kanta Ummi tayi cikin kulawa tace. "Sannu ko, zaki samu sauƙi insha Allah." Raleeya ne tayi mata ya jiki, jinjina mata kai tayi alaman da sauƙi.
Zama sukayi awajenta suna ƙara shagwaɓata da kuma tattalinta, Saifuddeen ma kasa barin ɗakin yayi, idanunsa kawai ya zuba mata, ita kuwa kasancewar alluran da Dr.Adnan yayi mata nada ƙarfi, hakan yasa wani irin bacci me nauyi ya ɗauketa. Ba'awani ɗau lokaci sosai ba Dr.Adnan ya dawo, fuskarsa cike take da wani irin annuri haɗi da zallan farinciki, ahankali ya buɗe ƙofar ɗakin ya shigo, ganin yanda yake sakin murmushi hannunsa riƙe da wata farar takarda yasa suka zuba masa ido,
Saifuddeen ne ya fara cewa.
"Lafiya kuwa Dr. me yake damunta?." Ƙarasowa cikin ɗakin yayi tare da miƙawa Saifuddeen ɗin hannu, alaman su gaisa, da ɗan mamaki Saifuddeen ya basa hannunsa, cikin bayyana farinciki Dr Adnan yace.
"Congrats Bro, Zaleeha na ɗauke da cikinka almost 2 to 3 month." Tamkar shigar shock haka duka sukaji maganan acikin kunnensu, Jikin Saifuddeen ne ya soma ɓari, cikin matsanancin mamaki, jin abun yayi kaman al'amara, duk da yasan cewa shiɗin baida matsalan rashin haihuwa, amma hakanan yakejin batun cikin Zaleehan kaman amafarki, Allah mabuwayi me yin yadda yaso a lokacin da yaso, yau gashi Zaleeha macen da zuciyarsa ke tsananin so da muradi, tana ɗauke da cikinsa, zamewa yayi daga kan wheelchair ɗinsa yayiwa Allah sujjada, dan nuna godiya da kuma tsantsar farincikinsa. Ummi da Raleeya kuwa ba abun da suke cewa sai.
"Alhamdulillah Masha Allah."
Cike da matsanancin farinciki, Ummi ta dubi Zaleeha, wanda ita bata ma san meyake gudana ba, dan baccinta ya ɗanyi nisa, Murmushi me ɗauke da farinciki tayi, cikin jin daɗi tace.
"Allah sarki Zaleeha yarinyar kirki, Allah Ya miki albarka, ya kuma sauƙeki lafiya".
Sai alokacin Saifuddeen ya ɗago daga sujjadan da yayi, kan wheelchair ɗinsa ya hau, sannan ya ƙaraso jikin gadon, wani irin farinciki ne bayyane akan fuskarsa, rungume Ummin sa yayi ƙam, tamkar wani ƙaramin yaro, cikin kasa ɓoye farincikinsa yace. "Alhamdulillah, Ummi na kinga Allah me iko ko, yabani kyauta me mahimmanci alokacin da ba zata ba, Ummi ki taɓa zuciyata kiji, har wani tsalle take saboda tsabar farinciki." murmushin jin daɗi Ummi tayi, cikin kulawa tace.
"Nasan kana cikin farinciki Babana, kuma muɗinma hakane muna cikin farin cikin."
Ɗan janye jikinsa daga na Ummi'n yayi, inda ya ƙurawa Zaleeha mayun idanunsa, cute face ɗinta yake kallo, wanda tayi fayau da ita, lokaci ɗaya har taɗan rame. Wani sabon zazzafar soyayyarta da ƙaunarta ne ke ratsa duk jikinsa, haka yakeji kaman ya jawota ya rungumeta.
Fahimtar hakane yasa. Ummi miƙewa,
ta fita cikin jin daɗi, hakama Raliya ta bita a baya,
suka tafi cikin tsananin jin daɗi.
A ɗakin Saifuddeen ɗin kuwa cikin kula ya Adnan ya ɗaura mata wani ɗan leden ruwa ƙarami,
dasa mata alluran cin abinci,
daurewa iya daurewa Zaleeha tayi amman duk da haka saisa ta fidda hawaye da anasa mata allurar ruwan a hannunta,
Hamma Saif kuwa cikin kula da lallama yake in boddy language yake cewa.
"So sorry Sannu ko, da zafi ko? Ya Adnan ayimata a hankali".
Dariya Ya Adnan yayi kana ya tattara kayan aikinshi yace.
"Raki da raki sun haɗu, a kula da cin abin cinta, domin bawai cikinne ya sata amai da jirinba, rashin cin abinci ne yasa yunwa yayi ta murɗanta, yunwarce kuma tasa mata jiri da kasala da duhun da take gani, so dole a kula da ita da cin abinci."
cikin gamsuwa Hamma Saif in boddy language ɗinsa yace.
"In sha Allah zan kula ya Adnan, na lura kam tunda na dawo bata son cin abinci".
ƙarishe haɗa kayanshi yayi kana ya sallamesu ya tafi.
Yana fita Hamma Saif ya hau gadon da kyau, hannunshi yasa yana shafa gashin kanta,
ita kuwa Zaleeha tunda taji Ya Adnan ya ambaci kalmar ciki sai tayi shiru tana bin Hamma Saif ɗinta da ido,
cikin tsananin jin daɗi yayi mata rubutu a wayarshi ya miƙa mata,
"Maman Baby, maman yara Ammin Adeel, my happiness my life my Everything. Ngd Ngd Ngd matuƙa,
Alhamdulillah Zaleeha Allah ya azurtamu da samar da abu ɗaya, jinina da jininki sun kasance a sashi ɗaya, burina da fatana sun cika kina da ciki har na tsawon wata biyu da sati uku".
