mayen Boko Kawai,sai yangan jaraba yake min Dan yaga Yana da kyau Nima yanzu nabi inda yake da dahir ki tayani Addua Allah yasa ya dawo,Wallahi ya hadu so Gentle gashi kyakyawa,tunda na ganshi naji ya min yasan me yake ba irin Yayanki ba yaro sai kuruciyar masifa,Manal Tace Zan Miki rashin mutunci Wallahi Shukrah Yaya Yazed Din? Ae shi din fa wani girmata yayi abinda sa'a nane,Manal tace kinci abinci,yaushe Zaki zo? Shukrah Tace wannan gidan naku marasa mutunci inzo suna min kallon banza,Manal Tace akwai labari pls idan naje school Zan biyo na daukeki,sannan zamuje gidan Matar Nan na siyo kayan aiki Fuzail akwai kwarzaba dole sai Ana kara gyarawa,Dariya Shukrah ta dinga Yi tace a Ina kuke haduwa kika ce min ke Ummi ta Hana komai,Ina ruwanki nace kizo zanzo na dauke ki Kawai,Okay Allah ya kaimu Hajiya Princess ta Prince Fuzail an Zama babbar yarinya.

Bayan Kwanaki Tanko ya Gama shirinsa shi da Fuzail,Duk wani Kaya an dinkawa Tanko kyauta,tun kafin Ranar Tanko ya koma me tsafta Yana gyara ya siyo sabulunsa na maza me kyau Yana wanka da shi yayi wani fresh,yau Saturday zasu je, wanka ya fesa,yasha wata Shadda Silver me tsada, Sani abokinsa Suka nada Masa rawani na girma,Billen Dake gefen fuskar Tanko kusa da kunnuwansa Yan biyu biyu rawani ya rufe shi,Tanko ya dawo wani kyakyawan matashi Kamar ba shi ba,Takalminsa Half cover na sarauta me kyau da tsada,Wata sabuwar Motar Fuzail Fara ya shiga,Sani shine Driver, mota Daya Kuma na takewa Tanko baya,suna tafiya a hankali cikin nutsuwa,Babu me Gane Tanko sabo da rawani ya canja Masa kamanni duk an rufe inda za a Gane shine,a Kofar gidan Su Farida sukayi parking a Kofar gidan su Farida,Lokacin da Yamma su Falaqi sun dawo daga school da gudu Suka shiga gidan suna cewa motoci sunzo,Hajiya tace sai me Farin jini wallahi maza tashi Jeki shine ma Dama ance da motoci zai zo ba mota ba.

Farida dama ta dau wanka zata fita gantali sai ta fasa ta fito wajen Masu mota ko Bari Bata Yi an Kira ta ba,sai tayi Kamar Unguwa dama zata tafi ta fara tafiya,Sani ne ya fito da sauri dama da sauri yace Farida da Allah Dan tsaya Abokin Yarima Fuzail ne yazo wajenki,tun wajen Daurin auren Fuzail ya ganki yaji Yana sonki Dan Nuhu Tanko ne wani Hamshakin me kudi a Adamawa Kuma Nuhu Tanko Kanin Sarkin Adamawa ne jinin sarauta ne,yanzu Haka Shi wannan Hakimi ne ma Kuma shine Dan Majen Adamawa,yanzu ma Ziyara yazowa sarki shine Yace zaizo wajenki,Farida ji take Kamar tayi ihu sabo da Murna,harda cewa Sani Ina wannan Garan Abokin naka Tanko? Sani yace ke rabu da gara Yana can bakin gate,Muje ga saurayi kinyi na kece raini wallahi karki sake ki tsallake rabonki daga sama,Karki ki Amincewa sunansa Hakimi Iliyasu Nuhu Tanko,Kowa yasan waye Nuhu Tanko a kasar Nan idan Baki sani ba ki tambaya kiji.

