Mata Muntari Lokacin yana can Gidan da zasu Zauna da Amaryar sa yana Gyarawa,haka nan yazo Ladidi ta tareshi.
"Muntari nikam wai kai bakasan Hansai ba 'yar Gidan nan bace?"
Gabansa ne ya fad'i yace "haba Gwaggo kidena damuwa da jita- jita."
"Kai Muntari ba wani Jita- Jita sai Gaskiya.
Dai -dai Lokacin Maigari ya shigo ya tarar da su a tsaye nan ya tambayi ba'asi Gwoggo tace "Malam nikam ayi bincike kan auren nan nifa Gaskiya ina juya maganar Gwamma ,shiru yayi baice komi ba can yayi gyaran murya yace "nima kawai ji nake bansan Auren gabana har fad'uwa yake. Amma yau zan samu shi Malam d'in akan Maganar.
*Bayan Awa Hud'u*
Malam ne tsaye Shida Maigari suna Magana, idan ka kalli fuskar Malam tsab zaka Zakulo razanar dake kai .Amma sayya dake yace "wato ranka ya Dad'e Maganar Gaskiya Hansai ba 'yata bace nan ya gaya mai Asalin Had'uwar su San nan yace "Kaga kuwa mai Asalice Rabuwa ce kawai Sanadin daya sa bata tare dasu iyayen nata, idan akai duba da yanda abun ya faru, ayanzu nine matsayin uban ta."
Maigari yace "Lalle Abin tausayi ce .Amma zan gayawa ita Mahaifiyar yaron aji ta bakinta.
"Toh! toh! ba damuwa" inji Malam.Jikin sa asanyaye ya shiga gida .
Shikam Maigari yajewa da Gwogg Maganar nan tayi tsalle ta dire kan D'anta bazai Auri wanda ba asan iyayenta ba, shima Maigari d'in baya so Amma kunyar Mutane yake ji, nan suka k'ark'are kawai Afasa Auren.Turk'ashi! wata Sabuwa kenan inji 'yan caca.
Washegari kamar k'arfe Goma na Safe Malam na shirin tafiya Gona akai sallama dashi ya fita, Yaron Maigari yagani saida K'irjin sa ya buga, nan Yaron ya gaidashi sa'an nan yace da Malam Maigari na neman sa, tare suka jera nan sukaje Maigari na Zaune kan tabarma Asoron Gidan sa, ya shiga suka gaisa .
Sai da yayi tsai San nan ya tashi ya Zauna yayi Gyaran Murya yace "wato Malam komai dama Muk'addari ne daga Allah, Matar Mutum Kabarin sa, kayi Hak'uri Auren nan abarshi, tunda uwar Yaron tace bataso, haka 'yan Uwa da Azo daga baya Ana kace nace! .Gwanda A Hak'ura.
Dumm!! Malam yaji akansa Idon sa yayi ja "yace bakomi dama Matar Mutun kabarin sa, Allah ya had'a kowa da rabon sa".
Maigari yace "Amin ,Amma aimin afuwa" Malam yace "Haba de wanda baisan k'addara ba shine zai damu" .
Haka ya fita yana tafiya a Hanya yana Magana har yaje tsakar gidan sa, Gwamma na gefe tana shara Jumma na d'aki kawai sai ya zauna bakin Bishiya ya dafe kai.
Gwamma ta taso "Aa Malam ya na gan ka haka?" Shikan Malam yace "An fasa Auren nan, Maigari yace ba zasu Aura wadda bata da Asali ba".
D'ora Hannu tayi a ka kamar zata kurma ihu Malam yace "Aa meye haka? sai kace wanda akai Mutuwa". Gwamma data juya ta yi dariya ganin hak'an ta ya cimma ruwa tace "Allah sarki Hansai .
Nan Jummai ta fito tana Malam Lafiya haka?"
Gaya yayi take ta hau kuka, "shike nan na shiga uku yanzu abinda Zasuyi mana kenan! yau saura kwana takwas wayyo Allah" .