Sai kuma ya sunkuyo yayi kissing goshinta,
ita kuwa Zaleeha lumshe ido tayi da sauri bayan ta karanta abinda ya rubuta mata,
hannunta tasa bisa lafeffen cikinta, wani irin daɗi farin ciki salama ne suka cika mata zuciya a baiyane tace.
"Alhamdulillah. Allah na gode maka da kyautar da kayi min, ya Allah ka al'barkacin abinda ke cikina,
ka bani shi mai kama da mahaifinsa".
Sai kuma ta ɗan buɗe ido ta, Hamma Saif ɗin nata, rubutun da yayine ta kuma karantawa.
"My dear meyasa!? Meyasa!!? Meyaaa!!!? Baki sanarmin kinada cikiba, meyasa kika ɓoye min abin farin cikinmu?".
A hankali ta kalleshi cikin sanyi tace.
"Hamma Saif nima bansan ina da cikiba".
Da sauri ya rubuta mata.
"Kamar yaya baki sani, tunda bakiga al'darkiba har wata biyu har na uku, ai yaci kisan kinada ciki".
A hankali tace.
"Hamma Saif ni ba ko wanne wata nake al'adaba, ina tsallake wata, wani lokacin har wata biyu nake tsallakewa sai ana uku sai ingani, shiyasa yanzunma da ban ganiba ban damuba dama duk zatona wata ƙil ƙarshen watannan zanyi dan ban taɓa tsallake wata ukuba a tunanina nanda kwana biyar zan gani".
Da sauri yasa hannu ya zare alluran ruwan dan ganin ruwan ya ƙare,
ɗagota yayi ya ruggumeta a jikinshi tsam, yana kissing nata tako ina.
A cikin gida kuwa,
Dr Adnan na fita Ameena na shigowa.
A can falon Ummi kuwa cikin farin ciki Ummi tace.
"Ni dama na daɗe da zargin Zaleeha nada shigar ciki, dan har kamar zan gayawa Saifuddeen sai kuma nace bari dai in barsu inga zasu gane da kansune ko sai an ganar dasu, kuma da yake sabbin shigane duk basu ganeba, kai yarinta da daɗi ƙuruciya dangin hauka.
Hayatuddeen ne da Ahmad dake ta farin cikin labarin suka haɗa baki wurin cewa.
"Au Ummi itama Zaleeha bata san tana da cikinba".
Raliya ce tace.
"Ato da alama kam bata saniba, dan in ta sani ai Hamma Saif zai sani".
Dariya sukayi baki ɗayansu.
Dai-dai lokacin Ameena ta shigo.
bayan sun gaisa da sune ta kalli Hayatuddeen daketa cilla Adeel sama suna dariya tace.
"Autan Ummi yau farin ciki da sassafe babu baƙin halin tashi daga bacci mai ka samu haka?".
Cikin dariya yace.
"Yo Aunty Ameena ai dolena in girma tunda naga kun dage tuƙuru zaku cika mana gida da yara, Adeel zaiyi ƙani ai dole in daina yarinta kada ayi uban banza".
Cikin mmki da rashin fahimta ta kalli su Ummi dake dariyar mgnar Auta, a hankali tace.
" Ummi me muka samune".
Cikin kula Ummi tace.
"Ammin Adeel ne, ta kwana ba lfy, to shine da Yayanku yazo ya gwada yake cewa cikine gareta".
Wani irin sassanyan murmushi Ameena tayi cikin jin daɗi da kekyawan zuciya tace.
"A a Alhamdulillah. Adeel ya girma, ya zama babban yaya, Allah ya sauketa lfy".
Amin Amin suka amsa baki ɗayansu.
Sosai sukayi farin ciki,
Nan Ameena da Raliya suka shiga kitchin.
Ummi kuwa ɗakinta ta koma,
a waya ta sanarwa Raihana dan tasan Adda Rahma kam mijinta zai gaya mata.
ta kuma sanarwa Goggo Dada da Aunty Mina ma sosai yan uwa da abokan arziki sukayi ta murnar cikin.
A can sashin Saifuddeen kuwa,
shi da kanshi ya taimaka mata, a tare sukayi wonka,
kana suka shirya,
rigar daya cire mata ta maida,
daga nan ta nufi ɗakinta dan canza sakekkiyar riga.
Shi kuwa Saifuddeen tana fita ya fara kiran abokanshi yana sanar musu,
sosai sukayi ta farin ciki sunayiwa Zaleeha tsiya wai ai dolema ta gudu ta kuma dawo da kafarta, wai Adeel ne ya korata, cikin kuma shi ya dawo da ita.
Ishaq ne ƙarshen kira dan yasan angone kar ya takurashi da sanyin safiya.
Ishaq kuwa yana jin wayarshi na rigging amman bai samu damar ɗagawa ba,
sabida yana lallaɓa amrya Rashida da yayi mata Dalla Dalla, sabida sam ya kasa ɗaga mata kafa, kun san riƙaƙƙun tuzurai ba sauƙi.
Yana tafe yana kuma gwada kiran Ishaq, yana shiga falonshi Ishaq na amsa kiran cikin tsokana yace.
"Ango kasha mai".
Dariya Ishaq yayi tare da cewa.
"Caɓa-caɓa ma kuwa mai kam harda lagwada, ai da nasan haka abin yake da ɗan karen daɗi da tuntini nayi aure".
Dariya sukayi baki ɗayansu,
Rashida dake manne jikin Ishaq ɗinne ta ɗan sune kanta a jikinshi.
shi kuwa Saifuddeen cikin happy yace.
"Al'bishirinka".
