Uwata,Hajiya ta washe Baki Tace to daga yau ba raini Kuma wallahi kika sake taba ta sai ta sa an koreki daga garin nan,Manal Tace ikon Allah yaushe zai zo zance?Hajiya Tace ya kusa zuwa Kinga ko Aiki sai ki dinga zuwa kina Yi a gidan Surakan Farida,Manal ta rike Baki Tace cab Ni Kuma bauta zanyi? Ina Yar uwarta Ina laifin ma a talauce ta siya min mota ta milliyan goma Haka,Baki Suka Bude Farida tace Baki Isa ba wallahi yarinya ai ko keke tunda Baki da mutunci,Manal Tace Dan Allah Yaya Farida kiyi Hakuri ance da ac a gidan ko iya ac ki lamince min in Dan Sha ko ta kwana biyu ce ko ma ta yini Daya ce.
Yazed da Malam suna jinsu suna ta dariyar Haukar Su har Manal da Bata San duk a mafarki bane,Farida tace sai dai idan daga yau Zaki dinga wanke min kayana kina gyara Mana gidan Nan sannan duk wani Aiki ke Zaki Yi q gidan Nan to idan ya aureni har Makkah Zan sa ya kaiki, bana so a dinga Bina gidan sarauta Ana kunyata Ni,Kun San gidan sarauta basa son Hayaniya kudi Ne da mulki dankare a gidan,Manal tafi tayi tace Allah ya yarda na Yar Uwa shike Nan Dan aikin gidan Nan ai karki damu Matukar ac da nake Jin labarinta naurar sanyi zata fifita Ni ba abinda bazanyi Miki ba.
Karki sake Fatarki ta lalace Yaya Farida,Farida Tace ke dalla Yar Kauye Aunty ake cewa Aunty Farida karki sake ce min Yaya Haka Kawai salon Fuzail yazo yaji kauyancinki,Manal tace gaskiya Anty Ina yinki irin wannan soyayya Haka,Farida tace Yau zamu Fara shirye shiryen ya auren Nan nawa zai kasance,littafi ma Zan siyo zamu rubuta komai,Manal tace ai Yasin hakan yayi ayi sauri a tsara komai sabo da idan lokaci yazo komai an tsara yafi.
Farida kallon Manal tayi Tace ranta min Naira Hamsim idan Fuzail yazo Zan biyaki abarki ba kyauta nace a bani ba,Farida da sauri ta fada dakinta tana murna harda Waka ta dakko Hamsim cikin kayanta ta bawa Farida,Hajiya Tace Masatura karbi maza kuje kanti ke da Falaqi ku Siyo littafin ku dawo,karba suka Yi suka tafi siyo littafin,Manal tana kallo Suka dawo aka dakko Tabarma tare da shimfidawa a gindin bishiyar Dake tsakar gidan har Hajiya,Farida ta rike Biro tace ranar Thursday za a fara bikin Haka na gani a mafarki,Hajiya tace Party ne ranar a Raais Guess palace kin San Nan sai manyan mutane maza rubuta,Farida ta rubuta tare da cewa sai Friday ranar Bridal Shower 8pm,Masatura Tace kamata yayi a Juji palace Kin ga sai Gomnoni ne ke shiga wajen sabo da tsada,Farida Tace haka za ayi,Sunday Kuma daurin Aure da Kai Amarya sabo da kar a ja bikin gwara na hau karagar mulki na Zama Gimbiya cikin gaggawa,a mafarkin Nan Naga ba Delay a Harkar bikin cikin gaggawa aka daura.
Hajiya Tace to yanzu Kinga Muna da munafukai da mahassada a Unguwar nan, mutane suna gulmar mu suna zagina cewar Ina fasa Miki,Ina lalata ki,Baki da tarbiyya,to Dan ubansu rubuta duk Wanda muka sani makiyanmu a Unguwar Nan,Yana aurenki zamu sa aci ubansu,Farida Tace Fire for Fire wallahi duk sai mun Rama zasu ci ubansu.
Masatura Tace Haka Maman Haneef ma ta dinga Mana Dariya Wai Ina Mijin mafarki yake,Da Sauri Hajiya Tace munafuka sai anyi auren su lallabo suce zasu kulla alaka Dan a taimaka musu to karya sukeyi Basu Isa ba,Farida tace waye ya Isa ma yazo Gidan sarautata yace zai dinga nuna min yanda Zan gudanar da zamana a masarauta,Hajiya Tace rubuta Maman Haneef itace a farko cikin Bracket kisa Uwar Gulma sai mun sa an kore su daga garin Nan gaba Daya mun siye gidan nasu na gado da suke takama da shi,Haka Farida ta rubuta Kuwa,Hajiya Tace ta Biyu Hajiya Abu Naga tana min gani gani kwana Nan rubuta ta Dole ta ci ubanta Nan gaba,Nan ma aka rubuta,Hajiya Tace saka Sunan Malam Zikirilla Rannan harda Yi min wa'azi Wai na dinga kula da tarbiyyyarki kaji munafuki yarsa na lalata da zai dameni Dan bakin ciki,Farida ta rubuta Malam Zikirillah prison na shekara goma a gidan yari,Rada Hajiya tayiwa Farida Tace rubuta Manal a ciki tsinanniya na tsaneta so nake Ana auren a dauketa Aiki a gidan,ko Kuma kafin a aureki mu kaita can aikin Bauta,Manal Bata iya karatu da Rubutu ba a gabanta aka rubuta sunanta da duk irin azabar da za a gana mata ba tare da ta Gane ba,ita dai tana mamaki akan za a auri me kudi Dan sarki sai a wulakanta mutane Kuma tun ba ayi Auren ba,Yazed ne ya fito cikin kodaddiyar shaddarsa peach zai fita yace Manal tashi bana son ki shiga wannan haukar wannan Mijin da ake lissafi duk a mafarki ake ganinsa,Manal Tace ban Gane ba? a takaice ya Bata labarin a Gaban Kuma su Hajiya,Manal sabo da dariya harda faduwa a kasa tana kwalla tace Wai dama a mafarki ne? Hajiya ce ta Bata Rai matuka taji haushi Manal Shuru tayi ganin Rai zai baci Tace fatan Alheri nake Miki Anty Farida Allah ya tabbatar.
