Raye ko wajen danginta ko Dangin Ubansu ma ayi musu fada basa Jin maganarta sun gallabeta Bayan ita ta jawa kanta.
Wallahi Hajiya kika sake abinda Farida sukewa Baba Yasin sai sun Miki ai gashi Nan kina gani ke Bata Miki wanki ba kin moreta a matsayin ke kika haifeta sai kece ma kike Mata wanki da guga da sauran ayyuka idan Baki Yi ba baza suyi ba Kinga kin maida su kazamai kuma laifinki ne,sannan duk abinda Tace shi Zaki Mata,ga Yara su Sa'iha duk basa Jin maganarki Nan gaba Zaki ga wulakanci kuwa wallahi kafin kowa yayi kuka ke Zaki fara yi mu Yan jaje ne,Iyaye Yara Suki yin Aiki idan anyi magana Tace idan sunje gidan mijinsu ai zasu Yi dole,Basu Saba ba ta Ina zasuyi Dole? yanda yanzu aka daina biyayyar aure,yanzu ke Farida ko kin auri Prince din Haka Zaki Masa kazanta? Nufinki akwai Bayi su zasu Miki komai? Ko shafe shafen naki zai kalla Kawai? Hajiya tunda Manal ta fara magana ta saki baki har wajen minti talatin Manal tana zazzaga musu fada, kowa yaji fadan Manal yasan gaskiya ta fada Amma Hajiya ta fashe da kururuwa Tace Manal ta zazzageta, Farida Tace sai ta Mata duk ta dakko tabarya,ganin da gaske sukeyi ta fece dakinta Farida tace ai Zaki fito ne wallahi ko Zaki shekara a daki Indai kika fito sai na fasa Miki Kai,Manal Taki Fitowa Haka suka kwana da yunwa rashin fitowar Manal sun San da Manal ta fito ko a shago sai ta ci bashi ta siyowa su Falaqi ko garin kwakwi ne da sugar,Su Falaqi sun Sha haushi yau rashin fitowar Manal.
Da Sassafe Kuwa zasu tafi makaranta Manal tana daki a kulle ta hau gyara dakinta yunwa na cinta sai ko ta tsinci dubu Uku a kasan pillow sababbi dal dal,ko Bincike batayi ba Manal Tace baiwa daga Allah wallahi Allah ne ya ciyar dani,tana cikin murna su Falaqi Suka hau dukan Kofar Manal suna Manal zamu tafi makaranta ki fito,Manal tace ku tafi Mana Haka Kawai Anty Farida ta nakasa Ni da tabarya,Alhaqatu tace Bamu karya ba Anty yunwa wallahi zata kashe mu jiya Falaqi Kwana yayi Yana kuka,Manal Taji tausayinsu,Sa'iha Tace ki fito Manal tunda kina da karfi ki dauki Anty Farida ki nunawa Allah ki bugata da kasa,Dariya Suka bawa Manal Shegu Yara sunji wuya cewar Manal ta furta tare da Bude kofar.
Ihu suka fara yeeeeeeee
eeeeewwwwww Suka cika gidan,Hajiya ta leko da kanta tsakar gidan Tare da tambaya Nepa aka kawo ne? Falaqi yace Aunty Manal ce ta fito yanzu zamu ci mu koshi Yeewwwwwwww suka Kama Rawa da tsalle,Manal tana sani ta kalli Hajiya ta daga dubu Uku sama ta karkada su a Iska,Hajiya ta zaro Ido Tace bakya sana'a wallahi Sata kike Yi barauniya an koma satar kudin mutane.
Falaqi ya shiga Kare Manal yace Hajiya Sana'a take fita Yi a kasuwa,inji Ubanka kullum Muna tare da ita a Ina taje Neman kudin? ka koyi karya shegen Kai Kamar randar kauye,Falaqi yace to tunda kullum Muna tare da ita a Ina zata sato kudin mutane tunda Bata fita ko Ina kince,Allah ne ya Bata mudai muje Anty Manal ki siya Mana dafaffe a gidan Maman Aisha, Manal tace yawwa muje a siyo Kawai ku tafi da abinku school sabo da karku makara,Falaqi da gudu ya kwaso kulolinsu na Yan makaranta suka fita gaba Daya,Gidan Maman Aisha babu abinda Bata dafawa na abincin siyarwa ko me kake so komai dare komai safiya zaka samu,Manal tace kowa ya zabi abinda zai ci,Suka zaba aka cikawa kowa Cooler dinsa sannan ta Basu Naira talatin kowa kudin Break Suka tafi school da murna.
Doya da kwai ta siyo da lemonta,Ta gaji da Halin su Hajiya Bata siyo da su ba ta kyalesu ta dawo gida da nata,tana zuwa ta zauna a tsakar gida ta baje abinci da maltina,Farida yunwa ta fito da ita ko za a tausaya Mata,Itama Hajiya ta dinga zaga tsakar Gidan ko za ace gashi Amma Shuru sai taje daki ta fito ta shiga kitchen ta fito,ta wuce ta Gaban Manal ta zabga Mata Harara ta wuce,ta sake dawowa Tace Allah sawwake abinda za a ce wani ne zai baka,me zaka Yi da kayan wani,Nima maganina kenan Dana ke karba,Farida tayi Mukus ita dai tana so a San Mata,Hajiya ta kalli Farida Tace Yar Iska marar zuciya sai kwalalo Ido kikeyi ke da kike shiga har gidan Sarki ki zaga inda kike so ko a gidan Sarki baza kici ki koshi ba muma ki taho Mana da shi banza lusara,doya da Kwan ce Baki sani ba kinyi asara wlh.
