kasa daurewa Tace Amma Dan girman Allah Dan Allah Sa'iha Kinga ance Rasha Basu da tarbiya Dan Allah Banda Shan giya da wiwi,Idan kika ga Barasa to kiyi arewa ita tayi kudu,ba ruwanki da shaye shaye kinji Sa'iha,Farida tana fari da Ido Tace woo Ni Ina ta yin sunan Nawa fari kana Kara DA ya koma FARIDA,ya kike da suna ma Manal ko?Hajiya Manal ki fito fili kice kina maula ko Chadi ko Cameroon a kaiki kema,Dariya Manal tayi tace ai wallahi gwara ki barni a Nigeria yafiye min Wata Chadi,Hajiya Tace to munafuka da kika samu ma za a kaiki banza Yar Kauye har abada baza ki waye ba,kalli kayan jikinki ko kunya bakya ji uban waye zai ganki a Haka ya so ki banza akuya,Manal taji haushi tace naji dama ai Ni bance a so ni Dan kyau ko Dan wani abin jikina ba.
Wata Dariya Suka kwashewa Manal da ita Hajiya tace Manal kike suna ko Dadi babu Dan Iyayin Yayanki harda wani canja Miki suna akan yaga na canjawa Farida shine kema ya canja Miki ai wallahi gwara sunanki na asali Waqi'a yafi Dadi ma Amma Mene wani Manal,tun daga Jin sunanki saurayinki zai gudu,Farida tana Dariya Tace Kuma Hajiya Wai Bata so a so ta Dan kyau wani Abu na jikinta to ki daina batawa kanki lokaci mazan yanzu sun daina soyayyar gaskiya Jerusalem naki ne Kawai burinsu gwara ma ki Bude idonki,Manal Tace ku kuka San wani Jerusalami ta ci gaba da Shirin soya gyadarta,tana aikin gyadar Tace ga me siyen Gyada marau marau me gishiri yau Zan fara duk kulli Naira Ishirin naira hamsim babu bashi bare kyauta,Farida tayi wata shewa tare da Furta wa zaici gyada? Allah kiyaye kuraje su fito min a Fuska tun Fuzail Bai zo ba,Hajiya Tace kwantai ma zata Yi mu Nan ba Kauye bane basa cin wata Gyada kayan wahala,Manal tana aikinta ko kulasu batayi ba.
Tunda Manal ta fara Gyada sai ta samu kasuwa sabo da yanda take soyata me Dadi,riba take samu sosai,idan ta soya ko kwana Bata Yi take karewa,ganin Haka yasa Yaya Yazed ya samo kudi ya Kara Mata kwano Daya take soya ta kwano biyu kullum duk da ya hanata talla a gida ake sintirin zuwa siya maza da Mata,a cikin ribar Kuma da ita yawanci ake cefane Ana ciyar da gidan,Ganin Haka sai Yazed ya auno Mata waken suya ta fara awarar siyarwa shi ya koya Mata yanda ake soyata da kwai sannan a yanka Mata su Albasa da kayan Miya harda cabbage,Manal sai kasuwar Awara ta Bude sosai ko Basu samu sunyi girki ba to awarar Nan ake ci kowa ya Sha ruwa,idan jari ya karye Yazed ya Dora jarin,Haka Malam masifar Jin dadin sana'ar Manal yakeyi,Kuma kullum itace take kula da shi idan Yazed Baya Nan,Haka ita da Yazed suke hada kayan Malam Dana Manal Dana Yazed su wanke abinsu tas su goge kullum cikin tsafta suke,Zuwan Manal gidan ya cire kazantar gidan komai ita take gyarawa shi yasa sai kaga ko Ina Kal Kal,jikinta ma fes matsalar Kawai rashin sutura,Sabanin su Farida da Hajiya tana da Yan uwa masu Dan Hali suna tallafa musu da kudi da sutura,idan Suka samu kudin Kuma a jikin Farida suke karewa wajen gyarawa Fuzail jiki sabo da ya sota sosai.
Bayan Kwana biyu tsakani Sai ga Farida tana Hawaye jiki a sanyaye ta shigo gidansu,takalminta Dan dubu bakwai me tsini ta cire a hannunta,English Gown dinta Yar dubu Tara ta dageta sama a Haka ta karaso wajen Hajiya dake goge Mata kayan sawarta da dutsen guga sabo da ta Hana Farida daukan ko tsinke a gidan sabo da kar skin dinta ta lalace,a tsorace Hajiya tace Farida lafiya kike Hawaye? Dan Sarkin ne ya wulakantaki?Farida ta girgiza Kai tana share hawayenta ta furta mafarki na ne wani a ciki ya Zama karya,Gaban Hajiya ne ya yanke ya Fadi tace yau na Shiga Uku ba dai auren ne bazai yuwu ba? Farida Tace a'a dama Hajiya Ni mafarki na ban taba ganinsa ba Ashe na taba ganinsa sau biyu ma,sannan a mafarki na Bai taba zuwa kasar nan ba Ashe ya taba zuwa har sau biyar ma,Kuma Yana Jin Yar hausarsa Yana Yi Kuma Amma ba can ba sabanin mafarki na, Lokacin Dana taba ganinsa a wani kazamin goslow ne da aka taba yi,Ina taxi ya fito da escort dinsa a wasu mahaukatan Motoci,sannan na sake ganinsa Yana rabawa talakawa tallafi a kusa da makarantar mu Muka wuce shi da kawayen mu,Kinga yau na ganshi Dana je gidan Sarkin Muna tare da Bafaden gidan ya fito zai fita Allah yasa zai Shiga mota na saita wayata na dinga Masa hotuna,sannan Kinga Bafaden ya tura min wasu hotunan Fuzail sunfi ashirin,zanje gidan Hoto a wanke min su nazo na lika su a dakina..