Yazed Hannunta ya rike tare da janta gefe yace bana son fada,karki Shiga harkarsu bare kuzo Kuna tayarwa Malam Hankali idan aiki ne ko mene idan Basu Yi ba kiyi,gidan Nan kazamai ne idan Baki gyara ba babu me Yi kiyi Hakuri da rayuwa kiyiwa Hajiya Biyayya,itama Faridan ta girmeki ki Mata biyayya,nasan halinki da Shiga abinda ba ruwanki wallahi naji anyi fada dake sai na Miki dukan tsiya a gidan Nan,ba ruwanki,duk abinda zasu Yi ba ruwanki kinji na fada miki,ki jira zanyi kokari na sakaki a makarantar Boko da Islamiyya ko ta Gomnati ce sannan Zan dinga koya Miki karatu da kaina a gida,Manal tana murna Tace to Yaya Inshaallah,Fita Yayi Ita Kuma ta koma dakinta.
Kwanan Manal Daya a gidan ta fara aikin gidan Kamar jaka,komai ita ke Yi ga Yaya Yazed ya hanata Taki yi,Idan baya Nan itace take kula da komai na mahaifinsu Malam,Su Kuwa su Farida shirye shirye sukeyi na zuwan Dan sarki abinsu,Yazed gaba Daya ta Gama Kare Masa da talauci ga ba gonakin Malam yanzu,babu nemowa sai shi,Makarantar ma da yake kurin zai sa Manal sai a ta Islamiyya ya saka ta Kawai Allah yasa har boko Ana koya musu,idan ta dawo gida ta Gama uban aikinta Yazed Kuma zai Sata gaba suyi karatu,a hankali Manal ta fara Dan tsintar wani abu,sannan Yana kokarin hanata yin shigar su ta kauye,Yana Dan sata a Hanya kadan,Su Kuwa su Farida ganin Haka sai Suka Fara bakin ciki Suka tsani Manal ganin sai Kara kyau takeyi kyawunta Yana Fitowa duk Kuwa da irin wahalar aikin da takeyi sati Daya tal ta fara canjawa,tsoro ya Kama Hajiya ta ja Farida Daki tace Dan Ubanki Farida tsoron Kyawun Yarinyar Nan ya kamani,Kinga kyau Haka Kamar aljana to wallahi Ina tsoro Kar Yarima Fuzail yazo ta birge shi,Farida ta buga tsalle Tace wallahi wallahi wallahi Kuwa da sai na kashe Manal har lahira da wuka, yankan rago Zan Mata,Nifa na tsani ma yanda Yaya Yazed yake Mata Yana nunawa sunfi kusanci.
Hajiya cikin rada tace Ni ai kau da Kara ba Wani Abu bane a wajena,Muje wajen Malam Dan Haru ayi Mana fata fata da su,mu rabasu ya tsaneta sannan mu rabata da gidan Nan Kawai shine kwanciyar hankali Amma Matukar Muka kyalesu to zasu ci mu da yaki,satin Manal Uku kacal yau da dare Hajiya da Farida Suka saci jiki sai gidan Malam,Hajiya tace Malam na dawo akan Yaron Nan Yazed kaga duk yanda Muka so mu rabashi da Mahaifinsa abin yaci tura,Talauci ma da muka ce ka Dora Masa ba laifi wannan yayi Amma duk da Haka Malam idan ya fita Yana samowa ai a toshe Masa hanyar samun ko ficika kawai,Malam yace shi fa yake daukan nauyinku idan an hanashi Nema wa zai kula da ku,ai gwara ayi Masa Wanda zai koma sai abinda kika ce,ko Uwarsa ya daina tunawa Kawai sai yanda kika Yi da shi Kinga in ya samo kudin ke zai damkawa,Hajiya Tace Allah ya gani bana son kudinsa Ni da yarinya zata auri Dan sarki me kudi Nan kusa me zanyi da kudin Yazed Wanda Bai wuce na Shan garrin kwakwi ba,Ni bana bukatar biyayyarsa ko kudinsa na kusa Zama me kudi nima,sannan idan nayi kudin shi zai min biyayya Dole, Kawai bukatata ka raba shi da Yar Uwarsa Manal,Yana Sonta Kuma Uwarsu Daya ubansu daya,ko uwarta karka Bari ta tuna shima Haka a Raba su Kawai shi ya zauna tare damu Kamar yanda Muke a baya ita kuma a jefata duniya kawai ta tafi ta bar Mana gida,Kuma mahaifinsu Malam shima Kar ya tuna da wata Manal Kawai a rufe shafinta,Malam yayi dariyar Mugunta yace ajiye dubu goma ki tafi cikin kwana Uku ki dawo ki bani labari,Hajiya duk masifa Bata rasa kudin gidan Malam Haka ta zube Masa dubu goma cash Suka tafi gida.