Farida tayi Shuru Kar ta fusata Manal ta hanata,Manal Bata kulasu ba sai ma kafa data harde kafa Daya Kan Daya ta daga gongonin Maltina ta tiltilawa bakinta tayi gyatsa me karfi Wai Dan suji tafa koshi,Wakar barmani coge ta fara Yi... sai dai tatashi nokai nokai sakarai Bata da wayo....muryarta ta Karo da karfi tana wakar sai dai ta tashi Nokai Nokai....Farida taja kwafa a ranta Tace Zaki sani Duk Randa na Zama Gimbiya Farida wallahi sai na tozartaki a duniya,Wayar Manal ce tayi Kara,Farida ta zaro Ido ita da Hajiya sai yanzu Suka kula da Wayar Manal,Farida ta taba ganin Wayar a Hannun Farooq ba shakka shine ya bawa Manal ita,wani bakin ciki ya Kama Farida Taya Manal zata rike Pop 3 ita tana fama da Vivo karama.
Manal Wayar ta daga tana kwankadar Maltina,Farida ta bayan Manal ta koma Dan taga waye ya Kira sai taga an sa (Maganin kuka na)Dariya ta Kama Farida Manal tana cewa Hello Farooq ita Kuma Farida da karfi Wai Dan Farooq din yaji ta sunkuyo da kanta saitin Wayar tare da cewa Yar Kauye Kawai Haka ake sawa Masoyi suna Wai wani maganin Kuka na banza doluwa Ana My love,Honey, Sweetheart ke Kuma kina wani maganin Kuka na kinji kunya kinyi asara wallahi,Fuzail Yana ji radau a wayarsa yaji duk Maganar Farida,wani Sanyi da murna ta kamashi shine ma maganin kukan Manal wayyo shi Kam ya haye Ashe tana sonsa haka,ya dinga Murna da nishadi Farida tana ji Yana ta dariya ta waya Yana tambaya da gaske Haka kika sa? Manal tana tsoron zai kalleta Yar Kauye ta daure a kunyace Tace ae,Wow ya Furta I'm such a lucky Man,Baki Farida ta tabe tare da furta Jaki ta Kara gaba,shi baiji me Tace ba yanzu ma bare.
Me kike ci ne Haka? Manal tana Dariya tace ai yau Allah ne ya jefo min kudi daga sama Ina gyaran dakina in fada maka na tsinci dubu uku a kasan pillow,Yan dubu dubu sababbi baka gansu ba Kamar Kar na kashe su,sabon kudi da kyau suke a Ido Amma Haka na fara kashe su,Jiyama nayi sabuwar kawa anjima Zan baka labarinta sunanta Shukrah jiya tazo,Fuzail yasan sakonsa ya fara zuwa yaji Dadi Shukrah ta fara Aiki,Yace to dubun ukun ya kika Yi da ita?
Gashi Ina cin dadina da ita Bata fada Masa har kannenta da su Suka ci abinci ba sabo da Kar ya rainata da yawa ko taje tayi Abu Dan Allah ta zobe ladanta sai Tace ita kadai taci abin Dadi bayan ta karya,Yace Uhm Good kinji dadinki,Manal ta Mike ta bar ragowar abincinta ta saka Hijab suna waya tayi waje,Farida ba jira ta dauke ragowar ta lashe aka bar Hajiya sai hanji a ciki.
Manal tana fita katin MTN ta siya na dari biyar a cikin kudin Tace da Fuzail Ina zuwa Kawai ta copying Numbers din katin a kasa ta rubuta Ina sonka ta tura Masa ta text,Sai ganin Kati yayi ya shigo, ya dinga dariya Allah sarki tausayinsa take ji talaka ne shima bashi da kudi.
Sending back ya Mata abinta ya kirata Yana Mata fada shi baya so zai Fara sana'a Kuma Dan uwansu Yana Basu kudi,Manal Tace to Ni me zanyi da Kati tunda kana kirana,Nifa bana so na gode ban tura miki ba sai kece kina mace Zaki bani kudi karki sake turo min,Manal Tace to Dan Allah naji bazan sake ba Amma ka saka wannan Dana turo,Fuzail yaki yarda Ameer Yana jinsu yace Ni dalla bani na saka Nima naci irin kudin Prince,Fuzail ya kyafta Masa Ido Wai Kar ta ji,Ai Kuwa Manal Tace to bawa Ameer ya saka shi tunda na maka kyauta baka so ka watsa min kasa a Ido ai ya maka kyau Kuma Kar ka sake kirana munyi fada, idanba munyi fada ba ta kashe wayar tana cewa a bar katin ya gaji ya bushe a waya wallahi bazan saka ba.
Dole sai Ameer ne yasa katin Yana dariya Yana tsokanar Fuzail kaga na me tausayi inyee Dan gata har Kati ake sa maka,Fuzail ya share shi kawai.
Zuwa dare 10pm Manal tana dakinta suna waya da Fuzail da gwarancin hausarta tace Wai hadin gwiwa akayi da larabawa aka haife ka? Fuzail shima yace a'a mutum da mace Daya ne Suka haife Ni Zaki ce Wani Hadin gwiwa sai kace wani Business,Dariya Suka Yi gaba Daya tace kayi Hakuri ba nufina mutum da mutum ba Ina nufin Kai ruwa biyu ne Mamanka ko babanka ciki akwai Balarabe? Fuzail yayi Dariya yace ko Daya Haka Kawai Allah ya halicceni,Labarin Shukrah ta dinga bashi,yace kinyi Friend amma Banda fadar sirrinki ki kiyaye wasu matan Basu da hankali karki saurin yarda da mutum,to ai dama bazan saki jiki ba babu ruwana cewar Manal,Yace Good suna ta Hira a Haka suka Yi bacci ba tare da sun shirya ba.