Ashe na taba ganinsa rashin ganiya ce irin tawa Amma Allah a fili yafi kyau ma Sau dubu fiye da mafarki na,wayyo Allah na more da Mijin aure,Ni Kam na taka sa'a shike Nan Ni Hajiya Farida ta furta tana Juyi da murna da Ihu gaba Daya
Hajiya ta sauke Ajiyar zuciya tace akan wannan kike kuka nayi tunanin ma wani Abu ne Babba nuna min hotunan nasa,Farida ta kamo Hotunan Fuzail masu shegen kyau wasu ma duk a kasar waje ne,duk inda kake neman me kyau Fuzail ya Gama cika sharadan,ai sai murna ta Kama Hajiya tana bin hotunan da kallo Daya bayan Daya tana Inyeeee....Carkwadi,ke Kam Farida kin Dace kalli fatarsa dinsa wani irin haske me wani dum dum...wow Kai kalle shi a dusar kankara wannan Bai Saba da zafi ba Dole mu Nemo ac mu saka ko a Rubabben dakin ki ne tunda Nan gaba zai dinga zuwa zance,Farida tana murna tace wallahi har hotunan Zan na yiwa fifita kafin a sa ac.
Manal tana ji tayi Dariya tace Haba Ni nasan Yasin kin sanshi kin taba ganinsa Amma sai kace wata waliyya ace ka dinga mafarkin mutum baka taba ganinsa ba Kuma ya Zama gaske Haba Anty yanda kike da bakin Hali yaushe ma zaki ga mutum a mafarki baki sanshi ba,Uwarki Hadiza nace cewar Hajiya,muguwa Yar bakin ciki,yarinya Zo kiga saurayi hadadde me kudi,Manal taje ta leka Wayar gabanta ne ya yanke ya Fadi ganin irin wannan mutumin me Arnen Kyawun da Bata taba gani ba tsawon rayuwarta,ga kudi ga Hutu,wasu pics din ta gani tace chab Allah ya samu a danshinki,Farida tana murna tace ya kika hango Ni a gidan sarauta na Sha alkyabba? Manal Tace ta bature yace wow...Dariya sukayi gaba daya Hajiya tana murna Tace jibi Zan karbo dinkuna na sababbi sabo da tarbar bakin gidan Sarki.
Tunda Manal take Sana'a tana samun ciniki hakan Yana konawa su Farida da Hajiya Rai,Hajiya tace wannan Yarinyar fa Muna zaune sai wani juya kudi takeyi Kuma ace Wai itace ma take yawan yin cefane a gidan Nan,Farida tace ai wallahi gwara ma mu dinga yini da yunwa akan ace wannan tatsitsiyar Yar kauyen ce zata dinga wani bada kudin cefane,Hajiya Tace kyaleta gidan Malam Dan Haru zamu je a toshe Mata hanyar samun,gaba Daya ta daina ciniki a daina siya ta koma yin kwantai Kinga Dole ta daina sana'ar, ai kuwa dare Nayi Hajiya sai gidan Malam.
Malam yace Hajiya meke tafe dake? Hajiya Tace bukatata na kawo Malam,Gani Malam ka taimaka Manal Yarinyar kishiyata bayan mun koreta na fada maka ta dawo asirin ya karye da wuri,yanzu ba bukatata a kore ta ba,tana Nan ta Kama sana'ar Gyada da Awara Malam Yarinyar ciniki takeyi sosai yanzu ma ita ke cefane a gidan Muna zaune,Ina bakin ciki Naga maza da Mata Ana sintiri a gidan Nan domin siyen kayanta,yini akeyi siyayya,tun tana soya gyadar kwano Daya yanzu kwano Uku take soyawa,Haka Awara yanzu ta kwano Uku tas take karewa Kuma abin haushin ko talla Bata fita a gida take zuba Uban ciniki Haka wallahi Rannan a ganmu ta irga dubu biyar ribar data hada ta damkawa Dan Uwanta Yazed ya siyo taliya da macaroni wallahi ranar kwana nayi banyi bacci ba,Ni Malam akan ace sune zasu dinga ci damu wallahi gwara mu dinga kwana da yunwa.
Malam Dariya yayi yace sana'ar da takeyi Awara da Gyada ko? Hajiya tace tabbas,yace indai Awara ce da Gyada daga yau an daina siye ko mutum Daya bazai Zo ba,Hajiya tana murna Tace duk abinda tasa Hannu akai Malam ya lalace Kar a Bari ta ci gaba,Malam yace ba lallai akan ko me ta taba zai lalace Amma duk abinda ta fara kika ga bakwa so kuzo ku sanar min a dakatar da abin,Hajiya tace dama yaushe Muna kallo zata Zo daga Kauye ta wuce mu ai bazai yuwu ba.
