⚜❣❣ ⚜❣❣ ⚜ ❣ ⚜ ❣ ⚜ ❣ ⚜


❣ ⚜ ⚜❣

*❣RABUWA CE SANADI❣*

*_⚜BY QUEEN MEEMI_*⚜
❣60❣

_Sadaukarwa ce ga Basheer usman family's_



This page 4 u Anty sis much luv❤


*********

Tafiya suke amota ta inda Dady yake shiga bata nan yake fita ba,fad'a sosai yake mata har driver yayi parkin a k'ofar gidan su ta fito,itakam sharb'ar kuka take kamar me d'akinsu direct ta zarce Sumy na danna waya tace "meya faru sis naganki kina kuka" ta d'ago "na rasa Shuriem wlh ba zan iya rayuwa ba shiba" dai -de lokacin mama ta shiga d'akin fuskarta atamke tace "sai kuje Dady na kira" jikin Sady ya fara rawa duk rashin kunyartaa tana tsoron Dady ,direct falonsa suka shiga yana zaune sai fad'a yake kumayi Umma azaune tana bashi hkr .
Tsawa ya kuma dakawa Sady Sumy tayi gefe suka zauna ya kallesu "wato Dan kunga na sakar muku ko! shine kuke abinda kuke so Musamm ke Sady Naga kanki rawa yake, yanzu inbanda lalacewar zamani har Sady ta santa had'a tuggu akan saurayi dan zubar da kima, kina binsa yana gudunki, wato har ma sharri kikewa Wacca yakeso ko? to Anyi na farko duk cikinku yanzu kuna lvl 4 ko? to ya isa kowacce na bata 2 week ta fito da Miji in ba haka ba zan mummunan sab'a muku" ya kalli Sady "shashar banza da hofi tashi ku bani gu. Asanyaye suka mik'e suka fice. Umma tace "Amma Dady a sauk'ak'a" ya d'aga Mata hannu "dama ku ke sakar musu suyi abinda ransu ke so to ya kau! wlh duk waccen ta sab'awa Umarnina za taga hukunci bazan zauna yarinya ta janyon abin fada."


*****


Tunda suka shiga d'aki Sumy hankali atashe ta kalli Sady dake kuka "ni bansan ya zanba babu Wanda fa ke zuwa guna" Sady ta d'ago "nifa inba Shuriem ba bazan Aureba" Sumy tace "ke bakya jin magana kin faye taurin kai, ni kam dama kinga Uzaifa na sona nice dai nake tsoron sakar masa Saboda yaudarar da Nazi yayi mani sai nake gani kamar shima haka ne. Amma kinga yanzu zan kulashi." Sady ba tace komai ba, tayi shiru abin duniya na damunta .