Da sauri Ishaq yace goro".
dariyarsa mai sanyi yayi cikin jin daɗi yace.
"Ka kusa samun ƙanin Adeel, jiya tunda muka dawo Baby keta amai ashe, cikine ni bamu saniba sai ɗazu ya Adnan ke sanar min."
Cikin tsananin jin daɗi Ishaq yace.
"Alhamdulillah, kai nayi farin ciki, kai mutumina ba sauƙi kai ko yaushe bugu ɗaya kake jefa ƙollo a raga".
Dariyar keta Saifuddeen yayi tare da cewa.
"Sune zalamammu daga na basu sai su ƙarɓa, kuma dama Zaleeha kam addu'ar da nayi tayi kenan, har a kaba na roƙi Allah ya azirtamin samun haihuwa da ita akai-akai kafinma ta ankara, gidana ya zame mata farin cikin duniyar ta, ta haifo min yara dozin-dozin".
Dariya sosai Ishaq yayi kana yace.
"Mugu, to Allah ya sanya al'khairi ya sauƙeta lfy".
Amin Amin yace kana sukayi sallama".
Daga nan ya shiga falon Zaleeha a falon suka haɗu cikin kula ya miƙo mata hannu, kana suka nufi falon Ummi.
Suna shiga, duk suka gaggaisa, hannu Zaleeha tasa ta karɓi Adeel dake hannun Hayatuddeen,
cikin kula sukayi mata sannu da jiki.
Ameena da Rayila ne da suka gama shirya breakfast a dinning table suka iso falon cikin sakin fuska Ameena ta kalli Saifuddeen fuska a sake tace.
"Congrats Abban Adeel, Allah ya sauƙeta lfy".
Amin Amin sukace baki ɗayansu,
Ita kuwa Zaleeha sunkuyar da kanta tayi ƙasa cikin tsananin jin kunya.
Shi kuwa Saifuddeen wani irin fitinenne kallo yakewa Ameena kallo mai cike da mutun taka, ji yake tamkar ya kamota ya ruggumeta, amman ba dama, ita kuwa ganin kallon da yake matane yasa ta meda kanta kan Zaleeha sabida taga Saifuddeen kallon farin cikin tayashi murnar da tayi yake mata ta hango wani baiyanenne farin ciki a fuskarshi cikin kula tace.
"Ammin Adeel ya jikin?".
A hankali tace.
"Na worke fa Ummu Adeel".
Dariya Raliya tayi tare da cewa.
"In kinci abinci ne zamu yarda kin worke".
Da sauri Saifuddeen ya jinjina mata kai alamar da kyau.
Ahmad kuwa dariyar ƙeta yayi tare da cewa.
"Allah ya fito mana da _Sodangi_ mu lfy, dan dai shine ya somu yasa aka gudu aka kuma dawo,
Jingudo haka sunan yake ko macece ko na mijine".
Dariya sukayi dukansu, Ameena kuwa shiru tayi.
Kalmar Jingudo da Ahmad ya kira ta amsa mata tarin tambayoyin dake ranta na cewa ina Zaleeha taje
Dan duk cikekken bafulatani in yaji an kira yaro da Jingudo ko Sodangi to yasan auren dole akawa mace, ta haifeshi a gidan wanda aka aura mata dolen, to shi ake cewa Jingudo."
A ranta ta tuno kalmar Adda Rahma inda take cewa mata.
"Kan Abu ɗaya ya taɓa nuna ƙulafashinsa a duniya a kanta ne kaɗai,
Sai ta kuma nazarci kalmar Ahmad na cewa Allah ya fito mana da Sodanginmu lfy don dai shine ya somu an gujemu an dawo".
Kai ta rausayar jin Ummi na cewa suje suci abinci.
kan dinnin table ɗin suka nufa, tana mai magar zuciya.
"Uhumm Ahmad kenan da kenan ka sani yanzu son Abban Adeel da nake hangowa cikin idonta ya wuce zaton mai zato, Allah sarki wato auren dole akayi mata, da alama kuma guduwa tayi lokacin da Adda Maryam ta rasune ta dawo ikon Allah to meyasa Zaleeha zataƙi Abba Adeel duk da tarin kyanshi da dukuyarshi basu ruɗeta ba."
Jin Saifuddeen ya murza hannunta alamun taci abinci ne yasa tasa hannu ta fara ci.
Zaleeha kuwa sanadin alluran da akayi mata to ta samu taci abinci sosai,
shiyasa duk jiri da murɗa da duhun suka tafi sai ɗan kasalar da ba'a rasaba.
Ranar dai Saifuddeen wuni yayi yana jinya,
shida kanshi kuwa ya kira Ya Ameenu da ya Ahmad ya sanar musu batun cikin Zaleeha,
sosai Ya Ahmad yai tawa Zaleeha wasa wai ashe yanzu kam girma yazo zata bar guje-guje.
A can gidan ya Ameenu kuwa suna gama yin mgnar ya kalli Ziyada dake zaune gefenshi hannunta ya rike a hankali yace.
"Kinji Adda Zaleehan takima bata da lfy, tanata aman laulayi ciki gashi kema har yanzu tafiyarki bata gama gyaruwa ba,
kiyi haƙuri sai kin ƙara samun sauƙi sai in kaiki ku wuni kinjiko Mar'tus saliha na tuba".
Kai ta jinjina cikin sanyinta irin na adda Maryam tace.
"To Ya Ameenu".
Jawota yayi ya ruggumeta domin biyeyyarta sak Maryam yake gani sam basu da gardama.
Bayan sati ɗaya lokacin cikin Zaleeha ya cika watanni uku cib-cib kuma Alhamdulillah ba laulayi sosai yanzu sai yawan cin abinci.