Tun ranar bayan Kwana hudu tsakani Shi Yazed Haka Kawai yaji Sam ya manta ma Yana da kanwa wata Manal,Malam cikin kwana Uku Sam Bai San wata Manal ba shima,Ita Kuma Manal Sam asiri Bai kamata ba,Allah baiyi tsafin zai ci Manal ba,ita tana hayaccinta,,ba Wani Addini take Yi ba amma ita tasan kowa Kuma tana ganewa ba abinda ya faru da ita,Kawai taga Yazed dinta cikin kankanin lokaci ya canja Mata Sam ya nuna Bai santa ba,tun tana daukan abin Wasa har abin ya dameta,Su Farida Kuma ko kallonta basa Yi sai dai zagi da harara,Idan taje wajen Malam ko Toilet baya Bari ta tura shi,a baya su Farida ko kallon Malam basa Yi Amma ganin yanzu Manal suke son Kora sai komai na Malam ya dawo Hannunsu tare da Yazed sun hade Kai sun ware Manal babu me kulata sai duka da zagi kullum.
Manal Gata yarinya ga kuruciya da Rashin wayo musamman da ta taso a Kauye,tana zaune tayi tagumi Yazed ya shigo da kayan cefane,Da sauri ta Mike tana Yaya Sannu da zuwa,Wata Uwar Harara ya zuba mata tare da hankadeta gefe yace ke wacce irin dabba ce? Na sanki ne? Ko kin Sanni? Yaya Manal dinka ce fa wacce kace na dawo Nan birni na bar Kauye zaka kula da ni Amma Yaya Ni zaka manta Dani? Manal fa ta Annatu Yaya Annatunmu fa? Shuru Yazed yayi ya tsaya tunani yace Annatu munyi waya na tambayeta sunanki Tace Bata sanki ba Itama,ya sunanki ma? Manal ta rushe da kuka tare da zubewa a wajen,Hajiya suna daga daki suna ta dariya da murna ita da Farida,Yazed Waya ya zaro tare da Kiran Annatu ya saka a Handsfree tana dagawa suka gaisa tana Yazed ya Birnin yace lafiya Annata,Kinga Wai kin San wata Manal? Annatu Tace Manal? Manal? Kamar na taba Jin sunan Amma na manta Dan Allah karka dameni na gaji da tambayarka wace Manal ban Santa ba,Manal tana Jin Haka ta sake rushewa da kuka tana Annatu ta nice Manal dinki me tallan Furar fa? Manal da kika saka Ni a mota na taho Birni wajen Yaya Yazed,shi dai Yazed ganin yanda Manal take zunduma ihu sai ta bashi tausayi Haka Kawai duk da Bai Santa ba yanzu sai yaji tana bashi tausayi.
Hannunta ya rike yace kiyi Hakuri wallahi na kasa tunaki Kamar na sanki Amma naji ban sanki ba,Manal gani tayi Kawai Raina Mata hankali sukeyi sabo da wauta bakin ciki yasa ta shiga dakinta ta Hado kayanta kaf a Ghana Must go zata tafi tana kuka kanta babu ko dankwali bare Mayafi,Da sauri ta Shiga dakin Malam ta karewa mahaifinta kallo Yana Wheelchair Yana kallonta ,Baki ya tabe yace bana son a tsaya min a Kai Wai bakuwa ce ke ko Kuwa daga Ina kike? Manal Hawaye ya shiga sintiri a kumatunta taso ace ta iya Rubutu da karatu da kafin ta bar gidan sai tayi Rubutu a takarda ta Ajiye musu Amma Kash Bata San komai ba,Bata Yi nisa da karatun ba wannan ibtilain ya fada mata,sai Kawai ta fito da Jakarta ta fita,Hannunta Yazed ya riko ya Kura Mata Ido itama shi take kallo Dan uwanta abin kaunarta Uwa Daya uba Daya,Hawaye ne suke tsiyayowa a idanuwan Yazed Wanda shi Kansa Bai San na Mene ba,Manal tana ta jira ya furta ya tuna itace kanwarsa Amma Ina sai ya kasa cewa komai sai Hawaye,zobensa na azurfa dake yatsansa na tsakiya ya zaro babu dalili ya cirewa Manal sarkarta karama ya zare Dan kwadon sarkar tare da jefar da Kan sarkar,Zoben nasa na azurfa ya zura a cikin silin zaren sarkar ya sakawa Manal a wuyanta da kansa,zoben nasa ya koma Kamar sarka,Jakar Hannunta ya fisge ya Bude ya dakko wani katon Hijab har kasa ya Mika Mata,binsa takeyi da kallo Kawai da mamaki,Kuma a Haka zai ce Bai Gane wacece ba,har yasan ya Bata zobensa Kuma yasan ta suturta jikinta,a fili tace karya ne kasan Ni wace kana sani zaka Raina min hankali wallahi sai Allah ya saka min kana Dan Uwana na jini ashe baka kaunata Yaya,Shuru ya Mata Yana ta kallonta Yana so ya tuna wace Amma ya kasa,Fisge Jakarta tayi tayi tafiyarta cikin sauri harda gudu,tana kuka Kuma Haka ta bacewa ganinsa.
Su Hajiya suka saki shewa daga daki,Manal na tafiya Yazed ya samu nutsuwa a ransa Haka ma Malam rayuwarsu ta dawo Kamar da a baya kafin zuwan Manal.