******

Ab'angaren su Hassay kuwa yanzu hankalinsu ya kwanta domin Shuriem y bawa husy hkr sun shirya inda yake shaida mata manyan sa zasu so ai magana, tayi murna ta sanar da mum .Suna zaune suna hira Wayar Husy tayi K'ara taga sunan miji Suhaima nan ta d'auka yake sanar mata Haihuwar Suhaima wani ubn tsalle ta daka ya shaida Mata an Samu Baby Boy dukkansu kowa ka kalla farin ciki wajen k'arfe 2 suka je asibitin lokacin Suna shirin tafiya don an sallamesu hassy ta k'an-k'ame Jariri Mum ta roki Safwan da yabar Suhaima tazo gida wanka, bai musa ba don yasan za'afi kula da itaa agidan,kafin yamma Dangi kota ina don jin haihuwar musammn b'angaren Safwan. Hassy da hussy kamar suke jegon yauma suna zaune Ana shirya baby wayar husy tayi K'ara ta dauka "my husby" yace "ba wani nan!! kin manta dani ko? tace kasan munyi d'a dole kai hkr" yayi dariya "zan kamaki ne tunda bakya missn dina." "Anjima zanzo barka" tace "to."
Da yamma sai ga shinan yazo yauma fararen kayan ne jikinsa ya dade azaune sai ga husy rik'e da Baby ta shiga d'akin baki yana ganin ta ya tashi ya karb'i Babyn yace "wow Masha Allah Amma babyn me kyau dashi" tace "agabana!" yace "to meye kema next yr da naki" ta rufe fuska "haba dai aini sai na dad'e" dariya yayi yana yaba babyn wata leda ce babba shak'e da kaya ya mik'a Mata "gashi abawa Maijego." Hussy tace "lalle harda hidima!" "To meye yiwa kaine" haka ya gama ganin baby ya tafi.*Washegari*
Su Anty da Mubarak suka zo husy tayi murna suna zaune suna hira. Suhaima na gyara baby hassy tace "Anty ina wan nan Sadyn?" tace "tana nan" suka tuntsire da dariya .Hassy tace "ai bata da kirki kin san me taiwa husy kuwa!" Anty ta girgiza kai "sai kin fad'a" nan suka gaya mata tace "biri yayi kama da mutum, ashe shiisa Naga Dady ya kafa musu doka" hassy ta tashi danjin gulma "ai gwanda" tace "ai cewa yayi duk sufito da miji nan da 2weeks" dariya suka sa "Ai maganinta kenan! ba ita mugunta ba" Anty tace "ai Sady sai ahankali kinga da dasu Zuby nanan duk itace ba ruwanta. Amma Ana musu Aure taga fili ta fitsare." husy tace "eh nima.nayi mamaki donfa muna shiri da ita lokacin dana zauna gidansu." Hassy tace "ita ta sani saita tafi neman miji ai" Suhaima tace "bar 'yar banza ai ni yanzu ba sosai muke wurd'aba duk kan abinda take muku."Anty tace "Allah ya kyauta."




***********

Sati ya za gayo akai suna yaro yaci suna Muhd nan suka cigaba da taya suhaima jego.
Ranar Asabar iyayen Shuriem maza suka zo lokacin Dady na nan su uku akai musu iso nan suka nema Dady ya amince atake suka zaro 200k aka bada kud'in mun gani munaso wato engaged. zo kuga murna gun Shuriem da husy ,nan Dady yayima Mum bayani tace "Aa kace auren yara 2 zanyi to Allah ya kaimu" Dady yace "Ameen" tunda Sady taji zan-cen kawo kud'in Husy gun Anty yasa ta kuma tashin hankalinta harda su Zazzabi ga Dady ya addabesu su. Hassy kuwa kowacce yanzu Normal suke dame santa suna zuba soyayyrsu inna Jummai taji dadi wan nan kenan.

*Bayan Sati biyu*

Yau satin da Dady ya dibarwa su Sady ya cika. nan ya kirawo su kowacce ta zauna ya kalli Sumy tace "Dady akwai wani Uzaifa mun dai-daita da shi" yace "to umma" tace "amma sai de fa bashida kudi sosai" Dady yace "ai anshani na warke yanzu ga Zuby kullum bani ke taimakonta ba! duk kuma kud'in sa fawwz dana babansa kin san ya zama matsolo baya wadata ta,ni yanzu kawai inde yaro na da mutumci zan bashi kuma zai iya rik'eta" yace "ke Sumayya na gama dake saiki ce ya aiko." ya kalli Sady wacce ido ya firfito "ke kuma fa? ta saka kuka "Dady wlh ban tsayar ba ,don Allah kayafen! nan da wata daya zan samo" da yaki yarda sai da su mama suka sa baki ya amince, nan ta mik'e suka tafi daki Sumy tace "kinga abinda nake gaya miki ko! gashi nan ba shureim ,ga Faruq yayi aurnsa tun-tuni sai kamalu Allah yasa dai baki koreshi ba shima" Sady tace "ke ni ki kyaleni" sumy tace "ki bugawa Kamalu "muji mana"! ganin Sumy ta dameta yasa ta bugamai ta dade tana ring San nan ya d'auka "ya dai lafiya?" tace "Aa dama kwana 2 na jika shiru ne" yace "ba komi kawai naga bakya sona ne ni kuma bana jurar wulakanci shiisa na hak'ura yanzu haka na samu wacce muka dai- deta an kusa engaged ma Allah ya hadaki da rabonki." dama a hands-free tasa nan Sumy tace "wata sabuwa kingani ko dama na fad'a yanzu baki ga tsuntsu ba tarko" Sady tasa kuka "wayyo wlh ni banso Dady ya had'ani da kowa" Sumy tace "ta baya ta rago dai dama ranar Dana sani ake tsoro ga mara daukan shawara."


