[1/1, 10:23 PM] Sis Asma: 🧭🧭MAFARKIN FARIDA🧭🧭
COPY BY ZAINAB BUTALAWA







BISMILLAH


INA MATUKAR GODIYA GA ALLAH DA YA BANI IKON RUBUTA MUKU NOVEL KYAUTA BANA KUDI BA FANS,WANNAN SADAUKARWA NE GAREKU MASOYANA NA AMANA.






BA NA KUDI BA NE




WANNAN NOVEL SADAUKARWA NE GA YAN GROUP DINA NA


DUNIYATA AAMNA FANS GP.








1-3







LITTAFAN DANA RUBUTA
SUNE

GASKIYA CE
MA'AIKACIYAR GOMNATI
CIRANIN AMANA
DUK INDA TA FADI
KAMARSU CE DAYA
KASUWANCI NA
JIN DADI SABO
ME MAGANI
TUBABBIYA
HADIN KAI
RASHIN SA'A
TA GYARU
YAR KWANGILA
ADDUAR KAWA
GIDAN GWAURO/DAN NAZIA
DANGIN RABI
DUNIYATA AAMNA
MAFARKIN FARIDA....








Official










By
AsmaBaffa












Page naku ne

UMMI DEEJAT
MAMU GALADIMA
ALHUSNA (MRS IDRIS)
AUTA
HAFSATOU
NAFEE














Baki ta cuno gaba tana baccinta tana mutsutsu tare da kankame jikinta waje Daya tana sake cinno bakinta gaba,Juyi tayi tare da Bude hannaye kamar zata Rungume wani tana Kara turo labbanta gaba,wata Dattijuwa ce wankan Tarwada ta fito Daga daki sanye da t-shirt da zanin wata jar atamfa Wanda atamfar da t-shirt din sun Gama Jin jiki,sun kode sun jeme sun fita a hayyacinsu,wuyan rigar har ta farke,daga bakin wuyan kamar bera ya gwigwiye,Kanta ba Dankwali gashinta Kamar shekar Ungulu,an Masa kitso Amma kitson ko jela babu sabo da Rashin gashi na wannan dattijuwa,Kitson ya Gama tsufa tukuf shima.

Yarinyar da baza ta wuce 19yrs ba wacce ke bacci a saman wata fukatacciyar Tabarma karkashin bishiyar mangoro,Dattijuwar ce ta shiga tashinta Farida....Farida....ke Faridaaaaaa......a firgice Budurwar ta farka ta Mike zaune tana wani murmushi ita kadai ta kalli kasa Kawai tayi wani mutuwar zaune tace Hajiyanmu.... Hajiyata wani mafarkin ne,wallahi wani mafarkin ne,mafarkin da nake tayi kusan kullum,mafarkin hadadden,zukeken,santalelen charming prince,the Handsome prince,The Honey Prince and Amazing prince Hajiya,Iyyeeeeee...Dattijuwar da aka Kira da Hajiya ta furta,tana wani washe Baki tana murna ka rantse itace tayi mafarkin,Farida tace Hajiya karki so ki ganshi kamar Aljani sabo da kyau,fari wani irin haske me wani sa Ido dum da shi Hajiya,Dattijuwar ta karyar da Kai gefe tana uban murna tana kallon Yarta tana Iyyeeeeee,Ehemmm....Ina jinki Farida ta.....

Farida taci gaba da furta yau mafarkin ya banbanta Dana kullum Hajiya,yau a wata duniya na hango mu Ni da shi,munsha fararen Kaya,Yana cikin wata shegiyar suit fara zata Kai million Hamsim,Eyemmmm Hajiya ta Furta da karfi tana murna tana washe Baki,Farida taci gaba da cewa Hajiya da mota fa naje Wajensa wata baka zata Kai ta Million dari da wani Abu,shi Kuma tasa motar fara zata Kai wajen million dari uku da wajen saba'in da Yan kwandaloli, Dattijuwar rawa ta fara da Juyi sabo da Murna tana Waka
Lale Iye rambada
Lale Iye Rambada
Wallahi 'yata ta Haye,kwana Nan Zan fara gani na cikin Lace da manyan shaddoji,ai matar Gomna ma Uwata karya ne ta kaini hutawa,kwana Nan Zaki rushe Mana wannan gidan na talauci ki Gina Mansion,Takawarki Lafiya Gimbiya Farida.