Kin San sunayen masu kudin Nan ba Dadi ne da su ba amma idan da kudi sai aji sunan yayi Dadi,Yanzu ki duba Dangote Mene Dangote Dan Allah Ina sunan yake da Dadi Amma dake akwai kudi ya kika ji idan aka ce Dangote? Farida Tace wallahi Dadi Kawai kudin kake hangowa,Yace mu tafi cikin Birnin Kano kiji Isyaka Rabiu,yanzu ce nine Ake ce min Isyaka ya kika ji? Farida Tace sai ka koma Wani Gara,Yace Buhari Dan Allah Ina Dadi Buhari fa,Yanzu kalli talaka ace sunansa Buhari,Ko Dadi babu cewar Farida,Yace Attahiru Bafarawa,Mene Wani Bafarawa,Yanzu Kamar Tanko Ace Bafarawa,Dariya Farida ta fara tace cab Dakiki Tanko,Yace kawo min Sunusi Lamido Sunusi Dan Allah Dake kudi ne ba sai yayi Dadi ba?Amma Talaka ace Sunusi ya kika hango Sunusi me kayan Miya? Mirgayi Ado bayero,yanzu ace Ado nine yanda nake Talaka akace Ado ya zakiji Amma Dake masu kudi ne sai yayi Dadi cakwai abin ya bada citta,to Ga Baban Iliyasu ya kika Ji Nuhu Tanko,Farida Tace idan na tuno Tanko abokinka sai naji ba Dadi Amma tun daga Motocin wannan me kudin naji sunan yayi Onga,Sani yace shi yasa kike birgeni muje Dan Allah Nima ki kankaro min girma ko na rabauta da kyauta me tsoka,Angama cewar Farida Suka karasa.

Sani da sauri ya budewa Tanko Kofa Yana Masa kirari harda durkusawa kasa,Tanko kafa Daya ya zuro waje sai da ya Dade a Haka Ac da Raba suna busowa Farida wacce tana ganin Tanko ya fito bala'in son kudi ya rufe Mata Ido ta haukace,Tanko ya kafa wani shegen bakin glass ka rantse gaske ne kudin Yana kamshi Yana Gadara da Izza kafin ma yayi magana Aiki ne.
Da kyar ya Iya Bude Baki kadan a hankali Kamar ba shine zai magana ba Yana Gadara yace Farida ko? Farida Tace ae tana washe Baki,Tanko Dake duk sunyi Diploma a gidan Sarki suna da Dan iliminsu na Boko Dana addini Maimartaba Bai barsu da Jahilci ba,yace You look Good I like that,Farida Dadi ya kamata,Idan yayi magana sau Daya sai ya kwashe minti Guda Bai sake magana ba,Yace hope Yarona ya Miki bayani? Farida tace ae na Amince ma Ina sonka,Good Very Good cewar Tanko,Yace Ki tambayi Abokina Fuzail idan Baki yarda ba Iliyasu Nuhu Tanko nake by name,Amma You can call me Defender,Nick name Dina ne,duk friends Dina dake Uk,Us,Russia,Turkysh,Armaniya etc da Defender Suka Sanni sabo Kwallon kafa Dana ke bugawa a kasashen ketare, a Nan kasar Kuma wasu suna kirana da T&k ,Kamar yanda Zaki ji su Dangote,Su Bua,su Mashal,Kaura etc muma T&K muke,Sai da ya huta yace kin taba cin Macaroni Dan Company dinmu? Zaki ga Ansa T and K Macaroni,Muna yin su Madara T and K da sauransu,Farida Bata iya Gane Tanko bane sabo da wankan da yasha gashi da tsafta wannan,sannan Ina Tanko Zai samo motoci da Kaya Haka masu tsada,,Ga yanda ya canja Murya ya maida ita ta jikakkun masu kudi.

Yace ba dadewa zanyi ba Ina da aikin Yi akwai wasu da Suka biyo Ni Nan daga Ghana Zan musu Signing a wasu takardu,Sannan by 2am Ina da Meeting a Kandahar Hotel da wasu turawa,Zanyi kokari na samu time na dawo,Ni ba Wasa nazo ba Hajiya Farida,aurenki nake so Kuma a shirye nake bana so na wuce 1mnth ba a daura Mana aure ba,Kinga Maimartaba Sarki Baban Fuzail ya ware min part Guda a gidansa Wai lallai sai an fara ajiye Amaryar a gidansa kafin mu koma Abuja, kin San Yana mugun Respecting Dina,shi a sonsa ma na dawo gidansa da zama gaba daya,Ni Kuma nafi so mu zauna a Abuja yafi .

