Iyaye bazan ga laifinki ba wannan nasan ta Kai ayi yanke ya nke akanta.
Dariya sukayi gaba Daya har Uche yace Beloti I will Miss you,Harara Belloti ya galla Masa,Farida ta rike Dan Bellotinta Tace let's go and eat something,Belloti ya Mata kallon kauna tare da Furta ai yau final kafin muje Kauye fita zamuyi Joint mu rakarkashe dadinmu kafin mu sadu da Gabza a Kauye,Ran Farida ya jagule tunawa da tayi Kauye zasu tafi kamar zata Yi kuka,Belloti ya kalleta Yana Bata Rai sai Kuwa ta washe bakin dole ba shiri sabo da Kar Belloti Yaji haushinta,Son Belloti da Tsoronsa ya Gama ratsa jininta.
Da Yamma likis su Belloti Suka dauki wankan sugar Farida sabuwar atamfa ta saka ta lefe dinkin Riga da skert tayi mugun kyau Pink and blue,Farida hips din Nan gashi nan Kamar me,ta zuba kyau ta kafa daurinta,Belloti harda Saka sabuwar shaddarsa wata Blue ya dinka su Kala hudu Bai taba sakawa ba Kawai ya ajiye masu kyau,Dinkin matasa,Belloti akwai Kyawun sura duk kayan da yasa kyau yake masa,Sumar Nan taci kudi Farida tana taje Masa tace Kar a aske min Sumar Nan Ina sonta da yawa,Belloti Yana waya da Babarsa Yana cewa gobe zasu Zo a gyara musu dakinsa Yana Jin Me Farida take furtawa yace an Gama,Tace da gemun ma da sajen duk a bar min shi,Belloti Yana wani daura agogo a dole Babban yaro Yana Mata magana da Ido Wai yaji za ayi hakan,Yana Gama Wayar ya dauki wayarsa da key din room din tare da rike Hannun Farida Suka fita ya rufe dakin Farida takalminta me tsini da hand bag duka pink,ta Sha Daurin Zahra Buhari,Farida tayi kyau sosai,Belloti yace kullum kyau kike karawa Farcy Beb,Farida Sarkin Fari tayi wani walwal da idanuwa tare da Furta kullum fa Fresh cucumber nake ci ba Dole na canja ba,Belloti yace hakane,Napep Suka shiga Farida tana mamakin kanta Wai ita me son mota yau itace ta Kare a Miji ko Keke baida shi,Kanta ta bawa laifi tasan ita ta jawowa kanta amma shege So Farida Son Belloti yasa Haka take gani yanzu gwara Haka akan a Bata duniya da abinda take ciki gwara a barta da Bellotinta,Hajiya ce ta Kira Farida suka gaisa,Farida tace Hajiya ya gida?
Ke dai Bari gida Yana wajen Masu shi,Ni da nake Dan rabawa Ina Naga wani gida, kin ganni matar yayan ma abinci sai taga Dama take bani Farida,ga aikin gidan Nan kaf yanzu Ni nakeyinsa sai kace yarinya,da girmana ai Ko darajar girmana Yaya ya kalleni ya tausaya min sai ma zagina da masifa da yakeyi Wai laifina nane,Dangina yanzu bani da Iko na shiga cikinsu sai a dinga jefar min da babaken maganganu Ni wannan zaman ya isheni nasan Nan gaba ma Yayana Korata zaiyi daga gidansa....Hajiya ta karasa da kuka Tace Farida yanzu naira Hamsim gagarata takeyi ga yunwa ba a bani abinci akan lokaci duk na rame,Yan Yaran ma da suke zuwa wajena Ina kallonsu Ina Jin Dadi Malam ya hanasu zuwa,Yau ma Farida tun safe ba abinda na samu na saka a cikina,Yaya da matarsa sunyi Tafiyarsu Lagos Wai sai Nan da sati biyu zasu dawo Kuma wallahi sisi bani da shi,ko kwallon shinkafa Basu bar min ba,tasa key ta kulle store dinta Wai idan Ina da kudi na siyo da kaina ga kitchen Nan na dafa,Kuma Yayan ya biye mata Suka kwashe har yaransu Suka tafi abinsu,Ina Jin Farida yunwa ce ajali na,kowa na tambaya a dangi babu me taimaka min sai suce ba ruwansu Wai Ni na kashe aure na,yanzu bani da kowa Farida Sai ku yarana tunda mijinki Yana da Dan arziki Kuma kince Kuna zamanku lafiya sai abinda kika ce Dan Allah Farida ki turo min ko dubu biyu ce a accnt Dina na samu naci wani Abu,Allah ya kyauta kiyi Hakuri Hajiya Inshaallah Zan San yanda za ayi,Hajiya da sauri ta dinga godiya.
Bayan Farida ta kashe wayar suna Napep da Belloti yaga ta fada tunani da damuwa sosai a fuskarta tana Neman yin kuka sabo da Farida Bata da ko kwandala Sadakinta ma Fridge aka siya Mata da shi anyi zaton za a Mata jere,Kuma kayan gaba Daya suna gidan Yayan Hajiya,Kiran Hajiya ta sake yi ta daga tare da cewa Farida kin tura? Farida tace Hajiya Ina kayan kitchen da muka Dan siya wasu abubuwan ki dauki wani abin me tsada ki siyar da su kiyi amfani da kudin,Hajiya Tace tab yo ai tunda na dauki Blender a ciki na siyar Yaya ya boye kayan a wani Empty house yasa key ya garkame Kuma yace idan na taba wallahi sai ya ci mutunci na,Farida Kawai ki bani ko dari biyar ce ma ki turo min abin kunya ne na Bude sirrina naje na tambayi wani kudi ke kin San me Mukayi wallahi Dariya za a min.
