ci da kansu duk sun fice a hayyacinsu amma babu bazawara matashiya,Indai Kinga bazawara matashiya to mutuwa mijinta yayi ko kuma wata babbar kaddara Amma badai akan abin duniya ta fito ba.

Kije ki gani yanda butar me gida daban,kwanon abinci,ba a Isa ko Dansa yaci abinci a kwanonsa ko cokalin megida daban ne sabo da ganin darajarsa da mutuntuwa,Ana bashi girmansa komai sai da izininsa akeyi, Kawai kice Farooq talaka ne zasuyi shawara Bai da kudin kawowa Zaki min wani kwane kwane to a Haka nake sonsa ai ba ke Zaki zauna min ba,Shukrah ta zaro Ido tare da Furta Allah ya Baki Hakuri daga Wasa,Ameen wannan ba Wasa bane cin Fuska kika min ku dama Haka kuke Baku iya magana ba sai Kawai ku kwabowa mutum magana,shi yasa Wasu idan Suka Yi aure suke fada da mazajensu sabo da Rashin iya sarrafa harshe, a koma baya a duba rayuwar Iyayenmu ai ba Haka Suka Yi ba,ko a Bayan Ido mace ta zagi mijinta gani akeyi kamar ma Allah ta taba,Mukus Shukrah tayi.

Rannan Ina jinku kawayenki Yan wajen akinku sunzo kuka hadu Kuna ta zagin Mijin Yusrah,Kuma itama wawiya harda ita tana tsinewa mijinta tana zaginsa akan zai Mata kishiya Kuna tayata ita Kuma ta saki Baki tana ta tonawa kanta asiri wallahi ku gyara halinku barikin Nan da Iya shege muma fa mun iyata,kudin Nan mun San dadinsa hakura mukeyi Kawai Zaki fada min magana Ina ganinki Babba da hankalinki Ashe kema gososuwa ce? Shukrah tace to jaraba naji Haba wannan masifa Haka akan Farooq,Murmushi Manal tayi tace ai kece Ni Ina da zafi gaskiya,to Afwan cewar Shukrah.

Ameer shi ya samu tiryan tiryan ya kwashe labarin komai ya Bawa Yazed da Malam sabo da mamaki kasa magana sukayi sai da ya cire gashin ma suka tabbatar,Nan take Malam da Yazed murna ta kamasu Kuma Manal ta birgesu, hankalinsu ne ya kwanta da Auren,karshe Suka ce a sirrinta auren,Yazed da Malam Suka Fara tunanin mafarkin Farida da yanda abin ya faru Wato Farida Akan Manal take mafarkin,gashi ita ta fara haduwa da shi Amma ta wulakantashi ta samu dama,Malam a ransa yace iko sai Allah Farida tayiwa kanta Ashe da gaske ne mafarkin nata amma ta gudu ta bar ladanta ita da uwarta mafarki ya Kare Kam,Yazed zai Basu labarin mafarkin Farida Malam Yayi sauri ya canja zancen ya Hana a fada musu,Fuzail yace sisi baza ku kashe ba a bikin,Sannan kafin bikin Inshaallah za a canja ginin gidan nan,Yazed Ma Idan ka karbi takardunka ka sanar min,Yazed shi dai mamaki yakeyi wata azurtawa ta Allah dare daya,a wajen Yazed dare daya ne mana,Malam sai murna da farin ciki yakeyi ,Su Fuzail suna gamawa Suka fito Har Yazed Sai Manal taga Yazed Yana ta murna,Sai taji wani sanyi,Amma gogan Fuzail ko magana baiyiwa Manal ba shi a Dole ya Gama hayewa,Yazed ne yace baza ki raka su ba?Manal Tace to ya kulani ne? Kee Yazed ya daka mata tsawa...mikewa tayi tare da tafiya rakiya,Shukrah ta zauna sai faman satar kallon Yazed takeyi ita dai akwai son me kyau,gaba Daya tunda taga Yazed ta nacewa zuwa gidan tana fakewa da Manal.