Bayan Kwana biyu Shukrah Bata Zo ba sai a kwana na Uku taci kwalliya ta sake zuwa da Yamma,Manal sanye take da wani tsohon lace dinta pink,ta ja Shukrah Suka shige dakinta,Shukrah ta dinga Jan Manal da Hira har ta Dan saki jiki sannan Tace Manal a rugar da kika Bari kinyi makaranta? Manal Tace a'a Amma na fara iya karatun hausa da Dan wani turancin ma,Shukrah tace to ba damuwa ki tanaji littafi da biro daga yanzu kullum na samu time Zan dinga shigowa Ina Dan koya Miki wasu abubuwan,Manal tace Kai Amma na gode Allah ya bada Lada,Tace Ameen,Shukrah tace akwai wasu Kaya Kala hudu Dana dinka,Amma telan ya min shirme yayi min Dinki karami gaba Daya baifi size dinki ba,telan Nan ya cuceni Zan kawo Miki su ki dinga sawa naga kina da karancin sutura gaki Budurwa ya kamata kema ki canja,Manal ta dinga Murna tana godiya harda Rungume Shukrah sabo da ta tuno Farooq zai zo zance zata Masa kwalliya sosai shi yasa take ta faman murna,Shukrah Tace harda takalmi da mayafi Zan hado Miki,Manal tace wayyo muje ki nuna min gidanku kawancen Nan naki Naga da gaske kikeyi,Shukrah ta dinga dariyar Manal duk ta haukace akan kayan sawa,Shukrah tace gashi an Mana Albashi harda kayan kwalliya Zan siyo Miki,Manal ta Bude Baki harda Hawaye Tace Dole muzo gidanku da Farooq Dina ya Miki godiya ta musamman,Shukrah tace au har saurayi ne dake? Laaaa ai na kusa aure jira nake Yaya da Babanmu su dawo za a kawo kudi,Shukrah Tace mashaallah na tayaki murna Yar uwata yanzu dai kawo min ruwa na sha,Manal ta Mike da sauri ta fice lokacin Shukrah ta sake Bude kayan sawar Manal Wanda ta wanke ta linke,cikin ninkin zanin atamfa ta sawa Manal dubu biyu.
Bayan Shukrah ta tafi Manal tana gyara kayanta kudin suka Fado Amma wannan karon tsofaffin kudi ne tukuf,Manal tsoro ya kamata Nan take ta Kira Fuzail a waya tana kuka,tsoro ne ya kamashi duk ya rude Yana tambayarta lafiya? Tace kaga wani kudin na sake tsinta a cikin kayana dubu biyu,Fuzail ya sauke Ajiyar zuciya tare da furta kin bani tsoro wlh nayi zaton ko Baki da lafiya ne,Allah ne ya Baki karki ji komai ki kashe abinki,Zuciyarki ce me kyau Allah yake dafa Miki,Manal tana shesheka Tace nidai Kar nazo ko Aljani ne yake biyan Sadaki na,sai na ci kudinsa da yawa yace ya aure ni,Dariya ta Kama Fuzail da kyar ya Mata wayo hankalinta ya kwanta.
Hajiya ta kwana da yunwa ta yini Nan fa Ulcer ta shigeta me karfi ta fara ciwon ciki da ciwon baya tare da zafin kirji,kwana tayi tana murkususu,Farida Suma ta cikinsu sukeyi da kyar Tace ki tashi muje wajen Kawu Sani a kaiki asibiti,Hajiya tana rike ciki da kirji tace Manal ce tayi min asiri na sani a samu a kaini wajen Malam Dan Haru shi zai min magani wayyo gadon bayana,Farida Tace Ni wallahi wajen Ruma zanje ta bani dari biyar nazo naci abinci sai dai ki jira tukun tayi ficewarta ta bar Hajiya su Falaqi suna jinya, sai da Rana sosai Farida ta dawo cikinta a cike ko wajen Hajiya Bata kalla ba Ganin Manal ta tafi raka Shukrah sai ta shiga dakin taga irin kayan da Shukrah ta kawowa Manal sababbi na sawa Takaici ya Kama Farida,Wayar Manal ta hango saman katifa,da sauri ta dauki Wayar ta dauki ragowar pure water ta samu ta dura ruwa a ko Ina na kafafen Wayar sai da ta tabbatar ruwa ya ratsa Wayar sannan ta goge jikin Wayar yanda baza a Gane ba ta fice.
Ita Kuma Manal Bayan ta raka Shukrah Chemist taje ta kwatantawa me Chemist irin ciwon da Hajiya ke fama da shi,Ya hado Mata maganin Ulcer,ta tsaya ta siya Mata Maltina da Madara da abincin ci sannan ta siyowa su Falaqi ta dawo gidan har dakin Hajiya ta Kai mata,Wahala da yunwa ta ishi Hajiya ba shiri ta fara Shan kowanne maagani,Cikin Yan mintuna sai ga Hajiya ta warke,ta dauki abinci taci ta sha,Su Falaqi ma Suka koshi,Amma Farida tana zuwa Hajiya ta kalleta tace shegiyar ta karya tsafinta,Maganin Ruwa Gestid ta daga tace wala'allah a Nan ta Sako maganin taga mun ganeta shegiya har da siyo min abinci sabo da Kar na mutu na rataya a wuyanta,Falaqi yace Wai Me Manal tayi muku ne mu muna sonta tana kula da mu,Farida ta zuba Masa rankwashi,Sa'iha tace daga ya Fadi gaskiya,Masatura Tace Ni wallahi ma Nan gaba dakin Manal Zan koma da kwana,Alhaqatu itama Tace Nima Haka mu dinga koya Mata karatu.