Da dare Ameena ce ke zaune gefen Saifuddeen wanda yake waya da Dr Acash prasat,
nan yake gaya mishi. "Lokacin dawowarka fa ya kusa".
Kanshi ya gyaɗa dan video call sukeyi cikin nitsuwa yace.
"Eh inata shirin zuwa ai".
Da sauri Dr Acash prasat yace.
"No karka taho India, ƙarshen watan nan zamuyi taron ƙarawa juna sani na duniya baki ɗaya, zamuyi taron ne kuma a Istanbul na kasar Turkey.
So kayi ƙoƙari mu haɗu a can, zan haɗaka da wani babban Dr da zai dubaka wanda duk ya fimu sanin matakan warakar ciwon insha Allah zaka samu dace".
Cikin gamsuwa da wani sahirtaccen jin daɗi Saifuddeen yace.
"To ba matsala".
Daga nan suka katsa wayar,
cikin kula Ameena tace.
"Kai ƙasa mai daɗi kena Instabul weather su akwai masifar daɗi."
Murmushi yayi tare da cewa.
"Sanyi su ne keda yawa, tsarin ƙasar is Gud, a dai irinmu masu larurar spinal cord injury jikinmu irin garin yakeso".
miƙewa tayi tare da cewa.
"Eh sosai ma kuwa".
A hankali yace.
"Ina zakije kuma kika tashi."
Hannu tasa ta tallaɓe ƙirjinta tare da cewa.
"Zan ɗauko Adeel ne naji mamanshi nata tsastsafo alamun ya tashi a bacci kenan".
Dariya yayi tare da cewa.
"Tsakanin uwa da ɗanta sai Allah".
Murmushi tayi kana ta fita.
Shi kuwa text message ya turawa Zaleeha.
"Salam, Baby maman baby kinyi bacci ne?".
da sauri ta maida mishi amsa.
"A a banyi ba, ina cin abin daɗin ne Ummi na ta dafa min."
murmushi yayi tare da rubuta mata.
"Abin daɗin kam ai yana wurina".
Murmushi tayi.
da sauri ta duba sakon daya kuma tura mata.
"Kinada E Passport ne"?".
a hankali ta rubuta mishi "Eh to gsky nawa ya daɗe bazaiyi aikiba yanzu".
"To ki shirya gobe da safe zamuje imagireshon Office, aiyi miki E Passport ɗin".
ido ta lumshe cikin tsananin farin ciki dan dai tasan ƙasar za'a bari da ita kenan tunda taji ana neman E Passport a zahiri kuma sai cewa tayi to.
Washe gari kuwa da safe sukaje akayi mata E Passport ɗin ta,
daga nan airport suka wuce,
ya fara nema musu damar barin ƙasar,
sai azahar suka dawo gida.
Alhamdulillah yanzu tana cin abinci ba laulayi, kamar yadda Ameena ta raini cikinta a sauƙaƙe,
to haka itama ko dan jinin mutun ɗaya ke gudana a jikinsu.
Rashida da Ishaq kuwa sunata dandatsa Amarci baba kama hannun yaro.
Yanzu cikin Zaleeha ya shiga wata huɗu, kuma ya ɗan fara baiyana duk da ƙugunta da mazaunanta ne suka fi buɗuwa sukayi tib-tib gwanin sha'awa sai ƙirjinta da yayi tamtsan-tamtsan
Yau tunda safe Ziyada keta shirin zuwa gidan Adda Zaleehanta,
sai dai Ya Ameenu ya mata tsiya yana ganinta shirya ta shirya Ayman murmushi ya ɗanyi tare da cewa.
"Ayman zo in ai keka wurin baba maigadi, kace ya tsinko maka nunnen maggoro ka kawo min".
Da sauri yaro yace.
"To Daddy innce adda ni ko a bani mai yawa dana Aunty Ziyada ko?".
Kai ya gyaɗa mishi tare da cewa,
"Eh maza yi sauri ɗan al'barka".
Ai kuwa a guje ya fita,
yana ganin fitan yaron ya jawo hannunta sukayi cikin ɗaki a hankali ya rufe ƙofar da sauri tace.
"Ya Ameenu ka rufe ƙofar kuma?".
Kanshi ya gyaɗa mata tare da cewa.
"Kizo mu ɗanyi wata mgna kafin ya dawo, nasan zasu dade a cikin labbun kafin su samu nunnenen mangoro".
Ba musu ta bishi suka hau gadon cikin raɗa yace.
"Kullum in Maryam zataje anguwa, in tayi kolliyar sai mun ɓata kolliyar forkon muyi wonka tare kafin tayi na biyu".
Cikin sanyi ta tace.
"To in da zaka kaini?".
Zip ɗin rigarta ya fara zugewa tare da cewa.
"In kin min duk abinda nayi mikiba".
Da haka ya shagalar da ita ya biya musu buƙatarsu sannan, suka sake wonka suka sake sabon shiri sannan ya kaita gidan Zaleeha,
yana sauƙeta ya juya ya fita
Ita kuwa a hankali ta nufi sashin Ummi tana tafe cikin nitsuwa.
A hankali ta murɗa ƙofar falon tare da yin sallama.
Da sauri Raliya tace.
"A a Ziyada maraba da zuwa."
Zaleeha dake kitchin ne ta fito da sauri jin an kira sunan ƴar uwarta.
Da sauri ta nufesu tare da cewa.
"Oyoyo my Ayman miss you so much".
ɗagoshi tayi tsam ta riƙeshi.
Kana ta kalli Ziyada dake ɗan murmushi cikin jin daɗi tace.
"Allah sarki Ziyada sai yau kika tunani?".
