar
Meerah
Rahmatu Kunde
Rukayyatu
Bilkisu
Lokacin da Manal ta koma gida su Hajiya ko kallonta basuyi ba Itama Bata kulasu ba ta shige dakinta tayi kwanciyarta da Niyyar bacci Amma ya gagareta Kamar yanda ya gagari Fuzail,ga kwanciya a kasa ga Kuma tunanin Manal.
Gaba dayansu kasa bacci suka Yi sai dai Juyi kawai,Manal baccinsu na Jiya take tunani da yanda suke Muamula cikin Dan lokaci ya shiga ranta Bata son kasancewa sai kusa da shi,Shima bangarensa saman shimfidar zaninta yayi juyi tare da Jan Tsaki Yana mamakin Kansa daga Fitowa ganin rayuwar talakawa ko zai tsinci wani darasi a rayuwa Kawai ya hadu da yarinya mistakenly yarinya karama wacce Bata ma da ilmi,Yar Kauye amma gaba Daya tunda ya daura ido a kanta yaji duk duniya ba wacce yake so kamarta,Ji yake bazai iya rayuwa ba sai da Manal,Yana wannan tunanin ya Mike zaune abinsa gashi wayarsa Saura kadan ta mutu ba charge.
Kasancewar gidan yayi wajen Unguwa sosai ba gidaje kusa sai kukan wasu tsuntsu yake ji da wani jifa tassss a saman kwano,Tsoro ya Kama Fuzail ya Mike tsaye da sauri,kunne ya kasa yaji Shuru sannan ya koma ya kwanta,da kyar bacci ya kwashe shi.
Itama Manal Haka baccin tayi sabo da gajiya,Washe gari Sassafe ta farka,ai da sauri tayi wanka dama Bata sallah,Yau Harda saka wata Atamfarta me kyau Riga da skert sun kamata sosai sabo da ta Kara girma sun janye,Hijab ta saka Kawai yau Harda Shafa powder da lipgloss,Fitowa tayi tsakar gidansu duk su Sa'iha sun lalata shi,Farida da Hajiya tare da sauran Yaran sun zuba tagumi sunyi jungum jungum sabo da Basu da ko sisi yau ko na Koko Basu da kudin Siya,Hajiya a hankali ta furta tashin hankali baka da shi me baka ma babu, Farida ta zumbura baki tace Manal Sanda tana sana'a duk tsiya Muna ci yanzu ta rasa mun rasa.
Manal tana kallonsu sabo da suji haushi ta zaro dubu Daya da dari biyar ta karkade su tare da dagasu sama tare da furta Allah yasa ku isheni yau madarar gongoni Uku Zan juye a cikina yau Ni da Bawan Allah na bako na, Ta kalli Farida tare da furta Yar kurkura karfe nawa? Farida tana so a Basu ko dari biyu ce su karya da sauri Tace 7:30am,Manal ta kalli Yaran su Falaqi sunyi malaho sai Suka Bata tausayi ta zare dari biyar a ciki Tace Falaqi Zo ka karba ka siyo muku kayan shayi Allah bazai hana bawa abin kaiwa Baki ba,Allah sarki Masatura ta Mike tare da Furta an gode Manal Kai Falaqi tsaya na rakaka karka Yi shirme,Hajiya Kuwa da Farida tsabar ki Fadi ganin an Basu sai ma tabe Baki da sukayi Farida Tace mu Muna da kudin karyawarmu,ai ba ku na bawa ba kunji nace Hajiya ko Farida? Kanne na na bawa idan kune ai ko takardar littafi bazan Baku ba bare kudi na,ta juya tayi tafiyarta ta barsu Nan suna hassada.
Direct Gidan da Farooq yake ta karasa tana ta sauri,a lokacin Fuzail ya fito Kofar gida yafi sau goma Yana jiran ganin ta inda zata bullo sabo da Haka Manal ta samu Kofar gidan a bude ya gaji da jira ya koma dakinsa ya kwanta,a hankali Manal ta lallaba ta shigo gidan tare da wucewa dakin data Yi wanka a toilet din ciki, Lallabawa tayi zata fito
Itama wajen Farooq sai ya rigata shigowa dakinta da zanin shimfidar a hannunsa gaba daya.