Kuma Kar kayi Mana maganin Nan irin wancen fuuuu duf sai kace Wani kumfa,Wai wanne Dan Iskan Aljanin ka tura ne marar mutunci marar tarbiyya daga shiga jikinsu ya fice da wuri,Malam yace wallahi Yaron Nan dangidan Muniba shine, Yaro ne karamin gaske shekararsa dubu biyu da dari shida ai yaro ne kuruciya ce ke dibansa,Malam Dan Haru harda makale Murya ya gwada muryar Yaron Aljanin Wai har da wani fada min wai ai ni sauri nake Yi bazan iya Zama ba ina da party a club can kasar Pakistan,Kuma kwana Hamsim zasu Yi a club din suna party,Farida tace Kan uba suna Shan Dadi Malam Ina ma a cikinsu nake Nima wallahi bazai wuce Ni ba wannan party din,Malam irin shegen Nan Harda dariya da Gadara shi a dole kwaro.
Hajiya Tace za a ga iya rawa wajen Aljanu Kam,Malam yace wayyo Ina ma idonki zai iya daukan ganinsu da na hasko Miki babban club dinsu na duniya Dake kasar Paris da Kinga Yan Mata da samari masu kuruciya Yan Shekaru dubu hudu hudu,mu a Nan mutane Ana cewa Sweet Sixteen to su Sweet thausand ake cewa,Hajiya Tace mashaallah daga gani zasuyi kyau,Malam yace Bari ke dai ai wata under age Dana gani shekararta dubu uku da dari biyu karki ganta,mun fafata soyayya da ita,wani Kiss data taba Yi min lokacin Muna ganawa da ita cikin bacci na ta kawo min Ziyara sai da na kwashe wata Uku cur banci abinci ko cokali Daya ba ke ko digon ruwa Bai shiga bakina ba wannan Dan Sumbatar data min itace cina da Shana kullum sai dai naji cikina dam ai Kuwa na Kara kiba da haske nayi fresh,Hajiya Tace wohohi kaji baiwa Dan Allah,kaji karama,kaga Wanda Allah yayiwa baiwa,Farida Tace wallahi karama ce Kawai Allah ya dafa Malam,Malam yace ku tashi kuje Kawai wani abin Nawa idan Ina fada muku sai ku ce ba Dan Adam bane Suka haife ni ba,Kawai kuje zaku ga Aiki.
Su Hajiya tunda Suka fito suke murna da irin Baiwar Malam Dan Haru da Suka ji.
Farida Tace kiji Dan Allah Baiwa Hajiya kiss da Aljana ai Dole yayi wata Uku a koshe,Wallahi ai kadan daga baiwarsa shi yasa bani da malamin Daya wuce shi.
Hajiya tana barin wajen Malam Dan Haru da kwana biyu Manal ta daina ciniki ko Kare ba Wanda yazo siye,ta Gama soya awara da uban yawa duf kake ji ba Wanda yazo Manal ta jira Amma Shuru su Farida suna tsakar gida suna kallonta suna dariya,Manal ta gaji da jiran masu siye tace to yau Kuma mutanen lafiya? ai sai Kawai ta ebo a plate da yaji ta zauna tana cin abarta Tace yo kada Allah yasa kuzo siye,Dan wulakanci kamar Kun hada baki tana dangwalar yaji tana ci har ta koshi,Tace cab har yanzu shuru watakil sai anjima za a fara zuwa siye har la'asar ba ko karen da yazo,Manal Dariya ta dinga yiwa kanta su Hajiya suna kallo suna Jin Dadi,Manal ta fara kida da faranti ta saka tarin Awara a gabanta tana kida da cokali tana Waka nayi kwantai....Awara tayi sumbu....azo a siyi sumbu....Kwantaiiiii.....,Gyada ma tun safe ba Wanda yazo siye mutanen layin Nan kalau suke Kuwa? Mana ta sake tambayar kanta Bayan ta tsaya da kidan nata da wakar kwantai,Su Hajiya sai uban Sheka Dariya sukeyi.ganin dare zaiyi sai ta dauki awarar ta fita da ita ta Tara Almajirai tace ga Sadaka maganin masifa ai Kuwa Nan take aka warwashe Awara Tasha hadi.
Bayan ta Gama rabawa ta dawo gida tana hawayen Takaicin asarar awararta data yi su Hajiya suna ta dariya.
Manal tace Allah ya gani ba Sadaka nayi da zuciya Daya ba dalilin kwantai yasa ba Wani Lada da Zan samu idan na sake ma Mala'iku ne zasu jibgeni a lahira.
Da dare suna zaune aka ce Wai Ana Sallama da Farida inji Salisu,Hajiya Tace wannan Yaron da naci yake kace baza ta zo ba tafi karfinsa ba ajinsa bace,Yaron ya koma ya fadawa saurayin Salisu abinda Hajiya Tace,Salisu Yana son Farida yace Dan Allah shiga ciki kace Mata Sako Zan Bata Dan Allah tazo yanzu zata koma,Yaron ya koma ya Fadi sakon Salisu,Hajiya mikewa tayi tare da cafkar Hannun Yaron ta shiga kwada Masa Mari da kyar Yazed ya fito ya kwaci Yaron Yana cewa Haba Hajiya Bai Dace ba,me son naka ai abin a yaba ne, Fuuuuuuuu Hajiya ta fita Kofar gidan da kanta.