Manal Kuwa tunda ta duba Wayarta taga ta dauke duf,gaba Daya komai yaki Yi,batayi Hankalin budewa ta goge ba Kawai ta barta ta kwanta Haka gashi gobe Farooq zaizo zance ta Gama shirinta,shima Fuzail Yana ta Kiran Wayarta ya fada Mata zaizo fa Amma da dare Shuru Wayar Bata shiga ya rasa dalili Haka ya hakura zuwa da safe.
Da safe ma Shuru Wayar Manal,Manal Allah yasa ta haddace number Farooq Kawai Wajen me shagon Kofar gidansu taje tare da karbar Aron waya ta Kira Fuzail,Shuru ba a daga ba,shi Fuzail ba sosai yake daga number da Bai Sani ba,Yana Gaban sarki yaji an dameshi da Kira Tsaki Yaja sannan ya daga,sai yaji Muryar Manal zumbur ya Mike tare da barin wajen memartaba sarki.
Wace Manal?
Masu Sharhi kunfi kowa birgeni,Ina sane da ku akwai special pages kowacce Bata Guda.
Malam Rabiu Isa Wanda kowa ya sani da Malam shine cikakken sunan Baban Manal,Asalinsa yankin Nasarawa state ne can cikin wani kauyen Shagari,Su biyar Iyayensu Suka Haifa duka maza a kauyen,Malam Salahu Shine na farko sai Murtala,Malam Nasiru sai Malam Umaru Wanda Allah ya Masa Rasuwa,sai Mas'ud shima Allah ya Masa rasuwa,Saura su Uku Suka rage,kafin Iyayensu su Rasu ba abinda Suka gada sai Harkar malinta,gidansu kaf limaman kauye ne,kowannensu Yana da Almajirai Kamar yanda Suma daga almajiranta Suka Zama Malamai,Suna da Ilimi na Masu karatun Allo hakan yasa tun suna matasa Suka fada Harkar tsubbu,Suka shiga rigar Malamai Suka koma Harkar bokanci tare da kulla alaka da Aljanu Wanda zasu dinga Yi musu hidima Suma suna biya musu bukatunsu,kaf kauyen tsoron gidan lilaman akeyi sabo da an San Basu da Imani ko digo.
Cikin ikon Allah Rabiu ya tashi da almajiransa ya bar Kauye ya koma cikin birni tare da Kama hayar gida shi da yaransa Almajirai daga Nan kasuwar bokanci ta bude a birni har ya mallaki gidan da su Manal ke ciki yanzu,Ana Haka Ya hadu da Hajiya Babar su Farida Zulai wacce asalinta Yar Katsina state ce itama gaba Daya tashi tayi ta tsincesu da danginta da yawa a Nasarawa,Tana da Yayye maza biyu sai sauran Yan Uwa,Iyayenta Kuwa dama basa raye a Hannun Dan uwanta ta girma Kawu Sani.
Tallan goro takeyi a kasuwa Malam ya hadu da ita Suka Fara Soyayya har sukayi aure tare da Yan Uwansa Suma,Malam Baida Imani a lokacin,baya tausayin mace ga wulakanci gashi da son Mata,ko magani Mace tazo Nema Wajensa sai yayi Zina da ita zai Mata magani,sabo da Aljanun da yake Muamula da su sune suke sa shi hakan sannan bukatarsa zata biya.
Ana Haka ya tafi Bauci Karin Ilimin bokancinsa a can ya hadu da Annatu Wato Hadiza Me tallan Fura,fara kyakyawa,tun daga siyen fura yaji shaawarta lokacin Kuma Zulai Wato Hajiya Shuru Taki Haihuwa alamar Bata Haihuwa.
Yana auren Annatu
Shekararta Daya ta Haifi Yazed sankacece fari tas Dake Annatu Fara ce kwal Haka Malam ma Yana da haske daga Nan Kuma Malam soyayya ta kare, sai ya tsani Annatu da jaririnta,ba Wanda ya tsana irin Yazed.