Manal tana fita soro inda su Ameer suke Ameer ta yiwa magana itama Suka gaisa ta share Fuzail,ruwa Pure water ta kawo Amma sai ta mikawa Ameer Ruwan Tace Ameer gashi,Ameer Yana dauka yace Ina jiranka a waje ya fice,Yana fita Fuzail ya kalleta Kawai yaki magana sarauta ta motsa Manal Bata sani ba ita,Tace Maimartaba sannu Ina kwana tana cin magani,murmushi yayi yace ki barni naji da abinda yake damuna Manal kika sake bazan sake zuwa ba sai anyi biki,Ka ma Isa ta Furta,lallai Ni kike cewa ban Isa ba,to da ka Isan ne?idan ka Isa ka nuna min isar Mana,Kinci abinci duk Sanda na fito Miki a mutum baza ki iya min magana ba,Shine yanzu kika rainani,Manal Taji bawan Allah da son girman masifa Tace Dan kana ganina karama shi yasa ka rainani Farooq baka Sanni bane Yaro,Dariya yayi yace Shikenan Zan wuce na kiraki yau? Sanda kake kirana tambayeta kakeyi sai yau? Fuzail yace to wannan masifarfa? Kafi kowa saninta ai, sai na kiraki a waya Mayi magana akwai abinda
Yake damuna ki min Addua kawai,to ta Furta tare da Shiga gida,Ameer masifa ya fara Dan Allah muje yadin Nan kaikayi yake min a jiki Nima an jona min masifa,Dariya Suka Yi,Malam da Yazed kwana sukayi suna mamakin ikon Allah.

Maimartaba Suka samu tare da sanar Masa sun fadawa Abba zasu Kai kudin Aure,Memartaba Allah ya haneshi Bincike da Kansa sai yace zanyi magana da Dan Uwana yayi Bincike sosai,Ameer yace tun yaushe yayi Bincike ai ya Gama komai zaizo ya ma bayani,Sarki harda murna,Ana gobe za a Kai kudi Abban Ameer yazo ya samu sarki yace nayi duk Binciken da zanyi Yarinyar Yar malamaice Basu gaji sarauta ba Amma dai suna da asali da rufin asiri,Nan take sarki Ya Bata Rai yace what? Nufinka talaka na ce? Abban Ameer shima yayi tasa karyar yace a'a Babanta dai Dan Kasuwa ne na gaske ma Kuwa ya shahara,Sarki ya tabe Baki yace na rasa irin Yaron Nan me kwashe kwashen masifa ga Yara an Kawo Masa na mutunci yaki ya Kare a talaka,bana murna da wannan auren nasa,tunda Naga Yana nuku nuku nasan ba abin arziki a ciki,Abba yace tunda Yana Sonta ka kyale shi,Sarki yace ba ruwana wallahi shi da Mahaifiyarsa nasan baza su Kare lafiya ba,Kuma ba ruwana ko Baki tayi masa.

Allah ya gani nayi abinda Zan iya,kuma kasan Yan Uwansa na gidan Nan da Mata na ko? Idan ta shigo ta Zama Allah sarki babu me Shiga lamarinta Ni kuma bazan tsawatarba tunda shi ya jawa Kansa,Abba yace wannan fa ba tsari bane Yaya,babu Wanda aka Haifa da arziki ko wani mulki,Sarki yace ai Danka ne kaje kuyi abinku Allah Sanya Alkairi Amma idan matsala ta faru ba ruwana,Abba yace tunda ka Amince ba damuwa,sai ka fadawa uwarsa taji,Abba yace ba yanzu ba sai an daura za a fada Mata,Hmmm Kawai sarki ya furta ransa a jagule tun Bai ga Budurwar da iyayenta ba baya ma marmarin ganinsu.

Washe gari Abba da wasu Yan Uwan nasu aka Kai kudin auren Manal Itama su Kawu Salahu ne Suka karba,Annatu sai murna take yi,Yarta zata Yi aure,dubu dari biyar aka kawo kudin aure amma sai Yazed yace dubu sittin ne, su Farida Suka dinga yiwa Manal dariya,Lefen Ma Yazed yace ko an hada Kar a kawo sai bayan an daura Aure.
Babu Bata lokaci Fuzail yasa aka fara tsara gidan Malam da gini me kyau sabo kar azo aga gidan matarsa a Haka a halin Kuma Yana da kudi ace ya bar Iyayen matarsa a lalataccen gida suna Shan wahala abin a zage shi ne, ,kullum Ana Aiki ba dare ba Rana,Malam yace shine ya samu wasu kudi yake ginawa abinsa Yaran Basu Sani ba,Su Farida sai iyayi akeyi harda cewa Manal za a tafi gidan Talauci a bar Mana gidanmu na Yan gayu,Yazed Dariya Kawai yayi.

