hankali sai Hakuri yake bawa Belloti karshe yace kayi Hakuri kabar Maganar Neman aurenka na Manal ka canja Budurwa kawai.

Jiya Baffa na matsa Masa sai ya min Istahara a kanka da Manal to dai cikin ikon Allah yace yanzu ma Haka wani ne a ranta ba Kai ba Kuma kasan Istiharar Baffa babu karya,Gaban Belloti ya yanke ya Fadi,tsaye ya Mike tare da Furta yau Istiharar Baffa tayi karya,tsafi dama yakeyi ai ba malamin Allah bane,ka taba gani Istiharar gaskiya anga Abu kururu? Ka fadawa Baffan naka karya yakeyi matsafi,Uban ma waye yace a duba min?nace a ayi min duba Dan Uwarku? Karma ku dauki wannan zance wahala data saka Riga da Wando wannan ita ta jiyo idan taga Dama wahalar ta saka Wando Jeans ma Ni ba ruwana Kuma wallahi ko waye sai munyi rikici da shi akan Manal, Amma yanzu bazan zauna jiranta ba na gano wata cika a kasuwa Ranar Juma'a Ina so farkon watan sabuwar Shekara Januware (January)ake cewa ko ta a watan Kuna ganina ku kirani da Masoyi sai watan Zan fara soyayya karshen shekarar a daura min aure na samu wacce Zan dinga kankamewa cikin dare kafin nayi kudi na dawo da Manal wajena,Dariya Suka dinga yi,Lawi yace to Belloti yanzu fa me zai Hana ka bi Manal can birni? Ina fama da ciki na da kyar nake iya ci da kaina Ina Ni Ina birni ai yanzu Budurwa tafi karfi na.

Kasan mu sai Dole muke cin tuwo a kauyen Nan da kyar nake samun kudin shayi ma bare har nake rike wata,auren gata idan an maka sai dai fa a tukunyar cikin gida kuyi ta cin tuwo,matar tawa Zan dinga bawa tuwo ta lalace Ni da nake so ma Nan gaba na bar shanun Nan na koma birni,idan nayi kudi yarana kullum su Sha miyar dage dage da Mai Amma Nan Kauye sai dai a cika musu ciki da tuwo cikin yara duk ya kumbura kaga Yara Malam ciki Kamar Tulu ga jarabar Shan Madarar shanu cutar da shanu suke Yi wallahi itace take Kama yaran Fulani sabo da direct muke Shan Madara ba tare da an dafa ba,Ni Nan da Dan wani lokaci wallahi fecewa zanyi in tafi Neman arziki birni.

Tafi da dariya suke yiwa Belloti,Belloti yace sai Birni Nan gaba cikin Kano Zan tafi ma gaba Daya na huta da Gulmar mutanen Kauye ga jahilci,Kai Lawi kana da Yan uwa ma a birni ga Maryam Nan Yar birni Dana ita ka so,Lawi yace tab wannan tafi karfi na Shan jini zata Yi lashe money ce Ni inda zuciyata ta mutu ai me kudi nake Nema Yar Birni Bazawara ko Yar shekara saba'in ce Matukar zata dauki nauyi na to tazo ga Lawi a Free,Bazan Mata kishiya ba,kana wannan dajin Uban wa zai ganka Allah Lawi ka auri Ade yafi maka yarinya tana sonka cewar Ja'e, Lawi ya dauke Kai gefe yace Aden banza ta min yarinya me zata min in Banda hauka,Nifa duk kyan mace Matukar jahilace bani ba ita sai wacce Kuma tayi hankali daga shekara ashirin da bakwai zuwa Sama irinsu nake so wacce bata da kunya wajen soyayya Ina shiga gidan Zata min zigidir ta kwalkwale min jikina da soso da sabulu,Wacce ta girmeni me iya soyayya,me tsafta Amma wannan matan namu wasu dagajaja zaka gansu,kana aura ka shiga Uku wallahi Kai da ganin mace dai dai sai dai a lahira idan ka samu na Aljanna,Ina yaro na bazan cuci kaina ba,Duk irin su Belloti Yan matasan Yara Wanda gaba dayansu baza su wuce 25yrs ba suna yawan zuwa birni duk wajen Hutu suna zuwa,takanas suke hada Yan kudadensu su Shiga birni wajen shakatawa a wasu state din zuwa sukeyi su a Dole wayayyu.

