Iyalleta wani Dattijo ai Sarkin noma ne,shi aka bawa Sarkin noma last year, ai su Ahmad Suka dinga dariya akan Sarkin noma Kuma dangartakar ma tayi nesa Dan son bata kudi na Yar China,Haka Suka tafi suna ta dariya Aamna Tace da Yamma zata dawo su Sha kallo,tana ta dariyar abin tabi Ahmad Suka tafi gida idan ta huta zata koma,Wajen su Humaira ya sauketa ba tare da ta Kira drivern Mummy da ya kawo ta ba.









AsmaBaffa
10/29/21, 7:45 PM - Buhainat: 🌵🌵 DUNIYA TA AAMNA🌵🌵








NA KUDI NE








DUNIYATA IS DEDICATED TO GARBA BUTALAWA FAMILY.








111-115









Official









By
AsmaBaffa










Page naku ne

UMMU SHU'AB
SHAHRY
AUTATUL KHAIR














Bayan Yar China sun huta Sallah sukayi Suka sake sabon wanka,cikin Kawayenta akwai me makeup musamman Yar China tace tazo ta Yi Mata da rana,karfe hudu ba African time suna yin Sallah aka fara kwalliya dukkan Wanda sukayi anko shi Suka saka,ankon atamfa wata blue and red tayi kyau,Yan Mata Dukkansu anyi ankon kamar masifa,Yar China Kuma lace ta saka me kyau wani black and Orange,an Mata dauri me kyau da Orange Headtie kana gani kasan itace Amarya ba sai ka tambaya ba,takalmi da Jakarta black,abinka da fara,tun kafin ta Gama shirin Yan Algaita sun fara,Yar China wata Gadara take ji,kanta ya sake girma ita Yar Uwar Sarkin noma,Fili aka bawa masu Algaita,Yan matan da basu Zo da safe ba sune suka fara zuwa da Yamma sai yanzu ma Yan gayun ke zuwa,Angwaye ma sun dau sabon wanka sun zo,Ahmad Kuwa bayan Aamna ta cakare ita ma ankon ta saka,wacce take wa Humaira Kwalliya itace ta tsarawa Aamna kamar wata Amarya,ga dinkin fitted gown aka Mata dai dai ita surar Nan tata ta sake fitowa habawa ai Aamna one in million ce,babu Wanda zai so ya daina kallonta musamman yanda ta Kara wani kyau da kiba ta Kara wani haske,Ahmad ne ya canja Shadda fara Kal yazo a rantsatsiyar motarsa baka yazo har ciki ya Shiga wajen Mummy.

Humaira ta fesa gayu tazo ta rike shi ta saki kuka,Ahmad ya kalleta yace Mene haka Kuma sis? Kukanta ne ya karu tana kuka muryarta da kyar take fita tace Yaya Wai anjima za a kaini Inji Mummy Dan Allah Yaya Ahmad kace sai gobe,Dariya ma ta bawa Ahmad ya shiga lallashinta gani gaki sis ke da muke ma kusan gida Daya Mene abin damuwa? Ko kin daina so na ne? Kai ta girgiza tace Ina sonka Mana yace to ki kwantar da hankalinki Muna tare Baki da matsala,Humaira ta kwabe Fuska tana ta faman kallon Ahmad hankalinta a tashe da gani a firgice take,gashi ance ita za a fara kaiwa,Meke faruwa ne Humaira? Humaira tana so ta fadawa Ahmad me Mubarak dinta yace tana tsoro Kar ya Mata fada,Hannu ta Shiga yarfewa tace Yaya dan Allah ka yima Brown magana,akan me? Uhmm...uhm....cewa yayi ....Ahmad ya gane zancen Maganar first Night yayi ya firgita Masa kanwa,Murmushi yayi yace Jeki na gane Zan masa magana karki damu Wasa yake, Humaira tana Hawaye tace Allah Yaya ba Wasa yake ba,nifa na fada Miki sis Haba ko Baki yarda ba? Murmushi tayi tace na yarda,to shiga ciki kinji, okay ta Furta ta tafi wurin Kawayenta da suke ta chashewa da kida a mugun wasu speakers duk Yan Lagos ne Basu digon kunya ko ta minti Daya.

