Iyayensa kudi Wanda zasu siyi kayan abinci,sai haushin Farida suke ji sun San tana can tana karbewa Belloti kudi,ya auri Yar bariki,Goggo tace Bari na samu lokaci da kaina zanje Birnin na gani da Ido na,ya auro karuwa gaba Daya ya haukace a kanta wallahi bazan yarda ba.

Lokaci Yana ja Yayinda auren Tanko yazo gaf Saura sati Daya sai lokacin Ummi ta damu Fuzail ya dawo zata tafi ita amma tana so taga surukarta sai lokacin Fuzail Suka dawo gidan Sarki,sunyi wani kyau da haske suna ta hutawa,Ummi sai wani ji takeyi da Manal,ba dama taga Manal a kitchen sai ta dinga fada Wai cikinta Kar a samu matsala,Haka Yan gidan kowa kaunar Manal yakeyi sai Wanda ba a rasa ba sabo da duk yanda ka Kai sai ka samu makiya ba yanda za ayi ace kowa sai ya soka,Sabo da Haka akwai Wanda Basu damu damu da wata Manal ba a gidan,Sama sama ake Yi da su ba yabo ba fallasa musamman Yan bangaren Amarya.
Yau 9pm Manal tana sashenta Ummi ta shigo ta samu Manal tana Gyara kitchen ta Gama girki, Ummi tace bakya Jin magana Manal, me Yaron ciki Lallabawa akeyi kina ganin kamar ba Wani Abu bane wallahi sai ki samu matsala,Dan Allah ki kyale jikana yazo duniya lafiya ku Yara dama Sai Hakuri Sam Baku San ciwon jikinku ba,Dariya Manal tayi tana mamakin Ummi yanda ta damu da ita da Yaron cikinta ta hanata sakewa baza tayi komai ba, Inshaallah na daina Ummi Zan kiyaye,Haka kike cewa kullum Kuma ki dinga rage karfin ac Kar sanyi ya Kama shi yazo ba lafiya,Manal tana Dariya a ranta tace to,Ummi yanzu ta Gama takura musu ta dawo Kan cikin Manal da Jariri.

Ummi ta sake cewa girkin me kike Yi Kuma? Prince ne yace na Masa girki yanzu zai dawo,Ke sai ki biye masa duk ga Yan Aiki nan ko Ina Iyayin mazan zamani Zaki biyewa,Manal tace Ummi fada zaiyi fa ai ban Isa naki yin girkin Nan ba da na shiga Uku Yau,Ummi tace ku maza suke zarewa Ido Iyayin Yaron Nan yayi yawa Bari ya dawo mutum Yana da juna biyu baza a barshi ya sake ba,Fuzail ne ya shigo Yana Jin maganganun su Ummi me suke cewa Yace Ummi zuga min Mata Kuma zakiyi ta rainani? Fuzail na fuskanci ka rainani yanzu ban hanaka sa Yarinyar Nan Aiki ba? Kai Ummi wani Aiki tayi wannan so nake ma taje ta gyara min samana,Ummi ta kalleshi tare da cewa a'a ka barta ta huta ni sai na gyara maka saman naka tunda baka son Yan Aiki,Manal tana Jin Dadi a ranta,Fuzail Dan ya Kori Ummi ya fara kashewa Manal Ido Daya Yana Mata wani Signa da gira da Ido,ba shiri Ummi tayi tafiyarta tasan Dan nata ba kunya ce da shi ba.

Bikin Ameer Rana Daya ne Dana Tanko sai shiri suke Yi ba Zama,Wannan karon Islaha taga lefe na gaske akwati Takwas aka Mata Kaya masu tsada,Itama na Matar Ameer Akwati goma Sha hudu,duk abinda za ayi anyi komai na auren Fuzail ne yayi musu Tanko da Ameer duk mutanensa ne,Sabo da abin Alkhairi da Tanko ya yiwa Belloti shi yasa Maimartaba ya bashi part Guda kusa da part din su Ameer, 3rooms an Palo ga kitchen da komai,Haka komai an zuba gidan Amarya ba ruwansu da kayan daki sarki yayi komai,Ganin Fuzail Yana son Tanko Ummi ta siya Masa sahaddoji da yardika sunfin kala goma Kuma ta bada kudin dinki,Tanko sai Dadi yake ji ya wani Zama Dan gayu ga tsafta yanzu Kar Islaha tace Bata sonsa shi yasa ya dage ya maida Kansa mutum,duk abokan aikinsa sun San Tanko yanzu yafi karfinsu ya musu nisa,shima duk silar Farida ya samu wannan alkhairin sabo da tsafta ma tun daga kaunarta ya Fara tsafta ya canja halaye sanadiyar Farida,Haka komai da ya barwa Farida a matsayin Belloti ne yayi sai ya samu farin jini da daukaka kowa yake kaunarsa Ana masa kallon mutumin kwarai,gashi sanadin Farida an ninka Masa abinda ya rasa a kanta,yanzu ma bikin nasa na girma za ayi komai na kwarai kamar shine Dan Sarkin Sanadin Farida,Tanko yace Ina haifar mace sunanta Farida wallahi kawai.