Sai da ya tsorata da farko Bai San ta shigo ba,Karfa kaji tsoro nice yanzu nazo,Murmushi ya saki tare da Mata wani kallo,Manal ta Kare Masa kallo taga yayi wanka ya Sa Daya kayan nasa na gwanjo,Shuru tayi sannan ta gaisar da shi tare da furta Ina zuwa,da sauri ya furta no Ina Zaki tafi Kuma? Minti Biyar Zan dawo,Okay ya furta tayi waje ta bar gidan sai wajen me shayi ta siyo cup biyu Hadi me kauri sai Bread harda kwai Bata je gidan Baba Me kayan Miya karba ba, tana dawowa ya karbi kayan Hannunta Yana murmushi,Farooq yace wow kin San a Kauye na taso ban Saba da Zama da yunwa ba,Manal ta kyalkyale da dariya Tace Nima wallahi haka ai bakwai na safe tuni na karya,Farooq ya furta me too Yana Bude tea din, yace to Ina karamin cup? Manal tace Sha ka rage min sai na Sha,Yana kallonta da mamaki Haka ya Sha ya rage Mata komai itama ta Sha ta koshi sannan Suka zauna basa wata Hira sosai.
Yace bani labarin kauyenku,Manal kanta a kasa tace Ni me zance to sai dai in kana son labarin tinkiyata da Sanuwa ta da kaji na,Ina so bani labarinsu ya furta,Manal tace Tinkiyata ce dai-Tinkiyata ce dai Watarana tana da ciki cin abincinta ya karu ta dameni sai na Bata abinci,Rannan Ina bacci ban sani ba tazo garin Neman abinci ta taka min bakina da kafarta kallo ka gani inda ya fashe ya Zama tabo,Fuzail Ya kalli inda take nuna Masa kusa da lips dinta babu Wanda zaice wani tabo ne ma,Fuzail yace Very Bad wannan akuya ba kyau,Manal da sauri Tace Kai kyakyawa ce Dan baka taba ganinta bane.
Dariya ta sake Yi Tace baka San Sanuwa ta ba ko? Fuzail ya fara Dariya shi Ina zai San wani Saniyarta yace no ban sani ba,Manal Tace Kallo ya barka ai baka gani ba da aka Mata ciki Manal ta rufe Ido da kunya tana ta dariya Tace Allah sabo da Yan Iskan Shanayen bana zuwa garkensu kunya suke bani,Saurayin Saniyata na Uku yaga Saurayinta na farko yaje wajen Budurwarsa ai Kuwa kishinsa ya tashi naje Zan tatsi Madara akan kishinsa na jaraba ya samu ya min Wata Masga sai Dana fadi,Fuzail ya Kama Dariya yace Saniyoyi suna Yin Budurwa Suma? Manal tana ta faman Dariya da nishadi Ana zancen Saniyarta sabo da Murna ta manta ma Fuzail Namiji ne tayi zaton kawarta ce Khaltum ta dage ta dada Masa duka a cinya tana Dariyarta Tace nayi Mafarki Jiya Tinkiyata ta Haifi Yan Biyar, Fuzail ya saki Kara sabo da iya karfinta ta dake shi,cinyarsa ya duba da sauri ya janye Wandonsa yaga wajen yayi ja,Manal Baki ta rufe tare da tsayawa cak da dariyar kunya ta lullubeta tayi Shuru kamar ruwa ya cinye su,Fuzail Murmushin me tsada ya saki tare da Matsawa can nesa da ita yace Ina jinki daga Nan kar dadin Tinkiyarki ya kwashe ki kizo kina Balla min cinya Nan gaba.
Manal tayi murmushi sannan ta dinga bashi labari wani abin baya ganewa sam,Sun Dade a Haka sai da Rana Manal ta karbo Masa Wake da shinkafa gidan Baba me kayan Miya,kasa ci yayi yace yaji. Haka ta Masa Sallama ta koma gida sai Yamma likis ta taho Masa da doya da kwai da yawa a leda.
Zata tafi ya hanata tafiya tare da kulle gidan yanda baza ta iya budewa ba,ta dinga rokonsa amma yace sai anjima zata tafi Dole ta hakura ta zauna har bayan Sallar Isha yaki Bari ta tafi karshe ma yace sai dai ta kwana a Daya dakin.
Manal tayi kawaici duk da cewa tana tsoro amma ta yarda da shi ta Kuma yarda da kanta,Zama tayi har yayi shimfidarsa a dakin da take ya kwanta,zata tashi ta bar Masa dakin yace tsaya na fada Miki gaskiya I'm serious tsoro nake ji jiya da kyar na iya kwana Ni Daya,ya kamata a sallami Ameer Haka ya dawo Ni tsoro nake ji ya karasa da shagwaba,Manal tace Ah ta fara sheka Dariya tace Namiji da shagwaba sai kace wata ni lallai Ina shagwabaka Dole kayi min shagwaba.
Ita Bata da zanin lulluba bare na shimfida ma ga uban sanyin tiles shimfida Mata nasa yayi yace kwanta ke yarinya,dama I knew kin tsorata to babu komai calm down and Relax okay? Manal dai ita Bata San ya fita Jin tsoro ba Amma ta Gane nufinsa sai tace to tare da kwanciya saman zanin,Dayan ya shimfida shima can nesa da ita ya kwanta abinsa.