Okay Farida ta furta ta sake kashe waya ranta a jagule Idonta ya ciko da kwalla zata Yi kuka,Belloti ya fahimci matsalar kudi ce,yace Lafiya Baby? Farida tana goge hawayen da ya zubo Mata tare da furta ba komai,Ya Zaki ce ba komai ki fada min idan Bai fi karfi na ba Zan Miki,Farida Taki fada sabo da boye sirrinta Su Farida ba a son Raini,Belloti ya matsa sai ya ji dole ta hakura Tace Hajiya ce take son Kudi ko 1k ne Wai amfani da zata Yi da shi Bata ce yunwa bace Kar ya Raina su,Belloti yace Akan wannan kike Kuka har baza ki fada min ba,ke Nifa bana son irin wannan, waye Bai San rayuwa ba yanzu,kune komai sai kunyi karya ta Yan Birni da kin fada min da tuni ba a tura Mata ba Zan rasa kudin Bata ne kika ji? To ko abokina na sa yanzu zai tura Mata bani accnt number.
Farida Lokacin farin ciki ya kamata taji wani sabon son Belloti ya kamata Haka ta bashi account Number Nan take yayiwa Hajiya transfer na 5k, yace ki tambayeta idan ta gani sai ga Kiran Hajiya Tace naga 5k da accnt din mijinki 5k Bello Muhammad Tukur ko? Farida Tace ae,Hajiya godiya ta shiga zubawa harda sa Albarka Tace bani shi nayi Masa godiya,Farida tace My Hero ga Hajiya zata maka godiya Belloti yace Akan 5k Mene 5k gaskiya bazan iya amsa ba kunya ma nake ji 5k kacal a kanta za a gode min Fafur Belloti yaki karbar waya Wai kunyar Kansa yake Yi ma a hakan.
Farida a ranta tace Allah me iko a baya 20k ma mutum ya bamu Bai Isa mu gode Masa ba bare 5k wa zai saurare shi ma duk talaucin mu,Wani Shawarma Joint Suka Shiga kida na tashi iri iri ya musu order na Shawarma da fruits salat Sai ice cream,Belloti harda Bawa Farida a Baki sai da Suka ci suka koshi suna hirarsu cike da nishadi da kaunar juna.
Bayan Nan Shopping Mall ya kaita yace to karki karar Mana da Dan kudin tafiyar mu kauye yanzu Abu me ma'ana zamu siya,Wanne Body Lotion ne ya karbe ki? So nake a samu me kyau kiyi haske me kyau Normal bana son wannan hasken dau da kikayi kafin aurenki, gwara kiyi me kyau,Farida tace lokacin fa wata Allura ake min,Yace Kar a sake ba a gidana ba,Dan cream din ma me kyau Bai Isa ba sai anyi wani haukar haske tunda Allah yayo mutum Baki Ina laifi ma da Allah ya Bawa bature ikon Kirkiro body Cream a shafa ayi kyau duk haka ba a gode ba sai an Zama baturiya, siyi Cream me kyau me Dan tsada Wanda zai gyara skin ko hasken ne ayi me kyau na hankali na wayewa,Farida tace ai tunda nayi Allurar sau biyu na daina gashi duk na fara dishewa,Belloti yace yawwa kinfi kyau haka daga Cream na dubu Uku zuwa hudu Zan iya siya Miki dai dai karfi na.
Sai da suka Gama shawarwarin me zasu siya na tafiya Kauye Wanda ko sunje bazai Kare da wuri ba zasu Dade sannan Suka shiga ciki,Farida ya Siya Mata body Lotion Kalar data zaba Dan 4k Guda biyu,sai na face dinsa,su shampoo Kuwa duk ya Siya Mata duk da cewa tana da wasu a lefe,Turare zai siya Tace Ina da Humra fa da yawa ga Kuma na lefe it's okay,Belloti shima ya siyawa kansa abinda zai iya,Har su kayan shayi cornflakes sai da ya Siya musu Kar ma suje Kauye a samu matsala tunda yasan Farida bata Saba da cima ba ta kauye ba,Sai da suka Gama suka dawo wurin 12am a daren suka shirya komai nasu har tsarabar da zasu Kai sun siya,Belloti gaba Daya Dan abinda ya Tara ya kwashe harda siyawa Iyayensa Buhun shinkafa,taliya,macaroni,Mai,su Indomie da su sabulan wanka da wanki.
Washe gari 8am ya Kira wani Me Golf da ya dauka Drop zai kaisu har kauyen suka shirya kayansu tsaf sannan Belloti ya shiga bedroom din Uche ya bashi Hannu Suka tafa yace Zan wuce,Uche sai Kuma yaji ba Dadi gaba Daya yasan Bai kyauta ba,Nan take yace na hakura Bello ku zauna,mu zauna tare I'm so sorry for what I have done to you,Belloti yayi murmushi yace ai ba Haushinka naji ba Kawai Allah yayi tashi na ne ka barni na tafi Zan dawo verysoon Zan na zuwa Muna gaisawa,Uche Yace Alright Be a good Man ya ciro 10k ya bawa Farida yace ajiya gashi asha ruwa,Farida ta karba tayi godiya ta ci gayu cikin lace dinta peach doguwar Riga me kwala dinkin manyan Mata,Shi Kuwa Belloti wata Shadda ya saka ruwan toka an Masa gyaran gashi yayi kyau sosai da gani kasan ya waye ba Kalar Kauye bane.
