Baba ya sunkwi da kai "yanzu kai bakaji kunyar gayan Maganar nan ba na ko?! ai shike nan dama ai babarka tace bata so kuma nasan ita ta kitsa ma. Amma komi Mutun yayi Shi za ayi mai.

Mudi kam wata jakar bagkoy ya d'auko, ya tsaya "ni na tafi Lagos neman kud'i baba dama yau na tsara tafiyar".
Gwamma ta fito "Yawwa mudi yau ka biyani". Baba yace "ni kam ina Umartar ka A matsayina na Mahaifinka kar kaje duk da nasan ba ka Maidani komai ba." Gwamma tace "wallahi Sayyaje". Mudi ya d'uri jaka yace acan zan hadu da Lawandi ya fice.
Gwamma tayi shewa "Ahayye yaraye nanaye"
Kuka hansai keyi saboda tausayin Baba, tace "Baba kayi hak'ur. Baba yace "bakomi Hansai ina Alfahri dake Allah ya baki miji na gari" ya tashi ya fita.

Haka Malam duk ya sanar an fasa auren nan nan gari ya hau tsogwami anata Gulmace- Gulamace ko fita Hansai tayi sai a fara ga Hansai mai bak'in Jini "da kuka take dawo wa, sai da Malam yaje yayiwa tufkar hanci ,San nan aka sakar Mata Mara.
K'anin Maigari ne dake zaune a kano yazo mai suna Alhaji Salisu, Shi ya tashi a hannun k'anin Babar su Maigari to ita abirni take Aure shiisa ta d'auke Shi ya tashi yayi Boko ,yanzu hakan yana aiki A NNPC Manager ne, yana da 'ya'ya da Mata Biyu.

Zuwansa Gidan ya tarar Ana tak'addama akan Muntari kan ya kafe bazai Auri wata Lantana da Gwoggo ta kawo ya Aura yace tunda anraba Shi da Hansai ba 'yar da zai Aura, to ganin hakan Alhaji Salis yace zai tafi dashi can Birni ya cigaba da karatu ,Jin an ambaci karatu yasa ya Amince zai bishi. bankwana .. .

*BY QUEEN MEEMI* .
[12:55pm, 21/01/2017] 👑Meemi🔸: ⚜ ❣ ⚜ ❣ ⚜ ⚜❣❣ ⚜❣❣ ⚜ ❣ ⚜ ❣ ⚜ ❣ ⚜


❣ ⚜ ⚜❣

*❣RABUWA CE SANADI❣*

*_⚜BY QUEEN MEEMI_*⚜
❣15❣
*JAN 2017*



*Queenmeemi.WordPress.com*


*_Sadaukarwa ce ga Basheer Usman Family's_*


_TUNATARWA_
_'yan uwa muna hak'uri da rayuwa aduk yanda tazo mana,hak'uri maganin zaman duniya ne ,komai ya sameka mujarrabi ne daga Allah_


******
*Misalin k'arfe 9 na safe*
Shirin sa yayi tsaf ya had'a Jakarsa tunani yayi dole yayi bankwana da Hansai, hakan ya tashi ya tafi gidan su, ikon Allah adai-dai Lokacin Hansai ta fito, turus tayi suka K'urawa Juna Ido nan yace "zo muje bayan Dutse."

Haka kuwa akai ta bishi a baya har suka je ,nan ya zauna yace "Hansai birni zan tafi" dafe kirji! tayi ta Mik'e "na shiga uku." Muntari yace "gwanda na tafi Idan na zauna ina ganinki Zuciyata zata iya bugawa."

Saboda nasan an raba mu soyayyarki tana nan a Araina kece ta Farko Dana keso."
Hansai tace Rabuwa da kai Shine Sanadin cin Fuskar da na ke fuskanta daga gun Mutane da Ammana Aure da hankalina kwance,ba wanda zai min."

Kuka ta kuma fashewa "Wallahi bazan so kowa ba sai kai" Shima da k'walla ya fito mai yana jin Zuciyarsa kamar zata fashe. "Hansai da inada dama da sai na gudu muyi Aure. Amma ba dama San nan nama fasa tafiya Birnin ma, Zan Zauna na Jajirce har su yar da subani ke ko."
Hansai ta mik'e tsaye Muntari karkayi hakan ka tafi kawai. "Allah ya k'addara Saduwarmu."

Kollonta Yayi da Siraran Hawaye suka Zubo yace "Idan da rai da rabo.Hansai inde da rabo a tsakanin mu gaba zami Aure."
Murmushi tayi "Allah yasa"
Nan suka tafi a tare sun zo kwanar su yaga Maigar da Alhaji Salisu an saka Jakar sa a Mota kuka ne ya Kubcewa Hansai.

Maigari ya kwad'o Mai kira tafiya yayi yana waiwayon Hansai .Maigari yace Au gurin "Yarinyar can kaje? Iyayen naci ai gwanda ka tafi Birnin kowama ya wuta Soyayya ba Alkunya." Dariya Alhji salisu yayi yace "Zamani ne ai, Amma mai yasa Baku basi Auren ba.?

Maigari yace "Yarinyar ce ba usuli .
Dai-dai Lokacin Muntari ya K'araso Maigari yace "tafiya zakuyi." Idon sa
Showing 66001 words to 69000 words out of 155648 words