Komai zaiyi sai yayi shawara da aljanunsa sunan Jariri ma su Suka ce a sa Falaqi, ranar suna ya sa Masa Falaqi,Annatu Tace wallahi sai ta canja suna Dan baida ma'ana suka dinga Fada Hajiya tana ji tana
Showing 39001 words to 42000 words out of 153479 words
Wallahi Hajiya kika sake abinda Farida sukewa Baba Yasin sai sun Miki ai gashi Nan kina gani ke Bata Miki wanki ba kin moreta a matsayin ke kika haifeta sai kece ma kike Mata wanki da guga da sauran ayyuka idan Baki Yi ba baza suyi ba Kinga kin maida su kazamai kuma laifinki ne,sannan duk abinda Tace shi Zaki Mata,ga Yara su Sa'iha duk basa Jin maganarki Nan gaba Zaki ga wulakanci kuwa wallahi kafin kowa yayi kuka ke Zaki fara yi mu Yan jaje ne,Iyaye Yara Suki yin Aiki idan anyi magana Tace idan sunje gidan mijinsu ai zasu Yi dole,Basu Saba ba ta Ina zasuyi Dole? yanda yanzu aka daina biyayyar aure,yanzu ke Farida ko kin auri Prince din Haka Zaki Masa kazanta? Nufinki akwai Bayi su zasu Miki komai? Ko shafe shafen naki zai kalla Kawai? Hajiya tunda Manal ta fara magana ta saki baki har wajen minti talatin Manal tana zazzaga musu fada, kowa yaji fadan Manal yasan gaskiya ta fada Amma Hajiya ta fashe da kururuwa Tace Manal ta zazzageta, Farida Tace sai ta Mata duk ta dakko tabarya,ganin da gaske sukeyi ta fece dakinta Farida tace ai Zaki fito ne wallahi ko Zaki shekara a daki Indai kika fito sai na fasa Miki Kai,Manal Taki Fitowa Haka suka kwana da yunwa rashin fitowar Manal sun San da Manal ta fito ko a shago sai ta ci bashi ta siyowa su Falaqi ko garin kwakwi ne da sugar,Su Falaqi sun Sha haushi yau rashin fitowar Manal.
Da Sassafe Kuwa zasu tafi makaranta Manal tana daki a kulle ta hau gyara dakinta yunwa na cinta sai ko ta tsinci dubu Uku a kasan pillow sababbi dal dal,ko Bincike batayi ba Manal Tace baiwa daga Allah wallahi Allah ne ya ciyar dani,tana cikin murna su Falaqi Suka hau dukan Kofar Manal suna Manal zamu tafi makaranta ki fito,Manal tace ku tafi Mana Haka Kawai Anty Farida ta nakasa Ni da tabarya,Alhaqatu tace Bamu karya ba Anty yunwa wallahi zata kashe mu jiya Falaqi Kwana yayi Yana kuka,Manal Taji tausayinsu,Sa'iha Tace ki fito Manal tunda kina da karfi ki dauki Anty Farida ki nunawa Allah ki bugata da kasa,Dariya Suka bawa Manal Shegu Yara sunji wuya cewar Manal ta furta tare da Bude kofar.
Ihu suka fara yeeeeeeee
eeeeewwwwww Suka cika gidan,Hajiya ta leko da kanta tsakar gidan Tare da tambaya Nepa aka kawo ne? Falaqi yace Aunty Manal ce ta fito yanzu zamu ci mu koshi Yeewwwwwwww suka Kama Rawa da tsalle,Manal tana sani ta kalli Hajiya ta daga dubu Uku sama ta karkada su a Iska,Hajiya ta zaro Ido Tace bakya sana'a wallahi Sata kike Yi barauniya an koma satar kudin mutane.
Falaqi ya shiga Kare Manal yace Hajiya Sana'a take fita Yi a kasuwa,inji Ubanka kullum Muna tare da ita a Ina taje Neman kudin? ka koyi karya shegen Kai Kamar randar kauye,Falaqi yace to tunda kullum Muna tare da ita a Ina zata sato kudin mutane tunda Bata fita ko Ina kince,Allah ne ya Bata mudai muje Anty Manal ki siya Mana dafaffe a gidan Maman Aisha, Manal tace yawwa muje a siyo Kawai ku tafi da abinku school sabo da karku makara,Falaqi da gudu ya kwaso kulolinsu na Yan makaranta suka fita gaba Daya,Gidan Maman Aisha babu abinda Bata dafawa na abincin siyarwa ko me kake so komai dare komai safiya zaka samu,Manal tace kowa ya zabi abinda zai ci,Suka zaba aka cikawa kowa Cooler dinsa sannan ta Basu Naira talatin kowa kudin Break Suka tafi school da murna.
Doya da kwai ta siyo da lemonta,Ta gaji da Halin su Hajiya Bata siyo da su ba ta kyalesu ta dawo gida da nata,tana zuwa ta zauna a tsakar gida ta baje abinci da maltina,Farida yunwa ta fito da ita ko za a tausaya Mata,Itama Hajiya ta dinga zaga tsakar Gidan ko za ace gashi Amma Shuru sai taje daki ta fito ta shiga kitchen ta fito,ta wuce ta Gaban Manal ta zabga Mata Harara ta wuce,ta sake dawowa Tace Allah sawwake abinda za a ce wani ne zai baka,me zaka Yi da kayan wani,Nima maganina kenan Dana ke karba,Farida tayi Mukus ita dai tana so a San Mata,Hajiya ta kalli Farida Tace Yar Iska marar zuciya sai kwalalo Ido kikeyi ke da kike shiga har gidan Sarki ki zaga inda kike so ko a gidan Sarki baza kici ki koshi ba muma ki taho Mana da shi banza lusara,doya da Kwan ce Baki sani ba kinyi asara wlh.
Farida tayi Shuru Kar ta fusata Manal ta hanata,Manal Bata kulasu ba sai ma kafa data harde kafa Daya Kan Daya ta daga gongonin Maltina ta tiltilawa bakinta tayi gyatsa me karfi Wai Dan suji tafa koshi,Wakar barmani coge ta fara Yi... sai dai tatashi nokai nokai sakarai Bata da wayo....muryarta ta Karo da karfi tana wakar sai dai ta tashi Nokai Nokai....Farida taja kwafa a ranta Tace Zaki sani Duk Randa na Zama Gimbiya Farida wallahi sai na tozartaki a duniya,Wayar Manal ce tayi Kara,Farida ta zaro Ido ita da Hajiya sai yanzu Suka kula da Wayar Manal,Farida ta taba ganin Wayar a Hannun Farooq ba shakka shine ya bawa Manal ita,wani bakin ciki ya Kama Farida Taya Manal zata rike Pop 3 ita tana fama da Vivo karama.