Haka Fuzail Yana zuwa zance akan lokaci,yayinda Suke Bawa Shukrah kudi tana tallafar Manal ta ko ina yanda baza ta Gane ba,Haka Yazed da Malam Kakarsu ta yanke sake ta accnt Fuzail yake tura musu kudi akan lokaci ai tuni Gidan Malam ya canja da yaransa,Yazed wani kyau ya Kara da haske kullum dinkuna yake sawa masu kyau Yana fesa gayu abinsa.

Hajiya ganin Basu da wata matsala komai a gidan Shar za a ci a koshi ga makaranta Yara suna zuwa ba matsala ga sutura yanzu sosai Malam Yana ta gyara halayensa wajen kyautata musu Haka jikinsa Yana ta sauki Yana takawa kadan kadan har masallaci Yana zuwa yanzu,Ga gida ya dauki kyau dagwas,Manal tayi Niyyar Shan shagalin biki Yazed yace babu bikin aure kawai za a daura a kaita,Farida Suka dinga dariya ana Mata habaici Manal harda kuka.

Tunda Belloti ya samu labarin Auren Manal yace lallai Ja'e yayi gaskiya wahala ta saka Riga da wando Kai har da Singleti Amma ba komai Bari nayi kudi wallahi ko waye Bai Isa ba sai na kaishi Kara Nan gaba,Annatu Kuwa kayan gyara ta hadawa Manal aka Kai mata kafin taje, Manal Bata sani ba Yazed ya dauki Su Fuzail har wajen Annatu Suka je suka gaisar da ita itama Yazed ya Mata bayanin komai a sirrri,Annatu harda kukan Murna Ashe arziki ne ya Kira Manal Birni,ai Kuwa ta Sha kyauta a boye sabo da can ma da shigar Talaucinsu Suka je Kuma a motar haya.

Fuzail ne yace da Maimartaba Manal zata Zo ta gaisar da su yace Kar ta sake tazo ta Bari idan an daura shike nan,Fuzail yaji Haushi yace nifa idan aka takura min Barin kasar Nan zanyi wallahi Kuma bazan sake zuwa ba ko da yawo,Sarki yayi banza da shi har ya tafi,Abban Ameer ganin Abubuwa zasu iya kwabewa ko yaushe yace da Ameer suyi shiri a saka ranar aure Kawai tun kafin gulma taje kunnen Maman Fuzail,Sati biyu aka tsaida magana,Manal tayi mamaki amma Malam yace Haka yaga dama,Dama anyi sa'a Manal a birni Bata da kowa na kawaye sai Shukrah,Haka Fuzail Ameer ne sai Danginsa

Yau Farida taje gidan Sarki taji Ana labarin Yarima Fuzail zaiyi aure Nan da sati daya,Kuma Yarinyar Yar talaka ce a Nan garin take,ai Farida da kuka ta dawo gida ta bawa Hajiya labari, duk ta haukace Yarima zaiyi aure,Hajiya Kamar zata Yi hauka Haka take cewa sai naci uban Dan Haru Haru,ko Malam din ma an daina Fada, makaryacin banza ba abinda ya iya sai karya cewar Farida,Wasa Wasa Farida kwana tayi tana zubar da hawaye,Manal Taji tausayinta ta dinga kwantar Mata da hankali Tace Inshaallah Fuzail naki ne Yar Uwa zaizo ya aureki karki damu daula da kudin Nan sai kin ci,Sai kin hau jirgi,sai munje makka,Farida ta Bata Rai Tace kije Makkah? Lallai kece ma kike auren Dan Sarkin Ashe? lallai to ki cire Rai wallahi ko airport baza kije ba,Manal ta zaro Ido Tace tab Allah ya sawwake Miki Farida wannan wacce bakar zuciya ce dake? Takalmi me tsini ta dauka ta bugawa Manal a goshi,Goshin Manal ya fashe tare da kumbura sabo da bakin ciki za ayi bikin Manal shine ta fasa Mata goshi Dan aga Amarya da fashashen goshi,Yazed Yana shigowa yaga Manal tana danne goshinta da tsumma ransa ya baci yace mene ya faru,Manal Tace Farida ce ta fasa min goshi Amma ai Dan kadan ya fashe Yaya Kyale zancen,Ai Yazed yace wallahi tayi karya Bulala ya samo ya Kama Farida sai da ya Mata laga laga sannan ya kyaleta Yana masifa Dan Iskanci za ayi bikinta ki fasa Mata goshi Yar Iska Yar bakin ciki.