Islaha gidansu Yan Izala ne ba Wani party da za ayi Walima zata Yi Kawai,Bangaren Amaryar Ameer Kuwa a can Abuja zasu Yi abinsu a kawo masa Amarya,Manal kullum sai ta Kira Farida akan lallai tazo musu biki ita da Belloti,Yanzu Farida Basu da kunyar kowa tace ai Inshaallah zasu zo har anko tayi na bangaren su Ameer Dana su Islaha.
Belloti mutunci ya kullu sosai tsakaninsa da Alhaji Kasim,gidan Mai har biyu Belloti ke kula Masa da su,gashi Belloti Yana shirye shiryen shiga private University Nan gaba tunda ya duba Waec dinsa tayi kyau,Alhaji Kasim cikin motocinsa ya bawa Belloti kyautar 406 ruwan toka,Ranar Farida sai murna Kamar me,Lokacin Alhaji Kasim ya hada Belloti da danginsa dake Kano yace suje su gaisar da Yayansa Wanda Uwarsu Daya ubansu daya da Alhaji Kasim,Alhaji Al'amin shima me kudi ne sosai Yana da matarsa da yaransa shida Mata hudu maza biyu.

Ranar Saturday ba Aiki da Yamma Farida ta Sha Shadda Wata sea blue me adon Silver,irin kyan da tayi ba a magana,Belloti kuwa Shadda yasha me kyau Silver color,sunyi kyau sun birge Yan gayu a motarsa suka je gidan dake sun San da zuwansu aka sauke su gaskiya gidan ya hadu na masu kudi ne.

Alhaji Al'amin da Alhaji Kasim suna zaune a palon Su Belloti Suka kwashi gaisuwa,Matar Alahji Al'amin ta fito da fara'a cikin shiga ta Alfarma ta zauna Suka gaisa sosai,Yan Aiki Suka cika musu gabansu da Abinci iri iri,Hajiya Karima tace Bari a Kira Yaran ku gaisa ai ya kamata a San juna,Kiran Yaran tayi Suka fito Mazan Yara ne matan ma Basu da girma mace Daya ce Babba zata Kai sa'ar Manal,Belloti da sauri yace Rahila.... dama Nan ne gidanku? Rahila tace ikon Allah Kamar Belloti Dan fillo Wanda kaje bikin Maryam ta maka sharri ko?
Yace nine Mana ai da badan kayi magana ba bazan ganeka ba,Address din da kika bani faduwa yayi wallahi naso na kawo Miki Ziyara Allah baiyi ba.

Lokacin Belloti ya kalli Farida tare da furta Kinga wacce nake Baki labari ta taimakeni a wajen Yan Sanda,Rahila tayi Dariya tana bawa su Abbansu labarin abinda ya faru da Maryam ta Masa sharri,Alhaji Kasim yace wasu matan Basu da hankali wallahi ai gashi Nan Maryam din ko shekara Bata Yi ba ance Mijin ya sake ta tana gida tana Zawarci,Allah ya kyauta Farida ta furta tana karewa Rahila kallo wata kyakyawa da ita me hasken fata amma ba haske can ba,dariya Rahila idan tayi sai ta birgeka sabo da Kyawun murmushinta,gata Yar Duma Duma da ita ba ramammiya ba kuma za ace me kiba can ba.
Farida ta Riga tasan Mijinta Yana Sonta Sai ta saki jiki Suka Fara Yar hira,Rahila ta janyeta zuwa dakinta,Kafin wani lokaci sun Zama kawaye,sai da Yamma zasu tafi Rahila ta kalli Kanin Babansu tace Abba Karami yaushe zamu tafi Nasarawa din mun fa Gama Waec,Ni daga Nan Ghana Zan tafi gaskiya,Farida tace mu jibi zamu tafi can biki idan ta shirya ba sai mu tafi da ita ba,Yawwa shike Nan na huta cewar Alhaji Kasim.