Manal Wayar ta daga tana kwankadar Maltina,Farida ta bayan Manal ta koma Dan taga waye ya Kira sai taga an sa (Maganin kuka na)Dariya ta Kama Farida Manal tana cewa Hello Farooq ita Kuma Farida da karfi Wai Dan Farooq din yaji ta sunkuyo da kanta saitin Wayar tare da cewa Yar Kauye Kawai Haka ake sawa Masoyi suna Wai wani maganin Kuka na banza doluwa Ana My love,Honey, Sweetheart ke Kuma kina wani maganin Kuka na kinji kunya kinyi asara wallahi,Fuzail Yana ji radau a wayarsa yaji duk Maganar Farida,wani Sanyi da murna ta kamashi shine ma maganin kukan Manal wayyo shi Kam ya haye Ashe tana sonsa haka,ya dinga Murna da nishadi Farida tana ji Yana ta dariya ta waya Yana tambaya da gaske Haka kika sa? Manal tana tsoron zai kalleta Yar Kauye ta daure a kunyace Tace ae,Wow ya Furta I'm such a lucky Man,Baki Farida ta tabe tare da furta Jaki ta Kara gaba,shi baiji me Tace ba yanzu ma bare.
Me kike ci ne Haka? Manal tana Dariya tace ai yau Allah ne ya jefo min kudi daga sama Ina gyaran dakina in fada maka na tsinci dubu uku a kasan pillow,Yan dubu dubu sababbi baka gansu ba Kamar Kar na kashe su,sabon kudi da kyau suke a Ido Amma Haka na fara kashe su,Jiyama nayi sabuwar kawa anjima Zan baka labarinta sunanta Shukrah jiya tazo,Fuzail yasan sakonsa ya fara zuwa yaji Dadi Shukrah ta fara Aiki,Yace to dubun ukun ya kika Yi da ita?
Gashi Ina cin dadina da ita Bata fada Masa har kannenta da su Suka ci abinci ba sabo da Kar ya rainata da yawa ko taje tayi Abu Dan Allah ta zobe ladanta sai Tace ita kadai taci abin Dadi bayan ta karya,Yace Uhm Good kinji dadinki,Manal ta Mike ta bar ragowar abincinta ta saka Hijab suna waya tayi waje,Farida ba jira ta dauke ragowar ta lashe aka bar Hajiya sai hanji a ciki.
Manal tana fita katin MTN ta siya na dari biyar a cikin kudin Tace da Fuzail Ina zuwa Kawai ta copying Numbers din katin a kasa ta rubuta Ina sonka ta tura Masa ta text,Sai ganin Kati yayi ya shigo, ya dinga dariya Allah sarki tausayinsa take ji talaka ne shima bashi da kudi.
Sending back ya Mata abinta ya kirata Yana Mata fada shi baya so zai Fara sana'a Kuma Dan uwansu Yana Basu kudi,Manal Tace to Ni me zanyi da Kati tunda kana kirana,Nifa bana so na gode ban tura miki ba sai kece kina mace Zaki bani kudi karki sake turo min,Manal Tace to Dan Allah naji bazan sake ba Amma ka saka wannan Dana turo,Fuzail yaki yarda Ameer Yana jinsu yace Ni dalla bani na saka Nima naci irin kudin Prince,Fuzail ya kyafta Masa Ido Wai Kar ta ji,Ai Kuwa Manal Tace to bawa Ameer ya saka shi tunda na maka kyauta baka so ka watsa min kasa a Ido ai ya maka kyau Kuma Kar ka sake kirana munyi fada, idanba munyi fada ba ta kashe wayar tana cewa a bar katin ya gaji ya bushe a waya wallahi bazan saka ba.
Dole sai Ameer ne yasa katin Yana dariya Yana tsokanar Fuzail kaga na me tausayi inyee Dan gata har Kati ake sa maka,Fuzail ya share shi kawai.
Zuwa dare 10pm Manal tana dakinta suna waya da Fuzail da gwarancin hausarta tace Wai hadin gwiwa akayi da larabawa aka haife ka? Fuzail shima yace a'a mutum da mace Daya ne Suka haife Ni Zaki ce Wani Hadin gwiwa sai kace wani Business,Dariya Suka Yi gaba Daya tace kayi Hakuri ba nufina mutum da mutum ba Ina nufin Kai ruwa biyu ne Mamanka ko babanka ciki akwai Balarabe? Fuzail yayi Dariya yace ko Daya Haka Kawai Allah ya halicceni,Labarin Shukrah ta dinga bashi,yace kinyi Friend amma Banda fadar sirrinki ki kiyaye wasu matan Basu da hankali karki saurin yarda da mutum,to ai dama bazan saki jiki ba babu ruwana cewar Manal,Yace Good suna ta Hira a Haka suka Yi bacci ba tare da sun shirya ba.
