Shigo zama tayi Sam bata kula dasu ba sai da Zahra ta tawo "welcm Sady" me za'ai miki? tace "Steaming" nan idonta ya sauka akan husy taja wani wawan tsaki.
D'an kauye yazo birni" suka sa dariya itada Lubna.

Hassy ta had'e rai suka basar wata ce tazo dan shafa Mata man da ake steaming ta Zame d'an kwalinta kan nan ba tada gashi su hassy suka kwashe da dariya gwi da yara kenan!.

Sady ta k'ulu sosai don tasan da ita suke don dama bata da gashi.
Bayan kamar 1 hour aka gama musu Saloon aka fara k'unshi yayi balain kyau abinka da farar fata,k.k'irr wayar Husy ta kama ruri ta d'auka a slowa ganin Handsome ne a wani yanayi tace "Husby" Sady ta d'ago gabanta na fad'uwa ganin yanda husy ke waya tabbas tasan da Shuriem take nan taji kamar ta shak'e husy.

Jitayi husy tace "oh dear I missd u ,i want see u" Dan Murmushi tai "Okey dea i'm waiting" ta kashe wani d'an fari tayi tace "tweeny yanzu Shuriem zai zo ya ganni wai dama yana kan titin nan zai koma gida" Hassy tace "Weldone dear"


Sady ji tayi zaman ya isheta Allah Allah take agama mata ta k'addamar wa da Husy tsiya.

5:00 aka gama musu sunyi kyau lokacin Shuriem ya k'araso suka mik'e wayarta tayi K'ara "okey dea gani nan" mik'ewa tayi ta kalli Sady tai murmushi ta fita.

Afusace Sady ta mik'e "Zahra ina zuwa plss "tace oke

Tana fita taga Shuriem shida Husy a farfajiya Shagon tsaye sai yaba kyan fulawar yake, gani tayi sun juyo alamar zata koma shagon ,yana wan nan tafiyar tasa wadda ke fusgar Sady.Zahra ce ta fito zata aje abu Shuriem ya tabmbayeta list d'in abunda za'abiya ya tambayi Zahra tace "oga ai an sun biya tun damu" Sumar sa ya shafa "no karbi na baki kyauta ne don naga Amarya ta ta fito sosai" washe baki zahra tayi "Thank u oga" ta koma ciki Tace "Hassy ur Sister agaskiya tayi sa'ar boy frnd gashi handsome ga kyauta."

Hassy tace "eh wlh Zahra ai shiisa Mata ke sonsa Shi kuma yace sai sis Hussy ko garin ba kowa." Zahra tace "ai Sis naki tana da kyau sosai har ta fiki kyau fa!" hassy tace "kai zahra ai kamar mu d'aya."

Sady kamar ta kurma ihu Lubna ma haushi ya isheta afusace ta futa taje ta bayan Hussy ta juyo da kafad'arta 'yar k'ara Husy ta saki don jin kafadarta tayi zafi domin da kyau taja. Juyowa tayi taga Sady na Jijjiga tana harar ta idanuwan ta sunyi ja.

Shuriem kuwa wani banzan kallo ya bita dashi da mamaki akan face nasa irin k'arfin halinta yana huci...

My fans ga wan nan ba yawa abubuwa sun min yawa shiisa bana post kullum..


By
Queen Meemi.πŸ‘‘
[5:32pm, 19/03/2017] Queen: ⚜ ❣ ⚜ ❣ ⚜ ⚜❣❣ ⚜❣❣ ⚜ ❣ ⚜ ❣ ⚜ ❣ ⚜

⚜
❣ ⚜ ⚜❣
⚜
*❣RABUWA CE SANADI❣*

*_⚜BY QUEEN MEEMI_*⚜
❣54❣
*March 2017*

_Sadaukarwa ce ga Basheer Usman family's_


***********

Zuciya ce ta d'ebi Sady ta kai hannu zata Mareta. Jitayi an rik'e hannun nata da k'arfi an kai mata mari juyawa tayi sukai ido biyu da Hassy fusge hannun ta tayi zatai magana hassy tace "ba kida word da zaki fad'a domin komi akai miki ke kika janyo."