Farida sabo da Manal Taji haushi sai tace ba komai a fara ajiyeni a gidan Sarkin Mana kafin wani lokaci ko sati biyu idan nayi a can sai mu ware Abuja,Tanko yayi Murmushi irin na zaratan masu kudi da aji Yana karkada kafa yace karki damu za a San yanda za ayi,Zan wuce ya zaro rafar Yan dubu sababbi gal ya mikawa Farida yace ga Wannan kya sa Kati kafin na dawo kiyi Hakuri kunyar kyautar Nan nakeji sabo da tayi kadan, Farida da sauri ta karbe tare da furta ba komai idan ka dawo Next sai ka Kara min,Tanko yaga son kudi ba ko godiya a boye ya jinjina Kai a ransa Yana wayyo kudina shekarata biyar Ina tarasu,Suna Sallama Suka shiga mota Suka tafi,Suka dinga dariya,Tanko Yace ban taba ganin me son kudi irin Farida ba zata ci ubanta wallahi Ina aureta Sai na fanshe kudi na Jerusalemunta da take Adanawa me kudi wallahi a Kansa Zan huce Billahillazi sai yasan taci kudi na,dubu dari fa kut zai ci Uwarsa wajen Nan nata.

Farida tana komawa gida ta dinga ihu da Murna tana Rungume Hajiya tana Wallahi shine yazo,tana haki tana irga kudin Tace yace ma Bai so a wuce wata Daya ba ayi Auren ba,Hajiya Tace to mu ko Nan da sati Daya yace ai yarda zamuyi,Yazed da Malam suna jinsu,Malam yace bazan aura Mata shi ba sai nayi Bincike sannan ma Ni nayiwa Farida Miji akwai Dan gidan abokina da muke kasuwa Daya Yana Lecturing a university Babansa yace Yana so mu hada auren yaranmu shike Nan Farida shi zata aura,ba wannan ba,kika sani ma ko Yan karya ne.
Ai Hajiya tun daga wannan zance na Malam ta fara bala'i da masifa,Farida harda kuka ta daina cin abinci,Suka tafi Wajen Malam Dan Haru,Malam Dan Haru yayi dubansa yace Malam bazai Baki shi ba Haka duk Yan Uwanki baza su goyi bayan wannan auren ba Amma Kuma akwai Alkhairi a ciki ga rabo ciki karku Bari wannan ya wuce ku ayi Aiki akan Malam,Hajiya Tace shine magana a rufe Mana bakin Malam akan auren Nan Kawai ya yarda da Kansa a daura auren ko me za ace Kawai Indai akan auren ne ya Amince,Malam Dan Haru yace ku bani kwana biyu yayi yawa,sannan Shima Sunansa Iliyasu Saurayin Malam ayi Masa asirin da zai gigice a kaunar Farida,ayi Masa ya haukace a kanta yanda bazai iya fasa Aurenta ba,yace an Gama Hajiya,Haka Suka dawo da farin ciki,Da yawa wasu da sunga saurayi Dan anga abin hanunsa Iyaye sai a fada malamai Wai a rike shi Kar ya gudu ayi sauri a aure shi sabo da anga Yana da rufin asiri,ko ayi duba idan ance da Alkhairi sai Kawai a fara Masa asiri Kan lallai sai an aure shi,idan mijinta ne ko da asiri ko babu sai ya aureta Amma sai a manta da Allah sai anyi aure Abu ya kwabe azo Ana wayyo wayyo.

Bangaren Fuzail Kuwa Manal sai bala'i take Masa wallahi ba a Isa anyiwa Yar uwata karya ba an hada ta da Dan aiki kazami irin Tanko ba, wallahi bazai yuwu ba,Ba ruwanka da Yan Uwana yawwa Yan uwanka daban Nawa daban,kamar yanda kake son naka Haka nake son Nawa,wannan ai yaudara ce,ace ayiwa mutum karya a aure shi Kuma an San mutum bana kirki bane,koma mene Naka har abada naka ne Kuma ranar naka sai naka,kaje kaji da Yan Uwanka inji da Nawa Kawai sai ka daurewa karya Gindi na zaci da Wasa kake shine ka Basu Aron mota ma kashe musu kudi aje a yaudarar min Yar Uwa,ai kowa Yana son Hutu Kawai Dan tana son gidan Hutu sai a tsaneta,Fuzail Yana Zaune a gefen Bed Ya rike Haba Yana kallon Manal Kawai ta tsaya tana ta zazzaga Masa bala'i,Fuzail yace Wai Baby ba a gabanki akayi komai ba,to ai Ni nayi tunanin fada Masa kawai kayi Dan yaji Dadi, Alright nayi zaton gyara za ayi na Gane gaskiya naji Bai Dace ba common Beb ki kwantar da hankalinki ba hannuna ciki Bari na Kira Tanko a fasa,Yawwa Kira shi, a waya Fuzail ya Kira Tanko Yace Tanko shawara Zan baka ka hakura da Farida,tunda kaga ba sonka take ba,Bai Dace ayi Mata karya ba tazo taga ba Haka ba,Allah sai ya tuhume mu,karya ba kyau musamman a aure shima zalunci ne,Ni dai duk tallafi na Dana bada na janye,Kaya Dana siya maka kaje na bar maka kyauta mota da komai na Hana daga yau Kar a sake Muyi Mata Addua Allah ya shiryeta.