Idan zasu tafi ko Sanda basa dauka sannan shaddoji suke dinkawa masu kyau suyi gayu sosai sabo da yaduwar wayar Hannu da kallon Finafinai duk ya jawo har Kauye yanzu sai kaga wasu da yawa sun Dan waye wasu ma baza kace a Kauye suke ba,Dan ma su Belloti a Riga suke sosai Amma Indai za a fita to fa dinki me tsada ake Yi a birni kuma,shi yasa a garin ake musu kallon Yan Iska wayayyu,sune Shegun gari,idan baka zuwa Majalisar su Belloti to baka hadu ba,Su Belloti suna ganin Yan Birni sabo da Haka Suka kulla aniyar Dole sai sun bar Riga Nan gaba shi yasa Basu da Aiki sai zancen kudi da matan aure,Iyayensu sunyi sunyi suyi aure Amma sunki shi kanshi Belloti da. Manal tana da kyau ne Amma yasan yafi karfinta a kauyen,Yahaya yace Kai Belloti kace badan Manal tana da kyau ba kafi karfinta ma,Belloti yace Fadi ka Kara yanzunma sai tazo Naga yanda ta koma Amma har yanzu Ni nasan nafi karfin Manal na fita wayewa Yarinyar tana da kyau ne Kawai Zan rufa Mata asiri,Dariya sukeyi sannan suka fara Alwala sabo da Magriba ta gabato basa Wasa da Sallah su Kam matasan da Dan iliminsu ba irin matan garin ba da Suka sa tallan Fura a ransu ba.


Washe gari da safe Manal ita ce ta gyara gidan tare da tafasa ruwan zafi da Lipton da komai ta ebi nata ta bar wa su Hajjiya nasu,Farida suka fito dama Basu da kudin bread tunda sun samu Manal har sugar ta saka Haka suka eba zasu Sha,ga su Alhaqatu zasu tafi makaranta Basu da ko kudin break,Manal ta Basu kowa Naira dari cikin Yaran tace gashi Nan kudin Break,idan nace Zan siya muku Breadi to baza ku samu na break ba,tunda Kun kurbi Dan ruwan zafin ga na break kowa Naira dari kuci wani abin,Su Falaqi sai murna da godiya,Hajiya ta galla musu Harara tare da furta ku Bata kudinta ai muma Bamu rasa ba,Da gudu Yaran Suka fice sai makaranta,Manal ta sharesu taci gaba da safgarta.

Fuzail Tunani yake ta faman Yi ta wacce Hanya zai fitar da Manal daga Talauci ya rage Mata wahala kadan ta yanda baza ta Gane ba Kuma baza ta tsargu ba,Ameer ya Kira a waya da turanci yace kazo Ina son ganinka,Ba a dauki lokaci ba Ameer yazo part din Fuzail,Fuzail yace Akan Yarinyar nan ne ya kamata na rage Mata talaucin Nan nasan yanzu tana can tana wahala Taya zata dinga samun wani kudin ba tare data Gane ba Kuma yanda baza taji komai a ranta ba?
Ameer yace wlh Nima nayi tunanin hakan,Amma abinda za ayi Ni a ganina kawa zaka Yi Mata wacce baza ta Gane ba kaga kawar sai ta dinga zuwa wajen Manal ta Nan za a taimaka Mata kawai,Fuzail yace to wa za a saka? Baza mu hada safga da Yan gidan Nan ba kasan Gulmar masu aikin Nan sai su fallasa Abu ya kwabe,akwai Friend dita Shukrah tana Aiki a Hospital,Suma dai su Shukrah ba kudi ne da su ba amma tana Aiki sannan suna da Dan rufin asiri,Nima mutuncin da mukeyi kanwata da aka kwantar a asibiti ta kular min da ita sosai shi yasa muke Dan gaisawa ita zamu kaiwa wannan aikin a matsayin ita ce zata dinga taimakon Manal kafin ayi bikin,Bari Zan kirata idan tazo sai mu tsara yanda komai zai kasance.