By
Queen Meemi👑



. ⚜ ❣ ⚜ ❣ ⚜ ⚜❣❣ ⚜❣❣ ⚜ ❣ ⚜ ❣ ⚜ ❣ ⚜


❣ ⚜ ⚜❣

*❣RABUWA CE SANADI❣*

*_⚜BY QUEEN MEEMI_*⚜
❣61❣
_Sadaukarwa ce Ga Basheer Usman family's_



********

Haka Rayuwa tayi ta tafiya inda har an samu wata uku cir da maganar da Dady yayima Sady Amma shiru ba mashin shini domin duk samarin dataiwa wulaknci duk sun samu masu sonsu,kuma basa zuwa, kullum sai -de ta rok'i Dady daya k'ara Mata lokaci ak'arshen satin nan ne yace mata nan da sati zai yanke hukunci akanta.kwana biyu tsakani Sady duk ta tashi hankalin ta domin tsoron kar Dady ya had'ata da wani tsohon don yanda yaji haushinta ba lalle ya saurara mata ba.yauma tana zaune wajen k'arfe hud'u itada Sumy suna kallo azahiri ba kallon take ba sai tunani wanda ya Zame Mata tamkar me Sallama sukaji Anyi sallama.Lubna ce ta shigo tana murmushi da gudu Sady ta Rungumeta "Oh! my Frnd I Mssd u lubna" tace "nima haka" nan suka hau hirar yaushe gari Sady tace "ya katsinan" tace "Alhmdlh nafa kusa Aure" Sady tace "ke Dan Allah wazaki Aura? Ashobe ta zaro "gashi anko nan da 3 month sunan mijin Kamalu Sady tace "nunan pics nasa" nan ta zaro waya ta nuna mata dafe kirji sady tayi "me zangani! cin amana" lubna tace "name fa?" "Amma kinsan dai saurayina ne sonawa ina mai wulknci agabanki bayan ke kike ma zugani" lubna tace "lol to don tsohon saurayin kine sai akace ni na wulak'anta Shi alokacin kina mayen son wanda bai sanki shiisa kika kasa gane masu sonki" Sady tace "amma kin asara lubna Allah ya isa muguwa" Tabe baki tayi Amma Sady baki da wayo dame Allah ya ragi kamalu kika watsa mai kasa a ido nikam yayi min don haka kinga tafiya ta in kinga dama kiyi ankon" nan ta aje taai hanyar k'ofa Sady tabita "wlh lubna bani bake, muguwa Allah saiya sakan." Lubna tace wlh sai de ya tsaya akanki domin bance ki wulakanci ba waike gamai farin jini to ai ga irinta nan" ta fita tana juyi da gudu Sady ta koma gida Sumy dake jin duk abinda suke tace "lalle duniya budurwar wawa ai yanzu kyayi hankali Sady,kisan irin kawayen da zakina yi",ita kuwa kukanta take sha na bak'in ciki.


*************


Yau aka saka ranar Su hassy da hussy wata biyu nan fa Murna kamar me su hassy aka hau shiri ta b'angaren mazan kuwa Muktar yayi ginin sa akano shi kuma Shuriem yayi gininsa dank'arere A nan Abujar . Lefe kuwa kannen maminsa suka tafi dubai inda aka had'o akwati saiti 24 wane kyau domin tamkar a bud'e kanti mami kuwa ta tama bikin Shuriem bangaren Mum din su Hassy kuwa duk ta shiga busy domin kullum suna kano Sayen kayan k'awa komai 2 take saya domma Suhaima itama sati mai zuwa zasu tafi dubai da hassy da husy don sayo kayan fitar biki da wasu sauran kayan.
Bayan Sati d'aya suka d'aga dubai su uku sun sayo kaya na gani na fad'a na manyan mata domin Dadyn su ya saki kud'i domin daga su bazai kuma aurarwa ba kaya suke jibga musamm husy mai son abubuwa komi ta gani sai ta saya wan nan kenan.
Sai da sukai sati biyu San nan suka dawo Dan ma an musu huutu shiisa abin yazo da sauki.
Suna azaune mum na ganin kayan "kai My twins gaskiya kun iya zab'e wan nan kaya haka lalle" suhaima tace "ai mum komi suka gani sai sun saya musammn kayan kitchen" mami tace ai yarn nawa sun horu da girki shiisa suke saya" hassy tace mum ai dady "yafa bamu kudi sosai" Suhaima tace "yanzu ku Ana zancen auren naku kuke saka baki" husy ta rufe ido "kai Sis Suhaima" hassy tace "hmmm! siis suhaima lokacin bikinki fa! komai ke kika zab'a" mum tace "ku tashi kuje kuyi girki don yanzu dole ku dada k'warewa" nan suka tashi.