Duk wani Shirin biki an Gama shi Saura kwana biyu biki Belloti ya dora mataimakinsa akan komai na aikinsa sannan Farida,Rahila da Belloti Suka dauki Hanyar Nasarawa,Belloti Yana Driving Farida tana gaba sai murna takeyi zata ga Yan Uwa,Rahila tana Bayan mota suna ta Hira abinsu har Allah ya kaisu lafiya,Rahila gidan Alhaji Kasim ta gwada musu suka sauketa a gidan tace sai munyi waya Farida,Farida tace kizo fa muje bikin Nan dake na Harkar masu Walosi ne,Mene Kuma Walosi? Masu Hannu da shuni Mana,Dariya sukayi Tace sai nazo ta shige gida da katuwar Jakarta.

Belloti gidan Su Farida suka nufa tun kafin suje Farida tace Fara kaini gidan Yayan Hajiya Kawu Sani na fara ganin lafiyar Uwata,Belloti ya kaita Kuwa Farida ta shige gidan da sallama ta Iske Hajiya tana wanke wanke ,Salati Farida ta saki ganin Yanda Hajiya duk kibarta ta rame ta fikale,Farida tausayin mahaifiyarta ya kamata ta fara kuka tana tambaya Hajiya cuka kikayi me ya sameki? Itama Hajiyan Idonta ne ya ciko da kwalla Tace Rayuwa Farida,ya zanyi duniya ta juya min baya,na cuci kaina dama mutum shi yake wa Kansa yace an Masa,Kawunku tunda Suka tafi ko a waya Basu sake nemana ba,idan na kirasu ma basa dagawa,Dan abinda kike tura min shi nake cancanawa ga Matsalar Malam irin wulakancin da yake min,saukinta ma Yazed Yana tallafa min da Yan kudi,Nayi nadama Farida ki yafe min duk Ni na cuceki ban Muku tarbiyya ba,Dan Allah ki bawa Babanku Hakuri ko zai dawo Dani da wuri,na kusa Gama Idda fa,Farida tace Hajiya Nima da kika ganni yanzu ne Allah ya rufa Mana asiri Farida ta kwashe labarin tun tafiyarta da Belloti har zaman Kauye da komai ta fadawa Hajiya.

Hajiya Baki bude tace Sannu Farida Munga Iftila'in rayuwa, mu Muka jawa kanmu sai mu tuba ga Allah karki fadawa kowa zancen Nan bare ayi Mana Dariya,ai bazan fada ba,dama wannan ai sai ayi min dariya cewar Farida,Bari na tafi gidan can,Hajiya tace amma a Nan ma Zaki kwanan mun kafin ku koma ko? Farida tace ae ai Zan zauna ayi bikin su Shukrah tunda tsiransu sati Daya Idan anyi sai na tafi shi dai Ana daura auren Su Tanko Zai tafi sabo da yanayin aikinsa,Allah ya nuna Mana cewar Hajiya,Belloti ya shigo ya gaisa da Hajiya harda Hira Hajiya sai sa Masa Albarka takeyi tana godiya.

Farida ana gobe daurin aure ta tafi gidan Maimartaba wajen Manal,Belloti kuwa Yana cikin abokan Ango su Tanko shi a layin su Tanko yake ba ruwansa,Ranar da Farida tazo kwata kwata Manal ko a waya Bata saurari Fuzail ba,shima baya Nan suna Busy,sai dare ya dawo ya samu Bata bangarensa,Waya ya Mata kina Ina ne? tace kayi baccinka Aunty Farida tazo tare zamu kwana, ban Gane ba ke bana son shirme,Farida tace ke tashi ki tafi wajen mayen mijinki karki jawo min Ni waya dama zanyi da Baby,Manal tace Hirar zumunci mukeyi fa,mu ta kiyayya zamuyi ai ya kashe wayarsa,Sai da yayi Shirin bacci ya kwanta ma ransa na suya jira yake Kawai idan Bata Zo ba gobe ta Gane kurenta sai gata ta shigo,Hijab dinta ta cire kayan baccinta pink Suka bayyana,ya kashe light dama saman bed din ta Haye tare da kwanciya a gabansa ta matsa sosai tare da shigewa jikinsa ta makaleshi Tace gani cinyeni....sai ka sideni ka lashe ni....Yar Uwar mutum tazo baza ayi min afwa ba,ba tare da ya Bude Ido ba ko yayi maganaba yayi guntun murmushi Kawai.

