hakan kuwa akai ta kirawo iya mai Aikinta tace ta duba kan Hansai nan ta tsefe mata wajen 8 na dare aka wanke kan tayi wanka sosai ta ci Abinci tayi Sallah ta kwanta bacci.
*washegari*
Da safe Hansai ta karya da breakfast mai Dad'i nan iya tayi Mata kitso Mama na kan kujera Rabia ta bugo waya tace "an samu! Mama tace "gata nan kuwa Masha Allah, an samu" yanzu sai ki turo driver yazo ya d'auke ta, Rabia tace "to Mama Amma sai gobe, saboda yau yana da uzuri" Mama tace "ba matsala" nan ta kashe .
Ta kalli Hansai tace "ni meye Sunanki na Gaskiya ne? Hansai tace "Hansai Shine na Gaskiya" iya tayi Dariya "Hansai ai ba Sunan Gaskiya bane" Mama tace "A toh".
Amma kinayin Makarantar Allo Acan? Hansai tace "Eh ina Makarantar Allo, Nayi Izifi Arbain" Mama tace "Masha Allah.Boko fa" iya tace ai kinsan k'auye basu damu da boko ba,Na Addinin Ma wasu ko ansasu basa yi" Hansai tace "Nayi boko Ajina uku a Secondary" Mama tace Lalle ki Godewa Allah.
Bayan an agamai Mata kitson Mama ta kuma sata tayi wanka nan tace kinga Abuja za'a kaiki kina tsafta ,duk da naga balaifi." Hansai tace "to" Hansai kuwa duk bidirin nan zuciyar ta na kukan tuno inna da baba haka tayi yinin nan har ta dad'a fes ba Tsangwamar Gwamma.
Washegari kuwa wajen 12 sai ga Ashiru driver bayan yaci Abinci nan Hansai tasaka kayanta bayan motar suka d'au Hanya sai Birnin Tarayyya.
Bari na D'an huta kan su Hansan su sauka.
Sister's kuyi Hkr ba kullum zakuna jina ba saboda matsalar ba wuta ngd.
*By Queen Meemi*
[9:52am, 26/01/2017] 👑Meemi🔸: . . .
⚜ ❣ ⚜ ❣ ⚜ ⚜❣❣ ⚜❣❣ ⚜ ❣ ⚜ ❣ ⚜ ❣ ⚜
⚜
❣ ⚜ ⚜❣
⚜
*❣RABUWA CE SANADI❣*
*_⚜BY QUEEN MEEMI_*⚜
❣18❣
*JAN 2017*
*Queenmeemi.WordPress.com*
*_Sadaukarwa ce ga Basheer Usman family's_*
_Sakon ku ya iso gareni masoyana na gode da kulawa❤_
*****
Sai wajen k'arfe 6 dai -de su Hansai sukaje Lokacin taci bacci ta k'oshi Hon din da Ashiru nayiwa Maigadi ne ya tashe ta ta bud'e Ido tayi tozali da k'awataccen Gida juya baya tayi taga duk Layin da suka shigo kusan hakan Gidajen su ke .Maidadi ne ya tashi ya bud'e zirif Ashiru Driver ya shiga yayi parking a gurin adana Motoci ne Reras a ajiye, ahankali ta fita Ashiru ya fito Mata da kayanta daga bayan Motar, nan tayi Duru- Duru sai kallon gidan take wanda ada tana ganin na Maman Kano mai kyau ,sai taga ko Rabin kyan wan nan be kaiba da Girma da k'watuwa.
Ashiru ne yayi gaba tabishi suka danna door bell da dad'ewa wani Namiji yazo ya bud'e ya basu Hanya suka Shiga ya cigaba da goge -gogen sa y Mamaki k'arara akan fuskar Hansai,Masha Allah ta kira azuciyar ta Sakamakon Tozali datayi da had'ad'd'en falon wanda dukan sa acircle yake Ashiru ne ya tsaya can sai ga Anty Rabi ta fito daga Part nata da D'an saurin ta d'auke da Murmushi saman fuskar ta ,tace "Aa Sannu Ashiru kunsha Hanya!" Alamar russuna Mata yayi yace "eh Wallahi Maman tace agaishe ki" nan ya juya ya fita Rabia ta kalli Hansai "muje ko" zungi zungwi ta bita sai kallon waje -waje take tana Mamakin tsaruwar Gidan Ahankali ta furta "Aljannar Duniya"
Jikake ta guum! ta k'ume da k'ofar Shiga paty d'in Anty Rabia da Hanzari Anty ta jiyo "Aa kiyi ahankali fa" nan suka shiga b'angaren Antyn baki sakin baki Hansai tayi ganin wani falon wanda yafi kyau ,nan tayi ta k'auyancin ta zama tayi gefen kujera ta kafawa Tv Ido tana kallon film d'in da ake ga sanyin Ac na hurowa had'e da sanyayan turaren wuta zo kuga yanda Hansai ta langwab'ar da kai gefen kujera kamar tai bacci.
