bawa wata sabon aure,ya akayi Wai ban tuna bane Amarya ce,Haka bawan Allah Yana so na ya dinga ta daga min kafa Yana kyaleni Yana min abinda nake so, a kaina sai dai a mutu amma Ni sai nayi ta rashin ji Zan gyara halayena,to Wai Ni me nayi ne ma Kawai rashin kyautawa ta Dana Bata Alawa bayan sabun Shiga ce,kuruciya ce ta min yawa Zan bashi hakuri,ita kadai take ta maganganunta.
Bangaren Fuzail Kuwa dama can Yana da Shirin tafiya Abuja yau akan harkokinsa na komawa can da Zama yasan Yana fadawa Manal zasu Fara rikici zata ce sai ta bishi shi yasa Kawai dama tana zuwa yayi amfani da ita Amma ta bashi haushi yace Kar ya sake ganin Alawar Nan shine harda zuwa ta bawa Amarya ma,Bata Jin magana kenan ta Raina shi,dole ya koya Mata hankali,Mata idan Suka samu sake mutum Bai Jin da Dadi.

Tunda Yazed ya tafi Kuwa Kamar su Farida sun sani da kyar Raheela ta samu da Asuba tayi bacci tana ta tunanin sahibinta shima Haka,a ranar wurin Magriba yabi jirgi ya koma,zuwan Yazed Uku Zance aka Kai kudin aure tare da sa Rana Nan da wata Uku,Manal tana ta Jin haushi lokacin cikinta ya tsufa ko kyau baza tayi ba.
Fuzail Kuwa tunda ya tafi ya kasa sukuni ji yake me yasa ma Bai taho da Manal ba,anya Kuwa zai iya bacci,a wani katafaren hotel Bayan yaci ya koshi ya kalli dakin yace komai yaji Amma ba Sunshine a kusa Mene Haka kenan?,Kamar yasa ta taho amma idan ya tuna gwara ya Dan hora ta sai ya fasa a Haka ya kwana Daya da kyar,in Banda tunaninta ba abinda yakeyi,shi kadai ya dinga dariya,abinda ya kaishi ma kasa yinsa yayi ga Cassava Taki kwanciya tunda ya bar gida.

Manal Kuwa ranar ganin da gaske tafiya yayi sai kuka kwana tayi tana kuka,da Sassafe Ummi ta Kira a waya,Lokacin Ummi tana gidan Dan uwanta suna shirye shiryen za a maida Aurenta ita da Mai martaba,ta karkashin kasa suke komai ita da Sarki ba Wanda ya sani,zuwanta gidan yayi sandin tasar da tsohuwar soyayyarta ita da Sarki,Yana ta ganinta tana chasa gayu yaji bazai iya ba Itama Ummi Haka tunda ta dawo taji sha'awar komawa dakin mijinta,daga Nan suke komai a boye sai komai ya tabbata sannan mutane zasu ji,Manal tana kuka,Ummi tace lafiya? Manal tace Prince yazo Nan ne? Sai kace mace yayi yaji Ana tambaya ko yaje can,Ummi tace Bai zo ba lafiya? Manal tace ba komai Kawai yace zai zo ne wajenki ya taho Kuma na kasa Samunsa,Fuzail din ne zaizo Bai fada min ba Anya Kuwa lafiya? Naji kamar kina kuka Mene ne? Manal tace dama Wai akan mun Dan samu sabani shine Yace yayi yaji ya hada kayansa,Dariya Ummi tayi tace Bai so ya Miki fada ne fa Manal akan ya Miki fada yaga gwara ya bar gidan kawai, zai dawo ne,karki damu,Manal Tace Ummi yace bazai dawo ba Dan Allah ki Nemo inda yake sai naje bikonsa,Ummi tace zai Nene ki ne, wayarsa ko na Kira baya dagawa sai ya turo min text yace Kar na sake kiransa yanzu Ummi Haka ya dace Dan Allah?Ummi Tace Bai Dace ba Sam kyale Ni da shi,ya makarantar? Alhmdllh munyi hutun sati biyu ma,Okay to karki damu kici ki koshi kiyi banza da shi idan Ana damuwa da maza yanga sukewa Mata ki nuna Baki damu ba,Manal tace ai Ni nayi Masa laifi idan nayi Haka ban kyauta ba,Ummi Tace Haka zakiyi yanda nace shine Kawai,Ni dai zuciyata baza iya ba Manal ya furta,Ummi Tace to sai ya dawo Zaki ganshi.