Har Mota Uche ya rakasu suka tafi suna dagawa juna Hannu,Belloti da Amaryar sa Ana bayan Mota,tafiya tayi tafiya Farida ta kwantar da kanta a kafadar Belloti tana ta bacci, sai da Suka shiga garin Bauchi Belloti ya fita ya siyo musu wani Naman rago gasashe da ruwa da yogurt har driver din nasa daban,Suka ci suka koshi a motar,a Haka har suka dauki Hanyar rugar me shegen nisa Kamar ba a duniya suke ba,Farida ta kalli Belloti Tace sannunku kunyi kokari kowa da inda Allah ya ajiye shi,Murmushi yayi kawai har Suka karasa garin Farida taga gidajen Basu fi Guda Hamsim ba,Tace Lallai Manal ta waye da wuri idan Haka ne to Kuwa ba karamar basira Allah ya Mata ba,kaima Haka my Husband,kalli ikon Allah Wai kana Nan garin a wannan nisan amma har Allah ya kawoka garinmu ka aure Ni,lallai Mijin Aure daban yake,wanda baka taba zato ba Ashe duk wannan haukar da nake kana Nan kauyen ma tuni,da ace a lokacin za a fada min bazan yarda ba Amma gashi ya faru,Belloti yayi Dariyarsa me kyau abinka da Dan Fulani me kyau ga Hanci,Yace Allah kenan ai Allah ba abin Wasa bane abinda ko a mafarki baka zata ba shike faruwa,Farida Tace ko a mafarkina na jaraba ban taba ganinka ba ko me Kama da kai,Suna karasawa kusa da gidan su Belloti Suka hango wasu lafiyayyun motoci Guda biyu da securities tare da Dogarai,Belloti yace ga kanwarki Nan Maybe Manal,Wannan da Alama da mijinta suka zo,Farida gabanta ya Fadi,Belloti yace ki daina damun kanki kina daukarwa kanki karya Farcy,ba a daka ta Dan Adam a rayuwa,idan ka biyewa Dan Adam to a rayuwa ba abinda zaka iya yi,Ki saki ranki,Farida tayi murmushi tare da Furta ba damuwa wancen ne kenan gidan Annatu? Yace yes shine Mana,kannen Belloti Yan Mata da maza ne Suka fito suna ihun murna da oyoyo,Nan take Belloti yasa suka kwashe kayan kaf tare da shigewa cikin gidan da su,gidan su Belloti na Bulon Siminti ne,su biyu ne gida na bulon Siminti kaf garin,Bayan Belloti ya sallami Me Golf ya tafi,Farida Tace to Manal dinfa ya kamata na ganta Kar na tafi Bamu hadu ba,Farida so take Kawai taga wani na gidansu ko zata ji sanyi a ranta,Yan kauyen sai kallonta sukeyi sunga Yar gayu,Ganin ta damu yace Kira Manal din a waya kiji ko da ita aka zo,Farida ta Kira Manal Wayar Bata shiga ba sabo da karancin network,Belloti yace Naga kin damu Jeki gidan Ina jiranki a gidanmu sai kin dawo,Farida da shagwaba Tace Kai da kake Dan gari muje tare,Haka Suka jera suka tafi gidan Annatu.
Farida ce ta gyara handbag dinta tare da shiga gidan da sallama Belloti yace Ina jiranki a waje,Sallama tayi a gidan tunda taga wani shegen chogen takalmi me tsada tasan Manal ce ma,shiga tayi kusa da dakin,can ciki taji dariyar Manal suna magana ko da waye oho sai lokacin ta tuna taga takalman Fuzail masu tsada,ga kamshinsa ya cika ko ina na gidan,Gadon Annatu Me Spring ne yake Lilo Yana Kara kiiii...kiii....Manal tana ta dariya tana cewa prince da zafi fa kaji yanda ka sake Ni a saman bed na fada ka manta da Babynka,Farida ce da masifa tace Wai su waye ne suke dariye dariye Ana Sallama baza su amsa ba sabo da soyayya Haba,Manal tana daga ciki Tace ya naji kamar Aunty Farida kaji muryar prince,Shigo cewar Fuzail Yana Rufewa Manal cikinta da rigarta da ya janye Yana Mata Chakulkuli,Farida ta shiga,Manal ta Mike tsaye Tace laaaaa Aunty Farida yaushe kika Zo? Me ya kawoki kauyen Nan? Farida ta kalli Manal Tace uhm su Manal Wato dai an Zama mayyar miji Allah ya shiryeki yanzu har bedroom din Annatu? Tana Ina? Bata Nan sai anjima zata dawo ita Muke jira Bamu Dade da zuwa ba da Yamma zamu tafi,Farida ta Furta Uhm I can see,to kin manta garin Nan surukai na suke? Manal tace na tuna fa kinzo gaisar da su,yaushe zaku koma? Zanzo gidanki? Farida Tace to munafuka ba yanzu Zan koma gida ba sai na Saba da surukai na sunji dumi na,Dariya ma ta bawa Fuzail,Farida tace Kanina ya gida ya aiki? Bata taba gaisar da shi ba sai yau,Wai kaninta ta ma,Fuzail yace Aunty Lafiya nake,Farida Tace na gani ai,ka daina biyewa Yarinyar Nan wlh tasa kana ta rashin ta Ido a gadon Suruka tam,Fuzail dai Bai