Tanko da fara'a yace an Gama Inshaallah ya wuce da gaske har ransa ya hakura,Manal Tace ko wani Abu ta maka ka yafe Mata Dan Allah karka cutar da ita ta haka,Tanko yaji Nasiha yace Inshaallah baza a Kuma ba Allah ya yafe Mana gaba daya.
Bayan Kwana uku Asiri yayi aiki Iliyasu Tanko ya sake haukacewa akan Farida ji yayi bazai iya hakura da ita ba,ji yayi Yana mugun kaunarta Kamar zai mutu,yace bazai iya kyaleta ba sai ya auri Farida ko ta Yaya,Karyarsa zai shirya Kawai ya aureta bazai fasa ba,zaiyi komai a boye ba tare da su Manal sun sani ba, Malam Kuwa Haka Kawai yaji zuciyarsa tana Masa fada lallai ya hakura ya bawa Farida Wanda take so shine Kawai dai dai,da Kansa ya Kira Hajiya da Farida yace ya hakura duk Wanda Farida take so zai Bata ko waye shi,Suka dinga Murna abinsu harda tafawa.
Shi Kuwa Tanko salon karyar Suka canja shi da Abokinsa Sani wani sabon salo zasu Zowa da Farida shi.







😂😂😂

Masu Sharhi Ina godiya

Aci gaba pls sabo da naji dadin Typing





AsmaBaffa
[1/1, 10:25 PM] Sis Asma: 🧭🧭MAFARKIN FARIDA🧭🧭





DEDICATED TO
DUNIYATA AAMNA FANS GP





71-75





Official



By
AsmaBaffa







Page naku ne

Maman Ra'is
Deejah
Oumm Affan
Amina Baba
Bilkisu Aminu Ibrahim
Furayrah Garba Muhammad
Hauwa Mahmood
Mk Hussein
Maman Abul Abbas
Mom Affan
Sadiya.







Bayan Kwana Uku Tanko ya sa Sabon Layi Yana Kiran Farida a shine dai Iliyasu me kudi,Farida Ta Gama yarda ta saki jiki a waya Suka Fara zuba Soyayya da Tanko,Kullum raba dare sukeyi suna Hirar soyayya,Hajiya zuwan saurayi Daya duk sun haukace,Farida damuwa tayi akan lallai sai Iliyasu Nuhu Tanko yazo ko zata samu ya Kara Mata wata kyautar,Tanko kuma ba kayan karya haka mota babu,Duk Damunsa da Farida take Yi a waya yaki zuwa,Hajiya tace ki lallaba yazo kin San Harkar manya Basu da time a Haka Zaki wanke shi har mu samu Wanda zamu siyi kayan kitchen na kece raini,ai yace tsinke baza mu siya ba kin San fa manya,ko fili ai sai a siya Miki ko a Kauye ne me Araha Kinga mun karu tun kafin ayi Auren,Farida tace Hajiya wannan fa ba sai munyi gaggawa ba a nutse zamu ci kudinmu Kamar yanda Manal take can cikin Daula.

Bayan Kwanaki Tanko Yana waya da Farida a bakin gate Shehu Abokin aikinsu Bai Sani ba yazo wajen Yana Tanko ga Yarima Nan yazo bude Masa Gate,Tsaf Farida Taji a kunnenta,kanta ne ya daure,a ranta ta shiga nanata Kalmar Tanko Bude Gate ga Yarima Nan, tunani ta zurfafa lokacin da Tanko yazo da Sani,Tsoro ne ya shigi Farida dama tunda taji Muryar Tanko ta rasa a Ina ta taba Jin me muryar sabo da tayiwa Tanko Farin sani shi yasa duk da ya canja Murya take ji Kamar ta sanshi,Fuskewa Farida tayi tace ita lallai Tana so Iliyasu Yazo zance so take ta ganshi,Tanko Yace gaskiya Ni bana son zuwa Unguwarku ta talakawa gaba Daya a dinga kallon mutum Ni gaskiya basaja zanyi bazan Iya zuwa da motoci na Nan ba,Farida a ranta Tace zaka ci Ubanka a fada maka Ni irin Manal ce Yar Kauye wacce ake kifewa.