Ummi tana kashe waya ta Kira Fuzail ta hau shi da fada lallai ya koma gida,Dan Iskanci yarinya tana da ciki dama Haka kuke sai Kun Gama da yarinya Kuma ku tsiri Iskanci wlh idan baka koma ba sai na Saba maka,Ummi ita.....bana son ji Kawai ka koma yarinya tana ta uban kuka sai cikinta ya samu matsala ko? Haka kake so cikin nata ya samu matsala kana sa Mata bacin Rai.
Kiyi Hakuri Zan koma gidan Nan nake so Naga yanda aka hada shi,to shike Nan amma fa ya kamata kazo Brazil ka duba abubuwanka na gaji da kular maka da Business,Ina bibiyar komai Nawa fa Ummi nafi so Manal ta Haihu sai muje ko Ina Naga komai kin San Michiel idan Yana Kan komai har ya fini kula da alamuran ma,na sani ai Allah ya kaimu ta Haihu ai dole Ni Zan ci gaba da komai kafin ta haihu nafi so ka zauna ka kula da ita kafin ta haihu zanzo ai Inshaallah,Allah ya kaimu yace Kinga tunda Maimartaba ya barni na zauna inda nake so Nan gaba Kawai zamu koma Brazil ko London da Manal sai mu dinga zuwa ganin gida akan lokaci Kawai,idan ya barka shike Nan nasan yanzu bazai hanaka komawa ko wacce kasa ba tunda ka auri bahaushiya Yar uwarsa dama Haka yake so,murmushi Fuzail yayi Suka Dan taba Hira Kan harkokinsu.

Bangaren Yazed Kuwa shirye shiryen biki sukeyi bangarensa da bangaren Raheela sai dai ango da Amaryar basa wani soyayya sai dai suna Dan kula juna sama sama,duk yanda Raheela taso ya nuna Mata so da kauna yaki dole itama ta bishi a yanda yake so,hakan yasa take jimamin aurensa tasan zai wahalar da ita ,ita ta kasa Gane masa,ba waya ba komai sai yaga dama gashi an rigada an Gama komai shi yasa ta mikawa Allah alamuranta Bata wani murnar auren jikinta a mace yake gaba daya Kamar auren kiyayya,sai Farida ce ma ke Dan Kara Mata karfin gwiwa tana kwantar Mata da hankali.

Bangaren Prince Kuwa kwanansa biyu kacal ya tattara ya taho gida ya kasa Zama yayi kwanakin da yake so,Manal tana bedroom da katon cikinta kafafunta sun kumbura da jikinta Bata San dalili ba tana shafa musu magani tana faman Hawaye sai kace famfo taji kamshin mutum a kanta da sauri ta dago kanta da Hawaye a fuskarta.






Maman Samha Ina gaisuwa.





AsmaBaffa
[1/1, 10:25 PM] Sis Asma: 🧭🧭 MAFARKIN FARIDA🧭🧭






DEDICATED TO DUNIYATA AAMNA FANS GP






111-115





Official





By
AsmaBaffa






Page naku ne

Jamil 50
Sadiya Muhammad Bala
Sadiya Aliyusafiya89
Bilkisu Aminu Ibrahim
Safiya Bature
Mom Aneesa
Hajjaju
Khadija
Maman Dr


Ina miko gaisuwa Mai yawa

Bestynbeelat
Maryam T Baliya
Maman Murtala








Ido suka hada da prince ta wani Kara kwabe Fuska tare da amsa sallamarsa Alkslm, ganin ya dawo sanyi taji a ranta a fili kuma Bata Yi murna ba,sai ma hawayenta data goge,Kafatar ya Dan latsa da yatsa Yana tambaya lafiya? Shuru ta Masa yace Ina tambayarki tashi mu tafi asibiti Manal Nan ma tayi Masa banza,Ni kike sharewa Sunshine? Ya Furta tare da Zama a gefenta kafadarsu tana gugan juna,Maganar duniya yayi amma Manal Taki kulashi,hakan yasa ma ta kwanta tare da juya Masa baya,Okay naji nayi Miki laifi I'm sorry...so sorry Baby kin San kin Bata min rai taya Zaki Bawa Amarya magani Wanda zai iya cutar da ita,da ace wani Abin ya sameta fa ya zamuyi? Na Miki fada Amma bakya Jin maganata idan nace a kyale abu baza a daina ba,ban Isa da ke ba,ban Isa da gidana ba haba My wife,Karka dameni Dan Allah ka koma inda ka fito Ni bana son hayaniya sai da ka tafi yawon duniyarka zaka dawo ka dameni dama can kayi Niyyar tafiya wajen Budurwarka,ai Naga take takenka dama Budurwa kayi sabuwa mene idan ka fada min zaka Kara aure,Zan hanaka ne? Na rigada nasan nayi maka kadan, inji na ni na machine ne ba shike Nan ba tunda ko Haihuwa banyi ba ka tafi Neman aure ai na sani.