Washe gari daurin auren Tanko ranar Rahila gidan su Farida taje Wanda ta Bata Address tana shiga da Sallama ta Sha wani lace purple and peach ta zuba kyau,Yazed ne kadai a gidan Yana Zaune a saman wata kujera yasha Shadda Yana jiran Malam zasu tafi daurin auren suma Yana latsa wayarsa ya dago ya kalli Rahila zuciyarsa ce ta Buga, Rahila ma Haka ta kalleshi taga Haduwar Dan saurayi sai taji kunya ya Mata wani kwarjini,Kanta ta Sadda kasa Duk ta rasa inda zata sa kanta da kyar tace Farida nake Nema? Yazed uban Yan Isa fuskar Nan tamau yace Bata nan yaci gaba da latsa wayarsa.
Rahila tace ko ta tafi gidan bikin? Yace ae Kawai,Tace Dan Allah inane? Tsaki Yaja yace ki kirata a waya Mana Ni Ina Zan sani,Rahila ta matsa inda yake tace to bani kujerar taka na zauna sai na kirata kafin Nan na sameta a Wayar,Yazed yace Baki da hankali Amma ko? Rahila da shagwaba tace pleaseeeee ........Yazed yaji wani yarrrrrr a jikinsa,Bai kulata ta ba ta jijjiga kujerar ka bani ko na zauna a cinyarka ta tsokane shi da sauri ya Mike ya bar Mata kujerar ganin Yar duniya ce Haka,dakinsa ya koma ya bar Rahila a zaune,Tunda Yazed ya Shiga dakinsa ba Zama yayi ba labewa yayi ya leko ta window Yana kallon Rahila,a ransa yace har saje ne da ita,kalli gashi har Gaban goshi me santsi,Kansa yayiwa fada Ina ruwanka Yazed Wai,komawa yayi ya zauna a saman bed sai ya kasa yaji Bai son daina kallonta ya sake lekowa ta window,a zuciyarsa yace gata da kirji...bakinsa ya rufe da sauri a fili yace nooo...Dan jikinta irin na Manal Dina ce shi yasa na damu da ita,Bari na kalleta sosai sai nacewa Manal Naga me yanayinta yaci gaba da karewa Rahila kallo Bata sani ba,sai da tayi 5mnt sannan Wayar Farida ta Shiga,da sauri ta fice ta bar gidan,Yazed Yana wayyo ta tafi ban Gama ganin ko irin kafafinsu Daya da Manal ba.

A hakan tana tafiya ya Kira Manal,ta daga tace Yayana yace Ni ba gaisuwa nazo ba yanzu me irin yanayin jikinki ta bar gidan Nan,Kuna yanayi Baki ganta ba gashinta ma Yama fi naki baki Kamar me, Hancinta shigen naki,naso ma na gani ko irin kafarku Daya sai ta tafi,Manal tana ta dariya a ranta a fili tace Yaya wajen wa tazo? Farida take Nema gidan bikinku zata Zo Zaki ganta ne,Manal ta kyalkyale da dariya tace wallahi Yaya ka fada,Kauna ce ba Wani me Kama Dani sonta kakeyi Bari tazo na fada Mata Muna ciki wallahi,Bana son hauka Ina wasa Dake Ni Nace Miki Ina sonta ne?Kawai Yaja tsaki tare da kashe wayarsa.....











AsmaBaffa.
[1/1, 10:25 PM] Sis Asma: 🧭🧭 MAFARKIN FARIDA🧭🧭





DEDICATED TO
DUNIYATA AAMNA FANS GP






96-100






Official





By
AsmaBaffa






Page naki ne

GIMBIYA DIYAR KATIBI







Manal murmushi yayi kawai,ta Ajiye Wayarta gefe Ana musu makeup,Yan Abuja gaba Daya danginsu suna Nasarawa sabo da Haka sai Suka saukaka Kawai a daura a Nan tare Dana Tanko ba sai anje har Abuja ba,Ango Iliyas Tanko an Sha wanka yayi wani kyau dake baiyi wahalar komai na aure ba sai kiba da yayi ya wani hade gashi dogo sosai,Ya Sha farar Shadda taji Aiki babbar Riga,Ameer Kuwa Water Arsh yasa shima Babbar Riga 11am aka fara daura auren Tanko da Islaha Kan Sadaki dubu saba'in,Maimartaba da Kansa ya daura,Sai Ameer da Amaryarsa Badi'at shima Kan Sadaki dubu Saba'in gaba Daya sarki ne ya biya musu,Algaita da Maroka suna ta fama ana hada hada an kashe pics.