Da farin ciki Fuzail yace sai ta dinga Dan koya Mata karatu ma Sannan tana Dan Wayar da ita,Ameer yace Yeah ai Kuwa Shukruah Yar gayu ce ta waye da yawa,sabo da Murna Fuzail har da dukan kafadar Ameer Yana dariya,Ameer Dariya yayi yace Kai Mene Haka duk akan Manal din ne Allah ya yaye maka,Fuzail yace muje can Guess House a kirata please na matsu ,Ameer ya Mike Suka fita zuwa Guess House dinsa ,Fuzail yace Mata akwai munafunci wasu babu sirri sabo da tsaro ya dakko wani sabon hular gashin wani kitson Bob merly ya saka a Kansa me yawan gaske sannan ya Kara gemu da Sajensa tare da Manna face mask again duk Dan kar Shukrah itama ta Gane shi taje garin dadin zancensu na Mata ta fadawa Manal,Amma yanzu ita da me kitson Bob merly ta sanshi sannan Bata ga bakinsa da hancinsa ba bare Tace.

Kamar Yanda Shukrah tace 15mnt ta bar Hospital da uniform dinta tazo Guess House din babu tsoro tasan Ameer sosai,Tunda tazo katafaren gidan take kalle kalle Kamar Yar Kauye sabo da haduwa da tsaruwa,Musamman da ta Shiga palon kamshi da sanyi ya Dake ta,tunda ta shiga ta gaisar da su Fuzail tunda ya amsa sau Daya tal ya maida Kansa Kan waya Yana latsawa har Suka Gama maganarsu da Ameer Bai ce kala ba,Yana Jin yanda Suka tsara komai da Ameer,shi kanshi Ameer cewa yayi Kanwar abokinsa ce Manal Yana so ya taimakesu amma Bai so ta Gane shine zai taimaketa,ita kanta Shukrah ninke ta sukayi Bata San komai ba,Ameer Kuma yace Kar ta nuna ta sanshi ko sunansa ma,Nawa za a biya ki? Shukrah Tace dan wannan aikin sai an biyani ai mutunci yafi kudi idan nayi fa Nima Zan samu lada wallahi ban bukatar sisi.
Ameer yace duk da Haka zan dinga Baki kudin transport,Shukrah tayi godiya ta Sha wankanta cikin Uniform fari,harda farin Glass dinta,Chocolate ce kyakyawa da ita doguwa Amma zata Yi 25yrs ta girmi Manal nesa ba kusa ba.

Tana ta tunanin waye wannan,sai Ameer yace wannan Yayana nane Sunansa Ammar, Shukrah Tace a ranta wannan a Haka Wanda ko arzikin kallo Bata samu ba Kuma yaki magana gashi wankan nasa na azaba ya tafi da Imanin Shukrah,sai taji ya birgeta taji tana wani sonsa a ranta tana son Namiji me aji ga iya daukan wanka gashi da gani kasan ba karamin me kudi bane ita duk da kitson Nan na Bob merly ya birgeta iya wankan Kawai ta siya,Addua take Ina ma zai so ta,ko Dan shi sai ta dage tayi aikin Nan ko zata samu ya sota sabo da yawan Mu'amula da su zai iya fadawa sonta.
Ameer ne ya Bata dubu goma yace Taki ce Transport,sannan ya sake Bata 20k yace wannan Kuma na Manal kin Gane yanda nace zakiyi Mata kyautar ko? Shukrah tayi murmushinta me zafi Dan ta Burge Ammar wato Fuzail sabo da taga Ya kalli inda suke tsaye da Ameer,Suna gamawa Shukrah ta tafi abinta tana murna ita yau taga Miji tayi Gam da katar.