Ahmad a bedroom din Mummy ya Iske Aamna tana saka takalminta me tsini ta yafa mayafi,Yana Shiga ganin ba kowa ya rungumeta Yana Jin dadi a ransa shi Kam ya Gama dacewa,Mazaunanta ya shafa Yana sinsinar kamshinsa itama haka,kinyi kyau My world,ai ka fini yin kyau My King,you are the love of my life,I give you all of me my king,Kissing dinta zaiyi ta matsa da sauri sabo da kar shanye Mata jambaki,hand bag dinta ta dauka me tsada tace let's go,a Haka Zaki tafi kalli fa Dan mayafin Ni gaskiya maza zasu kallar min Mata,Dan Allah King kazo mu tafi wanne maza kalli fa Yan biki duk ba gyale, amma Ni na yafa ma gashi da girmansa ya rufe fa har bayana,juya to na gani,mayafin ya gani ya Dan sauka yace to muje,tare Suka fita Ana ta kallonsu duk inda Suka gifta,Su Tawaga tuni sunje can suna jiransa,gashi kowannensu ya canja wanka,Angon wani milk yard ya saka Dan gaske ga skin din Tawaga Kamar wani Dan Latin America Haka yake.

Ahmad Yana zuwa da Kansa ya fito ya zaga ya budewa gimbiyar tasa mota ta fito,Jakarta tana hannunsa ya rike mata ko kunya Bai ji ya rike Mata Hannu ga Jakarta ya rike,Yar China ce ta fito Daga cikin gidan da suke ta Sha gayu Aamna tace Yarinyar Nan tasan gayu fa Ina ganinta wata shashasha,Ahmad murmushi yayi yace Ni dama nasan tasan me takeyi tunda Tawaga ya sota zai aure ta,Yar China ta fito da Kawayenta can gefe Kuma masu Algaita ne da ganguna suke faman kida me shegen Dadi,masu busa Kamar zasu cire kumatunsu,Yar China ta biyasu kudi sosai ga ruwan liki suna Sha,ai Yar China tana hango Aamna da Ahmad tazo wajen tana murmushi Tace Aunty kina ji Dani kinzo da safe kin dawo da Yamma wannan ko kanwarki ce ni iyaka abinda Zaki Mata kenan Ina godiya da yawa da nayi Niyyar Yi Miki kyautar dubu yanzu amma Ango yace na daina,idan an kawo Ni nayi farfesun Amarci Zan kawo miki,Aamna tayi Dariya ita da Ahmad,Aamna a ranta tace Zaki bayani yarinya sai dai Ni na Miki farfesun nazo jinya,Masu Algaita Suka taho Gaban Yar China angwaye abokai sunfi su Goma suka fito da kudi za ayi liki,a tsakiya aka sa Ango Tawaga da Amarya Yar China,Mutane suna ta kallo Ana nishadi,masu Algaita Tsayawa sukayi da kida Suka fara yiwa Yar China Kirari Ana ta dariya suna cewa.

Lafiya Yar sarki jikar Sarki,kaga Yar na gada ba Yar na koya ba,gaishe ki Jikar sarki,Yar China tana wani girman Kai an nutsu Ana Izza,cikin Kirari suka ce kayi dace saurayi samun Jikar sarki ba Wasa ba,gabanki lafiya bayanki lafiya Jikar sarki,Hajiya Sadiya Yar Fulanin asali ta Ango Aliyu Haidar sa gabanka inda kake so kayi dace...ka tsallake rijiya da baya...sai Suka ci gaba da kida tare da busa algaita angwaye suka dinga fyalli da Naira,Aamna tazo tayi liki itama,ta likawa ango da Amarya Yan dari biyar biyar sababbi sannan ta koma likawa mijinta,Iyalle ce ta fito da sauran dangi suma Suka zuba nasu,Yar China tana murna ta rike Hannun Iyalle tace Iyalle ta Dan Allah kiyi rawa,bikin Yar Chinanki guda,Iyalle tace Allah ya sauwake min da rawa,Iyalle da sauranki fa birgewa zakiyi a Nan wajen,Iyalle tace ja'ira,Wai Ni Yar China Ina kika samo mutane Haka ne? Yan Mata sunki karewa,Yar China tace duk kwayena ne kowa da yazo wajen Nan Indai Ni na gayyace shi to ya sanni na shi babu wani gayyar sodi anan da kike gani,Iyalle tana Dariya tace amma sun Miki Halacci,Kar ma suyi Mana nima idan na hadu da yarinya naci ubanta,Iyalle ta furta Yar Nema to ayi sauri sunce 6pm Za'a Zo daukan Amarya sai an gama Kai sauran amaren kece ta karshe,Yar China tace Dan Allah Iyalle a Bari Mana sai gobe a kaini a nutse,kinyi kadan yarinya biki Daya zamuyi yau za a kaiki nasan halinki bakin Nan ba karewa zai Yi ba ana Kara Miki kwana daya Zaki ce gobe yini su dawo,Dariya Yar China tayi harda wani tafawa da Iyalle tace Iyalle kin San jikarki ai da Kun sake Kun Kara min lokacin alakoro to gobe Dan asharalle ne zaizo,to Baki Isa ba yanzu ma ya kamata ku sallami masu Algaita,Na fa biya kudi da su za a kaini suna bina da Algaita,Iyalle ta Bude baki tace dama Haka kika ce? Kwarai Kuwa na biya kudi Ni ku kyaleni Dan Allah yau Daya bafa ba Kara Yi zanyi ba har abada,Iyalle tace ai shike Nan ku karata ta tafi gida.