Kuka takeyi tana fyalla gudu Bata saurarar kowa tafiya Kawai takeyi Bata San Inda zata je ba,Tana kuka Tace wallahi Nima Annatu babu Ni ba ke tunda kika ce Baki Sanni ba,Har Yamma tayi gab da Magriba Bata daina gudu da tafiya ba har tazo wata Arniyar Unguwa Wanda daga ita sai Allah ya Isa Kuma,Unguwa ce ta masu Hannu da shuni,da gani kasan Bata jigari jigari bace,bacin ran da take ciki shi ya hanata kallon ko Ina,Wasu Mahaukatan Motoci ne na alfarma a kalla zasu Kai takwas Suka fito daga wani mahaukacin gida kirar gidan yayi dan yanayi da sarauta,gaba Daya Motocin number dinsu an Rubuta FUZAIL Amma sabo da Manal Bata iya karatu da Rubutu ba Bata ma San Mene ba,Sam Bata su take Yi ba.
Fuzail dake hakimce a Bayan mota Yana karanta jarida ya dago da Kansa kenan yayi Ido biyu da Manal wata kara ya saki tare da furta Horror Oh my God,Idonsa ya rufe Kam Yana ihu Horror ayi sauri a wuce wajen,ai Kuwa motoci suka fisga da matsiyacin gudu tare da barin layin Kamar zasu tashi sama ta glass a tsorace yake kallon Horror Manal ta Mirror tana masifa ita kadai tana kuka Kuma har nushin Iska takeyi sabo da bacin rai gashi Bata San Ina zata je ba,gani Unguwar ba kowa ga dare yayi sai karnuka ke sintiri a ciki sai ta ja jikinta ta koma Unguwar talakawa inda mutane ke hada hada.
UMMIN SADDEEQ
MMN SADDEQ
MAMAN ILHAM
NANA KHADIJA MAHAMMAD
KHADIJA ABUBAKAR HAMZA
UMMU LATEEPHA
M DEWU
OUM ABULKHAIR
Pure water ta siya da ragowar kudin Dake Hannunta ta Sha tare da yin Alwala ta shimfida dankwalinta tare da Gabatar da Sallar Magriba da Isha Bata Saba da Addua ba ga matsala jimgim a kanta amma Bata iya tunawa ba ga inda ya kamata ta Kai kukanta wajen Allah Kawai tana Idarwa ta fada tunanin rayuwarta Wai cikin Bai fi wata Daya ba rayuwarta ta canja Haka,daga zuwa birni gidan mahaifinta wajen Kuma Dan uwanta,Sarkar Zoben Yazed ta shafa Hawaye ya zubo Mata wani zuciyarta ke zafi Kamar ta fashe bakin ciki yasa ta Mike a fusace tana cewa Wai Yaya Yazed da Annatu Basu Sanni ba Kai jama'a hodijam,yo idan ma Malam yace Bai Sanni ba ai bazan damu ba Amma kamar Annatu da Yaya Yazed Ni zasu manta? Aradu yaci ubansa ba Wani Yaya daga yau babu sauran mutunci tsakani na da su Kuma duniya Zan shiga Allah yasa wani yayi min Cikin shege kowa ya huta, Ghana must go dinta ta fisga ta Kara gaba garin sauri ta masge wata Dattijuwa me abincin siyarwa ta tashi da kwanikanta zata koma gida amma sabo da karfi irin na Manal tayi gaba da Dattijuwar Nan tare da kayanta gaba Daya Kuma ko kallonta Bata Yi ba bare ta Bata hakuri,Ran Me abinci ya baci ta Shiga durawa Manal Ashar da tsinuwa,Kaga tsinanniyar yarinya,baza kiyi albarka a duniya ba Shegiya gantalalliya,Manal tsayawa tayi tace yo na nawa kuma ko ance Miki dama Albarka na fito Nema?Ni da Zaki taimaka ma ki nuna min gidan karuwai shi nake Nema Dan Allah ki nuna min,Mutunci na ya isheni so nake naje inda Zan watsa shi,Dan Allah Naga kinyi Kalar Yan bariki nuna min Hanya zanyi amfani da damata ne wajen dai dai ta Kima ta da daraja ta wacce take ta ya mace,me abinci ta karewa Manal kallo yanda ta ganta wata muguwar kyakyawa ajin karshe tasan za a samu kudi da ita Tace yarinya Ni Kuwa nasan Gidan karuwai ai duk garin Nan babu bariki sama da gidana idan kika shiga to darajarki ta dagu,kin shiga wani kundin tarihi a rayuwarki,Manal tace bana bukatar dogon turanci muje gidan,Me abinci ta tattara kwanikanta tare da furta Sunana Hajiya Amaratu,Manal Fuska ba Rahma Tace Manal Bariki nake suna na kenan, Hajiya Amaratu ta dinga dariyar Sunan Tace Manal Bariki? Manal harda guntun turancinta data tsinta a birni Yassss...(Yes)
Hajiya Amaratu Tace bini muje to,Tiryan tiryan suke Tafiya har zuwa Wata kazamar kasuwa wacce Sam Bata da kyau,wani gida na bulon Siminti me Dan kyau Suka shiga,gidan karami ne Amma duk wani Abu na gidan na Yan gayu akwai shi a gidan,Gidan ya kayatu gaba Daya sai
Showing 9001 words to 12000 words out of 153479 words
Yazed da Malam suna jinsu suna ta dariyar Haukar Su har Manal da Bata San duk a mafarki bane,Farida tace sai dai idan daga yau Zaki dinga wanke min kayana kina gyara Mana gidan Nan sannan duk wani Aiki ke Zaki Yi q gidan Nan to idan ya aureni har Makkah Zan sa ya kaiki, bana so a dinga Bina gidan sarauta Ana kunyata Ni,Kun San gidan sarauta basa son Hayaniya kudi Ne da mulki dankare a gidan,Manal tafi tayi tace Allah ya yarda na Yar Uwa shike Nan Dan aikin gidan Nan ai karki damu Matukar ac da nake Jin labarinta naurar sanyi zata fifita Ni ba abinda bazanyi Miki ba.