Chemist ya kaita aka Mata treating suna dawowa Fuzail yazo sanye da Shadda Fara me Araha yayi kyau matuka da gashinsa dai,Fuskar Manal dinsa ya kalla yasa yatsa a habarta tare da dago da Kanta yace me ya samu goshin Kuma? Manal ranta a bace tace ba komai,Ya Zaki ce ba komai waye ya miki wannan raunin? Farida ta Furta tare da yin shuru,Tsaki Yaja kawai tare da furta kiyi Hakuri Bata da hankali Naga alama, Manal tana kumbura Baki irin na Yan tabara ta furta Amma dai tasan kullum Shukrah ke kaini wajen gyaran jiki yanzu ta dawo da gyaran Baya,Dariya Fuzail yayi yace gyaran yaushe zai dawo baya Kuma Kai Baby ai yayi min haka,Manal tace ai dai an cuceni kafin ya warke fa?Amarya da kulu a goshi.

Dariya sukayi yace karki damu my Manal,Kallonta ya shiga Yi tayi ta Masa kyau a lace din maroon Wanda shima cikin kayan Shukrah ne,Fitted gown aka Mata tayi zam zam tare da yafa Dan mayafinta,Gemunsa ya shafa da Sajensa Yana kallonta kamar maye wani nishadi yake ji,Manal Fuska ta shagwabe Masa tace Kamar fa kallo na kake Yi Ni Allah kunya kake bani,kyawawan idanuwansa ya lumshe Manal tayi awon gaba da Imaninsa da wannan shagwabar tata,Manal din tasa ta fara chasa gayu itama,Kunya tasa ta Mike daga saman Tabarmar Tace bari na kawo maka ruwa ta fara cat walk dinta dagwas-dagwas,Fuzail yace Uhm kaga tafiya me kyau ya fara Irga Mata Yana cewa Left-Right....left-Right,juyowa Manal tayi tana Dariya da wata matsananciyar kunya ta shige gida da gudu abinta.
Ruwa da lemo ta kawo Masa tare da Zama a gefensa da mificinta suna Hira tana Masa fifita sabo da yanda yake Jada jufa abinka da sabo da ac.

Fuzail ya Kira ta da Yan matana? Tace Na'am Dan samarina tana gyara pink lips dinta Kamar wata me tsotsar Alawa,lips din ya kurawa Ido tare da furta na hango shi cikin Nawa Malam ba'a magana,Manal ta fara Dariya Tace Allah ka manta surukinka ne fa Malam din shine ka Kira sunansa wannan ai cin mutunci ne,shi sai yanzu ma ya tuna a ransa yace Kai Manal da yarinta take sai kace sunansa na gaskiya ya fada,a fili yace ai ba Malam namu nake nufi ba,ayyoooo na gane tace tana kokarin Bude Masa ruwan amma sai ta kasa sai shine yace kawo marar karfi ya bude da Kansa.

Farida ta saka jaraba a ranta na tunanin Fuzail zaiyi aure sai ramewa takeyi tana karmashewa,Biki Yana matsowa Saura kwana biyu biki Annatu tazo da sauran Yan uwanta Mata da maza lokacin Saura kadan a Gama Gina gidan Malam,kowa ya kalli gidan dagwas sai yayi sha'awa ya sha tiles ko ina,Hajiya tunda Baki Suka Fara sauka take ta Fushi tana bakin ciki,Bata da Aiki sai habaici da takewa su Annatu.

Su Annatu da kayan abincinsu da komai na abinci Suka zo sabo da sun San halin Hajiya,ai Kuwa ko cokalinta Suka dauka sai tayi zage zage a gidan,wani yaro tsautsayi yasa ya shiga toilet din Hajiya sabuwa taji Tiles tare da fatattaka zawo a kasa,Hajiya Katsam ta ganshi gashi Yaron Kauye cikinsa katon gaske,Hajiya Takaici yasa ta finciki hannunsa Kamar ta dauki tsinke ta hantsila Kansa kasa tayi Masa butar Malam tare da zaro tsintsiyar kwakwa ta Zane Masa gadon baya,yaro jikinsa duk Kashi Yana tsala ihu,Uwarsa Yar Fulani ta fito da gudu tana gwarancin hausarta Minena(Mene ne) Hajiya? Hajiya Tace Uwarki ce Minena Shegun yaranku ciki duk tuwo sunzo suna Bata Mana gida,aikin banza anyi Mana sabon gida za a Bata Mana akan bikin banza bikin wofi sai kace wacce zata auri Dan Gomn, Annatu ce tazo Tace Harira muje ki kyaleta Mene duniya Hajiya,Biki na lokaci daya wallahi Kowa yayi Fushi da bako zaiji kunya.