Yar China wajen Aamna taje ta ganta ta rike Hannun Ahmad Gam,Tace Kai Yar Mannau Dan girman Allah ki kyale bawan Allah ya sake wannan azo dake Unguwa ai masifa ce wlh Zaki jawo ya daina fita dake,Aamna tayi Dariya tace Wai ke Ina ruwanki ne kije ga sababbin kawayenki can sun zo,Yar China ta duba ta hango su an sauke su a Napep,Hannu ta Shiga daga musu su taho gata,Ahmad ta kalla Yana can suna magana da su Jibson Yar China Tace wannan ba gata bane ka saketa wayo take maka zata kashe maka kasuwa,Dariya Ahmad yayi ba tare da ya juyo ba.

Bash ne yace mu tsaya Kawai mu tafi da wannan Amaryar,Yar China Idonta ya kawo kwalla ta koma wajen Tawaganta tace baza a Kara min alakoron lokaci ba? Kina gani dai Yan Uwanki sunce sun fara shiri kina kallo duk kayanki har Wanda kika cire yau an Kai can gidan kice wani Karin lokaci,Yar China Baki ta rike tace Yau naji mayu yaushe suka kwashe kayan? Tawaga yace Brown ne fa ya Kai tare da Salamatu ai sunce tsinke naki babu a gidan Nan,sai kayan jikinki sai Wanda Zaki canja yanzu,Yar China tace shike Nan karyata ta Kare yau kuma,Tawaga yace na Gama gajiya ni maybe ma yau bazan iya ko motsa yatsa na ba idan na kwanta,Yar China taji sanyi a ranta tace na godewa Allah ya gaji yau ba abinda zai min,Yan bakin ciki su Habiba harda cewa wani Zan Sha zafi to suzo su gani ya gaji ma,tana Maganar zuci Batasan ma a fili ta fada ba Tawaga yaji,Dariyarsa ya kunshe dama wayo ya hada mata sabo da ta kwantar da hankalinta,su Habiba ne suka janye Yar China tazo ta shirya za a tafi kaita,Wanda baza su je Kai Amarya ba sun Gama biki duk sun tafi kasancewar magrib ta gabato,Dangin su Yar China kaf sunje sun ga gidan Yar China sun dawo da Santi suna mamaki.

Haka wasu kawayen duk sunje sun Sha kallo sun dawo dake wasu Yan Mata Yan Uwan Yar China suna can sune suka Kara gyara gidan,kayan kitchen da kayan kyale kyale da Suka Kara siyo Mata na dangi masu kyau Suka Kara a gidan, gidan Suka shirya Mata komai yanda zai bada kala,komai a tsari suka Yi,Brown Kuwa shi ya maida Aamna gida ta wuce part din Humaira sabo da Humaira aka fara kaiwa Basu da yawa daga ita sai Kawayenta su hudu,Suma duk sune suka gyara gidan da komai,Humaira an sake saka Mata wasu kyalekyalen masu tsada sabo da su akwai abin.
Itama Sameera lokacin da aka kawota sun sake zuba abinda babu da Kuma wasu abin na bukata na Yan gayu tunda an Gama musu me wahalar, Bangaren Nafeesat Kuwa wow itama ba karya sabo da Naira itama an Kara zuba wasu abin masu tsada musamman a kitchen,Ita Babanta da babarta su Suka kawota dakin Miji su biyu rak sabo da Yar Malam ce,sai da yayi Mata Nasiha,dama angwaye tun kafin bikin ya tarasu ya musu Nasiha sosai da sosai,Humaira da Sameera ma daidai gwargwado sun Sha Nasiha wajen Iyayensu sannan aka kawo su.