Anty Rabia kam dawowa tayi d'auke da Khalil a Hannu ta zauna tace "ya Sunanki ne?" Hansai ta sunkwi da kai Sunana Hansai .
Anty tace "Madallah Garinku fa?"
Tace "Bunkure".
kina Makarnta tace "eh Ajina Uku a secondary" (oh su Hansai Ana ji da Aji ukun din nan da akai)Anty tace "Madallah, tom kinga yanzu Aiki kikazo na Farko banason k'azanta na Biyu Banson Gulma kinga da 'yan Aiki wajen biyu A Gidan nan Kamar ki da tsohuwa ga Namji mai Goge -Gogen Babbann falo, ki Kame kanki,Banda shiga inda ba hurumin ki ba, Zakina min Renen boys D'ina Mubarakh da khalil ,San nan Zakina Wanke- Wanke da Gyaran kitchen, nan falon Zakina Shareshi da Goge kujera ,zakina Goge kayansu Tv vedio ,center Table su Dining Teble duk kiyi sai ki Moping tile d'in da D'an abinda baka rasa ba. Shine kad'ai iya Aikin ki, Maganar kud'in Aikin ki Kuma dama Munyi Maganar da Lami."
Dadi ne ya kama Hansai Jin Aikin bame yawa ba don ak'auye wanda take ya ninka wannan ,nan ta d'ago "Insha Allahu Anty zanyi abinda kika ce finsa Ma" Anty Rabia tace "yawwa yanzu kije zan nuna Miki toilet kiyi wanka duk da ba anan Zakina kwana ba akwai Shashin Masu Aiki" Hansai tace "tam Anty."
Dai-dai Time d'in aka kira Sallah nan ta tashi tayi gaba ta bita suka fita Daga part d'in suka koma Ainihin Big Falon, San nan sukayi wani dan sako daga Arewa nan suka Shiga wani korido San nan suka shiga wangamemen daki da Madaidaitun katifu Guda Hud'u aciki,Gefe ga wasu akwatin Katako Babba Doguwa kayan su ne aciki.
Kande ce da Karime suna Alwala a Band'akin dake Cikin D'akin Anty tayi Magana nan suka fito duk suka Zube.
Anty tace "ina kuke kwance? wacce katifa ce Empty Kande tace "waccen ta Lokon e babu ,wan nan ta Tsakiyar nice akai sai ta Gefen Karime waccen kuma ta iya Abu ce sai ta Lokane ba kowa."
Anty tace "ok naji ke Hansai kije waccen nan zakina kwana ki aje kayanki Acikin Wan nan doguwar Kwatin tunda nasan akwai inda babu komai aciki, Bayan haka yanzu ki fara wanka kan ki sallar tunda ba a tayar ba." Idan kinyi Sallaar kizo side Dina."
Hansai tace "to" nan ta fita zuwa kuwa tayi ta aje kayan nata Acikin akwatin ta zauna kan Luntsumar katifar San nan ta tashi tashiga band'akin tayo Wankan ta fito .
Lokacin su kande na zaune sai hira suke ta canja kaya tayi Sallah San nan ta kalli su Karime tace "Sanunku" sukace "yawwa" suka D'an tab'a hira San nan ta tashi ta fita.
Sai hanyar ta kauce Mata ta Manta part din Anty tarasa ina yake sai zagaye falon take duk girman Shi, take nan tayi part din Dake Gabanta b'angaren Hagu Alhalin ita Anty tana side na Dama shiga tayi a hankali ta Danyi sallama ta shiga Zuby ce ta d'ago "waye?.
Hansai tace "nice" sai Lokacin ta gane ba gun bane Zuby tace "ke daga ina?".
Hansai tace "nayi Makuwa ne!! gun Anty Rabia zani."
Zuby tace "oya get out ,ba nan bane."
Haka ta juya sai Lokacin ta gano gun ta shiga da Sallama Anty na Sallah ta d'au Khalil tana mai Wasa sai Dariya yake bayan gama Sallar Anty tace "Jeki kitchen akwai abinci ki d'auka" ta nuna mata.
Showing 72001 words to 75000 words out of 155648 words
*washegari*
Da safe Hansai ta karya da breakfast mai Dad'i nan iya tayi Mata kitso Mama na kan kujera Rabia ta bugo waya tace "an samu! Mama tace "gata nan kuwa Masha Allah, an samu" yanzu sai ki turo driver yazo ya d'auke ta, Rabia tace "to Mama Amma sai gobe, saboda yau yana da uzuri" Mama tace "ba matsala" nan ta kashe .