Dariya ta Bawa Fuzail yace me yasa kike son kala min abinda banyi ba? Bana son shirme tashi mu tafi asibiti,bazan je ba da ka damu Dani ai da baka tafi wata Uwa duniya ka barni ba har in kiraka ka dinga kashe min waya Wai Kar na sake kiranka,Manal tana nuna kanta Tace ni...ni...kamar Ni? na girmi wulakanci wlh kayi kadan ka wulakantani, sai yanzu ma Naga dacewa da Farida ta kwala ma botiki,Ni harda wani taimakonka ba komai ba laifinka bane, dama sai da akace ba Yan goyo bane ku naki yarda harda dakko zani na goyaka a bayana, ba ruwanka da rayuwata,laifi fa kika min Sunshine,naji na maka laifi ai na baka Hakuri ko? To kiyi Hakuri bazan sake ba,bazan hakura ba ta furta Masa direct, Kamar Wasa Manal sai ta koma part dinta ta kulle ta barshi,ba yanda baiyi ba Taki kulashi.

Rasa inda zai Kansa yayi lallashin duniya da buga kofa Taki kulashi ma,a jikin Kofar ya tsaya tare da furta Manal Hospital fa please....Baby.....Sunshine......dan Allah kiyi Hakuri ki fito ko baza ki kulani ba muje Asibiti,Shuru ta Masa tana ji dole ya hakura zuciyarsa a cunkushe, Haka ya koma bangarensa ranar kwana yayi baiyi bacci ba ga rashin lafiyarta ta dameshi,gashi ya Mata laifi tana Fushi da shi ga sha'awarta ta dame shi,da safe 9am ya shigo bangarenta sai ji yayi ance ta tafi asibiti ma,Tsaki Yaja ya fili yace Wai me take nufi ne da wannan uban zuciyar tata,yarinya sai taurin kai zama yayi Yana jiran dawowarta tare da zuba Uban tagumi.

Sai wurin 2pm ta dawo Yana Zaune yaga ta shigo jikinta a sanyaye suna hada Ido ta fashe da kuka,gabansa ne ya Fadi yace lafiya?rudewa yayi ya rungumeta tsam a jikinsa taci gaba da kukanta,mayafin ya zare Mata ya kaita Bedroom tare da zaunar da ita a saman cinyarsa Yana tambayarta lafiya? Result ta Mika Masa ya duba yaga ance tana da hawan jini an Rubuta Mata magunguna,hankalinsa ya Dan kwanta sabo da yayi zaton wani Babban Abu ne,Mene ne to Dan kina da hawan jini na masu ciki ne dama wasu suna Samunsa idan suna da ciki kina Haihuwa Zaki warke ko Likita Bai Miki bayani ba? Manal tace da gaske yake? Sosai ma Inshaallah Zaki warke,Dan ya kwantar Mata da hankali yace ai Nima na taba Yi gashi na warke,Sanda kana Brazil? Fuzail yace Sosai,Sanyi taji a ranta ya Shiga kwantar Mata da hankali har ta manta ma tana Fushi da shi,sunyi missing juna suka fada saman bed suna nunawa juna kauna Kamar zasu cinye kansu Manal da katon cikinta ya girma sosai,sai da yayi nisa gab da zai fada wata duniyar ta zare jikinta,lafiya? na gaji ni Allah bacci zanyi bani da lafiya,Hankalin Fuzail tashi yayi ya kankame Manal,Tace wayyo cikina da sauri ya saketa Yana lallashinta,har yanzu Baki huce ba? na huce Mana,Baki yafe min ba ko? Shine Zaki min wannan hukuncin? Manal Tace a'a ba Wani hukunci,Rirriketa yayi yace please ki bani Sunshine Dan Allah nace,bazan iya sake kwana Haka ba,Sanda ka tafi ka barni ka tuna Ni Zan iya nemanka ko bukatarka ce Kawai bukata,na dinga hadaka da Allah kaki saurarona,na yarda nayi laifi na fada Miki Zan fada Miki Kuma me ya kaini Abuja akan komawarmu can naje Naga tsarin komai ba Wani Abu ba,nafi so sai na Gama komai idan kin Haihu sai mu koma,Manal tace Alright it's okay Amma Allah Indai ka sake min Haka Ni bazan iya hakura ba,bazan sake ba nace ko please ya Furta,Manal sai lokacin tace a bani Cassava na shanye abata to....shi yasa kike birgeni,gashi Nan kin Gama zauta ni Bana iya komai idan bakya kusa,Manal harda yanga daga Nan suka fada sabuwar duniya,sai da Manal ta nemi afwa sannan ya Dan rage zafinsa.