Ai Farida wani Dadi ya sake kumeta Jin kirarin da Hajiya ke Mata,Farida Tace Hajiya ki tsaya kiji karashen mafarkin Mana,Hajiya tana ihun murna Tace Ina jinki Yata ta kaina,Farida tace Ina fada Miki da naje da motar million dari din Nan shima yazo data million dari uku da haya haya ai sai Muka fito Hajiya Ina Jin kunyarki Amma Zan fada Miki tunda bana boye Miki komai,Hajiya da sauri tana wangale Baki tace Allah na tuba Farida me kike boye min ai nice mahaifiyarki Kuma kawarki,wannan Abu ma da ya samu idan mafarki ya tabbata ai Zan shiga daula karki ji komai fada min ko kunyi aure ne a cikin mafarkin? Farida tana dariyar murna tace Ashe kina da kwakwalwa Hajiya ta munyi aure Muna soyayya,ya Rungume ni fa a jikinsa kam,Hajiya tana rufe Baki Amma tana tuntsurewa da dariyar murna ta furta kudi suna Kan hanya mun kusa Zama masu kudi,daga Nan sai aka Yi Yaya Kin Haihu a cikin mafarkin? Farida tace a'a an dai daura Aure Muna soyayya Ina jikinsa Hajiya yayi min wani mahaukacin Kiss sai na ganni a wata Aljannar duniya gaba Daya wajen American Dollar ne sun baibayeni sune grass din wajen,Ai Hajiya sai ta saki rawa da Juyi bilhakki sabo da Murna.

Farida Tace a wajen yace Baby ki bani Jerusalem naki,Ihu Hajiya ta kurma tana wayyo wannan yasan soyayya na Gane Jerusalem din da yake nufi yo in da kudi me zai Hana,Farida tafin murna tayi tare da mikewa tsaya tana Juyi tana Taku dai dai tana yanga,Hajiya tana kaga gimbiya Takawarki Lafiya ta prince ikon Allah,Alherin Allah ya Kai Miki wata tafiyar sai a Birnin tarayya,Farida Tace hmm ai kafin a Kai ga na bashi Jeru din Hajiya sai na farka,Hajiya da tausayi Tace wayyoooo banji Dadi ba,Amma karki damu Dole mu tafi gidan Malam Haru Haru ya fassara Mana wannan mafarki,wannan Bai kamata ayi ta mafarki shekara kusan biyu Amma Bamu San ma'anarsa ba,nasan ma mijinki ne,shine Zaki aure,ai tunda na tsuguna na haifeki kika Fado duniya naji a jikina ke matar manya ce,ke matar Hamshakin me kudi ce, Farida tunda na haife ki naji a jikina da ke Zan jingina,a jikinki Zan huta,kece silar arzikinmu,nasan ma ya kusa kawo Kansa gareki,nasan kwanan Nan zaizo Neman aurenki.

Farida ta sheka da gudu ta Kai karshen bangon gidan ta dawo wajen Hajiya sabo da Murna ta rasa inda zata sa kanta tana haki Tace Hajiya ya kamata na fara koyon tafiya da takalmi choge,ya kamata na iya yanga da karairaya,sannan yanzu ne ya kamata na fara canja salon Taku da magana a city din Nan,so nake kowa ya kalleni yasan Ni ba matar Kana Nan Yara bane,maganata ta koma ta Yan gayu sabo da kar Prince yazo ya Iske Ni ba Yar gayu ba,kin San su manya ne sun Saba da Yan gayu,Hajiya Tace yo ai ba ke kadai ba Farida har Dani sabo da Nima Kar Iyayensa suzo Yan gayu ban iya magana da taking gayu ba,Maganar Hajiya ta fara gwadawa itama.

Sassanunku da zuwa...kit Farida ta katseta Tace turanci fa Zaki Yi Hey ku shigo haka Zaki ce,Hajiya tace Hey ku shigo sannunku da Hanya,Sai ki Kara da Wow cewar Farida tana Gyarawa Hajiya,Hajiya Tace to Kinga dai Farida ke Baka ce Amma kyakyawa Black Beauty,Yan Uwanki Kuwa Manal da Yazed ne kadai Farare sabo da kyan Yarinyar Nan bana so ta rabe mu,to yanzu ma ke gashi Allah ya kusa yanke Mana zakiyi aurenki da wuri gobe sai mu shirya muje wajen Malam Muji Mene ke tafiya.