ce komai ba,Farida tace Manal Zan tafi gidanmu Zan na zuwa ai Muna gaisawa da Annatu kafin mu tafi,Manal tace hakan yayi zanzo Nima muyi Sallama, Alright Farida ta juya zata tafi,Manal Tace Aunty kinyi kyau wallahi sai kiba kike Yi, to ya na iya komai zam zam ai ko ya kika ce? ,Manal ta Kama Dariya tace Aunty kina Jin Dadi,zanci uwarki nasan Gulmar da kike ta Yi kizo mu sa labile tunda kin matsu kiji in ba munafunci ba mace da mijinta kin damu da matar wani kije kema a Baki Mana ai gaki gashi Nan,Tashi Manal tayi ta biyo Farida har tsakar gida tana karewa Farida kallo tun daga sama har kasa tace Aunty ana harka...harka...harka.....Farida tayi Dariya tace zanyi maganinki ne kin San Halina wallahi kika sake agaban mijinki Zan Baki kunya,Zan fadi kalmar fitsara a gabansa kinga Zaki ji kunya yayarki tayi Maganar banza Gaban suruki kin San Halina Allah idan kina min irin wannan abin sai na Baki kunya,Manal Tace ance Miki kunyarsa nake ji yanzu Ni,Yaya Aunty Hope dai Bellotin akwai Aiki? Hand bag Farida ta kwadawa Manal suna dariya Farida tace Cucumber ai tayi ta fice abinta,Manal tana ta dariya Wai Cucumber.
Dawowa tayi wajen Fuzail Tace idan Annatu baza ta dawo ba mu tafi Dan Allah,akan me? Sai mu koma cikin garin Bauchi mu kwana a hotel gobe sai mu dawo, Fuzail yace sabo da me? Manal ta kwanta a jikinsa da shagwaba tace cucumber zaka bani,Fuzail yayi Dariya yace lallai Yarinyar nan to Ni tawa ba Cucumber bace Cassava ce,Manal ta fara Dariya harda rike ciki,yace karki kashe min yarona da dariyar masifarki,Jin sallamar Annatu sukayi da sauri Manal ta koma kasa saman Tabarma ta bar Fuzail a gefen bed sabo da daki Daya ne irin dakin kauye,Sannu da zuwa Annatu,Yawwa Ashe Kuna ta jirana cewar Annatu tana shigowa sai kunyar Surukinta take ji,a kasa ya zube tare da kwasar gaisuwa ta amsa da fara'a Nan take ta hada musu Fura lafiyayya Anna Ina su Khairan ne?Suna gidan Kakarsu tun jiya,Yaran Ni ban San ya za a saka su a school ba wannan ta kauyen ta Gomnati ce,ko Birni zamu koma da ku? Annatu ta Bude Baki tare da furta Allah ya kiyaye kin San dai ba zaman kaina nake ba,Mijin Annatu ne ya dawo daga Gona ya Iske Ana zancen yace na tafi na barwar wa duk tarin shanu na da sauran kadaronina,Fuzail ne yace to shike Nan Zan samu ayi sabon gidan a Nan din a canja ginin gida,Mijin Annatu ya washe Baki Yana godiya,Annatu ta kalle shi kawai ta tuna Sanda yake dukan Manal Bata Masa komai ba,tace Allah me iko yau Albarkacin Manal zaka ci Kuma,ba irin duka da zagin da baka Mata ba iya yaranka sune mutane to gashi yau arzikin Manal zaka fara ci Wanda ma ba a San iyakacinsa ba sai Allah,Mijin Annatu jikinsa yayi sanyi yace Manal ki yafe min,Kaga rayuwa shi yasa akace da na kowa ne baka San me Jin kanka ba Akan Mahaifiyarki na samu Yara ki yafe min.
Baki Annatu ta tabe Masa tace da Bata yafe ba ai da baza ta bar mijinta ya taimaka maka ba,Manal tace Saudiya Annatu Inshaallah Zaku Yi aikin Hajji Yarima ya biya,Murna Kan murna suka dinga Murna,Manal tafi so su Annatu su koma birni sabo da karatun su Khairan amma ubansu bazai yarda ba sai dai Nan gaba idan sun girma sai suyi karatun a wajenta.
Fuzail yace Gama mu wuce Ummi Inshaallah kafin ta koma Brazil zata Zo ta gaisar da ke Annatu cewar Fuzail,Annatu tana mamaki tace Allah ya kaimu,Ya Riga Manal fita ya barsu suna zance na sirri irin tsakanin Uwa da Yarta,Annatu Tace Ina Dan Uwan naki? Manal tace Yaya Yazed tab ya fada Miki? Baki ga gidan da Malam yake
Showing 114001 words to 117000 words out of 153479 words
Dariya sukayi gaba Daya har Uche yace Beloti I will Miss you,Harara Belloti ya galla Masa,Farida ta rike Dan Bellotinta Tace let's go and eat something,Belloti ya Mata kallon kauna tare da Furta ai yau final kafin muje Kauye fita zamuyi Joint mu rakarkashe dadinmu kafin mu sadu da Gabza a Kauye,Ran Farida ya jagule tunawa da tayi Kauye zasu tafi kamar zata Yi kuka,Belloti ya kalleta Yana Bata Rai sai Kuwa ta washe bakin dole ba shiri sabo da Kar Belloti Yaji haushinta,Son Belloti da Tsoronsa ya Gama ratsa jininta.