Tana fita da bala'i tace Salisu kake ko uban me yarinya ta tafi karfinka ba sa',arka bace,yarinya ta ba matar talaka bace,me na sama yaci bare yaba na kasa? Uban me ka Tara? Mene sana'arka? Waye Ubanka a kasar nan? Ana Haka sai ga Farida ta fito da ruwa a katon kofi tana zuwa babu Bata lokaci ta watsawa Salisu a Fuska da jikinsa gaba Daya,suka koma gida ita da Hajiya Suka bar Salisu da mamaki ya daskarar da shi a wajen,Yana Jin Labari a Unguwa Ashe abin nasu Farida ya zarta hankali ma.
FUZAIL kwance yake a katafaren palonsa na Alfarma,Yana latsa waya fuskar Nan a murtuke,Kuyangu da fadawa dake palon ya Sallama cikin Harshen turanci yace ku je ni bana son wannan shirmen na sarauta Kamar ana bautawa mutum Ni duk irin abin Nan bana so ku daina zuwa Kuna takura min,me Aiki Daya nake so wacce zata na min abinci sai maza biyu masu kula da part Dina that's all,Ni duk abin Nan bana so.
Su dai basa Jin turanci Amma sun Riga sun San halinsa da bukatarsa me martaba ya sanar musu Amma shi yace Dole sai an bawa Fuzail kulawa,Haka Ya Hana a dinga kiransa Yarima amma Ina ma'aikatan gidan sarki ya Zama dole,sabo da Haka Prince Fuzail ake kiransa Dole,Tunda ya dawo Mai martaba ya kawo me koya Masa karatun Addini da Kuma yaren Hausa, Yana da basira Bai Dade ba ya Kara gane yaren Hausar ,Karatun addinin musulunci Kuwa Dama can Yana son addininsa Yana karatu sosai a turai,a masallaci ma Yana daukan darasi wajen wani balaraben Turkiyya da Abokinsa Kuma Dan Uwansa Ameer, yasan Addini sosai,Mai martaba yayi Matukar farin ciki ganin har yafi yaransa na Nan kula da Addini da Kuma halaye masu kyau duk cikin yaransa ba Kamar Fuzail,Duniya kenan dama idan Allah ya tsareka ko a Ina kake baka bin hanyar banza.
Maimartaba ganin Yaron Nasa yasan me yakeyi duk da cewa Dan Adam Tara yake Bai cika goma ba,kowa akwai halinsa me kyau da Kuma marar kyau,sai dai na wani me kyan ya rinjayi marar kyan,wani Kuma marar kyan ya rinjayi me kyau,Kawai abinda ya damu sarki rashin auren Fuzail,bashi da Burin da ya wuce Fuzail yayi Aure tunda ya Kai 32yrs bayan Haka ma abin surutu ne a masarautarsu,Haka Bai son yaronsa ya fada Harkar Mata sanadiyar rashin aure, Mahaifiyar prince Fuzail Kuma sunyi yarjejeniya da sarki zata yarda Fuzail ya dawo Nigeria amma Banda auren talaka,duk da baya Aurenta ya Amince sabo da Yana son rayuwar Dansa ta inganta,yazo ya Saba da Yan Uwansa,tunda Fuzail Yazo sarki yasa ake rakashi wajen duk wasu dangin sarki na birni Dana Kauye sai da duk Suka San Fuzail shima ya sansu,Fuzail sam baya son Hayaniya Bai da fara'a sosai,Bai son Kuma shiga Harkar kowa,asalin bature ne Dan ka'ida,Yana da magana Daya Idan ya kafe a Abu sai dai a kyale shi,gashi rayuwar turai yayi ba kunyar kowa yake ji ba,shi Bai ma San wata kunya ba,sannan akwai son girma baya son raini ko kadan Amma akwai kyauta da taimako Bai son ganin wani a cikin wani Hali.
Fuzail kyakyawa ne na karshen karshe,mutum ne me azabar kyau,idan aka ce kyau to azo wajen Fuzail sabo da shi gaba Daya Mamansa Balarabiya ita yayi Kama da ita,Hasken fatarsa ne Bai Kai na Larabawa ba Amma fari ne wani irin skin ne dashi me azabar kyau,wani Fari-Fari jaja- jaja haka yake,Dogo ne me masifar kyan sura da diri,Allah ya Masa Kyawun diri ko wanne Kaya ya saka sai ya tsula kyau a ciki,sumarsa baka wuluk me santsi ga saje da Dan gemunsa Wanda ya sake fito Masa da asalin kyansa,hancinsa santalele,idanuwansa su ba manya ba baza ace kanana ba farare tas,Dan bakinsa karami lips dinsa wasu jajaye masu birge me kallonsu,hakoransa kanana masu kyau da haske,Gashi Dan gayu kullum cikin daukan wanka yake,Ya iya sa Kaya da gayu Malam,ga kamshi Kamar me kullum cikin kamshi,lissafa irin Baiwar da Allah yayiwa Fuzail akwai Aiki,shi yasa danginsa kaf da gidan sarauta gaba Daya Alfahari sukeyi da Fuzail,kowa Yana kaunarsa gashi dama da kwar jini da farin jini,duk inda ya shiga sai an so shi Kuma an kalle shi,kana gani kasan ba girman Africa bane.