Karki sake Fatarki ta lalace Yaya Farida,Farida Tace ke dalla Yar Kauye Aunty ake cewa Aunty Farida karki sake ce min Yaya Haka Kawai salon Fuzail yazo yaji kauyancinki,Manal tace gaskiya Anty Ina yinki irin wannan soyayya Haka,Farida tace Yau zamu Fara shirye shiryen ya auren Nan nawa zai kasance,littafi ma Zan siyo zamu rubuta komai,Manal tace ai Yasin hakan yayi ayi sauri a tsara komai sabo da idan lokaci yazo komai an tsara yafi.
Farida kallon Manal tayi Tace ranta min Naira Hamsim idan Fuzail yazo Zan biyaki abarki ba kyauta nace a bani ba,Farida da sauri ta fada dakinta tana murna harda Waka ta dakko Hamsim cikin kayanta ta bawa Farida,Hajiya Tace Masatura karbi maza kuje kanti ke da Falaqi ku Siyo littafin ku dawo,karba suka Yi suka tafi siyo littafin,Manal tana kallo Suka dawo aka dakko Tabarma tare da shimfidawa a gindin bishiyar Dake tsakar gidan har Hajiya,Farida ta rike Biro tace ranar Thursday za a fara bikin Haka na gani a mafarki,Hajiya tace Party ne ranar a Raais Guess palace kin San Nan sai manyan mutane maza rubuta,Farida ta rubuta tare da cewa sai Friday ranar Bridal Shower 8pm,Masatura Tace kamata yayi a Juji palace Kin ga sai Gomnoni ne ke shiga wajen sabo da tsada,Farida Tace haka za ayi,Sunday Kuma daurin Aure da Kai Amarya sabo da kar a ja bikin gwara na hau karagar mulki na Zama Gimbiya cikin gaggawa,a mafarkin Nan Naga ba Delay a Harkar bikin cikin gaggawa aka daura.
Hajiya Tace to yanzu Kinga Muna da munafukai da mahassada a Unguwar nan, mutane suna gulmar mu suna zagina cewar Ina fasa Miki,Ina lalata ki,Baki da tarbiyya,to Dan ubansu rubuta duk Wanda muka sani makiyanmu a Unguwar Nan,Yana aurenki zamu sa aci ubansu,Farida Tace Fire for Fire wallahi duk sai mun Rama zasu ci ubansu.
Masatura Tace Haka Maman Haneef ma ta dinga Mana Dariya Wai Ina Mijin mafarki yake,Da Sauri Hajiya Tace munafuka sai anyi auren su lallabo suce zasu kulla alaka Dan a taimaka musu to karya sukeyi Basu Isa ba,Farida tace waye ya Isa ma yazo Gidan sarautata yace zai dinga nuna min yanda Zan gudanar da zamana a masarauta,Hajiya Tace rubuta Maman Haneef itace a farko cikin Bracket kisa Uwar Gulma sai mun sa an kore su daga garin Nan gaba Daya mun siye gidan nasu na gado da suke takama da shi,Haka Farida ta rubuta Kuwa,Hajiya Tace ta Biyu Hajiya Abu Naga tana min gani gani kwana Nan rubuta ta Dole ta ci ubanta Nan gaba,Nan ma aka rubuta,Hajiya Tace saka Sunan Malam Zikirilla Rannan harda Yi min wa'azi Wai na dinga kula da tarbiyyyarki kaji munafuki yarsa na lalata da zai dameni Dan bakin ciki,Farida ta rubuta Malam Zikirillah prison na shekara goma a gidan yari,Rada Hajiya tayiwa Farida Tace rubuta Manal a ciki tsinanniya na tsaneta so nake Ana auren a dauketa Aiki a gidan,ko Kuma kafin a aureki mu kaita can aikin Bauta,Manal Bata iya karatu da Rubutu ba a gabanta aka rubuta sunanta da duk irin azabar da za a gana mata ba tare da ta Gane ba,ita dai tana mamaki akan za a auri me kudi Dan sarki sai a wulakanta mutane Kuma tun ba ayi Auren ba,Yazed ne ya fito cikin kodaddiyar shaddarsa peach zai fita yace Manal tashi bana son ki shiga wannan haukar wannan Mijin da ake lissafi duk a mafarki ake ganinsa,Manal Tace ban Gane ba? a takaice ya Bata labarin a Gaban Kuma su Hajiya,Manal sabo da dariya harda faduwa a kasa tana kwalla tace Wai dama a mafarki ne? Hajiya ce ta Bata Rai matuka taji haushi Manal Shuru tayi ganin Rai zai baci Tace fatan Alheri nake Miki Anty Farida Allah ya tabbatar.