Murmushi Ziyada tayi kana ta juyo ta kalli Ummi da yanzu ta fito ɗakinta cikin kula tace.
"A a lale marhabin Ziyada sannu da zuwa".
A hankali tace.
"Yauwa Ummi sannu, ina kwana?".
"Lafiya lau ya mai gidanki?".
Ummi ta faɗi cikin kulawa ita kuwa Ziyada a sanyaye tace.
"Alhamdulillah Ummi yace in gaidaki ma, yace ince miki sai yazo ɗaukarmu zai shigo ku gaisa, yanzu yana sauri ne".
Cikin kula Ummi tace.
"Ayyah to mgd sosai".
Raliya ce ta kalli Ziyada tare da cewa.
"Ina kwana ya gida?".
Fuska a sake tace.
"Lfy lau Alhamdulillah, ya ayyuka?".
Alhamdulillah tace.
cikin girmamawa Ziyada ta kalli Zaleeha dake ta shafa kan Ayman tuni ida nunta sun cicciko da hawaye,
kanta ta kawar dan ganin hawayen Zaleeha zaisa nata hawayen fitowa a hankali tace.
"Inna kwana Adda Zaleeha".
Murya a sanyaya Zaleeha ta kalleta tare da cewa.
"Lfy Ziyada ya gida, ina ya Ameenu?".
"Alhamdulillah gida lfy Ya Ameenu yana lfy
Showing 225001 words to 228000 words out of 237945 words
Zama sukayi awajenta suna ƙara shagwaɓata da kuma tattalinta, Saifuddeen ma kasa barin ɗakin yayi, idanunsa kawai ya zuba mata, ita kuwa kasancewar alluran da Dr.Adnan yayi mata nada ƙarfi, hakan yasa wani irin bacci me nauyi ya ɗauketa. Ba'awani ɗau lokaci sosai ba Dr.Adnan ya dawo, fuskarsa cike take da wani irin annuri haɗi da zallan farinciki, ahankali ya buɗe ƙofar ɗakin ya shigo, ganin yanda yake sakin murmushi hannunsa riƙe da wata farar takarda yasa suka zuba masa ido,
Saifuddeen ne ya fara cewa.
"Lafiya kuwa Dr. me yake damunta?." Ƙarasowa cikin ɗakin yayi tare da miƙawa Saifuddeen ɗin hannu, alaman su gaisa, da ɗan mamaki Saifuddeen ya basa hannunsa, cikin bayyana farinciki Dr Adnan yace.
"Congrats Bro, Zaleeha na ɗauke da cikinka almost 2 to 3 month." Tamkar shigar shock haka duka sukaji maganan acikin kunnensu, Jikin Saifuddeen ne ya soma ɓari, cikin matsanancin mamaki, jin abun yayi kaman al'amara, duk da yasan cewa shiɗin baida matsalan rashin haihuwa, amma hakanan yakejin batun cikin Zaleehan kaman amafarki, Allah mabuwayi me yin yadda yaso a lokacin da yaso, yau gashi Zaleeha macen da zuciyarsa ke tsananin so da muradi, tana ɗauke da cikinsa, zamewa yayi daga kan wheelchair ɗinsa yayiwa Allah sujjada, dan nuna godiya da kuma tsantsar farincikinsa. Ummi da Raleeya kuwa ba abun da suke cewa sai.
"Alhamdulillah Masha Allah."
Cike da matsanancin farinciki, Ummi ta dubi Zaleeha, wanda ita bata ma san meyake gudana ba, dan baccinta ya ɗanyi nisa, Murmushi me ɗauke da farinciki tayi, cikin jin daɗi tace.
"Allah sarki Zaleeha yarinyar kirki, Allah Ya miki albarka, ya kuma sauƙeki lafiya".
Sai alokacin Saifuddeen ya ɗago daga sujjadan da yayi, kan wheelchair ɗinsa ya hau, sannan ya ƙaraso jikin gadon, wani irin farinciki ne bayyane akan fuskarsa, rungume Ummin sa yayi ƙam, tamkar wani ƙaramin yaro, cikin kasa ɓoye farincikinsa yace. "Alhamdulillah, Ummi na kinga Allah me iko ko, yabani kyauta me mahimmanci alokacin da ba zata ba, Ummi ki taɓa zuciyata kiji, har wani tsalle take saboda tsabar farinciki." murmushin jin daɗi Ummi tayi, cikin kulawa tace.
"Nasan kana cikin farinciki Babana, kuma muɗinma hakane muna cikin farin cikin."
Ɗan janye jikinsa daga na Ummi'n yayi, inda ya ƙurawa Zaleeha mayun idanunsa, cute face ɗinta yake kallo, wanda tayi fayau da ita, lokaci ɗaya har taɗan rame. Wani sabon zazzafar soyayyarta da ƙaunarta ne ke ratsa duk jikinsa, haka yakeji kaman ya jawota ya rungumeta.
Fahimtar hakane yasa. Ummi miƙewa,
ta fita cikin jin daɗi, hakama Raliya ta bita a baya,
suka tafi cikin tsananin jin daɗi.
A ɗakin Saifuddeen ɗin kuwa cikin kula ya Adnan ya ɗaura mata wani ɗan leden ruwa ƙarami,
dasa mata alluran cin abinci,
daurewa iya daurewa Zaleeha tayi amman duk da haka saisa ta fidda hawaye da anasa mata allurar ruwan a hannunta,
Hamma Saif kuwa cikin kula da lallama yake in boddy language yake cewa.
"So sorry Sannu ko, da zafi ko? Ya Adnan ayimata a hankali".
Dariya Ya Adnan yayi kana ya tattara kayan aikinshi yace.