Yayan sarki kaf Mata da
Showing 15001 words to 18000 words out of 153479 words
Wata Dariya Suka kwashewa Manal da ita Hajiya tace Manal kike suna ko Dadi babu Dan Iyayin Yayanki harda wani canja Miki suna akan yaga na canjawa Farida shine kema ya canja Miki ai wallahi gwara sunanki na asali Waqi'a yafi Dadi ma Amma Mene wani Manal,tun daga Jin sunanki saurayinki zai gudu,Farida tana Dariya Tace Kuma Hajiya Wai Bata so a so ta Dan kyau wani Abu na jikinta to ki daina batawa kanki lokaci mazan yanzu sun daina soyayyar gaskiya Jerusalem naki ne Kawai burinsu gwara ma ki Bude idonki,Manal Tace ku kuka San wani Jerusalami ta ci gaba da Shirin soya gyadarta,tana aikin gyadar Tace ga me siyen Gyada marau marau me gishiri yau Zan fara duk kulli Naira Ishirin naira hamsim babu bashi bare kyauta,Farida tayi wata shewa tare da Furta wa zaici gyada? Allah kiyaye kuraje su fito min a Fuska tun Fuzail Bai zo ba,Hajiya Tace kwantai ma zata Yi mu Nan ba Kauye bane basa cin wata Gyada kayan wahala,Manal tana aikinta ko kulasu batayi ba.
Tunda Manal ta fara Gyada sai ta samu kasuwa sabo da yanda take soyata me Dadi,riba take samu sosai,idan ta soya ko kwana Bata Yi take karewa,ganin Haka yasa Yaya Yazed ya samo kudi ya Kara Mata kwano Daya take soya ta kwano biyu kullum duk da ya hanata talla a gida ake sintirin zuwa siya maza da Mata,a cikin ribar Kuma da ita yawanci ake cefane Ana ciyar da gidan,Ganin Haka sai Yazed ya auno Mata waken suya ta fara awarar siyarwa shi ya koya Mata yanda ake soyata da kwai sannan a yanka Mata su Albasa da kayan Miya harda cabbage,Manal sai kasuwar Awara ta Bude sosai ko Basu samu sunyi girki ba to awarar Nan ake ci kowa ya Sha ruwa,idan jari ya karye Yazed ya Dora jarin,Haka Malam masifar Jin dadin sana'ar Manal yakeyi,Kuma kullum itace take kula da shi idan Yazed Baya Nan,Haka ita da Yazed suke hada kayan Malam Dana Manal Dana Yazed su wanke abinsu tas su goge kullum cikin tsafta suke,Zuwan Manal gidan ya cire kazantar gidan komai ita take gyarawa shi yasa sai kaga ko Ina Kal Kal,jikinta ma fes matsalar Kawai rashin sutura,Sabanin su Farida da Hajiya tana da Yan uwa masu Dan Hali suna tallafa musu da kudi da sutura,idan Suka samu kudin Kuma a jikin Farida suke karewa wajen gyarawa Fuzail jiki sabo da ya sota sosai.
Bayan Kwana biyu tsakani Sai ga Farida tana Hawaye jiki a sanyaye ta shigo gidansu,takalminta Dan dubu bakwai me tsini ta cire a hannunta,English Gown dinta Yar dubu Tara ta dageta sama a Haka ta karaso wajen Hajiya dake goge Mata kayan sawarta da dutsen guga sabo da ta Hana Farida daukan ko tsinke a gidan sabo da kar skin dinta ta lalace,a tsorace Hajiya tace Farida lafiya kike Hawaye? Dan Sarkin ne ya wulakantaki?Farida ta girgiza Kai tana share hawayenta ta furta mafarki na ne wani a ciki ya Zama karya,Gaban Hajiya ne ya yanke ya Fadi tace yau na Shiga Uku ba dai auren ne bazai yuwu ba? Farida Tace a'a dama Hajiya Ni mafarki na ban taba ganinsa ba Ashe na taba ganinsa sau biyu ma,sannan a mafarki na Bai taba zuwa kasar nan ba Ashe ya taba zuwa har sau biyar ma,Kuma Yana Jin Yar hausarsa Yana Yi Kuma Amma ba can ba sabanin mafarki na, Lokacin Dana taba ganinsa a wani kazamin goslow ne da aka taba yi,Ina taxi ya fito da escort dinsa a wasu mahaukatan Motoci,sannan na sake ganinsa Yana rabawa talakawa tallafi a kusa da makarantar mu Muka wuce shi da kawayen mu,Kinga yau na ganshi Dana je gidan Sarkin Muna tare da Bafaden gidan ya fito zai fita Allah yasa zai Shiga mota na saita wayata na dinga Masa hotuna,sannan Kinga Bafaden ya tura min wasu hotunan Fuzail sunfi ashirin,zanje gidan Hoto a wanke min su nazo na lika su a dakina..
Ashe na taba ganinsa rashin ganiya ce irin tawa Amma Allah a fili yafi kyau ma Sau dubu fiye da mafarki na,wayyo Allah na more da Mijin aure,Ni Kam na taka sa'a shike Nan Ni Hajiya Farida ta furta tana Juyi da murna da Ihu gaba Daya
Hajiya ta sauke Ajiyar zuciya tace akan wannan kike kuka nayi tunanin ma wani Abu ne Babba nuna min hotunan nasa,Farida ta kamo Hotunan Fuzail masu shegen kyau wasu ma duk a kasar waje ne,duk inda kake neman me kyau Fuzail ya Gama cika sharadan,ai sai murna ta Kama Hajiya tana bin hotunan da kallo Daya bayan Daya tana Inyeeee....Carkwadi,ke Kam Farida kin Dace kalli fatarsa dinsa wani irin haske me wani dum dum...wow Kai kalle shi a dusar kankara wannan Bai Saba da zafi ba Dole mu Nemo ac mu saka ko a Rubabben dakin ki ne tunda Nan gaba zai dinga zuwa zance,Farida tana murna tace wallahi har hotunan Zan na yiwa fifita kafin a sa ac.