Sai da suka samu nutsuwa ya rungumeta sosai Yana shafa gashinta cikin rada yace I'm Sorry My Sunshine Nasha wahala Dana tafi babu Ke kusa ba shiri na dawo gida,naji jiki shi yasa na dawo gida ba shiri bazan iya rayuwa babu ke ba,Manal tace hmm Kawai,Karki sake na sake abu kisa damuwa a ranki gashi kin jawo Mana Hawan jini,ai Kaine kasan Ni bana son damuwarka bana so na Bata maka Rai shine kayi Fushi Ni Kuma Ina da sa abu a Raina shi yasa dama Doctor Tace jini na ya kusa Hawa na kiyaye Kuma ka tafi na Shiga damuwa ai gashi Nan ya hau sai kaji dadi.

Zai warke Inshaallah kinji,Allah yasa ta furta tana sake shigewa jikinsa yace nayi missing da yawa second round Baby,Manal tana Jan aji Tace sai 5:30am,da Asuba fa kenan kike nufi? Baka ga bani da lafiya ba,Dan Allah kiyi Hakuri ki taimaki Dan Ummi nayi missing dinki da yawa bazan iya kaiwa 5am ba,Manal Tace bacci idan ka shirya ka tashe Ni,bafa Haka kike min ba Sunshine ko har yanzu Haushi na kike ji?haushin me Zan ji,ko 30mnt ba ayi ba Fuzail ya damu Manal sai da ya sake,a Haka kafin safiya yayi sau Uku,bayan Sallar Asuba ya sake Yi.

Ameer kuwa dadin da yaji da Manal ta bawa Matarsa alawa yasa ya Kira Fuzail Duk da Badi'at taji wahala yace daga yau na Zama Abokin Belloti nima,Fuzail ya dinga dariya yace Dan Allah ku Nemo inda ake siyar da ita ko kwali Guda na siya wacce zata Mana shekaru,Suna ta dariya,Ameer yace ku bani number din Belloti shegen Gari, Haka aka bashi number Belloti.
Rumaisa tana can da Fahad dinta a kasar waje Yayin da Shukrah ke GRA katafaren gidanta ita Daya tal.

Ameer ne ya Kira Belloti Suka gaisa yace Ameer ne Abokin Fuzail Belloti yace ah guy ya garin ne ya ake ciki ya amarya? Ameer dama Nan yake so a tabo,yace Dan Allah Alawar daka siya nake so wata wacce.....ba sai ka fada ba na ganeta ai kala wajen biyar ne alawoyin kowacce da aikinta akwai ta Mata akwai ta maza akwai wacce ake Sha mace da namjin,Ameer yace kana birgeni kasan Kan gari Belloti yace ai ba a Zama Haka matan yanzu sai Namiji ya hada da tsumi shima sabo da kullum a cikin Shan Kayan aiki suke idan ka zauna sai a zaune ka,Ameer ya dinga dariya Belloti sai kace wata mace,yace akwai wasu tsumi ma na karfin maza zaka Dade kana Aiki ba tare da Injinka yayi sanyi ba,Ameer yace a sa Mana a mota a kawo Mana sai mu karba a Tasha,Belloti yace angama,ai Ni sabo da a Kauye abokaina da yawa suna da Aure sannan wannan Alawar Uche ne ya bani as a gift na aure na.,Ameer yace shege Uche,Haka suka Gama iya shegensu sannan Suka Yi Sallama.