"Raki da raki sun haɗu, a kula da cin abin cinta, domin bawai cikinne ya sata amai da jirinba, rashin cin abinci ne yasa yunwa yayi ta murɗanta, yunwarce kuma tasa mata jiri da kasala da duhun da take gani, so dole a kula da ita da cin abinci."
cikin gamsuwa Hamma Saif in boddy language ɗinsa yace.
"In sha Allah zan kula ya Adnan, na lura kam tunda na dawo bata son cin abinci".
ƙarishe haɗa kayanshi yayi kana ya sallamesu ya tafi.
Yana fita Hamma Saif ya hau gadon da kyau, hannunshi yasa yana shafa gashin kanta,
ita kuwa Zaleeha tunda taji Ya Adnan ya ambaci kalmar ciki sai tayi shiru tana bin Hamma Saif ɗinta da ido,
cikin tsananin jin daɗi yayi mata rubutu a wayarshi ya miƙa mata,
"Maman Baby, maman yara Ammin Adeel, my happiness my life my Everything. Ngd Ngd Ngd matuƙa,
Alhamdulillah Zaleeha Allah ya azurtamu da samar da abu ɗaya, jinina da jininki sun kasance a sashi ɗaya, burina da fatana sun cika kina da ciki har na tsawon wata biyu da sati uku".
Sai kuma ya sunkuyo yayi kissing goshinta,
ita kuwa Zaleeha lumshe ido tayi da sauri bayan ta karanta abinda ya rubuta mata,
hannunta tasa bisa lafeffen cikinta, wani irin daɗi farin ciki salama ne suka cika mata zuciya a baiyane tace.
"Alhamdulillah. Allah na gode maka da kyautar da kayi min, ya Allah ka al'barkacin abinda ke cikina,
ka bani shi mai kama da mahaifinsa".
Sai kuma ta ɗan buɗe ido ta, Hamma Saif ɗin nata, rubutun da yayine ta kuma karantawa.
"My dear meyasa!? Meyasa!!? Meyaaa!!!? Baki sanarmin kinada cikiba, meyasa kika ɓoye min abin farin cikinmu?".
A hankali ta kalleshi cikin sanyi tace.
"Hamma Saif nima bansan ina da cikiba".
Da sauri ya rubuta mata.
"Kamar yaya baki sani, tunda bakiga al'darkiba har wata biyu har na uku, ai yaci kisan kinada ciki".
A hankali tace.
"Hamma Saif ni ba ko wanne wata nake al'adaba, ina tsallake wata, wani lokacin har wata biyu nake tsallakewa sai ana uku sai ingani, shiyasa yanzunma da ban ganiba ban damuba dama duk zatona wata ƙil ƙarshen watannan zanyi dan ban taɓa tsallake wata ukuba a tunanina nanda kwana biyar zan gani".
Da sauri yasa hannu ya zare alluran ruwan dan ganin ruwan ya ƙare,
ɗagota yayi ya ruggumeta a jikinshi tsam, yana kissing nata tako ina.
A cikin gida kuwa,
Dr Adnan na fita Ameena na shigowa.
A can falon Ummi kuwa cikin farin ciki Ummi tace.
"Ni dama na daɗe da zargin Zaleeha nada shigar ciki, dan har kamar zan gayawa Saifuddeen sai kuma nace bari dai in barsu inga zasu gane da kansune ko sai an ganar dasu, kuma da yake sabbin shigane duk basu ganeba, kai yarinta da daɗi ƙuruciya dangin hauka.
Hayatuddeen ne da Ahmad dake ta farin cikin labarin suka haɗa baki wurin cewa.
"Au Ummi itama Zaleeha bata san tana da cikinba".
Raliya ce tace.
"Ato da alama kam bata saniba, dan in ta sani ai Hamma Saif zai sani".
Dariya sukayi baki ɗayansu.
Dai-dai lokacin Ameena ta shigo.
bayan sun gaisa da sune ta kalli Hayatuddeen daketa cilla Adeel sama suna dariya tace.
"Autan Ummi yau farin ciki da sassafe babu baƙin halin tashi daga bacci mai ka samu haka?".
Cikin dariya yace.
"Yo Aunty Ameena ai dolena in girma tunda naga kun dage tuƙuru zaku cika mana gida da yara, Adeel zaiyi ƙani ai dole in daina yarinta kada ayi uban banza".
Cikin mmki da rashin fahimta ta kalli su Ummi dake dariyar mgnar Auta, a hankali tace.
" Ummi me muka samune".
Cikin kula Ummi tace.
"Ammin Adeel ne, ta kwana ba lfy, to shine da Yayanku yazo ya gwada yake cewa cikine gareta".
Wani irin sassanyan murmushi Ameena tayi cikin jin daɗi da kekyawan zuciya tace.
"A a Alhamdulillah. Adeel ya girma, ya zama babban yaya, Allah ya sauketa lfy".
Amin Amin suka amsa baki ɗayansu.
Sosai sukayi farin ciki,
Nan Ameena da Raliya suka shiga kitchin.
Ummi kuwa ɗakinta ta koma,
a waya ta sanarwa Raihana dan tasan Adda Rahma kam mijinta zai gaya mata.
ta kuma sanarwa Goggo Dada da Aunty Mina ma sosai yan uwa da abokan arziki sukayi ta murnar cikin.
A can sashin Saifuddeen kuwa,
shi da kanshi ya taimaka mata, a tare sukayi wonka,
kana suka shirya,
rigar daya cire mata ta maida,
daga nan ta nufi ɗakinta dan canza sakekkiyar riga.