Manal tana ji tayi Dariya tace Haba Ni nasan Yasin kin sanshi kin taba ganinsa Amma sai kace wata waliyya ace ka dinga mafarkin mutum baka taba ganinsa ba Kuma ya Zama gaske Haba Anty yanda kike da bakin Hali yaushe ma zaki ga mutum a mafarki baki sanshi ba,Uwarki Hadiza nace cewar Hajiya,muguwa Yar bakin ciki,yarinya Zo kiga saurayi hadadde me kudi,Manal taje ta leka Wayar gabanta ne ya yanke ya Fadi ganin irin wannan mutumin me Arnen Kyawun da Bata taba gani ba tsawon rayuwarta,ga kudi ga Hutu,wasu pics din ta gani tace chab Allah ya samu a danshinki,Farida tana murna tace ya kika hango Ni a gidan sarauta na Sha alkyabba? Manal Tace ta bature yace wow...Dariya sukayi gaba daya Hajiya tana murna Tace jibi Zan karbo dinkuna na sababbi sabo da tarbar bakin gidan Sarki.
Tunda Manal take Sana'a tana samun ciniki hakan Yana konawa su Farida da Hajiya Rai,Hajiya tace wannan Yarinyar fa Muna zaune sai wani juya kudi takeyi Kuma ace Wai itace ma take yawan yin cefane a gidan Nan,Farida tace ai wallahi gwara ma mu dinga yini da yunwa akan ace wannan tatsitsiyar Yar kauyen ce zata dinga wani bada kudin cefane,Hajiya Tace kyaleta gidan Malam Dan Haru zamu je a toshe Mata hanyar samun,gaba Daya ta daina ciniki a daina siya ta koma yin kwantai Kinga Dole ta daina sana'ar, ai kuwa dare Nayi Hajiya sai gidan Malam.
Malam yace Hajiya meke tafe dake? Hajiya Tace bukatata na kawo Malam,Gani Malam ka taimaka Manal Yarinyar kishiyata bayan mun koreta na fada maka ta dawo asirin ya karye da wuri,yanzu ba bukatata a kore ta ba,tana Nan ta Kama sana'ar Gyada da Awara Malam Yarinyar ciniki takeyi sosai yanzu ma ita ke cefane a gidan Muna zaune,Ina bakin ciki Naga maza da Mata Ana sintiri a gidan Nan domin siyen kayanta,yini akeyi siyayya,tun tana soya gyadar kwano Daya yanzu kwano Uku take soyawa,Haka Awara yanzu ta kwano Uku tas take karewa Kuma abin haushin ko talla Bata fita a gida take zuba Uban ciniki Haka wallahi Rannan a ganmu ta irga dubu biyar ribar data hada ta damkawa Dan Uwanta Yazed ya siyo taliya da macaroni wallahi ranar kwana nayi banyi bacci ba,Ni Malam akan ace sune zasu dinga ci damu wallahi gwara mu dinga kwana da yunwa.
Malam Dariya yayi yace sana'ar da takeyi Awara da Gyada ko? Hajiya tace tabbas,yace indai Awara ce da Gyada daga yau an daina siye ko mutum Daya bazai Zo ba,Hajiya tana murna Tace duk abinda tasa Hannu akai Malam ya lalace Kar a Bari ta ci gaba,Malam yace ba lallai akan ko me ta taba zai lalace Amma duk abinda ta fara kika ga bakwa so kuzo ku sanar min a dakatar da abin,Hajiya tace dama yaushe Muna kallo zata Zo daga Kauye ta wuce mu ai bazai yuwu ba.
Kuma Kar kayi Mana maganin Nan irin wancen fuuuu duf sai kace Wani kumfa,Wai wanne Dan Iskan Aljanin ka tura ne marar mutunci marar tarbiyya daga shiga jikinsu ya fice da wuri,Malam yace wallahi Yaron Nan dangidan Muniba shine, Yaro ne karamin gaske shekararsa dubu biyu da dari shida ai yaro ne kuruciya ce ke dibansa,Malam Dan Haru harda makale Murya ya gwada muryar Yaron Aljanin Wai har da wani fada min wai ai ni sauri nake Yi bazan iya Zama ba ina da party a club can kasar Pakistan,Kuma kwana Hamsim zasu Yi a club din suna party,Farida tace Kan uba suna Shan Dadi Malam Ina ma a cikinsu nake Nima wallahi bazai wuce Ni ba wannan party din,Malam irin shegen Nan Harda dariya da Gadara shi a dole kwaro.