Ta kalli Hansai tace "ni meye Sunanki na Gaskiya ne? Hansai tace "Hansai Shine na Gaskiya" iya tayi Dariya "Hansai ai ba Sunan Gaskiya bane" Mama tace "A toh".
Amma kinayin Makarantar Allo Acan? Hansai tace "Eh ina Makarantar Allo, Nayi Izifi Arbain" Mama tace "Masha Allah.Boko fa" iya tace ai kinsan k'auye basu damu da boko ba,Na Addinin Ma wasu ko ansasu basa yi" Hansai tace "Nayi boko Ajina uku a Secondary" Mama tace Lalle ki Godewa Allah.
Bayan an agamai Mata kitson Mama ta kuma sata tayi wanka nan tace kinga Abuja za'a kaiki kina tsafta ,duk da naga balaifi." Hansai tace "to" Hansai kuwa duk bidirin nan zuciyar ta na kukan tuno inna da baba haka tayi yinin nan har ta dad'a fes ba Tsangwamar Gwamma.
Washegari kuwa wajen 12 sai ga Ashiru driver bayan yaci Abinci nan Hansai tasaka kayanta bayan motar suka d'au Hanya sai Birnin Tarayyya.
Bari na D'an huta kan su Hansan su sauka.
Sister's kuyi Hkr ba kullum zakuna jina ba saboda matsalar ba wuta ngd.
*By Queen Meemi*
[9:52am, 26/01/2017] 👑Meemi🔸: . . .
⚜ ❣ ⚜ ❣ ⚜ ⚜❣❣ ⚜❣❣ ⚜ ❣ ⚜ ❣ ⚜ ❣ ⚜
⚜
❣ ⚜ ⚜❣
⚜
*❣RABUWA CE SANADI❣*
*_⚜BY QUEEN MEEMI_*⚜
❣18❣
*JAN 2017*
*Queenmeemi.WordPress.com*
*_Sadaukarwa ce ga Basheer Usman family's_*
_Sakon ku ya iso gareni masoyana na gode da kulawa❤_
*****
Sai wajen k'arfe 6 dai -de su Hansai sukaje Lokacin taci bacci ta k'oshi Hon din da Ashiru nayiwa Maigadi ne ya tashe ta ta bud'e Ido tayi tozali da k'awataccen Gida juya baya tayi taga duk Layin da suka shigo kusan hakan Gidajen su ke .Maidadi ne ya tashi ya bud'e zirif Ashiru Driver ya shiga yayi parking a gurin adana Motoci ne Reras a ajiye, ahankali ta fita Ashiru ya fito Mata da kayanta daga bayan Motar, nan tayi Duru- Duru sai kallon gidan take wanda ada tana ganin na Maman Kano mai kyau ,sai taga ko Rabin kyan wan nan be kaiba da Girma da k'watuwa.
Ashiru ne yayi gaba tabishi suka danna door bell da dad'ewa wani Namiji yazo ya bud'e ya basu Hanya suka Shiga ya cigaba da goge -gogen sa y Mamaki k'arara akan fuskar Hansai,Masha Allah ta kira azuciyar ta Sakamakon Tozali datayi da had'ad'd'en falon wanda dukan sa acircle yake Ashiru ne ya tsaya can sai ga Anty Rabi ta fito daga Part nata da D'an saurin ta d'auke da Murmushi saman fuskar ta ,tace "Aa Sannu Ashiru kunsha Hanya!" Alamar russuna Mata yayi yace "eh Wallahi Maman tace agaishe ki" nan ya juya ya fita Rabia ta kalli Hansai "muje ko" zungi zungwi ta bita sai kallon waje -waje take tana Mamakin tsaruwar Gidan Ahankali ta furta "Aljannar Duniya"
Jikake ta guum! ta k'ume da k'ofar Shiga paty d'in Anty Rabia da Hanzari Anty ta jiyo "Aa kiyi ahankali fa" nan suka shiga b'angaren Antyn baki sakin baki Hansai tayi ganin wani falon wanda yafi kyau ,nan tayi ta k'auyancin ta zama tayi gefen kujera ta kafawa Tv Ido tana kallon film d'in da ake ga sanyin Ac na hurowa had'e da sanyayan turaren wuta zo kuga yanda Hansai ta langwab'ar da kai gefen kujera kamar tai bacci.
Anty Rabia kam dawowa tayi d'auke da Khalil a Hannu ta zauna tace "ya Sunanki ne?" Hansai ta sunkwi da kai Sunana Hansai .