Yazed Hannunta ya rike tare da janta gefe yace bana son fada,karki Shiga harkarsu bare kuzo Kuna tayarwa Malam Hankali idan aiki ne ko mene idan Basu Yi ba kiyi,gidan Nan kazamai ne idan Baki gyara ba babu me Yi kiyi Hakuri da rayuwa kiyiwa Hajiya Biyayya,itama Faridan ta girmeki ki Mata biyayya,nasan halinki da Shiga abinda ba ruwanki wallahi naji anyi fada dake sai na Miki dukan tsiya a gidan Nan,ba ruwanki,duk abinda zasu Yi ba ruwanki kinji na fada miki,ki jira zanyi kokari na sakaki a makarantar Boko da Islamiyya ko ta Gomnati ce sannan Zan dinga koya Miki karatu da kaina a gida,Manal tana murna Tace to Yaya Inshaallah,Fita Yayi Ita Kuma ta koma dakinta.
Kwanan Manal Daya a gidan ta fara aikin gidan Kamar jaka,komai ita ke Yi ga Yaya Yazed ya hanata Taki yi,Idan baya Nan itace take kula da komai na mahaifinsu Malam,Su Kuwa su Farida shirye shirye sukeyi na zuwan Dan sarki abinsu,Yazed gaba Daya ta Gama Kare Masa da talauci ga ba gonakin Malam yanzu,babu nemowa sai shi,Makarantar ma da yake kurin zai sa Manal sai a ta Islamiyya ya saka ta Kawai Allah yasa har boko Ana koya musu,idan ta dawo gida ta Gama uban aikinta Yazed Kuma zai Sata gaba suyi karatu,a hankali Manal ta fara Dan tsintar wani abu,sannan Yana kokarin hanata yin shigar su ta kauye,Yana Dan sata a Hanya kadan,Su Kuwa su Farida ganin Haka sai Suka Fara bakin ciki Suka tsani Manal ganin sai Kara kyau takeyi kyawunta Yana Fitowa duk Kuwa da irin wahalar aikin da takeyi sati Daya tal ta fara canjawa,tsoro ya Kama Hajiya ta ja Farida Daki tace Dan Ubanki Farida tsoron Kyawun Yarinyar Nan ya kamani,Kinga kyau Haka Kamar aljana to wallahi Ina tsoro Kar Yarima Fuzail yazo ta birge shi,Farida ta buga tsalle Tace wallahi wallahi wallahi Kuwa da sai na kashe Manal har lahira da wuka, yankan rago Zan Mata,Nifa na tsani ma yanda Yaya Yazed yake Mata Yana nunawa sunfi kusanci.
Hajiya cikin rada tace Ni ai kau da Kara ba Wani Abu bane a wajena,Muje wajen Malam Dan Haru ayi Mana fata fata da su,mu rabasu ya tsaneta sannan mu rabata da gidan Nan Kawai shine kwanciyar hankali Amma Matukar Muka kyalesu to zasu ci mu da yaki,satin Manal Uku kacal yau da dare Hajiya da Farida Suka saci jiki sai gidan Malam,Hajiya tace Malam na dawo akan Yaron Nan Yazed kaga duk yanda Muka so mu rabashi da Mahaifinsa abin yaci tura,Talauci ma da muka ce ka Dora Masa ba laifi wannan yayi Amma duk da Haka Malam idan ya fita Yana samowa ai a toshe Masa hanyar samun ko ficika kawai,Malam yace shi fa yake daukan nauyinku idan an hanashi Nema wa zai kula da ku,ai gwara ayi Masa Wanda zai koma sai abinda kika ce,ko Uwarsa ya daina tunawa Kawai sai yanda kika Yi da shi Kinga in ya samo kudin ke zai damkawa,Hajiya Tace Allah ya gani bana son kudinsa Ni da yarinya zata auri Dan sarki me kudi Nan kusa me zanyi da kudin Yazed Wanda Bai wuce na Shan garrin kwakwi ba,Ni bana bukatar biyayyarsa ko kudinsa na kusa Zama me kudi nima,sannan idan nayi kudin shi zai min biyayya Dole, Kawai bukatata ka raba shi da Yar Uwarsa Manal,Yana Sonta Kuma Uwarsu Daya ubansu daya,ko uwarta karka Bari ta tuna shima Haka a Raba su Kawai shi ya zauna tare damu Kamar yanda Muke a baya ita kuma a jefata duniya kawai ta tafi ta bar Mana gida,Kuma mahaifinsu Malam shima Kar ya tuna da wata Manal Kawai a rufe shafinta,Malam yayi dariyar Mugunta yace ajiye dubu goma ki tafi cikin kwana Uku ki dawo ki bani labari,Hajiya duk masifa Bata rasa kudin gidan Malam Haka ta zube Masa dubu goma cash Suka tafi gida.
Tun ranar bayan Kwana hudu tsakani Shi Yazed Haka Kawai yaji Sam ya manta ma Yana da kanwa wata Manal,Malam cikin kwana Uku Sam Bai San wata Manal ba shima,Ita Kuma Manal Sam asiri Bai kamata ba,Allah baiyi tsafin zai ci Manal ba,ita tana hayaccinta,,ba Wani Addini take Yi ba amma ita tasan kowa Kuma tana ganewa ba abinda ya faru da ita,Kawai taga Yazed dinta cikin kankanin lokaci ya canja Mata Sam ya nuna Bai santa ba,tun tana daukan abin Wasa har abin ya dameta,Su Farida Kuma ko kallonta basa Yi sai dai zagi da harara,Idan taje wajen Malam ko Toilet baya Bari ta tura shi,a baya su Farida ko kallon Malam basa Yi Amma ganin yanzu Manal suke son Kora sai komai na Malam ya dawo Hannunsu tare da Yazed sun hade Kai sun ware Manal babu me kulata sai duka da zagi kullum.