Shi kuwa Saifuddeen tana fita ya fara kiran abokanshi yana sanar musu,
sosai sukayi ta farin ciki sunayiwa Zaleeha tsiya wai ai dolema ta gudu ta kuma dawo da kafarta, wai Adeel ne ya korata, cikin kuma shi ya dawo da ita.
Ishaq ne ƙarshen kira dan yasan angone kar ya takurashi da sanyin safiya.
Ishaq kuwa yana jin wayarshi na rigging amman bai samu damar ɗagawa ba,
sabida yana lallaɓa amrya Rashida da yayi mata Dalla Dalla, sabida sam ya kasa ɗaga mata kafa, kun san riƙaƙƙun tuzurai ba sauƙi.
Yana tafe yana kuma gwada kiran Ishaq, yana shiga falonshi Ishaq na amsa kiran cikin tsokana yace.
"Ango kasha mai".
Dariya Ishaq yayi tare da cewa.
"Caɓa-caɓa ma kuwa mai kam harda lagwada, ai da nasan haka abin yake da ɗan karen daɗi da tuntini nayi aure".
Dariya sukayi baki ɗayansu,
Rashida dake manne jikin Ishaq ɗinne ta ɗan sune kanta a jikinshi.
shi kuwa Saifuddeen cikin happy yace.
"Al'bishirinka".
Da sauri Ishaq yace goro".
dariyarsa mai sanyi yayi cikin jin daɗi yace.
"Ka kusa samun ƙanin Adeel, jiya tunda muka dawo Baby keta amai ashe, cikine ni bamu saniba sai ɗazu ya Adnan ke sanar min."
Cikin tsananin jin daɗi Ishaq yace.
"Alhamdulillah, kai nayi farin ciki, kai mutumina ba sauƙi kai ko yaushe bugu ɗaya kake jefa ƙollo a raga".
Dariyar keta Saifuddeen yayi tare da cewa.
"Sune zalamammu daga na basu sai su ƙarɓa, kuma dama Zaleeha kam addu'ar da nayi tayi kenan, har a kaba na roƙi Allah ya azirtamin samun haihuwa da ita akai-akai kafinma ta ankara, gidana ya zame mata farin cikin duniyar ta, ta haifo min yara dozin-dozin".
Dariya sosai Ishaq yayi kana yace.
"Mugu, to Allah ya sanya al'khairi ya sauƙeta lfy".
Amin Amin yace kana sukayi sallama".
Daga nan ya shiga falon Zaleeha a falon suka haɗu cikin kula ya miƙo mata hannu, kana suka nufi falon Ummi.
Suna shiga, duk suka gaggaisa, hannu Zaleeha tasa ta karɓi Adeel dake hannun Hayatuddeen,
cikin kula sukayi mata sannu da jiki.
Ameena da Rayila ne da suka gama shirya breakfast a dinning table suka iso falon cikin sakin fuska Ameena ta kalli Saifuddeen fuska a sake tace.
"Congrats Abban Adeel, Allah ya sauƙeta lfy".
Amin Amin sukace baki ɗayansu,
Ita kuwa Zaleeha sunkuyar da kanta tayi ƙasa cikin tsananin jin kunya.
Shi kuwa Saifuddeen wani irin fitinenne kallo yakewa Ameena kallo mai cike da mutun taka, ji yake tamkar ya kamota ya ruggumeta, amman ba dama, ita kuwa ganin kallon da yake matane yasa ta meda kanta kan Zaleeha sabida taga Saifuddeen kallon farin cikin tayashi murnar da tayi yake mata ta hango wani baiyanenne farin ciki a fuskarshi cikin kula tace.
"Ammin Adeel ya jikin?".
A hankali tace.
"Na worke fa Ummu Adeel".
Dariya Raliya tayi tare da cewa.
"In kinci abinci ne zamu yarda kin worke".
Da sauri Saifuddeen ya jinjina mata kai alamar da kyau.
Ahmad kuwa dariyar ƙeta yayi tare da cewa.
"Allah ya fito mana da _Sodangi_ mu lfy, dan dai shine ya somu yasa aka gudu aka kuma dawo,
Jingudo haka sunan yake ko macece ko na mijine".
Dariya sukayi dukansu, Ameena kuwa shiru tayi.
Kalmar Jingudo da Ahmad ya kira ta amsa mata tarin tambayoyin dake ranta na cewa ina Zaleeha taje
Dan duk cikekken bafulatani in yaji an kira yaro da Jingudo ko Sodangi to yasan auren dole akawa mace, ta haifeshi a gidan wanda aka aura mata dolen, to shi ake cewa Jingudo."
A ranta ta tuno kalmar Adda Rahma inda take cewa mata.
"Kan Abu ɗaya ya taɓa nuna ƙulafashinsa a duniya a kanta ne kaɗai,
Sai ta kuma nazarci kalmar Ahmad na cewa Allah ya fito mana da Sodanginmu lfy don dai shine ya somu an gujemu an dawo".
Kai ta rausayar jin Ummi na cewa suje suci abinci.
kan dinnin table ɗin suka nufa, tana mai magar zuciya.
"Uhumm Ahmad kenan da kenan ka sani yanzu son Abban Adeel da nake hangowa cikin idonta ya wuce zaton mai zato, Allah sarki wato auren dole akayi mata, da alama kuma guduwa tayi lokacin da Adda Maryam ta rasune ta dawo ikon Allah to meyasa Zaleeha zataƙi Abba Adeel duk da tarin kyanshi da dukuyarshi basu ruɗeta ba."
Jin Saifuddeen ya murza hannunta alamun taci abinci ne yasa tasa hannu ta fara ci.
Zaleeha kuwa sanadin alluran da akayi mata to ta samu taci abinci sosai,
shiyasa duk jiri da murɗa da duhun suka tafi sai ɗan kasalar da ba'a rasaba.