Hafsat ce ta hudu da aka kawo da dunbun Yan Mata da Yan uwa,Basu Dade ba Suka tafi aka bar Hafsat tana ta kuka Ita Daya tal,duk cikinsu Sameera ce Bata Yi kuka ba,Itama Hafsat ita Daya tal aka bari ba ko mutum Daya dama su tuni duk gyaran gidan da zasuyi sunyi dama komai a Leda yake ba abinda yayi Kura da kansu Suka bare komai Suka shirya Mata,Suma abinda ya Dace zasu karawa Hafsat duk anyi komai ko wacce gidanta sai kamshi yake zubawa Yana walwali,ko wanne gida a kasa 2 bedroom and Palo ne sai kitchen store da dining area,sama Kuma 2bedroom and Palo shima ko wanne daki da toilet dinsa masu Fadi da kyau gidan ya kayatu,kowa ya gani sai abin ya birge shi, compound din ko wacce yasha Interlock da fulawoyi ga parking space,harda Dan wurin hutawa anyi wata rumfa ta haduwa da shuke shuke ga wasu kujeru da table masu kyan gaske a wajen.

Yar China kawaye sun sata a gaba sai tsokanarta sukeyi yau zata gane kurenta,Dariya Yar China tayi tace to algungumai ya gaji da yawa Angon yau bacci zaiyi yace ko motsi bazai iya ba ta Allah ba Taku ba,Dariya Suka dinga kyalkyalawa Yar China Suna cewa wlh wayo ya Miki,Yar China Tace bama wasan karya da Tawaga na,wanka tayi ta fito Suka kwashe kayan data cire da komai nata Suka zuba a leda,wata kaza Salamatu ta kawowa Yar China kafin ta shirya aka takura Mata sai da ta cinye,aka Bata wasu tsumin ta Sha,Salamatu Tace kayan maganin tsuminki ki ya bedroom dinki an ajiye Miki su Safiyya zasu nuna Miki ki boye Banda hauka karki Bari ya gani Kuma,Tace to tana shafa lotion bayan ta gama wata atamfa super aka Bata ta saka dinkin Riga da skert sun kamata cif,Yar China ta tsula kyau,Atamfar Wata brown and red ta tsaru ka rantse ma ba atamfa bace wani material ne daban,gashin da yasha gyara Yan matan suka gyara Mata shi aka Mata wani acuci da shi Suka ce baza ta daura dankwali ba ai Amarya za a Kai Mayafi zata yafa,Mayafi Kato Amma me sharara da kyalli mayafin ya hadu shi aka bawa Yar China ta yafa sai ta fito kamar wata Yar India,takalminta me tudu Kalar mayafin red Haka jakar ma,Habiba ce ta rike kayan da Yar China ta cire a Leda har Inner wears baza su Bari ba sai an Kai gidanta,Kuma Iyalle ce ta sasu,Sallar Nafeela aka sa Yar China tayi tare da adduoi,tana Idarwa taji ance motoci sun Zama Ready Amarya ake jira,Yar China tana Jin Haka ta fara kuka Tace karyata ta Kare Ashe da gaske akeyi bikin Nan,Ashe ba karya bane kaini za ayi wayyo Iyalleta,Yan Mata suka dinga ihu da shewa Ana dariya,Habiba tace masu Algaita ma sun Zama ready suna mota sun shiga,Yar China Tace sunci Uwarsu Shegu dasu aka hada baki za a kaini yau,mutane Suka dinga dariya itace fa tace sune zasu rakata da Algaita.