Kwanci tashi ba wuya komai Yana tafiya dai dai cikin so da kaunar juna,cikin Manal ya Gama Isa Haihuwa ya cika wata Tara cif Yayin da bikin Yazed Saura kwana Uku rak duk wani shirye sun gama.
Manal tana Jan cikinta Haka take lallabawa sai da Fuzail ya kyaleta dole ta tafi gidansu zata kwana,Farida sunzo Belloti Yana can sai an daura Aure zasu taho da amarya gaba Daya,a Haka Kuma Belloti yace Faridansa a jirgi zata je ba Hawa mota, ya dage ya Siya Mata ticket. Dangin Malam Dana Annatu sun cika gidan Malam,Hajiya da kishiyarta Karimatu Suma nasu Dangin sunzo,Hajiya wannan lokacin ta nutsu duk wannan bakin cikin babu da ita ake komai itace Akan komai ma ka rantse ita ta Haifi Yazed,Haka Amaryar Malam ma mace me Hakuri ba ruwanta ango yayi gayyata ta gaske,Ana shagali Amarya tsoro ne a ranta sabo da Yazeed ba Wani Daukanta yake da muhimmanci ba,hakan yasa Tace baza tayi komai ba a daura Aure Kawai ya Isa.

Manal tunda tazo gidan Bata tashi ba,Sallah ma a zaune takeyi,Fuzail sai aikin bugo uban waya ba ji ba gani,washe Gari da safe Ango,Fuzail,Ameer,su Malam harda Maimartaba da tawagarsa da wasu abokan Ango jirgi Fuzail ya biya musu Suka tafi masu zuwa Kuma wasu Suka wuce a Motoci lafiyayyu, 11am dot aka Daura Auren Yazed da Raheela,Ango yasha farar Shadda irin kyan da ya zuba ba'a magana,Bangaren gidan Maimartaba Hajiya Babba da Amarya tare da wasu Yaran Mata biyu sunzo gidan su Manal sunyi Allah Sanya Alkhairi,Farida ansha Lace,Manal Kuwa Shadda tasa doguwar Riga katuwa sabo da cikinta,Farida ce akan komai tare da Kannenta,Yazed ko pics dinma Bai tsaya anyi ba Suka taho gida,bayan sun dawo prince direct cikin gidan ya shigo sabo da ya Gaida su Annatu sannan ya duba lafiyar Manal,tana bedroom a kwance tayi turus,Bayan ya gaisar da su Annatu ya Shiga wajenta.

Zama yayi a gefenta tare da duka Kansa a saitin kunnenta Yana tambaya ya jikin? Kalau kike Kuwa? Manal ta fashe da kuka tace Dan Allah ka kaini asibiti a janyo min nakuda ta karfi wallahi na gaji,Edd dinki fa ya cika tun last week kiyi Hakuri kin kusa,tunda ma an samu hawan jinin babu ai da sauki,lallashinta yayi kafin Maimartaba ya Kira shi a waya ya tafi,Yana zuwa Kiran Maimartaba yace aikenka zanyi Lagos zaka Kai Sako,yace Manal fa ta kusa Haihuwa Taya Zan dinga nisa da ita,yau zaka je ka dawo Inshaallah minti Nawa ne a flight,Fuzail badan yaso ba Haka ya Kira Manal a waya ya sanar Mata Tace a dawo lafiya lokacin Kuma ta fara Nakuda tun safe take Jin ciwon kasa kasa Bata San nakuda bace sai da taji abin ya gagareta sannan ta Kira Farida,Tace Farida ku kaini asibiti Ina Jin mutuwa zanyi,Farida tana Jin Haka ta bazama ta sanarwa su Annatu da Hajiya Sharifa a sirri sabo da mutane a gidan da yawa.

Kafin a Kira Yazed yazo a kaita asibiti Manal ta fara kuka duk ta tonawa kanta asiri,Yazed yazo aka tafi da ita Asibitin da take ganin likita,anji matar prince da wuri aka karbeta Ana lallabawa dama abinka da private,Manal duk kukanta ya ishi mutane,Hajiya Sharifa tace ke Dan Allah karki ja Mana abin kunya mace da kukan Haihuwa,duk macen da tayi kukan Haihuwa sau Daya to har ta Gama haihuwarta sai tayi kuka abin kunya
Showing 135001 words to 138000 words out of 153479 words