Da Yamma likis su Belloti Suka dauki wankan sugar Farida sabuwar atamfa ta saka ta lefe dinkin Riga da skert tayi mugun kyau Pink and blue,Farida hips din Nan gashi nan Kamar me,ta zuba kyau ta kafa daurinta,Belloti harda Saka sabuwar shaddarsa wata Blue ya dinka su Kala hudu Bai taba sakawa ba Kawai ya ajiye masu kyau,Dinkin matasa,Belloti akwai Kyawun sura duk kayan da yasa kyau yake masa,Sumar Nan taci kudi Farida tana taje Masa tace Kar a aske min Sumar Nan Ina sonta da yawa,Belloti Yana waya da Babarsa Yana cewa gobe zasu Zo a gyara musu dakinsa Yana Jin Me Farida take furtawa yace an Gama,Tace da gemun ma da sajen duk a bar min shi,Belloti Yana wani daura agogo a dole Babban yaro Yana Mata magana da Ido Wai yaji za ayi hakan,Yana Gama Wayar ya dauki wayarsa da key din room din tare da rike Hannun Farida Suka fita ya rufe dakin Farida takalminta me tsini da hand bag duka pink,ta Sha Daurin Zahra Buhari,Farida tayi kyau sosai,Belloti yace kullum kyau kike karawa Farcy Beb,Farida Sarkin Fari tayi wani walwal da idanuwa tare da Furta kullum fa Fresh cucumber nake ci ba Dole na canja ba,Belloti yace hakane,Napep Suka shiga Farida tana mamakin kanta Wai ita me son mota yau itace ta Kare a Miji ko Keke baida shi,Kanta ta bawa laifi tasan ita ta jawowa kanta amma shege So Farida Son Belloti yasa Haka take gani yanzu gwara Haka akan a Bata duniya da abinda take ciki gwara a barta da Bellotinta,Hajiya ce ta Kira Farida suka gaisa,Farida tace Hajiya ya gida?
Ke dai Bari gida Yana wajen Masu shi,Ni da nake Dan rabawa Ina Naga wani gida, kin ganni matar yayan ma abinci sai taga Dama take bani Farida,ga aikin gidan Nan kaf yanzu Ni nakeyinsa sai kace yarinya,da girmana ai Ko darajar girmana Yaya ya kalleni ya tausaya min sai ma zagina da masifa da yakeyi Wai laifina nane,Dangina yanzu bani da Iko na shiga cikinsu sai a dinga jefar min da babaken maganganu Ni wannan zaman ya isheni nasan Nan gaba ma Yayana Korata zaiyi daga gidansa....Hajiya ta karasa da kuka Tace Farida yanzu naira Hamsim gagarata takeyi ga yunwa ba a bani abinci akan lokaci duk na rame,Yan Yaran ma da suke zuwa wajena Ina kallonsu Ina Jin Dadi Malam ya hanasu zuwa,Yau ma Farida tun safe ba abinda na samu na saka a cikina,Yaya da matarsa sunyi Tafiyarsu Lagos Wai sai Nan da sati biyu zasu dawo Kuma wallahi sisi bani da shi,ko kwallon shinkafa Basu bar min ba,tasa key ta kulle store dinta Wai idan Ina da kudi na siyo da kaina ga kitchen Nan na dafa,Kuma Yayan ya biye mata Suka kwashe har yaransu Suka tafi abinsu,Ina Jin Farida yunwa ce ajali na,kowa na tambaya a dangi babu me taimaka min sai suce ba ruwansu Wai Ni na kashe aure na,yanzu bani da kowa Farida Sai ku yarana tunda mijinki Yana da Dan arziki Kuma kince Kuna zamanku lafiya sai abinda kika ce Dan Allah Farida ki turo min ko dubu biyu ce a accnt Dina na samu naci wani Abu,Allah ya kyauta kiyi Hakuri Hajiya Inshaallah Zan San yanda za ayi,Hajiya da sauri ta dinga godiya.
Bayan Farida ta kashe wayar suna Napep da Belloti yaga ta fada tunani da damuwa sosai a fuskarta tana Neman yin kuka sabo da Farida Bata da ko kwandala Sadakinta ma Fridge aka siya Mata da shi anyi zaton za a Mata jere,Kuma kayan gaba Daya suna gidan Yayan Hajiya,Kiran Hajiya ta sake yi ta daga tare da cewa Farida kin tura? Farida tace Hajiya Ina kayan kitchen da muka Dan siya wasu abubuwan ki dauki wani abin me tsada ki siyar da su kiyi amfani da kudin,Hajiya Tace tab yo ai tunda na dauki Blender a ciki na siyar Yaya ya boye kayan a wani Empty house yasa key ya garkame Kuma yace idan na taba wallahi sai ya ci mutunci na,Farida Kawai ki bani ko dari biyar ce ma ki turo min abin kunya ne na Bude sirrina naje na tambayi wani kudi ke kin San me Mukayi wallahi Dariya za a min.