***********

Husy ce zaune da Shuriem suna hira inda suka Saba zama Dan kallonta yayi da murmushi d'auke akan face nasa 'Amaryata nan da one month kina gidana" sunkwi dakai tayi "angona Kenan" yace "ki gayan meye bai miki ba agidan a gyara" nan ya bud'e tsaleliyar wayarsa yana nuna mata masha Allah kawai take ambata tace "nikam husby ko ina yayi wlh ai wan nan na zama yar gata" yace "baby kinfi haka ma" haka suka gama hirar su ya tafi.

*Bayan sati daya*


Dangin su Shuriem suka kawo Lefe Motoci ne manya manya ke. fakawa a farfajiyar gidan su hassy. manyan mata keta fita inda katti ke d'aukan jakun kuna suna shiga dashi cikin gidan ma dank'am yake da mata nan aka hau gud'a kota ina Masha Allah aketa anbata "lalle yarinya tayi goshi" su maman kano da goggo duk sun zo nan aka basu tukwici na 200k da Snaks kala- kala amutunce suka gama suka tafi inda aka saka date On 30 April.bayan tafiyar su akaita san barka hassy ta haye d'akin su tace "tweeny gaskiya kinyi goshi kinga kaya! Amarya kenan." Husy ta dago "kema ai hakan wai yaushe mukatr zasu kawo" tace "shima a dis week" nan suka zauna suna ta shirya yanda event sai wakana.


***********

"Kai muktar yanzu wan nan shirgegen Lefen Shi za'a kaiwa yarinya d'aya ai wan nan sai an kaiwa yarinya Goma in a k'auyen nan ne! Ai dama nasan su Antyn kano su lefen karya zasuyi don sunga yar birni ce shiisa ba akawon na gani ba saida ka gama haba muktar! kodan yar manya ce" muktar dake durk'ushe don tunda aka fara hada lefen ya hada abinsa da tainakon su Antyn kano (inda yake) Su gaggo tun ganin su da lefen suke maganganu kan yayi yawa shiisa ma har yanzu ba'a kaiba.Muktar yace "haba gogg kinsan dai gidan Dana d'auko aure dole komai ai na bajinta kuma falilkahil hamd inada Halin yi."daka tsalle tayi "wallahi sai an rage" nan ta d'ebi wasu atamfofi ta aje agefe da mayafai "haba aje lefe saiti goma sha shida zaka kaiwa mace d'aya wlh sai an rage" kamar yayi kuka don ya dade yana shirinsa. shigowar maigari ya tarar da tak'ardama yace "meye?" nan ta sanar mai yace "kinga ban san haka! ke kinga inda ya samo auren ne? kibarsa kawai tuwon girma miyarsa nama,duk damu k'auye bamu san wan nan k'aryar ba ,to shi abirni yake yanzu dole tunda 'yar can ya samo dole yayi masu tunda yana da hali" nan ya dauke duk kayan ya maida a fusacce ta d'au wani atamph "wlh Banda wan nan" muktar yace "gogg kinga fa akwatinki can da kaya keda baba na ciko muku don fitar biki ga kuma dubu hamsin akai." nan ta washe baki "yanzu naji magana, Amma de duk da haka sunyi yawa" yace
Showing 144001 words to 147000 words out of 155648 words