Hajiya lebenta na sama Yana tashi tace Indai kunyar bako irinku ne Allah ya sawwake min Yan Iska arnan daji,wa zai kalleku yace mutanene ku aikin banza kafa duk kaushi,Annatu tace Li'ilafi kurayshin aniyarki ta biki Suka juya Suka tafi dakin da Manal take.
Hajiya danginta ko Daya Bata gayyata ba,Yazed duk wani cefane na abinci yayi Wanda Baki zasu ci su Sha.
Manal sai murna takeyi taga su Annatu da su Khairan,harda Kiran Fuzail lallai yazo yaga Yan biyu kannenta Bata San har kauyen yaje ba wajen Anna,Haka yazo Suka gaisa da Dangi daban daban.

Gidan Sarki Kuwa ba Wanda ke murnar auren,Kowa ya shiga harkarsa,Hassan da Hussain ne Kawai ke kula abin su dai suna son Manal Haka duk da Basu taba ganinta ba,auren a katafaren masallacin idi na unguwar su Manal za a daura,tunda Memartaba yaji Sunan Unguwar su Manal yasan sai mutum ya shahara a Talauci yake Zama a Unguwar, Takaici ne ya Kama shi Yace Uhm uhm hum, Ko a radio Maimartaba Bai bada sanarwa ba,Ranar auren ranar Mai martaba ya sanarwa Ummin Fuzail,Fuzail yasan zata Neme shi sai ya sa wayoyinsa a flymode gaba Daya,Yau wankan na daban ne.

Gidan Su Manal kuwa Yan Fulani sai hada Hadar girki akeyi ana shewa da Murna,Hajiya da Farida sai kunci suke yi,Hajiya ganin irin uban Naman da aka kawo za ayi Miya da shi ai Kurar sai ta shige cikin Yan girki tana tayasu sabo da ta samu dama ta saci Nama ta Kai dakinta,Sai shishigi take musu,Kuma Tace lallai sai abinda Tace shi za ayi a girkin,Hajiya tana juya Miya da ludayi ta dandana Tace ba curry Ina Uwar 'ya a bayar da kudi a sa Mana Curry zata fi shiga, Annatu ta bayar da kudi aka siyo,Dan mugunta ta sake cewa an saka Mr Chef Kuwa? Annatu Tace Mene Haka Kuma? Hajiya tana goge Gumi Tace Kauye Bata Yi ba wallahi Maggi ne shima,Annatu ta sake bada kudi dubu Daya,Hajiya Tace Saura Onga da Curry me tafarnuwa,Annatu Tace ya Isa Haka Hajiya asha miyar Nan Tasono Kawai Kawai na gaji.

Hajiya Tace ban Gane a shata Tasono ba? Anna Tace ai Haka ake cewa idan Miya Bata ji Hadi ba ko ba nama a ciki sai ace ayi ta Tasono,Hajiya tace magana sai Kauye Yan Kauye anji jiki, burunku tuwo ko? ku dai aci tuwo Kawai mashaallah Amma tasono ai mahadin majina ne a Hanci ku komai sai Kun hada da kazanta,Harira Hajiya tayiwa Habaici tace shi yasa Muka ga gidanku ga shi Nan fes da shi ko Ina Kal,Karki zageni dai,Baza kizo har gidana ki fada min magana ba,Shuru suka mata duk ta hanasu sakewa.

Fuzail da Ameer sun fita iya fita,Ango yasha Farar Shadda me tsadar gaske,da wata hula ta musamman Kalar dinkin babbar rigar, takalmi,Wayar ma fara,Haka motarsa ma,kowa ya kalli Fuzail bazai so ya dauke Idonsa ba, har Maimartaba kallon Dan Nasa yakeyi kawai yanda yayi kyau sai nishadi yake Yi,duk danginsa sun Sha wankan ganske,Ameer kuwa Shaddarsa silver ya saka shima da babbar Riga da hula sun wani cokota gaba yanda matasa Yan gayu ke Yi, Manal kuwa musamman aka kawo Mata kayan da zata saka
Showing 51001 words to 54000 words out of 153479 words