Hansai dake shigowa Gidan da leda A Hannu ta aje da sauri ta tari Jummai tace "Inna Mayya faru?".
Jummai tace "an fasa Aurenki da Muntari". Hansai taji kanta na yuuu saboda Mamaki. Luuu tayi k'as Asume.
Da sauri sukayi kanta Gwamma kam D'aki ta Shige tana rawa, yay yafawa Hansai ruwa sukayi take ta Farfad'o da kuka, nan Jummai ta shige da ita D'akin ta, ta kwanta tana Mata nasiha ita kam Hansai son Muntari ne taji ya nunku kuka ta fasa.
Can kwa Gidan Maigari Muntari shima Kukan yake saboda tsananin son da yakewa Hansai da shak'uwar da ke tsakanin su, Shekara biyar kenan daya k'wallafa ransa akan ta ,haka sukai ta lallashi shikam yace haka yake sonta koda bata da kowa d'aki ya shige ya kulle ,suka bishi suna bugawa Amma yak'i ya bud'e.
Haka dai wad'an nan rayukan masu tsananin son juna ,suka rayu a kwana biyun nan cikin k'unar Rai ga gari ya d'auka ai Hansai bata da iyaye an fasa Auren ta, ko ina Maganar abuga k'auye.
"Jummai inaga zanyi huce Haushi kawai domin duk Lokacin Dana sa Auren baza a fasa ba, sai a d'aura da Mudi".
Fit Gwamma ta fito "Aikuwa badai a Gidan nan ba, wai abada Auren D'ana da wan nan abar, to sai de ko Bayan Raina".
Showing 57001 words to 60000 words out of 155648 words
"Muntari nikam wai kai bakasan Hansai ba 'yar Gidan nan bace?"
Gabansa ne ya fad'i yace "haba Gwaggo kidena damuwa da jita- jita."
"Kai Muntari ba wani Jita- Jita sai Gaskiya.
Dai -dai Lokacin Maigari ya shigo ya tarar da su a tsaye nan ya tambayi ba'asi Gwoggo tace "Malam nikam ayi bincike kan auren nan nifa Gaskiya ina juya maganar Gwamma ,shiru yayi baice komi ba can yayi gyaran murya yace "nima kawai ji nake bansan Auren gabana har fad'uwa yake. Amma yau zan samu shi Malam d'in akan Maganar.
*Bayan Awa Hud'u*
Malam ne tsaye Shida Maigari suna Magana, idan ka kalli fuskar Malam tsab zaka Zakulo razanar dake kai .Amma sayya dake yace "wato ranka ya Dad'e Maganar Gaskiya Hansai ba 'yata bace nan ya gaya mai Asalin Had'uwar su San nan yace "Kaga kuwa mai Asalice Rabuwa ce kawai Sanadin daya sa bata tare dasu iyayen nata, idan akai duba da yanda abun ya faru, ayanzu nine matsayin uban ta."
Maigari yace "Lalle Abin tausayi ce .Amma zan gayawa ita Mahaifiyar yaron aji ta bakinta.
"Toh! toh! ba damuwa" inji Malam.Jikin sa asanyaye ya shiga gida .
Shikam Maigari yajewa da Gwogg Maganar nan tayi tsalle ta dire kan D'anta bazai Auri wanda ba asan iyayenta ba, shima Maigari d'in baya so Amma kunyar Mutane yake ji, nan suka k'ark'are kawai Afasa Auren.Turk'ashi! wata Sabuwa kenan inji 'yan caca.
Washegari kamar k'arfe Goma na Safe Malam na shirin tafiya Gona akai sallama dashi ya fita, Yaron Maigari yagani saida K'irjin sa ya buga, nan Yaron ya gaidashi sa'an nan yace da Malam Maigari na neman sa, tare suka jera nan sukaje Maigari na Zaune kan tabarma Asoron Gidan sa, ya shiga suka gaisa .