Bayan Kwana biyu Shukrah Bata Zo ba sai a kwana na Uku taci kwalliya ta sake zuwa da Yamma,Manal sanye take da wani tsohon lace dinta pink,ta ja Shukrah Suka shige dakinta,Shukrah ta dinga Jan Manal da Hira har ta Dan saki jiki sannan Tace Manal a rugar da kika Bari kinyi makaranta? Manal Tace a'a Amma na fara iya karatun hausa da Dan wani turancin ma,Shukrah tace to ba damuwa ki tanaji littafi da biro daga yanzu kullum na samu time Zan dinga shigowa Ina Dan koya Miki wasu abubuwan,Manal tace Kai Amma na gode Allah ya bada Lada,Tace Ameen,Shukrah tace akwai wasu Kaya Kala hudu Dana dinka,Amma telan ya min shirme yayi min Dinki karami gaba Daya baifi size dinki ba,telan Nan ya cuceni Zan kawo Miki su ki dinga sawa naga kina da karancin sutura gaki Budurwa ya kamata kema ki canja,Manal ta dinga Murna tana godiya harda Rungume Shukrah sabo da ta tuno Farooq zai zo zance zata Masa kwalliya sosai shi yasa take ta faman murna,Shukrah Tace harda takalmi da mayafi Zan hado Miki,Manal tace wayyo muje ki nuna min gidanku kawancen Nan naki Naga da gaske kikeyi,Shukrah ta dinga dariyar Manal duk ta haukace akan kayan sawa,Shukrah tace gashi an Mana Albashi harda kayan kwalliya Zan siyo Miki,Manal ta Bude Baki harda Hawaye Tace Dole muzo gidanku da Farooq Dina ya Miki godiya ta musamman,Shukrah tace au har saurayi ne dake? Laaaa ai na kusa aure jira nake Yaya da Babanmu su dawo za a kawo kudi,Shukrah Tace mashaallah na tayaki murna Yar uwata yanzu dai kawo min ruwa na sha,Manal ta Mike da sauri ta fice lokacin Shukrah ta sake Bude kayan sawar Manal Wanda ta wanke ta linke,cikin ninkin zanin atamfa ta sawa Manal dubu biyu.
Bayan Shukrah ta tafi Manal tana gyara kayanta kudin suka Fado Amma wannan karon tsofaffin kudi ne tukuf,Manal tsoro ya kamata Nan take ta Kira Fuzail a waya tana kuka,tsoro ne ya kamashi duk ya rude Yana tambayarta lafiya? Tace kaga wani kudin na sake tsinta a cikin kayana dubu biyu,Fuzail ya sauke Ajiyar zuciya tare da furta kin bani tsoro wlh nayi zaton ko Baki da lafiya ne,Allah ne ya Baki karki ji komai ki kashe abinki,Zuciyarki ce me kyau Allah yake dafa Miki,Manal tana shesheka Tace nidai Kar nazo ko Aljani ne yake biyan Sadaki na,sai na ci kudinsa da yawa yace ya aure ni,Dariya ta Kama Fuzail da kyar ya Mata wayo hankalinta ya kwanta.
Hajiya ta kwana da yunwa ta yini Nan fa Ulcer ta shigeta me karfi ta fara ciwon ciki da ciwon baya tare da zafin kirji,kwana tayi tana murkususu,Farida Suma ta cikinsu sukeyi da kyar Tace ki tashi muje wajen Kawu Sani a kaiki asibiti,Hajiya tana rike ciki da kirji tace Manal ce tayi min asiri na sani a samu a kaini wajen Malam Dan Haru shi zai min magani wayyo gadon bayana,Farida Tace Ni wallahi wajen Ruma zanje ta bani dari biyar nazo naci abinci sai dai ki jira tukun tayi ficewarta ta bar Hajiya su Falaqi suna jinya, sai da Rana sosai Farida ta dawo cikinta a cike ko wajen Hajiya Bata kalla ba Ganin Manal ta tafi raka Shukrah sai ta shiga dakin taga irin kayan da Shukrah ta kawowa Manal sababbi na sawa Takaici ya Kama Farida,Wayar Manal ta hango saman katifa,da sauri ta dauki Wayar ta dauki ragowar pure water ta samu ta dura ruwa a ko Ina na kafafen Wayar sai da ta tabbatar ruwa ya ratsa Wayar sannan ta goge jikin Wayar yanda baza a Gane ba ta fice.
Ita Kuma Manal Bayan ta raka Shukrah Chemist taje ta kwatantawa me Chemist irin ciwon da Hajiya ke fama da shi,Ya hado Mata maganin Ulcer,ta tsaya ta siya Mata Maltina da Madara da abincin ci sannan ta siyowa su Falaqi ta dawo gidan har dakin Hajiya ta Kai mata,Wahala da yunwa ta ishi Hajiya ba shiri ta fara Shan kowanne maagani,Cikin Yan mintuna sai ga Hajiya ta warke,ta dauki abinci taci ta sha,Su Falaqi ma Suka koshi,Amma Farida tana zuwa Hajiya ta kalleta tace shegiyar ta karya tsafinta,Maganin Ruwa Gestid ta daga tace wala'allah a Nan ta Sako maganin taga mun ganeta shegiya har da siyo min abinci sabo da Kar na mutu na rataya a wuyanta,Falaqi yace Wai Me Manal tayi muku ne mu muna sonta tana kula da mu,Farida ta zuba Masa rankwashi,Sa'iha tace daga ya Fadi gaskiya,Masatura Tace Ni wallahi ma Nan gaba dakin Manal Zan koma da kwana,Alhaqatu itama Tace Nima Haka mu dinga koya Mata karatu.