Manal Gata yarinya ga kuruciya da Rashin wayo musamman da ta taso a Kauye,tana zaune tayi tagumi Yazed ya shigo da kayan cefane,Da sauri ta Mike tana Yaya Sannu da zuwa,Wata Uwar Harara ya zuba mata tare da hankadeta gefe yace ke wacce irin dabba ce? Na sanki ne? Ko kin Sanni? Yaya Manal dinka ce fa wacce kace na dawo Nan birni na bar Kauye zaka kula da ni Amma Yaya Ni zaka manta Dani? Manal fa ta Annatu Yaya Annatunmu fa? Shuru Yazed yayi ya tsaya tunani yace Annatu munyi waya na tambayeta sunanki Tace Bata sanki ba Itama,ya sunanki ma? Manal ta rushe da kuka tare da zubewa a wajen,Hajiya suna daga daki suna ta dariya da murna ita da Farida,Yazed Waya ya zaro tare da Kiran Annatu ya saka a Handsfree tana dagawa suka gaisa tana Yazed ya Birnin yace lafiya Annata,Kinga Wai kin San wata Manal? Annatu Tace Manal? Manal? Kamar na taba Jin sunan Amma na manta Dan Allah karka dameni na gaji da tambayarka wace Manal ban Santa ba,Manal tana Jin Haka ta sake rushewa da kuka tana Annatu ta nice Manal dinki me tallan Furar fa? Manal da kika saka Ni a mota na taho Birni wajen Yaya Yazed,shi dai Yazed ganin yanda Manal take zunduma ihu sai ta bashi tausayi Haka Kawai duk da Bai Santa ba yanzu sai yaji tana bashi tausayi.
Hannunta ya rike yace kiyi Hakuri wallahi na kasa tunaki Kamar na sanki Amma naji ban sanki ba,Manal gani tayi Kawai Raina Mata hankali sukeyi sabo da wauta bakin ciki yasa ta shiga dakinta ta Hado kayanta kaf a Ghana Must go zata tafi tana kuka kanta babu ko dankwali bare Mayafi,Da sauri ta Shiga dakin Malam ta karewa mahaifinta kallo Yana Wheelchair Yana kallonta ,Baki ya tabe yace bana son a tsaya min a Kai Wai bakuwa ce ke ko Kuwa daga Ina kike? Manal Hawaye ya shiga sintiri a kumatunta taso ace ta iya Rubutu da karatu da kafin ta bar gidan sai tayi Rubutu a takarda ta Ajiye musu Amma Kash Bata San komai ba,Bata Yi nisa da karatun ba wannan ibtilain ya fada mata,sai Kawai ta fito da Jakarta ta fita,Hannunta Yazed ya riko ya Kura Mata Ido itama shi take kallo Dan uwanta abin kaunarta Uwa Daya uba Daya,Hawaye ne suke tsiyayowa a idanuwan Yazed Wanda shi Kansa Bai San na Mene ba,Manal tana ta jira ya furta ya tuna itace kanwarsa Amma Ina sai ya kasa cewa komai sai Hawaye,zobensa na azurfa dake yatsansa na tsakiya ya zaro babu dalili ya cirewa Manal sarkarta karama ya zare Dan kwadon sarkar tare da jefar da Kan sarkar,Zoben nasa na azurfa ya zura a cikin silin zaren sarkar ya sakawa Manal a wuyanta da kansa,zoben nasa ya koma Kamar sarka,Jakar Hannunta ya fisge ya Bude ya dakko wani katon Hijab har kasa ya Mika Mata,binsa takeyi da kallo Kawai da mamaki,Kuma a Haka zai ce Bai Gane wacece ba,har yasan ya Bata zobensa Kuma yasan ta suturta jikinta,a fili tace karya ne kasan Ni wace kana sani zaka Raina min hankali wallahi sai Allah ya saka min kana Dan Uwana na jini ashe baka kaunata Yaya,Shuru ya Mata Yana ta kallonta Yana so ya tuna wace Amma ya kasa,Fisge Jakarta tayi tayi tafiyarta cikin sauri harda gudu,tana kuka Kuma Haka ta bacewa ganinsa.
Su Hajiya suka saki shewa daga daki,Manal na tafiya Yazed ya samu nutsuwa a ransa Haka ma Malam rayuwarsu ta dawo Kamar da a baya kafin zuwan Manal.
Kuka takeyi tana fyalla gudu Bata saurarar kowa tafiya Kawai takeyi Bata San Inda zata je ba,Tana kuka Tace wallahi Nima Annatu babu Ni ba ke tunda kika ce Baki Sanni ba,Har Yamma tayi gab da Magriba Bata daina gudu da tafiya ba har tazo wata Arniyar Unguwa Wanda daga ita sai Allah ya Isa Kuma,Unguwa ce ta masu Hannu da shuni,da gani kasan Bata jigari jigari bace,bacin ran da take ciki shi ya hanata kallon ko Ina,Wasu Mahaukatan Motoci ne na alfarma a kalla zasu Kai takwas Suka fito daga wani mahaukacin gida kirar gidan yayi dan yanayi da sarauta,gaba Daya Motocin number dinsu an Rubuta FUZAIL Amma sabo da Manal Bata iya karatu da Rubutu ba Bata ma San Mene ba,Sam Bata su take Yi ba.