Husy dake sosa wajen ta wurgawa Sady harara itama ta wulla mata tace "wlh duk me zakiji sai de kiji domin Shuriem yayi maki nisa nawane kibi wani sarkin domin nawa ya miki nisa,dafa da yanzu ba d'aya ba karki k'ara saka dirty hand naki ki tab'a ni, ko ki dakeni haba! kizama mace me class mana, ai wallahi da nice ke sai de son Saurayi ya kasheni dana nuna mai ballan tana ina hauka agaban sa wai don ya soni Mutunci ai madara ne,don Allah ki gane mana mutum na k'ara girma yana shiga dawa."

D'aga hannu tayi zata mareta tace "kul! Ahir dinki karki K'ara kai hannu Jikina kingane don naga ke saurin hannu gareki."

Sady tace "ke ki sani wlh sai na rabaki da Shi koda bazan Aureshi ba domin kwata -kwata bai dace da yar kauye irinki ba." dariya hassy da hussy suka saka san nan suka tafa hassy tace "ai baby kinyi sake d'an zaki ya girma ,domin wlh d'an hakin daka raina shikan tsone ma ido gashi kuwa tweeny ta tsone idanuwanki,koda yake hausawa sunce samu yafi iyawa.'

Shikam yana jikin motar sa cike da takaici wani wulak'ataccen kallo ya yiwa Sady domin bai da time d'in magana da ita sai de dole ya taka Mata birki gurin Hussy yace "finest ni zan tafi wacceen yarinyar ta b'atan rai plss kema kubar wajen don zan iyayi Mata kwaf d'aya inta kaini end."

Daria hassy tasa hankali taiwa Sady gwalo.
Hussy tace "Okey dear semin waya" motar sa ya hau ya figa haka hassy ma taja hannun husy suka fad'a tasu motar suma suka ja.

Kamar gunki Tai atsaye ta kasa motsi huci kawai take lubna tazo ta dafa ta "frnd ya da ajinki kina biyewa wadan nan yaran banso kikai magana ba, domin bada kanki kike agaban sa hakan fa bashi zai sa ya soki ba kinyi kuskure don ba kiga yanda 'yan matan can suka fito ba suna kallo haba sai dariya suke suna cewa gaki big gal amma kina abin yara, har cewa suke Husy tafi birgesu."

Sady ta fashe da kuka ban san kalmar da zan miki explain domin sonda nake ma Shuriem wlh ban san ya zan ba , kishi ke cikani duk yayin dana gansu tare plsss help me."

Liubna tayi dariya "kece ance tun-tuni ga Simple way farat daya zasu rabu kin zauna waike mumina kibar komi ahannuna ko kin mantani ne hmmm."

Sady ta tsaya tace "koma meye ayi wlh sedai ayi biyu babu domin da narasa Shuriem gwanda ko wama ya rasa." da k'yar taje aka karasa musu suka tafi gida.

**********
*Bayan wata daya*

Rayuwa sai dad'a tafiya take komai na wakana daki- daki inda tsakanin hasssy da Sady akoda yaushe husy ke wining sady taci alwashin saita Rabasu ita da lubna sai shige da fice suke Wanda ni ban san meye ba sai de mungani.

Ayau su Husy suka gama first semester exams,shiri suka shiga yi domin tafiya k'auye hutu sun bugawa Dady da mum suna son zuwa Bunkure nan Dady ya turo musu da Kudi ta accnt don suyi tsaraba domin Washegari rankaya wa za suyi har su Hoggg inda zasu sauka a kano su kuma awuce dasu.


Washegari da safe misalin karfe 10 suka d'au hanyar kano basu su kaje ba, sai 2 bayan sun sauke su Gogg da kamilu sunyi sallah driver ya wuce dasu Mangalu.


K'arfe 5 sukaje K'ofar gidan malam suka tsaya suka fir-fito suka shiga driver ya bisu da trolley nasu da tsaraba bayan yayi Sallah ya kama hanyar komawa kano.