Hajiya Tace za a ga iya rawa wajen Aljanu Kam,Malam yace wayyo Ina ma idonki zai iya daukan ganinsu da na hasko Miki babban club dinsu na duniya Dake kasar Paris da Kinga Yan Mata da samari masu kuruciya Yan Shekaru dubu hudu hudu,mu a Nan mutane Ana cewa Sweet Sixteen to su Sweet thausand ake cewa,Hajiya Tace mashaallah daga gani zasuyi kyau,Malam yace Bari ke dai ai wata under age Dana gani shekararta dubu uku da dari biyu karki ganta,mun fafata soyayya da ita,wani Kiss data taba Yi min lokacin Muna ganawa da ita cikin bacci na ta kawo min Ziyara sai da na kwashe wata Uku cur banci abinci ko cokali Daya ba ke ko digon ruwa Bai shiga bakina ba wannan Dan Sumbatar data min itace cina da Shana kullum sai dai naji cikina dam ai Kuwa na Kara kiba da haske nayi fresh,Hajiya Tace wohohi kaji baiwa Dan Allah,kaji karama,kaga Wanda Allah yayiwa baiwa,Farida Tace wallahi karama ce Kawai Allah ya dafa Malam,Malam yace ku tashi kuje Kawai wani abin Nawa idan Ina fada muku sai ku ce ba Dan Adam bane Suka haife ni ba,Kawai kuje zaku ga Aiki.
Su Hajiya tunda Suka fito suke murna da irin Baiwar Malam Dan Haru da Suka ji.
Farida Tace kiji Dan Allah Baiwa Hajiya kiss da Aljana ai Dole yayi wata Uku a koshe,Wallahi ai kadan daga baiwarsa shi yasa bani da malamin Daya wuce shi.
AsmaBaffa
[1/1, 10:24 PM] Sis Asma: 🧭🧭MAFARKIN FARIDA🧭🧭
MAFARKIN FARIDA IS DEDICATED TO
DUNIYATA AAMNA GP
11-15
Official
By
AsmaBaffa
Page naku ne
Maman Samha
Hauwancy cool life
Ummy Hibban
Safiyyat Nabebe
Maman Humairah&Ikhram
Anty Nurse Zaria
S.y.ssagagi
Maman Baby
Mum Sayyed&Noor
Bilyn Nas
Fatima Auwal
Amina Adamu Usman
Hajiya tana barin wajen Malam Dan Haru da kwana biyu Manal ta daina ciniki ko Kare ba Wanda yazo siye,ta Gama soya awara da uban yawa duf kake ji ba Wanda yazo Manal ta jira Amma Shuru su Farida suna tsakar gida suna kallonta suna dariya,Manal ta gaji da jiran masu siye tace to yau Kuma mutanen lafiya? ai sai Kawai ta ebo a plate da yaji ta zauna tana cin abarta Tace yo kada Allah yasa kuzo siye,Dan wulakanci kamar Kun hada baki tana dangwalar yaji tana ci har ta koshi,Tace cab har yanzu shuru watakil sai anjima za a fara zuwa siye har la'asar ba ko karen da yazo,Manal Dariya ta dinga yiwa kanta su Hajiya suna kallo suna Jin Dadi,Manal ta fara kida da faranti ta saka tarin Awara a gabanta tana kida da cokali tana Waka nayi kwantai....Awara tayi sumbu....azo a siyi sumbu....Kwantaiiiii.....,Gyada ma tun safe ba Wanda yazo siye mutanen layin Nan kalau suke Kuwa? Mana ta sake tambayar kanta Bayan ta tsaya da kidan nata da wakar kwantai,Su Hajiya sai uban Sheka Dariya sukeyi.ganin dare zaiyi sai ta dauki awarar ta fita da ita ta Tara Almajirai tace ga Sadaka maganin masifa ai Kuwa Nan take aka warwashe Awara Tasha hadi.
Bayan ta Gama rabawa ta dawo gida tana hawayen Takaicin asarar awararta data yi su Hajiya suna ta dariya.
Manal tace Allah ya gani ba Sadaka nayi da zuciya Daya ba dalilin kwantai yasa ba Wani Lada da Zan samu idan na sake ma Mala'iku ne zasu jibgeni a lahira.
Da dare suna zaune aka ce Wai Ana Sallama da Farida inji Salisu,Hajiya Tace wannan Yaron da naci yake kace baza ta zo ba tafi karfinsa ba ajinsa bace,Yaron ya koma ya fadawa saurayin Salisu abinda Hajiya Tace,Salisu Yana son Farida yace Dan Allah shiga ciki kace Mata Sako Zan Bata Dan Allah tazo yanzu zata koma,Yaron ya koma ya Fadi sakon Salisu,Hajiya mikewa tayi tare da cafkar Hannun Yaron ta shiga kwada Masa Mari da kyar Yazed ya fito ya kwaci Yaron Yana cewa Haba Hajiya Bai Dace ba,me son naka ai abin a yaba ne, Fuuuuuuuu Hajiya ta fita Kofar gidan da kanta.
Tana fita da bala'i tace Salisu kake ko uban me yarinya ta tafi karfinka ba sa',arka bace,yarinya ta ba matar talaka bace,me na sama yaci bare yaba na kasa? Uban me ka Tara? Mene sana'arka? Waye Ubanka a kasar nan? Ana Haka sai ga Farida ta fito da ruwa a katon kofi tana zuwa babu Bata lokaci ta watsawa Salisu a Fuska da jikinsa gaba Daya,suka koma gida ita da Hajiya Suka bar Salisu da mamaki ya daskarar da shi a wajen,Yana Jin Labari a Unguwa Ashe abin nasu Farida ya zarta hankali ma.