Fuzail dake hakimce a Bayan mota Yana karanta jarida ya dago da Kansa kenan yayi Ido biyu da Manal wata kara ya saki tare da furta Horror Oh my God,Idonsa ya rufe Kam Yana ihu Horror ayi sauri a wuce wajen,ai Kuwa motoci suka fisga da matsiyacin gudu tare da barin layin Kamar zasu tashi sama ta glass a tsorace yake kallon Horror Manal ta Mirror tana masifa ita kadai tana kuka Kuma har nushin Iska takeyi sabo da bacin rai gashi Bata San Ina zata je ba,gani Unguwar ba kowa ga dare yayi sai karnuka ke sintiri a ciki sai ta ja jikinta ta koma Unguwar talakawa inda mutane ke hada hada.
Sharhi Fans.
AsmaBaffa
[1/1, 10:23 PM] Sis Asma: 🧭🧭MAFARKIN FARIDA🧭🧭
MAFARKIN FARIDA IS DEDICATED TO
DUNIYATA AAMNA FNS GP.
7-10
Official
By
AsmaBaffa
Page naku ne
UMMIN SADDEEQ
MMN SADDEQ
MAMAN ILHAM
NANA KHADIJA MAHAMMAD
KHADIJA ABUBAKAR HAMZA
UMMU LATEEPHA
M DEWU
OUM ABULKHAIR
Pure water ta siya da ragowar kudin Dake Hannunta ta Sha tare da yin Alwala ta shimfida dankwalinta tare da Gabatar da Sallar Magriba da Isha Bata Saba da Addua ba ga matsala jimgim a kanta amma Bata iya tunawa ba ga inda ya kamata ta Kai kukanta wajen Allah Kawai tana Idarwa ta fada tunanin rayuwarta Wai cikin Bai fi wata Daya ba rayuwarta ta canja Haka,daga zuwa birni gidan mahaifinta wajen Kuma Dan uwanta,Sarkar Zoben Yazed ta shafa Hawaye ya zubo Mata wani zuciyarta ke zafi Kamar ta fashe bakin ciki yasa ta Mike a fusace tana cewa Wai Yaya Yazed da Annatu Basu Sanni ba Kai jama'a hodijam,yo idan ma Malam yace Bai Sanni ba ai bazan damu ba Amma kamar Annatu da Yaya Yazed Ni zasu manta? Aradu yaci ubansa ba Wani Yaya daga yau babu sauran mutunci tsakani na da su Kuma duniya Zan shiga Allah yasa wani yayi min Cikin shege kowa ya huta, Ghana must go dinta ta fisga ta Kara gaba garin sauri ta masge wata Dattijuwa me abincin siyarwa ta tashi da kwanikanta zata koma gida amma sabo da karfi irin na Manal tayi gaba da Dattijuwar Nan tare da kayanta gaba Daya Kuma ko kallonta Bata Yi ba bare ta Bata hakuri,Ran Me abinci ya baci ta Shiga durawa Manal Ashar da tsinuwa,Kaga tsinanniyar yarinya,baza kiyi albarka a duniya ba Shegiya gantalalliya,Manal tsayawa tayi tace yo na nawa kuma ko ance Miki dama Albarka na fito Nema?Ni da Zaki taimaka ma ki nuna min gidan karuwai shi nake Nema Dan Allah ki nuna min,Mutunci na ya isheni so nake naje inda Zan watsa shi,Dan Allah Naga kinyi Kalar Yan bariki nuna min Hanya zanyi amfani da damata ne wajen dai dai ta Kima ta da daraja ta wacce take ta ya mace,me abinci ta karewa Manal kallo yanda ta ganta wata muguwar kyakyawa ajin karshe tasan za a samu kudi da ita Tace yarinya Ni Kuwa nasan Gidan karuwai ai duk garin Nan babu bariki sama da gidana idan kika shiga to darajarki ta dagu,kin shiga wani kundin tarihi a rayuwarki,Manal tace bana bukatar dogon turanci muje gidan,Me abinci ta tattara kwanikanta tare da furta Sunana Hajiya Amaratu,Manal Fuska ba Rahma Tace Manal Bariki nake suna na kenan, Hajiya Amaratu ta dinga dariyar Sunan Tace Manal Bariki? Manal harda guntun turancinta data tsinta a birni Yassss...(Yes)
Hajiya Amaratu Tace bini muje to,Tiryan tiryan suke Tafiya har zuwa Wata kazamar kasuwa wacce Sam Bata da kyau,wani gida na bulon Siminti me Dan kyau Suka shiga,gidan karami ne Amma duk wani Abu na gidan na Yan gayu akwai shi a gidan,Gidan ya kayatu gaba Daya sai
Book Chapters
Chapter 1Chapter 2Chapter 3Chapter 4 Chapter 5Chapter 6Chapter 7Chapter 8Chapter 9Chapter 10Chapter 11Chapter 12Chapter 13Chapter 14Chapter 15Chapter 16Chapter 17Chapter 18Chapter 19Chapter 20Chapter 21Chapter 22Chapter 23Chapter 24Chapter 25Chapter 26Chapter 27Chapter 28Chapter 29Chapter 30Chapter 31Chapter 32Chapter 33Chapter 34Chapter 35Chapter 36Chapter 37Chapter 38Chapter 39Chapter 40Chapter 41Chapter 42Chapter 43Chapter 44Chapter 45Chapter 46Chapter 47Chapter 48Chapter 49Chapter 50Chapter 51Chapter 52