Jummai ce kad'ai atsakar gidan da gudu husy ta Rungumeta Jummai tace mutan Abuja sai yau tace hassana ya kika tsaya runfar ta suka shiga harda kayan kallo lalle su Jummai anci gaba ko ina fes fes hira ce ta b'arke a tsakanin su da gudu Dan jummai yazo ya samesu yana oyoyo husaina ta rungumeshi suna dariya basu dad'e ba akai kiran sallah sukaje sukayi suka ci abinci kafin isha malam ya dawo yayi murnar ganin su husy taji dad'i ganin su kowa fess don malam har babur ga reshi nan duk suka firfito da tsara suka basu don har ta gwamma da Dije suka bayar hassy tace "yaude zanga muguwar nan" Jummai tace ay yanzu ta zama abin tausayi hussy tace tab! Allah ya kyauta hassy tace "ke gobe muje muga k'wak'waf hussy tasa dariya "kai hassy."
Itama dariyar tayi "yo koma meye ai ita ta jawo" Jummai tace "wlh kuwa hassana."

Washegari wajen 11 sukayi wanka suka fita d'an zaga gari Sun wuce ta gidan su Muntari husy tace "yauwa ga gidan surukanki hassy" dariya tayi "to meye saima na shiga" husy tace "ai kuwa da kin bar abin fada".sunje gidan iya suna ta sallama shiru daga can suka jio kamar magana sai suka shiga d'akin iya ce kwacr da alama bacci take taji sallamar su ta tashi "wanake gani kamar husaina" tace "nice iya" tace sannu 'yar albarka suna d'an tab'a hira Husy tace "ina kwa gwamma" iya ta tabe baki kede yar nan kina da kyan zuciya har kike nemanta, ta tafi Bara kin san tunda ta rasa k'afarta shikenan kuma ta tsiri Bara cikin bunkure suke shiga suda sauran mabaratan."

Jusy tace "Allah yayi mana mekyau" nan ta aje turmin atampha guda 2 da kudi tace na gwamma haka ta bawa iya ma sai godia take tace duniya kenn.

Suna fita hassy tace "ke dak'yar nake hadiyar miyau gaskiya suna kazanta" husy tace "ai dama gwamma nada k'azanta hassy tace inna jummai kuwa wlh kamar ba akauye take ba,ga tsafta ga iya girki. Amma naso ganin ta wan nan Gwammar muguwa." husy tace "ai kan mutafi zaki ganta."

Sun koma gida suka zauna husy tace "ashe Bara gwamma keyi? jummai tace tun yaushe wataran ai da dije take tafiya." husy tace Amma "ai Naga dije na zuwa Makaranta. Jummai tace ke tadena taki" "to ina mudi" jummai tace "ai Mudi yayi aure da kyar malam ya sashi agaba dole sai da ya nemo matar,tunda akai auren kullum cikin sulhu malam yake har saboda fad'a kamar kaji ai ni se yanzu nasan ilimi nada amfani domin wlh da ace mudi yayi duk bazai na irin hakan ba har dijen ma ai samun maslaha yanzu tare da malam suke tafiya kasuwa domin Mahaifinki wani zuwa da yayi ya tarar da fad'an duk dama rashin sana'a ne ya bashi jari" husy suka kalli juna da hassy "dama Dady na zuwa? Jummai tace "ai yana yawan zuwa ko yayi aike kafin su koma ai mukam ba abinda zamuce Sai godia." hassy tace "mune da godia."

Husy tace "to yanzu inna Mudin sun Dena fad'an?" tace "eh man yanzu ai yana sana'a sede abinda ba'a rasaba...