Sai da yayi tsai San nan ya tashi ya Zauna yayi Gyaran Murya yace "wato Malam komai dama Muk'addari ne daga Allah, Matar Mutum Kabarin sa, kayi Hak'uri Auren nan abarshi, tunda uwar Yaron tace bataso, haka 'yan Uwa da Azo daga baya Ana kace nace! .Gwanda A Hak'ura.
Dumm!! Malam yaji akansa Idon sa yayi ja "yace bakomi dama Matar Mutun kabarin sa, Allah ya had'a kowa da rabon sa".
Maigari yace "Amin ,Amma aimin afuwa" Malam yace "Haba de wanda baisan k'addara ba shine zai damu" .
Haka ya fita yana tafiya a Hanya yana Magana har yaje tsakar gidan sa, Gwamma na gefe tana shara Jumma na d'aki kawai sai ya zauna bakin Bishiya ya dafe kai.
Gwamma ta taso "Aa Malam ya na gan ka haka?" Shikan Malam yace "An fasa Auren nan, Maigari yace ba zasu Aura wadda bata da Asali ba".
D'ora Hannu tayi a ka kamar zata kurma ihu Malam yace "Aa meye haka? sai kace wanda akai Mutuwa". Gwamma data juya ta yi dariya ganin hak'an ta ya cimma ruwa tace "Allah sarki Hansai .
Nan Jummai ta fito tana Malam Lafiya haka?"
Gaya yayi take ta hau kuka, "shike nan na shiga uku yanzu abinda Zasuyi mana kenan! yau saura kwana takwas wayyo Allah" .
Hansai dake shigowa Gidan da leda A Hannu ta aje da sauri ta tari Jummai tace "Inna Mayya faru?".
Jummai tace "an fasa Aurenki da Muntari". Hansai taji kanta na yuuu saboda Mamaki. Luuu tayi k'as Asume.
Da sauri sukayi kanta Gwamma kam D'aki ta Shige tana rawa, yay yafawa Hansai ruwa sukayi take ta Farfad'o da kuka, nan Jummai ta shige da ita D'akin ta, ta kwanta tana Mata nasiha ita kam Hansai son Muntari ne taji ya nunku kuka ta fasa.
Can kwa Gidan Maigari Muntari shima Kukan yake saboda tsananin son da yakewa Hansai da shak'uwar da ke tsakanin su, Shekara biyar kenan daya k'wallafa ransa akan ta ,haka sukai ta lallashi shikam yace haka yake sonta koda bata da kowa d'aki ya shige ya kulle ,suka bishi suna bugawa Amma yak'i ya bud'e.
Haka dai wad'an nan rayukan masu tsananin son juna ,suka rayu a kwana biyun nan cikin k'unar Rai ga gari ya d'auka ai Hansai bata da iyaye an fasa Auren ta, ko ina Maganar abuga k'auye.
"Jummai inaga zanyi huce Haushi kawai domin duk Lokacin Dana sa Auren baza a fasa ba, sai a d'aura da Mudi".
Fit Gwamma ta fito "Aikuwa badai a Gidan nan ba, wai abada Auren D'ana da wan nan abar, to sai de ko Bayan Raina".
Book Chapters
Chapter 1Chapter 2Chapter 3Chapter 4Chapter 5Chapter 6Chapter 7Chapter 8Chapter 9Chapter 10Chapter 11Chapter 12Chapter 13Chapter 14Chapter 15Chapter 16Chapter 17Chapter 18Chapter 19Chapter 20 Chapter 21Chapter 22Chapter 23Chapter 24Chapter 25Chapter 26Chapter 27Chapter 28Chapter 29Chapter 30Chapter 31Chapter 32Chapter 33Chapter 34Chapter 35Chapter 36Chapter 37Chapter 38Chapter 39Chapter 40Chapter 41Chapter 42Chapter 43Chapter 44Chapter 45Chapter 46Chapter 47Chapter 48Chapter 49Chapter 50Chapter 51Chapter 52