Wajen Iyalle aka shigar da Yar China Iyalle taga Yar China tana kuka sai itama ta fashe da kuka tace bazan iya nasihar Nan ba naje daga baya nayi Mata a dakin mijinta,Yar China tana kuka tace Iyalle ki min Nasiha Allah idan Baki min ba sai tafka tsiya gobe bazan Yi girki ba a gidan,Iyalle kukanta ya tsaya cak ta bude Baki Tace Dan Ubanki karki girkin Mana yunwa ta Miki Illa,Yar China tace dama Baki Iya Nasiha ba tsoro kike ji Kar a kureki Baki iya ba komai ba,irin na mutanen da kike Yi,Iyalle maimakon Nasiha sai Suka bige da fada tace bazan Yi nasihar ba Dan ubanki idan nazo nayi Miki ai zanzo ganin gida salamatu ku tafi da ita ana jiranki,na fasa yin kukan rabuwar dake Yar banza fitsararriya cewar Iyalle, aka dinga dariya,Yar China taji ance a tafi sai kuka ta dinga Shure Shure da burburwa ana riketa taki fita daga dakin an rasa yanda za ayi da Yar China,tana kuka tana cewa Allah...Allah sai na fasa kofin da kika siya min Iyalle,Iyalle tace kinwa kanki marar kunyar karya,ke Baki ji kunya ba duk bikin da kika Yi kin koma kuka,ba fitsarar da bakiyi ba Ashe karamar marar kunya ce,Yar China kuka ta dage Jin koshi ko kunya babu,babu Wanda Bai lallabata ba taki hakura ta tashi a tafi,Iyalle tace ku jata ta karfi ku tafi,Yar China ta Dan Bude mayafinta ta leko tare da gallawa Iyalle harara ta rufe fuskarta again,Iyalle Tace Zaki ci Ubanki Kuwa wlh ku Kira min Tawaga Angonta Yana Nan a waje suna Jiran Amarya,ai Kuwa su Habiba suka tafi da sauri Suka Kira shi tare da fada Masa Taki yarda ta fito tana ta kuka an rasa yanda za ayi da ita,Tawaga Wanda da shi za a dauki Amarya yace gani Nan,su Jibson suna ta Masa dariya ya tafi gidan Haka ya kutsa har dakin Iyalle,yaga Yar China a lullube ta dunkule tana kuka,tana Jin Muryarsa tayi Mukus tsoron Tawaga take ji,duk haukarta tana nutsuwa idan ta ganshi,Iyalle tace gata Nan anyi anyi ta fita Taki,Yar China tana shesheka tace Haka nace Miki bazan fita ba? ai dai bance ba ko daga nace a Bari na huta,Iyalle tace to tashi ki bisu ko wallahi na Hana kowa zuwa rakaki ya dauke ki shi da Kansa,tun kafin Tawaga yayi magana ma ta Mike ta cikin Mayafi ta gallawa Salamatu Harara tace ai sai kuje ko.

Tafiya akayi aka sa Amarya a tsakiya,Sadiya tana kusa da Yar China ta Mata rada tace wai Yar China Ina kika samo wannan guy ne? Kinga yanda har abokansa duk hadaddu,Yar China ta daina kukan tace daga zagi wallahi,suna magana ai tana tunawa kaita za ayi gidanta sai ta sake fashewa da kuka tace shike Nan Yar unguwarmu,ga makwaftanmu duk su Maman Yusrah shiken nan ta sake sakin kuka angwaye suna ji,motar Ahmad da tafi ta kowa kyau Nan aka shigar da Amarya da Kawayenta su biyu sun sata a tsakiya,Yar China tana Zama tace kudi na Dana Tara a gidan Maman Yusra a karbo min abina na tafi da shi nasan kafin nazo Unguwar Nan sai da tsohon ciki na Dan Allah Habiba karbo min Tawaga ba mutunci ya sani ba wallahi ciki zai min da wuri,su Habiba suka dinga dariya Allah yasa Ahmad Bai shigo motar ba.

Haka suka je Suka karbi Mata dubu ukun ta duk akan dubu Uku take wannan abin,lokacin Ahmad ya Shiga motar Ana karbowa yaji Amarya duk uban kukan ta daina Tace ku rike kudin dubu ukun ku raba idan kun koma gida ku Siyo maltina da Madara ku Sha jininku ya tsatsafo sabo da a bikin Nan Kun Sha wahala,Suka ce mun gode Amarya.

Showing 111001 words to 114000 words out of 142807 words