Okay Farida ta furta ta sake kashe waya ranta a jagule Idonta ya ciko da kwalla zata Yi kuka,Belloti ya fahimci matsalar kudi ce,yace Lafiya Baby? Farida tana goge hawayen da ya zubo Mata tare da furta ba komai,Ya Zaki ce ba komai ki fada min idan Bai fi karfi na ba Zan Miki,Farida Taki fada sabo da boye sirrinta Su Farida ba a son Raini,Belloti ya matsa sai ya ji dole ta hakura Tace Hajiya ce take son Kudi ko 1k ne Wai amfani da zata Yi da shi Bata ce yunwa bace Kar ya Raina su,Belloti yace Akan wannan kike Kuka har baza ki fada min ba,ke Nifa bana son irin wannan, waye Bai San rayuwa ba yanzu,kune komai sai kunyi karya ta Yan Birni da kin fada min da tuni ba a tura Mata ba Zan rasa kudin Bata ne kika ji? To ko abokina na sa yanzu zai tura Mata bani accnt number.
Farida Lokacin farin ciki ya kamata taji wani sabon son Belloti ya kamata Haka ta bashi account Number Nan take yayiwa Hajiya transfer na 5k, yace ki tambayeta idan ta gani sai ga Kiran Hajiya Tace naga 5k da accnt din mijinki 5k Bello Muhammad Tukur ko? Farida Tace ae,Hajiya godiya ta shiga zubawa harda sa Albarka Tace bani shi nayi Masa godiya,Farida tace My Hero ga Hajiya zata maka godiya Belloti yace Akan 5k Mene 5k gaskiya bazan iya amsa ba kunya ma nake ji 5k kacal a kanta za a gode min Fafur Belloti yaki karbar waya Wai kunyar Kansa yake Yi ma a hakan.
Farida a ranta tace Allah me iko a baya 20k ma mutum ya bamu Bai Isa mu gode Masa ba bare 5k wa zai saurare shi ma duk talaucin mu,Wani Shawarma Joint Suka Shiga kida na tashi iri iri ya musu order na Shawarma da fruits salat Sai ice cream,Belloti harda Bawa Farida a Baki sai da Suka ci suka koshi suna hirarsu cike da nishadi da kaunar juna.
Bayan Nan Shopping Mall ya kaita yace to karki karar Mana da Dan kudin tafiyar mu kauye yanzu Abu me ma'ana zamu siya,Wanne Body Lotion ne ya karbe ki? So nake a samu me kyau kiyi haske me kyau Normal bana son wannan hasken dau da kikayi kafin aurenki, gwara kiyi me kyau,Farida tace lokacin fa wata Allura ake min,Yace Kar a sake ba a gidana ba,Dan cream din ma me kyau Bai Isa ba sai anyi wani haukar haske tunda Allah yayo mutum Baki Ina laifi ma da Allah ya Bawa bature ikon Kirkiro body Cream a shafa ayi kyau duk haka ba a gode ba sai an Zama baturiya, siyi Cream me kyau me Dan tsada Wanda zai gyara skin ko hasken ne ayi me kyau na hankali na wayewa,Farida tace ai tunda nayi Allurar sau biyu na daina gashi duk na fara dishewa,Belloti yace yawwa kinfi kyau haka daga Cream na dubu Uku zuwa hudu Zan iya siya Miki dai dai karfi na.
Sai da suka Gama shawarwarin me zasu siya na tafiya Kauye Wanda ko sunje bazai Kare da wuri ba zasu Dade sannan Suka shiga ciki,Farida ya Siya Mata body Lotion Kalar data zaba Dan 4k Guda biyu,sai na face dinsa,su shampoo Kuwa duk ya Siya Mata duk da cewa tana da wasu a lefe,Turare zai siya Tace Ina da Humra fa da yawa ga Kuma na lefe it's okay,Belloti shima ya siyawa kansa abinda zai iya,Har su kayan shayi cornflakes sai da ya Siya musu Kar ma suje Kauye a samu matsala tunda yasan Farida bata Saba da cima ba ta kauye ba,Sai da suka Gama suka dawo wurin 12am a daren suka shirya komai nasu har tsarabar da zasu Kai sun siya,Belloti gaba Daya Dan abinda ya Tara ya kwashe harda siyawa Iyayensa Buhun shinkafa,taliya,macaroni,Mai,su Indomie da su sabulan wanka da wanki.
Washe gari 8am ya Kira wani Me Golf da ya dauka Drop zai kaisu har kauyen suka shirya kayansu tsaf sannan Belloti ya shiga bedroom din Uche ya bashi Hannu Suka tafa yace Zan wuce,Uche sai Kuma yaji ba Dadi gaba Daya yasan Bai kyauta ba,Nan take yace na hakura Bello ku zauna,mu zauna tare I'm so sorry for what I have done to you,Belloti yayi murmushi yace ai ba Haushinka naji ba Kawai Allah yayi tashi na ne ka barni na tafi Zan dawo verysoon Zan na zuwa Muna gaisawa,Uche Yace Alright Be a good Man ya ciro 10k ya bawa Farida yace ajiya gashi asha ruwa,Farida ta karba tayi godiya ta ci gayu cikin lace dinta peach doguwar Riga me kwala dinkin manyan Mata,Shi Kuwa Belloti wata Shadda ya saka ruwan toka an Masa gyaran gashi yayi kyau sosai da gani kasan ya waye ba Kalar Kauye bane.