Daga cikin wani dagargajenjen daki Wanda gaba Daya ya Gama rubewa dakin Kamar zai Rufta duk Kuwa da cewa na Bulon Siminti ne,wani Mutum ne ke buga Kofar ta ciki wacce a kulle take gaba Daya,sai lokacin Hajiya da Farida Suka kalli Kofar Dakin suka ja tsaki a tare ,Hajiya Tace na Gama tsanar tsohon cen wlh ban San kaddarar da tasa na aure shi ba wlh,tunda nake sai yanzu na gane tsohon Nan bashi da mutunci sam, Farida Tace kece Hajiya kika cuce mu ke da Zaki auri me kudi da yanzu a can gidan me kudi aka Haifo mu Amma sai gashi kin Kare a malam,Wai shine Baban mu,wlh Ina Jin kunya Ni bana son nuna shi ma,shi yasa bana so Kawayena su dinga zuwa suna ganinsa a matsayin Mahaifi na wallahi Ina su Alhaqatu ne da su Masatura?Hajiya tace ai duk suna makarantar Allo Falaqi ne Kawai Yana dakinsu zazzabi ya rufe shi,Ina Uban Iyayin Nan Yazed? Hmm Hajiya ta tabe Baki Tace Yana lecture Bai dawo ba sai wani dagawa yake shi a Dole ya kusa Gama Degree Dan Iskan fikalallen banza,Degree din banza ya Gama Degree dinsa yazo na bashi Aiki cewar Farida.

Wata yarinya ce ta shigo zata Kai a kalla 9yrs,Farida tace Sa'iha ta dawo ga Sa'ihar mu ta dawo,Sa'iha ta karaso da gudu da Allonta tare da fadawa jikin Farida tadagata sama suna dariya,Kofar da Malam yake ce ta sake Kara yana ta dukan kofa babu Wanda ya kulashi sai da Yazed ya dawo daga lecture sanye cikin kana Nan kayansa Wanda sun Sha jiki da gani kasan Yana fama da talauci gashi kyakyawa fari tas da shi da gani shi ya fita zakka a gidan,da gudu ya karasa dakin Malam ya bude ya Iske Dattijon har ya Fado ma daga saman kujerarsa ta guragu wheelchair wanda shi ba gurgu bane da kafafunsa Amma baya iya hasalawa Kansa komai Dan Ma Allah yasa hannunsa Yana Dan aiki,Yazed yace Malam Ina Za'a kaika kayi Hakuri bana gidan Ina makaranta,Malam Ya kalle shi cike da kauna maganarsa da kyar take fita sannan ya furta Allah ya maka Albarka Yazed,kana cikin Wanda na zalunta a baya Amma yanzu Kaine gata na Malam ya fashe da kuka sosai,Yazed lallashinsa ya shiga Yi yace Malam Ka daina damuwa wlh Ni ban rike komai ba,ya wuce kana Mahaifina Ni bana son ganin kukanka.

Turo shi yayi a hankali tare da fito dashi waje ya kaishi toilet wacce ko wanketa ba'a Yi gaja gaja da wari,Ruwan wanka ya Kai Masa,ya maida shi Kan wata kujera Dake toilet din ya zauna sannan ya fito da Wheelchair din waje,Dakin da Malam yake ciki Nan Yazed yaje ya share ya gyara Masa ko Ina fes ya fesa Masa wani Roomfreshner me kamshi Dan dari biyu da Hamsim,Sai da Malam yayi wankansa fes tare da daura Alwala sannan Yazed yaje ya fito da shi,Ya taimaka Masa ya shafa Mai tare da canja Kaya sun Sha wanki da guga wannan aikin Yazed ne.

Kafin Malam yayi Sallah Yazed ya fito ya kalli Farida Dake zaune tana Shan kunu yace me aka dafa yau? Sai da tayi minti biyu kafin tayi magana Sabo da ta rigada tayi mafarki ta Zama matar Dan sarki prince,tana yanga tace shinkafa da wake ce tana kitchen,Amma Dan wulakanci shine kuka bar Malam da yunwa tun safe da ya Sha Kunu da kosai har 5pm Bai ci komai ba,uban waye yake siyo abincin gidan idan ba Malam ba da dukiyarsa yake ciyar damu Yana tufatar damu da komai ma Amma shine za a dafa abinci baza a bashi ba? Hajiya ce ta fito Tace to jarababbe me hakkewa kannai baka da Aiki sai masifa idan Yana Jin yunwar uban waye yace Kar yayi magana a bashi abincin aikin banza,Tsaki Yazed ya ja Kawai ya Shiga Rubabben Kitchen din da Kansa ya zubowa Malam abinci a plate ya Iske Hajiya ta yanka harda salat da tumatur ya zuba,shima ya zubawa Kansa ya shige dakin Malam.