Tanko cikin Shaddojinsa masu tsada ya zabo Wata grey ya dau wanka yau shi kadai ya tafi kowa yaga Tanko yasan yayi kyau,Napep ya shigo hannunsa rike da Handkerchief wata Yar Budurwa ya Iske a Napep din Fara tsaleliyar gaske sai dai da gani talakawa ne,Alawar Madara ta dakko a wani Farin bokiti Tanko ya kalleta ya sake kallonta yace Kaiiiii Allah Mai baiwa,Wato ko Ango ne a wajen Bikin nasa zai ga wacce tafi Amaryar tasa,Ke ya sunanki? Yarinyar da Bata fi Manal ba ta washe Baki jerarrun hakoranta Suka bayyana tace Sunana Islaha,Iyye Wannan sunan ya Dace Dake Islaha me Alawar Madara,Tanko Nan take jikinsa Yana rawa yace juye min ita a Leda na siyeta gaba daya,Islaha ta Bude Baki yace ko Dan kyanki ai a siya,Islaha tace ai ba leda,Tanko Yace Siyen Zuma Zan Mata na siyeta har Botikin,Islaha ta kalli Tanko ita sai taji Tanko ya birgeta,Dai dai din wani a karkacen wani.

Islaha ta bashi du Ya biya kudi gaba Daya,Tace Kai me kudi ne gaskiya,Tanko Yace Allah sarki Mission na fito Yi wallahi ba karya wani Aiki zanyi Amma da kike ganina Me Gadi ne a gidan Sarki,Islaha murna ta kamata tace wayyo Dan Allah a gidan Sarki kake Aiki?Tanko Yace Uhm Bayi ba mu a bauta Muka taso,Islaha Tace cab wallahi ai Kai ba bawa bane,ai yanzu an daina bauta tun zamanin Jahiliyya aka Yi wannan,Ya sunanka Kai? Tanko Yace Iliyas harda gyara suna Iliyas Ana ce min Tanko,Wannan Kaka ta cuceka wallahi ka canja suna gaka kyakyawa Ana ce ma Tanko Kawai ka koma tk,Tanko Yace No T&K ko? Islaha tace da yafi kasan Ni Ina son Inga mutum Dan wanka,sai ka birgeni,Tanko Yace lallai darajata ta karu,Nan take yace kina da waya? Islaha Tace Rannan ta Fadi,Tanko ya karkace ya zaro wata karamar wayarsa Tekno Yar Dubu Hudu ya zare Layinsa yace gashi Islaha Sarkin kyau na Baki kyautarta ki sa layinki,Islaha tace bazan karba ba Haka Kawai sai kace Yar Iska,Nifa Malam ba karuwa bace Ni,Baki Tanko Ya bude yace nayi Miki kala da Karuwiii Ni?Dariya Islaha tayi Tace Karuwii wai? Tanko ya nace Sai da Islaha ta karbi waya,yace Kai Me Napep bani aron Biro da takarda,Me Napep ya bashi ya rubutawa Islaha Number dinsa sannan ya sauka dauke da Botikin Alawar madararsa.

A ransa Allah Allah yake yaga Farida ji yake kamar Ana ruru Masa wutar kaunarta a zuciyarsa duk ya rasa dalili sai tunaninta yake ko wanne time,Haka ya karasa Kofar gidansu tare da Bawa Me kanti Ajiyar Alawar Madararsa,Farida ko kwalliya Bata Yi ba ta fito fit sanye da Hijab me Hannu,tana zuwa Tace Algungumi cire Takunkumin face mask da ka saka da wannan munafukin rawanin daga nada Wato Ashe Tanko ne ai Allah ya Toni asirinka,Tanko Ga Kaunar Farida ta Masa yawa gashi an kure shi,Haka ya tsaya sololo Farida ta Gama ci Masa mutunci sannan Tace bani ba Kai,Malam ne ya dawo yaji irin maganganun da Farida take watsawa Tanko,Malam yace ai Baki Isa ba Tanko sai kin aure shi ba abinda zai hanani daura muku Aure ko Zaki mutu Ni Iliyasu Ina kaunarsa yayi min,Malam ya kalli Tanko Yace ka turo Magabatanka,Tanko Yana ta murna da godiya ya kalli Farida ya zaro Mata harshe Wai gwalo sai ya tsaya a Gaban Malam yace Ni talaka ne har ga Allah Tanko ne me aikin su Fuzail,Malam ya washe Baki yace Ni kayi min Tanko karka damu ka turo manyanka.

Tanko Alawar Madarar ya karbo ya
Showing 93001 words to 96000 words out of 153479 words