Har Mota Uche ya rakasu suka tafi suna dagawa juna Hannu,Belloti da Amaryar sa Ana bayan Mota,tafiya tayi tafiya Farida ta kwantar da kanta a kafadar Belloti tana ta bacci, sai da Suka shiga garin Bauchi Belloti ya fita ya siyo musu wani Naman rago gasashe da ruwa da yogurt har driver din nasa daban,Suka ci suka koshi a motar,a Haka har suka dauki Hanyar rugar me shegen nisa Kamar ba a duniya suke ba,Farida ta kalli Belloti Tace sannunku kunyi kokari kowa da inda Allah ya ajiye shi,Murmushi yayi kawai har Suka karasa garin Farida taga gidajen Basu fi Guda Hamsim ba,Tace Lallai Manal ta waye da wuri idan Haka ne to Kuwa ba karamar basira Allah ya Mata ba,kaima Haka my Husband,kalli ikon Allah Wai kana Nan garin a wannan nisan amma har Allah ya kawoka garinmu ka aure Ni,lallai Mijin Aure daban yake,wanda baka taba zato ba Ashe duk wannan haukar da nake kana Nan kauyen ma tuni,da ace a lokacin za a fada min bazan yarda ba Amma gashi ya faru,Belloti yayi Dariyarsa me kyau abinka da Dan Fulani me kyau ga Hanci,Yace Allah kenan ai Allah ba abin Wasa bane abinda ko a mafarki baka zata ba shike faruwa,Farida Tace ko a mafarkina na jaraba ban taba ganinka ba ko me Kama da kai,Suna karasawa kusa da gidan su Belloti Suka hango wasu lafiyayyun motoci Guda biyu da securities tare da Dogarai,Belloti yace ga kanwarki Nan Maybe Manal,Wannan da Alama da mijinta suka zo,Farida gabanta ya Fadi,Belloti yace ki daina damun kanki kina daukarwa kanki karya Farcy,ba a daka ta Dan Adam a rayuwa,idan ka biyewa Dan Adam to a rayuwa ba abinda zaka iya yi,Ki saki ranki,Farida tayi murmushi tare da Furta ba damuwa wancen ne kenan gidan Annatu? Yace yes shine Mana,kannen Belloti Yan Mata da maza ne Suka fito suna ihun murna da oyoyo,Nan take Belloti yasa suka kwashe kayan kaf tare da shigewa cikin gidan da su,gidan su Belloti na Bulon Siminti ne,su biyu ne gida na bulon Siminti kaf garin,Bayan Belloti ya sallami Me Golf ya tafi,Farida Tace to Manal dinfa ya kamata na ganta Kar na tafi Bamu hadu ba,Farida so take Kawai taga wani na gidansu ko zata ji sanyi a ranta,Yan kauyen sai kallonta sukeyi sunga Yar gayu,Ganin ta damu yace Kira Manal din a waya kiji ko da ita aka zo,Farida ta Kira Manal Wayar Bata shiga ba sabo da karancin network,Belloti yace Naga kin damu Jeki gidan Ina jiranki a gidanmu sai kin dawo,Farida da shagwaba Tace Kai da kake Dan gari muje tare,Haka Suka jera suka tafi gidan Annatu.
Farida ce ta gyara handbag dinta tare da shiga gidan da sallama Belloti yace Ina jiranki a waje,Sallama tayi a gidan tunda taga wani shegen chogen takalmi me tsada tasan Manal ce ma,shiga tayi kusa da dakin,can ciki taji dariyar Manal suna magana ko da waye oho sai lokacin ta tuna taga takalman Fuzail masu tsada,ga kamshinsa ya cika ko ina na gidan,Gadon Annatu Me Spring ne yake Lilo Yana Kara kiiii...kiii....Manal tana ta dariya tana cewa prince da zafi fa kaji yanda ka sake Ni a saman bed na fada ka manta da Babynka,Farida ce da masifa tace Wai su waye ne suke dariye dariye Ana Sallama baza su amsa ba sabo da soyayya Haba,Manal tana daga ciki Tace ya naji kamar Aunty Farida kaji muryar prince,Shigo cewar Fuzail Yana Rufewa Manal cikinta da rigarta da ya janye Yana Mata Chakulkuli,Farida ta shiga,Manal ta Mike tsaye Tace laaaaa Aunty Farida yaushe kika Zo? Me ya kawoki kauyen Nan? Farida ta kalli Manal Tace uhm su Manal Wato dai an Zama mayyar miji Allah ya shiryeki yanzu har bedroom din Annatu? Tana Ina? Bata Nan sai anjima zata dawo ita Muke jira Bamu Dade da zuwa ba da Yamma zamu tafi,Farida ta Furta Uhm I can see,to kin manta garin Nan surukai na suke? Manal tace na tuna fa kinzo gaisar da su,yaushe zaku koma? Zanzo gidanki? Farida Tace to munafuka ba yanzu Zan koma gida ba sai na Saba da surukai na sunji dumi na,Dariya ma ta bawa Fuzail,Farida tace Kanina ya gida ya aiki? Bata taba gaisar da shi ba sai yau,Wai kaninta ta ma,Fuzail yace Aunty Lafiya nake,Farida Tace na gani ai,ka daina biyewa Yarinyar Nan wlh tasa kana ta rashin ta Ido a gadon Suruka tam,Fuzail dai Bai ce komai ba,Farida tace Manal Zan tafi gidanmu Zan na zuwa ai Muna gaisawa da Annatu kafin mu tafi,Manal tace hakan yayi zanzo Nima muyi Sallama, Alright Farida ta juya zata tafi,Manal Tace Aunty kinyi kyau wallahi sai kiba kike Yi, to ya na iya komai zam zam ai ko ya kika ce? ,Manal ta Kama Dariya tace Aunty kina Jin Dadi,zanci uwarki nasan Gulmar da kike ta Yi kizo mu sa labile tunda kin matsu kiji in ba munafunci ba mace da mijinta kin damu da matar wani kije kema a Baki Mana ai gaki gashi Nan,Tashi Manal tayi ta biyo Farida har tsakar gida tana karewa Farida kallo tun daga sama har kasa tace Aunty ana harka...harka...harka.....Farida tayi Dariya tace zanyi maganinki ne kin San Halina wallahi kika sake agaban mijinki Zan Baki kunya,Zan fadi kalmar fitsara a gabansa kinga Zaki ji kunya yayarki tayi Maganar banza Gaban suruki kin San Halina Allah idan kina min irin wannan abin sai na Baki kunya,Manal Tace ance Miki kunyarsa nake ji yanzu Ni,Yaya Aunty Hope dai Bellotin akwai Aiki? Hand bag Farida ta kwadawa Manal suna dariya Farida tace Cucumber ai tayi ta fice abinta,Manal tana ta dariya Wai Cucumber.