Malam Wanda Kansa Bai daguwa sosai da kyar yake iya ciyar da Kansa abinci sai Yazed ya hutar da shi ya dinga bashi a Baki Kamar kullum yanda ya Saba har Malam ya koshi sosai ya Sha ruwa Yana ta sawa Yazed Albarka,Shima Yazed yaci Abincinsa sannan ya tura Malam Suka fito ya kaishi Kofar gida gindin bishiyarsu ta Dattijai da suke Zama suna Hira Nan ya kaishi sabo da ya shakata,ai Kuwa suna ta Hira da abokai.

Shi Kuwa Yazed Toilet din ya wanke da Omo harda Detergent da yake siyowa na wanke farin kaya kullum shi yake wanke Toilet sannan ya gyara dakinsa Dana Malam,Bayan ya Gama yayi wanka ya shirya cikin wani Dan yadinsa dinkin matasa me kyau ya fita gab da Magrib ya dawo da Malam yayi Alwala zaiyi Sallah Shi Kuma ya wuce Masallaci abinsa.
Haka washe gari Yazed kafin ya tafi school shi ya zaro dari biyar kudin cefane ya bawa Hajiya ya fice abinsa ya barsu da bakin halinsu.

Yazed Yana fita Wata Yar wayarsa Tekno ya dakko wacce zata Kai dubu Arba'in da wani Abu irin dai ta matasa da suke Dan rage zafi da ita,Kira ya Danna bugu biyu aka daga Hello Yaya Yazed Manal ce Annatu tana Bayi yanzu zata fito,Yaya Ina yini? Murmushi yayi tare da amsawa yace lafiya lau sister ya kauyen naku? Allah Yaya mu ka daina ce Mana Kauye kana gani ma ginin Bulon Siminti har biyu ne fa a garin mu ai Billahillazi mun Faso gari muma,Dariya Yazed ya saki yace yaushe Zaki dawo gida ne zanzo har kauyen Nan na tattakaki yarinya ba ilimin Boko babu na Arabic itama laifin Annatu ne wlh da tun kina jaririya ta tafi Dake sai da nace ta bani ke na raineki Taki yarda da yanzu a Nan Nasarawa Lafiya kina Jin turanci sis sannan Ilimin addinin ma Sai kinfi samu haba Manal gaki kyakyawa ajin farko na tabbata kika dawo garin Nan ko Miji sai kinfi samun Wanda zai rike ki,gashi karatuna ya dau zafi da ace kina Nan Zaki taimaka min wajen kula da Malam,Kinga mu biyu Annatu ta Haifa da Malam ko ba komai Zaki samu lada,sai na saka ki a makaranta,Manal tace Allah Yaya? Sai nake ganin Kamar tallan furar Nan da nake taimakawa Annatu da ita yafi Lada,inji uban wa? Annatu ga kanwarki Nan Khausar da Khairan ai sun ishi Annatu dama tace kece bakya son zuwa birni.

Manal tace Yaya Annatu tace Allah wani satin zata hado min kayana na taho wajenka Wai nazo na zauna cikin Yan Uwana a gidan Ubana Kawai tunda kaga Mijin Annatu Yayansa su Khausar da Khairan yake kauna Kawai Ni Kuwa baya so na sabo da Ni agola ce jiya ma Sai da ya min duka akan na zubar da nono Manal ta rushe da kuka,Kuma Wai wani Belloti Dan Uwansa zai aura min har an kawo kudin auren ma shine Annatu Tace Kawai wani satin na gudo wajenka, Yazed da masifa yace wani Dan kauyen za a Baki? Wallahi kanwata Uwa Daya uba Daya ko an daura sai nazo an ware auren Nan gwara ki taho dama ke ba Wani hankali ne dake ba,kwata kwata 16years din za a Miki aure? Manal tana Dariya Tace Yaya na girma fa Allah baka ganni ba na Zama zankaleliya,Yazed yace to Ni dai ki taho birni Zan rike ki,idan kika Zo Nan Kinga dama Muna fama da talauci wallahi da kyar muke kaiwa badan ma Yan Uwan Malam Ana kawo Mana Yan kayan masarufi daga gonakinsa na Kauye ba da munci ubanmu,Ni Kuma ranar da ba makaranta sai naje kasuwa wajen uban gidana da nake Masa yaro Yana siyar da shaddoji,Manal tace Allah bazan dawo ba Haka Kawai Ashe wahala kuke Sha a birni,Ni bazanzo na dinga yini da yunwa ba sai dai kayi ta bani Hakuri a Nan Kuwa rigarmu ko banza na Sha Nonon Saniya na koshi,ko garken su Khaltum kawata naje na Sha nono na cika tumbi na,ga kayan marmari shine kake so nazo yunwa ta kasheni,Ni fa Yaya Allah ya gani ban San babu ba,bana Zama da yunwa,inyi talla na kaga a kasuwa inshi Burodi,kuli kuli,Gyada marau marau,in shi kosai na in shi fanke ranar Juma'a Annatu tayi Mana Tuwon shinkafa Miyar Taushe da manshanu ga nama ga tantakwashi in samu in Dibgawa ciki na Taushe Allah aradu Yaya bani dawowa Wani gari naku,Gwara in Auri Belloti na ko banza shayi Nika Sha kullum aradu sabo da Babansa me kuddi ne.