Yanda Ameer ya Bata Address din gidan su Manal Nan ta wuce Direct a Napep,gidan ta shiga da Sallama,Hajiya tana tsakar gida tana wankewa Farida kayan sawarta su Masatura suna tayata,ganin mace da Uniform Hajiya ta Bata Rai tace Allurar rigakafin aka fara ne ko Allurar polio dince haka Baku da Aiki sai rabon maganin jaraba Gomnati Bata San ta bada kyautar Kudi ba sai magani,mu yanzu ba magani bane a gabanmu yawwa a Kara gaba Bama so,Shukrah ta Bude Baki da mamaki daga shigowa ko amsa Sallama babu,Tace Manal nake Nema Dan Allah, Farida tana daki ta saka waya a gaba tana ta kallon Hotunan Yarima Fuzail tana nishadi,Fuskarsa ta kurawa Ido Tace kudi ba karya ga kyau ga kudi wayyo Allah na Dan Allah kayi sauri kazo ka Fara zubar min kalaman kauna ai wallahi tun a waje basai anyi aure ba ko Jerusalem Dina kake so tuni Zan baka,tunani ne ya fadowa Farida me zai Hana tun yanzu ta fara gyaran jiki,gyaran Amarya ta fara Shan maganin Infection da maganin Karin ni'ima kafin Yarima yazo ta Gama haduwa tsaf tana Haka taji muryar Wata tana neman Manal,Jin ance Manal sai ta fito da sauri taga uban wace ke Neman Manal.

Tana Fitowa ta kalli Shukrah Yar gayu tasan ma me zatayi da Manal ko a kawa, Farida ta kyalkyale da dariyar Mugunta tace Hala sata tayi muku? Nasan tunda nake ganin kudi a Hannunta sai dai sata ta koma,Shukrah ta dinga mamaki Yan Uwa suna Haka a junansu,dama Ameer yace ta kula da su,Shukrah Tace Dan Allah tana ina? Farida da sauri sabo da mugunta Tace muje na rakaki dakinta,Manal tana kwance ta fara bacci Ma taji Muryar Farida tace tashi Dan Ubanki anzo kureki,Manal ta Mike zaune a tsorace Idonta ya zazzaro ita tasan Bata da kawa a garin Nan bare wannan Yar gayu Haka ai Dole ma laifi tayi,Murmushi Shukrah tayi ta wani Yi acting kamar gaske Tace yanzu Manal Baki Gane Ni ba? Gaskiya kin bani haushi,Nurse ce fa Shukrah wacce kika taba Kai wasu marasa lafiya maza samari su biyu kin tuna? Manal ta tuna Sanda ta Kai su Ameer asibiti da sukayi hatsari Amma ita Bata Gane Nurse din ba,Dama Shukrah karya tayi a private Hospital take Aiki ba wata Manal data sani.

Manal Tace ban iya ganeki ba,Farida dake tsaye tana Jin gulma Jin ance maza da sukayi hatsari an kaisu asibiti Nan tasan su Farooq ne da suka cuceta ai sai taja Tsaki sabo da tsanar da take yiwa Farooq tayi gaba abinta Bata son Jin ko sunansu,Manal Kawai murmushi tayi Tace wallahi na kasa tuna ki kiyi Hakuri,Shukrah tayi Dariya Tace ba komai dama Kawai kin birgeni ne ganin yanda kike da tausayi gaki da hankali yarinya karama Dake kuma shi yasa nace Inshaallah sai na nemi gidanku,Rannan Katsam kin fito siyen Abu Ni kuma Zan wuce ta layin Nan Naga kin shiga gidan Nan shi yasa nazo yau na tambaya Ashe ma Nan ne gidanku,Manal Tace Amma na gode lallai kina kaunata,da fatan Zaki Zama kawata? Shukrah ta tambaya.
Manal da sauri Tace ba matsala na gode Dama bani da kawa ko Daya na samu abokiyar Hira,a wacce Unguwa kike? Shukrah ta fadawa Manal inda gidansu yake tare da cewa ta Nan layin nake wucewa idan zanje wajen Aiki Zaki dinga ganina akan lokaci,Manal tana murna tace to na gode Bari in kawo Miki ruwa.

Manal tana fita Shukrah ta zare dubu Uku ta daga pillow din Manal ta Ajiye Mata dubu ukun ta zauna jiranta,Manal tana shigowa da pure water Guda biyu a leda Shukrah ta Mike Tace sauri nakeyi Kawata bani na Sha na tafi, Shukrah ta Sha ruwan da sauri sannan Manal ta rakata har bakin Titi ta dawo gida tana tunanin me zasu ci da dare dubu biyun da Ameer ya bata sun Kare a abincin Rana da kudin makarantar su Falaqi,Zama tayi tana tunani gobe da me zasu karya ga Yara kanana,da ace ma iya su manya ne da sauki Amma yaro karami Yan makaranta a barsu da yunwa ga yunwar makaranta,gajiya tayi ta Mike ta fito ta Iske sun Kuma Bata gidan da Yamma ta share ta gyara.
Hajiya duk kudin da suke samu sai su Hana cikinsu su kaiwa Malam ko su siyawa Farida kayan kwalliya da gyaran jiki.