Dawowa tayi wajen Fuzail Tace idan Annatu baza ta dawo ba mu tafi Dan Allah,akan me? Sai mu koma cikin garin Bauchi mu kwana a hotel gobe sai mu dawo, Fuzail yace sabo da me? Manal ta kwanta a jikinsa da shagwaba tace cucumber zaka bani,Fuzail yayi Dariya yace lallai Yarinyar nan to Ni tawa ba Cucumber bace Cassava ce,Manal ta fara Dariya harda rike ciki,yace karki kashe min yarona da dariyar masifarki,Jin sallamar Annatu sukayi da sauri Manal ta koma kasa saman Tabarma ta bar Fuzail a gefen bed sabo da daki Daya ne irin dakin kauye,Sannu da zuwa Annatu,Yawwa Ashe Kuna ta jirana cewar Annatu tana shigowa sai kunyar Surukinta take ji,a kasa ya zube tare da kwasar gaisuwa ta amsa da fara'a Nan take ta hada musu Fura lafiyayya Anna Ina su Khairan ne?Suna gidan Kakarsu tun jiya,Yaran Ni ban San ya za a saka su a school ba wannan ta kauyen ta Gomnati ce,ko Birni zamu koma da ku? Annatu ta Bude Baki tare da furta Allah ya kiyaye kin San dai ba zaman kaina nake ba,Mijin Annatu ne ya dawo daga Gona ya Iske Ana zancen yace na tafi na barwar wa duk tarin shanu na da sauran kadaronina,Fuzail ne yace to shike Nan Zan samu ayi sabon gidan a Nan din a canja ginin gida,Mijin Annatu ya washe Baki Yana godiya,Annatu ta kalle shi kawai ta tuna Sanda yake dukan Manal Bata Masa komai ba,tace Allah me iko yau Albarkacin Manal zaka ci Kuma,ba irin duka da zagin da baka Mata ba iya yaranka sune mutane to gashi yau arzikin Manal zaka fara ci Wanda ma ba a San iyakacinsa ba sai Allah,Mijin Annatu jikinsa yayi sanyi yace Manal ki yafe min,Kaga rayuwa shi yasa akace da na kowa ne baka San me Jin kanka ba Akan Mahaifiyarki na samu Yara ki yafe min.
Baki Annatu ta tabe Masa tace da Bata yafe ba ai da baza ta bar mijinta ya taimaka maka ba,Manal tace Saudiya Annatu Inshaallah Zaku Yi aikin Hajji Yarima ya biya,Murna Kan murna suka dinga Murna,Manal tafi so su Annatu su koma birni sabo da karatun su Khairan amma ubansu bazai yarda ba sai dai Nan gaba idan sun girma sai suyi karatun a wajenta.
Fuzail yace Gama mu wuce Ummi Inshaallah kafin ta koma Brazil zata Zo ta gaisar da ke Annatu cewar Fuzail,Annatu tana mamaki tace Allah ya kaimu,Ya Riga Manal fita ya barsu suna zance na sirri irin tsakanin Uwa da Yarta,Annatu Tace Ina Dan Uwan naki? Manal tace Yaya Yazed tab ya fada Miki? Baki ga gidan da Malam yake
Book Chapters
Chapter 1Chapter 2Chapter 3Chapter 4Chapter 5Chapter 6Chapter 7Chapter 8Chapter 9Chapter 10Chapter 11Chapter 12Chapter 13Chapter 14Chapter 15Chapter 16Chapter 17Chapter 18Chapter 19Chapter 20Chapter 21Chapter 22Chapter 23Chapter 24Chapter 25Chapter 26Chapter 27Chapter 28Chapter 29Chapter 30Chapter 31Chapter 32Chapter 33Chapter 34Chapter 35Chapter 36Chapter 37Chapter 38Chapter 39 Chapter 40Chapter 41Chapter 42Chapter 43Chapter 44Chapter 45Chapter 46Chapter 47Chapter 48Chapter 49Chapter 50Chapter 51Chapter 52