Yazed Yana ta dariyar Hausar Manal Sam Manal hausarta abin dariya wata ma kadan ake ganewa idan baka Santa sosai Bama baza ka fahimci komai ba sabo da fillanci take ji da shi ta taso a Haka ma Dan Annatu tana Mata hausa ne amma wata kalmar ma Sai tayi minti biyu Bata tuno me zata ce da hausa ba,Yazed yace kizo sisto na kullum abinda kike so Zan Baki Baki da matsala kina da Ni kinji,Manal tace yo Yaya kana Iya kashe min kuddi Naira dari kullum? Yazed ya dinga dariya Naira dari har kudi ce,Yace Dari Uku ma Ina Iya kashe Miki kullum,Manal ta washe Baki Tace Yaya Wai Annatu tace Sunana na farko da Malam ya sa min wai Wa'qia? Yazed Yana dariya yace kwarai Kuwa Ni Kuma Wai Falaqi,Manal tace to ya akayi? Yazed yace Ni Nawa sunan da girmana na yanka rago na canja suna,shine da aka haifi kaninmu Malam ya mayar da sunan a Kansa Wai Falaqi,Ke ma Wa'qia Ni na canja Miki na yanka Miki rago na zabar Miki suna me ma'ana kika koma Manal tun kina jaririya sanadin Haka Malam Me Almajirai Mahaifinmu ya tsane Ni,da tuni ma sunanki Masatura,Manal Tace Yaya Masatura Kuma da Naga ta kaina Allah yasa Ina da Kai Yaya,Ai kin San fa Malam Wai shi Dan Babban malami ne me Almajirai shine ya dinga wannan irin abun na malaman gargajiya to gashi yanzu Almajiran ma babu Allah ya jarabce shi da lalura Allah ya yaye masa,Annatu Tace Malam Wai yayi tsiya kala kala shi yasa watakil Allah ya jarabce shi,Yazed yace Uhm ai shi yasa mutane Basu ganin kimarsa tunda kowa yasan abubuwan da ya dinga aikatawa Amma Mahaifin mune mu ba ruwanmu Dole muyi Masa biyayya,Manal tace hakane Yaya ga Annatu ta fito bari na Bata Wayar Ni talla Zan tafi,Yazed yace ki dai Iya Furar Nan in kinzo Zaki dinga Yi Mana Muna Sha,Manal tana Dariya tace to Yaya ta mikawa Annatu Yar kwakurar Wayar wacce ta Sha manni.

Annatu Bayan sun gaisa Tace ja'ira ta tafi tallan yanzu ta dameka da surutu ai tunda me gidan Nan Bai son rike Dan wani Yazed nace Mata Dole ta shirya ta dawo gidan ubanta,wallahi kullum tsangwama,Harara daga tayi Abu zai Mata dukan tsiya,Rannan ma Sai Dana kaita gyara ya sata a gaba sunje gona Wai Bata Yi aikin kirki ba wallahi Haka ya Mata duka sai da ya tsaga Mata kashin hannu Kuma Dan zalunci ya korata tabi shanunsa kiwo ranar ita tayi kiwon shanun ga Hannu ya kumbura a Kan haka nayi yaji na tafi gidanmu Nima da kyar na dawo,gashi yanzu Wai ya kakaba Mata Miji sabo da Yana aikin noma a gonar Baban
Showing 1 words to 3000 words out of 153479 words