Hansai tace "idan ba biyayya ba nima me zan dakai, wallahi darajar Baba kaci zan Aureka ne kuma wallahi bazan tab'a cewa bana son Auren ba."
Kai Mata hauri yayi tayi baya tana kuka,dama da Hijab d'inta ,kawai se ta zarce Bayan dutsen su tana zuwa ta zauna da abin busa d'inta, tanayi idon ta na b'ulb'ulo da hawaye ,domin ta tuno Muntarin ta, kamar Amafarki yaji sauti .
Firgigit ya mik'e daga baccin daya kwashe shi,tsai ya ganota durowa yayi daga kan Bishiyar ya je kusa da ita ya tsaya, yace "Hansai an rabamu ko?
Da sauri ta juyo suka had'a Ido tace "Muntari yanzu shikenan Mafarkin mu ya zama ba Gaskiya ba?". Muntari yace "nikam bazan iya babu ke ba".
Hansai itama tace "nima haka Muntari .Amma ba yanda muka iya". Kuka ne ya kubce Mata da gudu tayi baya ya bita, suka tsaya yace "har abada Hanasi kece Masoyiyata, ina Sonki Sona Gaskiya dama zasu Amince da Auren namu".
Tace "Muntari mu fawwalawa Allah shine zai iyar mana" haka sukai ta hira. Suka rabu cike da k'unar Rai.
******** Bayan kwana 2 anyi rigingimu a Gidan inda Gwamma ta kek'ashe baba ma ya kafe .
Yauma da take tsaye tana tunani "yo wai ni ko Maganin da boka ya ban baya Aiki ne? Naga Malam baya yarda da Magana ta" nan Taje ta duba kwanan ajiyarta,Mamaki ne ya cika ta Ganin Maganin da Bokan ya bata ,tace "kodai bashi na zuba ba!". "Lalle dole mana Malam yana min musu" da sauri ta d'auka Mayafinta,ta fita Gidan Delu, zuwanta ta Sanar da ita, Shine Delu tace "yanzu Shikenan kin b'ata Aikin ki da kanki".
Gwamma tace "to ni yazanyi ,yanzu?" Delu tace "ki kawo wani Kud'in na koma ya had'a wani Gwamma tace nikam wallahi ban da kud'i sai dai ki ran ta Min".
Tace "ba Matsala zan baki" nan suka K'ark'are zata je anjima haka ta tafi tana Surutai A hanya.
Wajen k'arfe 8 na dare sai ga Delu har taje gun bokan. Gwamma suka kule ad'aki tace "gashi Boka yace ki tabbatar ayau da daddare kin amfani dashi Hayak'i Zakiyi kamar turare, inde suka shak'a kin samu kansu."
Da rawar Jiki Gwamma ta boye a zanin ta,sukai Sallama da Delu ta tafi. Bayan Dan Lokaci ta turara Hayakin duk suka shak'a .
Washegari kuwa Malam ya tsare Mudi yace "kaga yau saura kwana 2 D'aurin Aurenka." Mudi ya kada baki yace "Baba ni bana son Auren nan".
Gwamma dake d'aki tace "yawwa".
Showing 63001 words to 66000 words out of 155648 words
Kai Mata hauri yayi tayi baya tana kuka,dama da Hijab d'inta ,kawai se ta zarce Bayan dutsen su tana zuwa ta zauna da abin busa d'inta, tanayi idon ta na b'ulb'ulo da hawaye ,domin ta tuno Muntarin ta, kamar Amafarki yaji sauti .
Firgigit ya mik'e daga baccin daya kwashe shi,tsai ya ganota durowa yayi daga kan Bishiyar ya je kusa da ita ya tsaya, yace "Hansai an rabamu ko?
Da sauri ta juyo suka had'a Ido tace "Muntari yanzu shikenan Mafarkin mu ya zama ba Gaskiya ba?". Muntari yace "nikam bazan iya babu ke ba".
Hansai itama tace "nima haka Muntari .Amma ba yanda muka iya". Kuka ne ya kubce Mata da gudu tayi baya ya bita, suka tsaya yace "har abada Hanasi kece Masoyiyata, ina Sonki Sona Gaskiya dama zasu Amince da Auren namu".
Tace "Muntari mu fawwalawa Allah shine zai iyar mana" haka sukai ta hira. Suka rabu cike da k'unar Rai.
******** Bayan kwana 2 anyi rigingimu a Gidan inda Gwamma ta kek'ashe baba ma ya kafe .
Yauma da take tsaye tana tunani "yo wai ni ko Maganin da boka ya ban baya Aiki ne? Naga Malam baya yarda da Magana ta" nan Taje ta duba kwanan ajiyarta,Mamaki ne ya cika ta Ganin Maganin da Bokan ya bata ,tace "kodai bashi na zuba ba!". "Lalle dole mana Malam yana min musu" da sauri ta d'auka Mayafinta,ta fita Gidan Delu, zuwanta ta Sanar da ita, Shine Delu tace "yanzu Shikenan kin b'ata Aikin ki da kanki".
Gwamma tace "to ni yazanyi ,yanzu?" Delu tace "ki kawo wani Kud'in na koma ya had'a wani Gwamma tace nikam wallahi ban da kud'i sai dai ki ran ta Min".
Tace "ba Matsala zan baki" nan suka K'ark'are zata je anjima haka ta tafi tana Surutai A hanya.
Wajen k'arfe 8 na dare sai ga Delu har taje gun bokan. Gwamma suka kule ad'aki tace "gashi Boka yace ki tabbatar ayau da daddare kin amfani dashi Hayak'i Zakiyi kamar turare, inde suka shak'a kin samu kansu."
Da rawar Jiki Gwamma ta boye a zanin ta,sukai Sallama da Delu ta tafi. Bayan Dan Lokaci ta turara Hayakin duk suka shak'a .
Washegari kuwa Malam ya tsare Mudi yace "kaga yau saura kwana 2 D'aurin Aurenka." Mudi ya kada baki yace "Baba ni bana son Auren nan".
Gwamma dake d'aki tace "yawwa".
Book Chapters
Chapter 1Chapter 2Chapter 3Chapter 4Chapter 5Chapter 6Chapter 7Chapter 8Chapter 9Chapter 10Chapter 11Chapter 12Chapter 13Chapter 14Chapter 15Chapter 16Chapter 17Chapter 18Chapter 19Chapter 20Chapter 21Chapter 22 Chapter 23Chapter 24Chapter 25Chapter 26Chapter 27Chapter 28Chapter 29Chapter 30Chapter 31Chapter 32Chapter 33Chapter 34Chapter 35Chapter 36Chapter 37Chapter 38Chapter 39Chapter 40Chapter 41Chapter 42Chapter 43Chapter 44Chapter 45Chapter 46Chapter 47Chapter 48Chapter 49Chapter 50Chapter 51Chapter 52