Suna zaune Yara suna Islamiyya Manal tana Jin hirarsu da Hajiya suna gani Basu da abin da zasu ci Amma Hira sukeyi Farida tana cewa ya kamata Hajiya na fara gyara jikina irin na amare sabo da Kar yazo yace bikin Nan a kusa yake sonsa maganin Sanyi da Wanda zai Dan karawa mace lafiyar jiki ya kamata ace Ina amfani da su kafin yazo,Hajiya Tace af ya akayi basirar mu ta Kare ai ya kamata yanzu tunda ba kudi zanje wajen Yaya Sani ya bani ko dubu biyu ce a Nemo Miki maganin Sanyi ko kala biyu ne masu kyau ki fara Sha yanda da yazo ko gobe ne a shirye muke,Manal ta kallesu tayi Dariya Tace wallahi Allah ya kamata a kaiku gidan masu tabin kwakwalwa,asibiti ya Dace a kaiku a auna hankalinku.

A duniya idan da a Film naji Ana Haka wallahi Zan zagi me film din ne zance karya ne,wani abin idan kaji a duniya sai ka rantse bazai taba faruwa a gaske ba,Amma sai kaga abinda yafi Haka ma yana faruwa a gaske mutane Kamar Basu da hankali idan suna wani abin,akan son zuciya da son kudi,son kudi duk ya haukata ku na tabbata yariman Nan da kuke so da ace talaka ne duk kyansa baza ku so shi ba,Amma sabo da kudi duk Kun maida kanku wasu zararru,Unguwar Nan sai gulmarku akeyi dangi da mutanen arziki ba Wanda Bai fada muku gaskiya ba kunki yarda,Mafarki har abin dogaro ne?,ke ba wata Waliyya ba bare ace wata Aya za a saukar a kanki,Dan Allah ku rungumi talaucinku mu dawo gaskiya mu nemi sana'ar Yi wacce zamu dogara da kanmu mu rufawa kanmu asiri mu hada kanmu, shirmen Nan mu daina mu zauna mu nemawa kanmu mafita Dan Allah Hajiya kece Babba ki daina wannan abin ke fa ya kamata ace kina Yi Mana fada kina Dora mu akan hanyar gaskiya,kece me Bamu tarbiyya Amma kin zauna Farida ta Gama lalacewa duk wata hira da kalaman Banza fada takeyi a gabanki Kuna Hira Kuna Dariya Kuna tafawa Dan Kawai kina da ya Budurwa,a kanki aka taba haifar yarinya budurwa,na tabbata abinda Farida keyi a gabanki ko da kawarta Ruma basa haka.

Yarki ce fa,kowa Yana so yaga Dansa ya Zama na gari duk da nasan yanzu Haka matasan Iyaye ke Yi gani suke wayewa ce da birgewa ka haifi yarinya budurwa sai su maida ta kawarsu,duk Maganar da Uwa taga Dama fada take a Gaban yarta,suyi Hira su tafa duk inda zata je su tafi tare tana nunawa duniya Yarta ta girma tayi Kai Daya da ita,shigar banza da kayan shafe shafe duk ita ke Dora Yarta akai ko yaranta Mata,tana Alfahari da su,a Gaban Yara Uwa zata ci mutuncin mijinta Kuma ubansu,wasu su tayata kishi harda masu gaba da Iyayensu maza akan anwa Uwarsu kishiya,su hadu da Uwar a gallazawa kishiya da yayan kishiya azaba,su Hana ubansu kwanciyar hankali,shi yasa yarinya sai kaga tafi karfin Iyayenta yanda taga Dama Haka zata fadawa uwarta magana son ranta,karshe Kuma Uwar data lalata su itace zasu gagareta ta rasa inda zatayi da su karshe ita kanta sai dai ta Kai kararsu wajen Iyayenta kakanni idan suna
Showing 36001 words to 39000 words out of 153479 words