FUZAIL kwance yake a katafaren palonsa na Alfarma,Yana latsa waya fuskar Nan a murtuke,Kuyangu da fadawa dake palon ya Sallama cikin Harshen turanci yace ku je ni bana son wannan shirmen na sarauta Kamar ana bautawa mutum Ni duk irin abin Nan bana so ku daina zuwa Kuna takura min,me Aiki Daya nake so wacce zata na min abinci sai maza biyu masu kula da part Dina that's all,Ni duk abin Nan bana so.
Su dai basa Jin turanci Amma sun Riga sun San halinsa da bukatarsa me martaba ya sanar musu Amma shi yace Dole sai an bawa Fuzail kulawa,Haka Ya Hana a dinga kiransa Yarima amma Ina ma'aikatan gidan sarki ya Zama dole,sabo da Haka Prince Fuzail ake kiransa Dole,Tunda ya dawo Mai martaba ya kawo me koya Masa karatun Addini da Kuma yaren Hausa, Yana da basira Bai Dade ba ya Kara gane yaren Hausar ,Karatun addinin musulunci Kuwa Dama can Yana son addininsa Yana karatu sosai a turai,a masallaci ma Yana daukan darasi wajen wani balaraben Turkiyya da Abokinsa Kuma Dan Uwansa Ameer, yasan Addini sosai,Mai martaba yayi Matukar farin ciki ganin har yafi yaransa na Nan kula da Addini da Kuma halaye masu kyau duk cikin yaransa ba Kamar Fuzail,Duniya kenan dama idan Allah ya tsareka ko a Ina kake baka bin hanyar banza.
Maimartaba ganin Yaron Nasa yasan me yakeyi duk da cewa Dan Adam Tara yake Bai cika goma ba,kowa akwai halinsa me kyau da Kuma marar kyau,sai dai na wani me kyan ya rinjayi marar kyan,wani Kuma marar kyan ya rinjayi me kyau,Kawai abinda ya damu sarki rashin auren Fuzail,bashi da Burin da ya wuce Fuzail yayi Aure tunda ya Kai 32yrs bayan Haka ma abin surutu ne a masarautarsu,Haka Bai son yaronsa ya fada Harkar Mata sanadiyar rashin aure, Mahaifiyar prince Fuzail Kuma sunyi yarjejeniya da sarki zata yarda Fuzail ya dawo Nigeria amma Banda auren talaka,duk da baya Aurenta ya Amince sabo da Yana son rayuwar Dansa ta inganta,yazo ya Saba da Yan Uwansa,tunda Fuzail Yazo sarki yasa ake rakashi wajen duk wasu dangin sarki na birni Dana Kauye sai da duk Suka San Fuzail shima ya sansu,Fuzail sam baya son Hayaniya Bai da fara'a sosai,Bai son Kuma shiga Harkar kowa,asalin bature ne Dan ka'ida,Yana da magana Daya Idan ya kafe a Abu sai dai a kyale shi,gashi rayuwar turai yayi ba kunyar kowa yake ji ba,shi Bai ma San wata kunya ba,sannan akwai son girma baya son raini ko kadan Amma akwai kyauta da taimako Bai son ganin wani a cikin wani Hali.
Fuzail kyakyawa ne na karshen karshe,mutum ne me azabar kyau,idan aka ce kyau to azo wajen Fuzail sabo da shi gaba Daya Mamansa Balarabiya ita yayi Kama da ita,Hasken fatarsa ne Bai Kai na Larabawa ba Amma fari ne wani irin skin ne dashi me azabar kyau,wani Fari-Fari jaja- jaja haka yake,Dogo ne me masifar kyan sura da diri,Allah ya Masa Kyawun diri ko wanne Kaya ya saka sai ya tsula kyau a ciki,sumarsa baka wuluk me santsi ga saje da Dan gemunsa Wanda ya sake fito Masa da asalin kyansa,hancinsa santalele,idanuwansa su ba manya ba baza ace kanana ba farare tas,Dan bakinsa karami lips dinsa wasu jajaye masu birge me kallonsu,hakoransa kanana masu kyau da haske,Gashi Dan gayu kullum cikin daukan wanka yake,Ya iya sa Kaya da gayu Malam,ga kamshi Kamar me kullum cikin kamshi,lissafa irin Baiwar da Allah yayiwa Fuzail akwai Aiki,shi yasa danginsa kaf da gidan sarauta gaba Daya Alfahari sukeyi da Fuzail,kowa Yana kaunarsa gashi dama da kwar jini da farin jini,duk inda ya shiga sai an so shi Kuma an kalle shi,kana gani kasan ba girman Africa bane.
Yayan sarki kaf Mata da
Book Chapters
Chapter 1Chapter 2Chapter 3Chapter 4Chapter 5Chapter 6 Chapter 7Chapter 8Chapter 9Chapter 10Chapter 11Chapter 12Chapter 13Chapter 14Chapter 15Chapter 16Chapter 17Chapter 18Chapter 19Chapter 20Chapter 21Chapter 22Chapter 23Chapter 24Chapter 25Chapter 26Chapter 27Chapter 28Chapter 29Chapter 30Chapter 31Chapter 32Chapter 33Chapter 34Chapter 35Chapter 36Chapter 37Chapter 38Chapter 39Chapter 40Chapter 41Chapter 42Chapter 43Chapter 44Chapter 45Chapter 46Chapter 47Chapter 48Chapter 49Chapter 50Chapter 51Chapter 52