Manal Kuwa tunda ta duba Wayarta taga ta dauke duf,gaba Daya komai yaki Yi,batayi Hankalin budewa ta goge ba Kawai ta barta ta kwanta Haka gashi gobe Farooq zaizo zance ta Gama shirinta,shima Fuzail Yana ta Kiran Wayarta ya fada Mata zaizo fa Amma da dare Shuru Wayar Bata shiga ya rasa dalili Haka ya hakura zuwa da safe.
Da safe ma Shuru Wayar Manal,Manal Allah yasa ta haddace number Farooq Kawai Wajen me shagon Kofar gidansu taje tare da karbar Aron waya ta Kira Fuzail,Shuru ba a daga ba,shi Fuzail ba sosai yake daga number da Bai Sani ba,Yana Gaban sarki yaji an dameshi da Kira Tsaki Yaja sannan ya daga,sai yaji Muryar Manal zumbur ya Mike tare da barin wajen memartaba sarki.
Wace Manal?
Masu Sharhi kunfi kowa birgeni,Ina sane da ku akwai special pages kowacce Bata Guda.
AsmaBaffa
AsmaBaffa
[1/1, 10:24 PM] Sis Asma: 🧭🧭MAFARKIN FARIDA🧭🧭
IS DEDICATED TO
DUNIYATA AAMNA FANS GP.
31-35
Official
By
AsmaBaffa
Page naku ne
UMMIE ~ZARIA
MRS OM@R
ASMAU SANI
ABDULMOUMUNIBARIRA
BILYN NAS
UMMU JAFAR
SADIYA GARBA SHESHE
MAMAN AFRAH
MUM KHADY
Malam Rabiu Isa Wanda kowa ya sani da Malam shine cikakken sunan Baban Manal,Asalinsa yankin Nasarawa state ne can cikin wani kauyen Shagari,Su biyar Iyayensu Suka Haifa duka maza a kauyen,Malam Salahu Shine na farko sai Murtala,Malam Nasiru sai Malam Umaru Wanda Allah ya Masa Rasuwa,sai Mas'ud shima Allah ya Masa rasuwa,Saura su Uku Suka rage,kafin Iyayensu su Rasu ba abinda Suka gada sai Harkar malinta,gidansu kaf limaman kauye ne,kowannensu Yana da Almajirai Kamar yanda Suma daga almajiranta Suka Zama Malamai,Suna da Ilimi na Masu karatun Allo hakan yasa tun suna matasa Suka fada Harkar tsubbu,Suka shiga rigar Malamai Suka koma Harkar bokanci tare da kulla alaka da Aljanu Wanda zasu dinga Yi musu hidima Suma suna biya musu bukatunsu,kaf kauyen tsoron gidan lilaman akeyi sabo da an San Basu da Imani ko digo.
Cikin ikon Allah Rabiu ya tashi da almajiransa ya bar Kauye ya koma cikin birni tare da Kama hayar gida shi da yaransa Almajirai daga Nan kasuwar bokanci ta bude a birni har ya mallaki gidan da su Manal ke ciki yanzu,Ana Haka Ya hadu da Hajiya Babar su Farida Zulai wacce asalinta Yar Katsina state ce itama gaba Daya tashi tayi ta tsincesu da danginta da yawa a Nasarawa,Tana da Yayye maza biyu sai sauran Yan Uwa,Iyayenta Kuwa dama basa raye a Hannun Dan uwanta ta girma Kawu Sani.
Tallan goro takeyi a kasuwa Malam ya hadu da ita Suka Fara Soyayya har sukayi aure tare da Yan Uwansa Suma,Malam Baida Imani a lokacin,baya tausayin mace ga wulakanci gashi da son Mata,ko magani Mace tazo Nema Wajensa sai yayi Zina da ita zai Mata magani,sabo da Aljanun da yake Muamula da su sune suke sa shi hakan sannan bukatarsa zata biya.
Ana Haka ya tafi Bauci Karin Ilimin bokancinsa a can ya hadu da Annatu Wato Hadiza Me tallan Fura,fara kyakyawa,tun daga siyen fura yaji shaawarta lokacin Kuma Zulai Wato Hajiya Shuru Taki Haihuwa alamar Bata Haihuwa.
Yana auren Annatu
Shekararta Daya ta Haifi Yazed sankacece fari tas Dake Annatu Fara ce kwal Haka Malam ma Yana da haske daga Nan Kuma Malam soyayya ta kare, sai ya tsani Annatu da jaririnta,ba Wanda ya tsana irin Yazed.
Komai zaiyi sai yayi shawara da aljanunsa sunan Jariri ma su Suka ce a sa Falaqi, ranar suna ya sa Masa Falaqi,Annatu Tace wallahi sai ta canja suna Dan baida ma'ana suka dinga Fada Hajiya tana ji tana
Book Chapters
Chapter 1Chapter 2Chapter 3Chapter 4Chapter 5Chapter 6Chapter 7Chapter 8Chapter 9Chapter 10Chapter 11Chapter 12Chapter 13Chapter 14 Chapter 15Chapter 16Chapter 17Chapter 18Chapter 19Chapter 20Chapter 21Chapter 22Chapter 23Chapter 24Chapter 25Chapter 26Chapter 27Chapter 28Chapter 29Chapter 30Chapter 31Chapter 32Chapter 33Chapter 34Chapter 35Chapter 36Chapter 37Chapter 38Chapter 39Chapter 40Chapter 41Chapter 42Chapter 43Chapter 44Chapter 45Chapter 46Chapter 47Chapter 48Chapter 49Chapter 50Chapter 51Chapter 52