Wayyo Battery low fans ga wan nan ba yawa




By
Queen meemi.
[4:44pm, 21/03/2017] Queen: ⚜ ❣ ⚜ ❣ ⚜ ⚜❣❣ ⚜❣❣ ⚜ ❣ ⚜ ❣ ⚜ ❣ ⚜

⚜
❣ ⚜ ⚜❣
⚜
*❣RABUWA CE SANADI❣*

*_⚜BY QUEEN MEEMI_*⚜
❣55❣

*March 2017*

_Sadaukarwa ce Ga Basheer Usman family's_



*******

Tunda Muktar yaji labarin zuwansu Mangalu shima ya tarkato ya tawo, tun da yazo bashi da aiki sai aukin lallashi yake gun hassy har ya samu ta saki jiki .yauma da suke zaune a soron gidan gidan Malam suna hira Muktar yace "Hassyna kafin ku tafi nake son turo magabata na, kawai ayita ta k'are." katsahan taji Maganar tace "haba de?" yace "wlh da gaske don an matsan agida" ta juyo suka had'a ido yace "ki amince" tace "senai shawara domin kasan su Dady basa nan" yace "na sani Amma ai akwai 'yan uwanku kosu sa karb'a" murmushi tayi "dear kabari nai musu waya duk abinda sukace I wll tell u" yace "tnx babyna."Bayan ya tafi ta shiga ciki lokacin har inna Jummai ta sauke dambun da suke itada Husy da gudu taje ta rungume husy tace "albishirunki tweeny" tace "goro" Dan dariya takumai "yau de Muktar yace zai aiko maganar auren mu" husy tace "ke dan Allah!" nan Jummai ta d"ago "me ake cewa ne?" nan suka sanar Mata tace "hmm lalle Matar Mutum kabarinsa Allah yayi bada Husy bace." Nan husy tace ay inna dama komai nufin Allah ne, yanzu sai agayawa su Dady aji mai zasu ce ko?" Hassy tace "nima haka nace mai. Bayan sunci sun sha Husy ta bugawa Mum waya ta d'auka nan ta sanar mata tace abari nan da 1 week zasu dawo domin Arif sunyi hutu Dad'I ma haka yace. husy dake mak'ake da waya ta daka tsalle "Allah ya kawo ku lafiyya" tana gamawa tace "tweeny Mum tace abar maganar next week zasu dawo sai ayi" Jummai tace "hakan ma yafi kuwa."


*Bayan sati daya*

*******
Su Dady suka sauka A Nigeria sai da sukai kwana biyu Wanda yayi dai-de da saura kwana d'aya biyu hutun su Hassy ya kare san nan suka zo Mangalu malam yayi masu tarbar arziki, bayan sun huta Dady yayi maganar Wanda ke san ita Hassy nan ya umarceta data bugama Shi Muktar d'in waya hakan kuwa akai tayi mai waya bai ma Dade da zuwa garin ba. Direct gidan Malm yaxo asunkuye ya shiga ya ga idasu sun yaba da shi yayi masu bayani Dady ya kad'a baki yace "naji yace shidan me garin nan ne inace shine wanda aka kusa Auren sa da husaina abu bai yiwuba" malam yace "shine" Dady ya had'e rai "Sam ba zata sab'uba" ya kalli Muktar "yaro kayi hkr domin kaga tun farko babanka yace baya so, kaga yanzu idan yaji 'yar uwar d'ayar ce bazai yarda ba" zufa ce take ta karyowa Mukatr wan nan shi ake kira ga koshi ga kwanan yunwa Malam dafe hannu yayi domin dama yasan za'arina a sanyaye Mukatr ya tashi ya fita kamar zaiyi kuka Hassy kuwa tana d'akin Jummai tana kuka domin taji yanda akayi sai hkr husy ke bata tace insha Allahu zai sakko.


*****
Shirin komawa Abuja sukayi suma su Hassy suka bisu su Malam sun yi kewar Su ,sunkai dai de titin da zai fudda kai babban titi husy taga Gwamma da taron mata suna bara nan tace wa Dady Adam tsaya zata bada sadaka tunkan su tsaya su Gwamma sun cika gun, ta zaro 1k ta mikawa Gwamma suka had'a ido Motar su taja. Gwamma sai kuka take tana domin tayi danasanin rayuwar datai abaya.Tafiya akace yankin azaba sai wajen k'arfe 7 suka je Abuja Hassy wani k'aramin zazzab'ine ya rufeta.
Ab'angaren Muktar kuwa hankali tashe yaje gida Goggon sa na zaune ta Ganshi abirkice tace "yadai?" yace "Goggg kunga ni ko! da tun farko ba ai haka ba wlh da Dadynta bazai hanani ba" tace "wai meye
Showing 135001 words to 138000 words out of 155648 words