Bangaren Islaha Amarya kuwa yarinya ce shi yasa tunda aka Daura Auren take kukan rabuwa da gida,ta kasa sukuni Ana magana sai kuka,an kashe kudi Tasha makeup amma duk ta Bata kwalliyar da Hawaye,Koda angwaye suka zo da kyar Kawayenta Suka lallabata ta daina kukan,har Fuzail aka zo yaci Uwar gayu cikin Shadda ta Alfarma sai kace shine Angon ana ta kallonsa,Ameer ma Yana Nan gidan su Islaha,Islaha ana hoto Hawaye ya kwace Mata Ameer yayi Dariya yace lafiya? Tana shesheka Tace K...ka....ka...kakataaaaa....ta karasa da kuka,Tanko yace Haba an Isla Isla na....aka sheke da dariya, Suna Nan Maman Islaha tace ga Fried rice din angwaye a take away,Islaha tace how many times Zan na repeating wannan Maganar Mama tun kafin abin Nan nace Ni Jullof rice...Ni Jullof rice nake so ita Zan Basu sai kusa ayi min Fried rice sai kuka tana Allah Ni bana sonta bazan Basu ba baza suci ba,Angwaye suka Fara dariya Kamar me...

Fuzail yace tab wannan duk rikicin Manal gwara ita,a bamu Haka cewar Fuzail,Islaha tace Ni bazan Baku ba ai ba ita nayi Niyya ba sai dai ku koma gida haka,Tanko yace to idan anyi Alawar Madara a bamu mu raba,Harararsa tayi tace Ina Naga lokacin wata Alawar Madara Ni,sai dai idan an kawoni ka dinga auno Madara Ina Yi,Tanko harda biye Mata yace ko Dan Baki ma ai a dinga Yi su Sha,Islaha tace tab bazan samu riba ba sai dai nayiwa baki?
Mama ce Tace ku rabu da ita Bata ji,haka aka kawo musu take away dinsu Fried rice da Rabin kaza kowa ga ruwan Roba ga lemo,Islaha zuciya tayi an bawa Angwaye abinda ba shi take ra'ayin Basu ba ta juya ta shige daki taci gaba da kukanta Wai an tozartata, suna ji Kawayenta suna Dan Allah kiyi Hakuri sai kin Bamu kunya an Raina mu ance Mana yara yanda Muke ji da kanmu,Ki daina kukan Nan,Islaha Tace Jullof nace ayi min Ni Jullof Zan basu,to shike Nan sai muyi Jullof din da Rana a sake kai musu can ba shike Nan ba, sai lokacin ta daina kukan,Dariya ma ta basu anyi hotuna Suka tafi da take away din a mota,Na Ameer dama suna Abuja matan sai da Yamma za a kawota a jirgi.

Kawayen Islaha Jullof Suka Dora da kansu suka dinga Iyayi su a dole Yan mata garin Haka Suka cikawa girkin gishiri sai Almajirai ne Suka cinye.
Da Yamma Badiat Amaryar Ameer aka fara kawowa gidanta ita kadai a layin gidan Maimartaba, Ameer shima Bai son Zama cikin gidan yawa shi yasa Abbansa ya dankara Masa gidansa daban a layin.
Islaha Kuwa kazar Amare aka Kara Bata ta cinye da sauran Magunguna sannan tayi wanka tare da Sallar Nafeela tayi Adduointa,Gaf da Magriba aka kawo motoci da yawa,Islaha ta kalli Yan Uwa Yan biki tace ku tayani da Addua Dan Allahhh.....sai ta barke da kuka,Haka aka kawota sashenta me kyau su Manal suna wajenta har aka maida Yan Kai Amarya gidansu,Farida tace to Amarya sai hakuri da zaman aure,sannan Kuma yau wannan kukan zakiyi me dalili gwara ma ki daina anjima Zaki Yi babban kukan,Manal tace wallahi Kuwa yau Zaki ga Cucumber,Rahila Dariya tayi kawai,Manal ta dafa kafadar Rahila Tace karki damu Baki da matsala ke ta Yaya Banana
Showing 123001 words to 126000 words out of 153479 words