Anty tace "Madallah Garinku fa?"
Tace "Bunkure".
kina Makarnta tace "eh Ajina Uku a secondary" (oh su Hansai Ana ji da Aji ukun din nan da akai)Anty tace "Madallah, tom kinga yanzu Aiki kikazo na Farko banason k'azanta na Biyu Banson Gulma kinga da 'yan Aiki wajen biyu A Gidan nan Kamar ki da tsohuwa ga Namji mai Goge -Gogen Babbann falo, ki Kame kanki,Banda shiga inda ba hurumin ki ba, Zakina min Renen boys D'ina Mubarakh da khalil ,San nan Zakina Wanke- Wanke da Gyaran kitchen, nan falon Zakina Shareshi da Goge kujera ,zakina Goge kayansu Tv vedio ,center Table su Dining Teble duk kiyi sai ki Moping tile d'in da D'an abinda baka rasa ba. Shine kad'ai iya Aikin ki, Maganar kud'in Aikin ki Kuma dama Munyi Maganar da Lami."
Dadi ne ya kama Hansai Jin Aikin bame yawa ba don ak'auye wanda take ya ninka wannan ,nan ta d'ago "Insha Allahu Anty zanyi abinda kika ce finsa Ma" Anty Rabia tace "yawwa yanzu kije zan nuna Miki toilet kiyi wanka duk da ba anan Zakina kwana ba akwai Shashin Masu Aiki" Hansai tace "tam Anty."
Dai-dai Time d'in aka kira Sallah nan ta tashi tayi gaba ta bita suka fita Daga part d'in suka koma Ainihin Big Falon, San nan sukayi wani dan sako daga Arewa nan suka Shiga wani korido San nan suka shiga wangamemen daki da Madaidaitun katifu Guda Hud'u aciki,Gefe ga wasu akwatin Katako Babba Doguwa kayan su ne aciki.
Kande ce da Karime suna Alwala a Band'akin dake Cikin D'akin Anty tayi Magana nan suka fito duk suka Zube.
Anty tace "ina kuke kwance? wacce katifa ce Empty Kande tace "waccen ta Lokon e babu ,wan nan ta Tsakiyar nice akai sai ta Gefen Karime waccen kuma ta iya Abu ce sai ta Lokane ba kowa."
Anty tace "ok naji ke Hansai kije waccen nan zakina kwana ki aje kayanki Acikin Wan nan doguwar Kwatin tunda nasan akwai inda babu komai aciki, Bayan haka yanzu ki fara wanka kan ki sallar tunda ba a tayar ba." Idan kinyi Sallaar kizo side Dina."
Hansai tace "to" nan ta fita zuwa kuwa tayi ta aje kayan nata Acikin akwatin ta zauna kan Luntsumar katifar San nan ta tashi tashiga band'akin tayo Wankan ta fito .
Lokacin su kande na zaune sai hira suke ta canja kaya tayi Sallah San nan ta kalli su Karime tace "Sanunku" sukace "yawwa" suka D'an tab'a hira San nan ta tashi ta fita.
Sai hanyar ta kauce Mata ta Manta part din Anty tarasa ina yake sai zagaye falon take duk girman Shi, take nan tayi part din Dake Gabanta b'angaren Hagu Alhalin ita Anty tana side na Dama shiga tayi a hankali ta Danyi sallama ta shiga Zuby ce ta d'ago "waye?.
Hansai tace "nice" sai Lokacin ta gane ba gun bane Zuby tace "ke daga ina?".
Hansai tace "nayi Makuwa ne!! gun Anty Rabia zani."
Zuby tace "oya get out ,ba nan bane."
Haka ta juya sai Lokacin ta gano gun ta shiga da Sallama Anty na Sallah ta d'au Khalil tana mai Wasa sai Dariya yake bayan gama Sallar Anty tace "Jeki kitchen akwai abinci ki d'auka" ta nuna mata.
Book Chapters
Chapter 1Chapter 2Chapter 3Chapter 4Chapter 5Chapter 6Chapter 7Chapter 8Chapter 9Chapter 10Chapter 11Chapter 12Chapter 13Chapter 14Chapter 15Chapter 16Chapter 17Chapter 18Chapter 19Chapter 20Chapter 21Chapter 22Chapter 23Chapter 24Chapter 25 Chapter 26Chapter 27Chapter 28Chapter 29Chapter 30Chapter 31Chapter 32Chapter 33Chapter 34Chapter 35Chapter 36Chapter 37Chapter 38Chapter 39Chapter 40Chapter 41Chapter 42Chapter 43Chapter 44Chapter 45Chapter 46Chapter 47Chapter 48Chapter 49Chapter 50Chapter 51Chapter 52