Manal Dadi ya kumeta sai taji ta samu nutsuwa,Shima Haka yaji,babu wuta a gidan bare ya saka charge sai uban duhu da kyar yake haska wuri da wayarsa,Kowa ya kwanta yayi Shuru can taji Muryarsa me Dadi,muryar Dake sata nutsuwa ya furta Baki da phone waya?
Manal da tausayi tace Dan Uwa tayani jaje mutumin namu ya hana Ni mallakar ko ta dubu biyu ce,Farooq yayi Murmushi tare da tambaya waye mutumin mu? Talauci Mana cewar Manal,yanda ka bani labarin talaucin da kake ciki,gaka Maraya baka da kowa sai Yan tsirarin dangi a Kauye,gashi Dan kudin daka Nema da guminka ka Tara ka taho Nigeria zaka Yi Business ka nemi kudi Wannan marasa kirkin Suka cuceka Suka maku fashi da makami ai wallahi kaga rayuwa ka fini ganin ta duniya shi yasa Idan na kalle ka sai naji masifar tausayinka,sai naji Hawaye Yana Neman zubo min,Haka Kawai nake Jin tausayinka a rayuwa,ai gaba Daya kayi a rayuwa wallahi Dole ma na tsaya na taimakeka sai ka samu wajen Zama.
Farooq Yana Jin Manal Yana ta dariya a duhu yanda take da surutu Wai,Zafi ne ya dameshi sai zufa ya hada sabo da ba ac,wayarsa ya haska dakin da ita Manal ita sanyi ma take ji harda dukunkunewa a cikin Hijab,Fuzail ya dinga ta mamaki Yana kallonta,tana kallonsa taga yanda ya jike da gumi Tace Kai Kai a wannan sanyi sai kace Wanda kayi rayuwa a iskimo,Dariya yayi ta dakko Plate din Robar da Suka ci doya a ciki dama ta wanke shi tas gabansa ta koma ta fara Masa fifita da plate din Robar Yana ta Jin Dadi tana Masa tana wani Waka Fi.... Fi.... fi....a hankali ya kalleta cikin hasken yace Manalll.....wani Dadi sunan ya Mata dake shi ya fada,ta washe Baki Tace Dan Kara fada naji Yasin baka taba Kiran Sunana ba sai yau Fadi naji,Yana murmushi sosai ya sake cewa Manalll....Plate din ta ajiye gefe tace wayyo Allah ka iya fada,duk Hausar da Manal takeyi a Gaban Fuzail ya Gama haddacewa shi Bai ma San ta mutanen Kauye bace Hausar duk kalolin rantsuwar da Manal ke Yi ya iya tas.
Manalll...ya sake furtawa Karo na Uku Manal harda rufe Fuska da hijab sabo da Murna da dadin sunan fuskarta boye a hijab tace Allah wallahi Yaya Yazed ya iya sa min suna Ashe Yana da Dadi Haka yau naji matsayin Yaya Yazed ya karu a zuciyata,Fuzail yana ta murmushi yace rigar jikina susar min ciwo takeyi,to cire Mana,Bai dace ka zauna da Abu ya dameka ba,rigar ya cire Manal taga Kira iya Kira Tace huuu tare da rufe idonta da sauri Wai kunya, Juya muga ciwon ko ya fara warkewa Tace Idonta a rufe sai da ya juya Mata baya sannan ta Bude idonta ta kafe bayan da kallo ko ta ciwon ma Bata Yi sai da ta Dade a Haka har ya gaji zai juyo tace tsaya na gani sosai kamar wani waje zai kwabe,Tsayawa yayi ya juya Mata baya Manal a ranta tace Wannan Allah ya bashi sura da fata me kyau,Sai da ta Gama tunaninta sannan tace Alhmdllh kallon Musulunci nayiwa bayanka wikil nayi
Book Chapters
Chapter 1Chapter 2Chapter 3Chapter 4Chapter 5Chapter 6Chapter 7Chapter 8Chapter 9Chapter 10 Chapter 11Chapter 12Chapter 13Chapter 14Chapter 15Chapter 16Chapter 17Chapter 18Chapter 19Chapter 20Chapter 21Chapter 22Chapter 23Chapter 24Chapter 25Chapter 26Chapter 27Chapter 28Chapter 29Chapter 30Chapter 31Chapter 32Chapter 33Chapter 34Chapter 35Chapter 36Chapter 37Chapter 38Chapter 39Chapter 40Chapter 41Chapter 42Chapter 43Chapter 44Chapter 45Chapter 46Chapter 47Chapter 48Chapter 49Chapter 50Chapter 51Chapter 52