Ranar dai Saifuddeen wuni yayi yana jinya,
shida kanshi kuwa ya kira Ya Ameenu da ya Ahmad ya sanar musu batun cikin Zaleeha,
sosai Ya Ahmad yai tawa Zaleeha wasa wai ashe yanzu kam girma yazo zata bar guje-guje.
A can gidan ya Ameenu kuwa suna gama yin mgnar ya kalli Ziyada dake zaune gefenshi hannunta ya rike a hankali yace.
"Kinji Adda Zaleehan takima bata da lfy, tanata aman laulayi ciki gashi kema har yanzu tafiyarki bata gama gyaruwa ba,
kiyi haƙuri sai kin ƙara samun sauƙi sai in kaiki ku wuni kinjiko Mar'tus saliha na tuba".
Kai ta jinjina cikin sanyinta irin na adda Maryam tace.
"To Ya Ameenu".
Jawota yayi ya ruggumeta domin biyeyyarta sak Maryam yake gani sam basu da gardama.
Bayan sati ɗaya lokacin cikin Zaleeha ya cika watanni uku cib-cib kuma Alhamdulillah ba laulayi sosai yanzu sai yawan cin abinci.
Da dare Ameena ce ke zaune gefen Saifuddeen wanda yake waya da Dr Acash prasat,
nan yake gaya mishi. "Lokacin dawowarka fa ya kusa".
Kanshi ya gyaɗa dan video call sukeyi cikin nitsuwa yace.
"Eh inata shirin zuwa ai".
Da sauri Dr Acash prasat yace.
"No karka taho India, ƙarshen watan nan zamuyi taron ƙarawa juna sani na duniya baki ɗaya, zamuyi taron ne kuma a Istanbul na kasar Turkey.
So kayi ƙoƙari mu haɗu a can, zan haɗaka da wani babban Dr da zai dubaka wanda duk ya fimu sanin matakan warakar ciwon insha Allah zaka samu dace".
Cikin gamsuwa da wani sahirtaccen jin daɗi Saifuddeen yace.
"To ba matsala".
Daga nan suka katsa wayar,
cikin kula Ameena tace.
"Kai ƙasa mai daɗi kena Instabul weather su akwai masifar daɗi."
Murmushi yayi tare da cewa.
"Sanyi su ne keda yawa, tsarin ƙasar is Gud, a dai irinmu masu larurar spinal cord injury jikinmu irin garin yakeso".
miƙewa tayi tare da cewa.
"Eh sosai ma kuwa".
A hankali yace.
"Ina zakije kuma kika tashi."
Hannu tasa ta tallaɓe ƙirjinta tare da cewa.
"Zan ɗauko Adeel ne naji mamanshi nata tsastsafo alamun ya tashi a bacci kenan".
Dariya yayi tare da cewa.
"Tsakanin uwa da ɗanta sai Allah".
Murmushi tayi kana ta fita.
Shi kuwa text message ya turawa Zaleeha.
"Salam, Baby maman baby kinyi bacci ne?".
da sauri ta maida mishi amsa.
"A a banyi ba, ina cin abin daɗin ne Ummi na ta dafa min."
murmushi yayi tare da rubuta mata.
"Abin daɗin kam ai yana wurina".
Murmushi tayi.
da sauri ta duba sakon daya kuma tura mata.
"Kinada E Passport ne"?".
a hankali ta rubuta mishi "Eh to gsky nawa ya daɗe bazaiyi aikiba yanzu".
"To ki shirya gobe da safe zamuje imagireshon Office, aiyi miki E Passport ɗin".
ido ta lumshe cikin tsananin farin ciki dan dai tasan ƙasar za'a bari da ita kenan tunda taji ana neman E Passport a zahiri kuma sai cewa tayi to.
Washe gari kuwa da safe sukaje akayi mata E Passport ɗin ta,
daga nan airport suka wuce,
ya fara nema musu damar barin ƙasar,
sai azahar suka dawo gida.
Alhamdulillah yanzu tana cin abinci ba laulayi, kamar yadda Ameena ta raini cikinta a sauƙaƙe,
to haka itama ko dan jinin mutun ɗaya ke gudana a jikinsu.
Rashida da Ishaq kuwa sunata dandatsa Amarci baba kama hannun yaro.
Yanzu cikin Zaleeha ya shiga wata huɗu, kuma ya ɗan fara baiyana duk da ƙugunta da mazaunanta ne suka fi buɗuwa sukayi tib-tib gwanin sha'awa sai ƙirjinta da yayi tamtsan-tamtsan
Yau tunda safe Ziyada keta shirin zuwa gidan Adda Zaleehanta,
sai dai Ya Ameenu ya mata tsiya yana ganinta shirya ta shirya Ayman murmushi ya ɗanyi tare da cewa.
"Ayman zo in ai keka wurin baba maigadi, kace ya tsinko maka nunnen maggoro ka kawo min".
Da sauri yaro yace.
"To Daddy innce adda ni ko a bani mai yawa dana Aunty Ziyada ko?".
Kai ya gyaɗa mishi tare da cewa,
"Eh maza yi sauri ɗan al'barka".
Ai kuwa a guje ya fita,
yana ganin fitan yaron ya jawo hannunta sukayi cikin ɗaki a hankali ya rufe ƙofar da sauri tace.
"Ya Ameenu ka rufe ƙofar kuma?".
Kanshi ya gyaɗa mata tare da cewa.
"Kizo mu ɗanyi wata mgna kafin ya dawo, nasan zasu dade a cikin labbun kafin su samu nunnenen mangoro".
Ba musu ta bishi suka hau gadon cikin raɗa yace.
"Kullum in Maryam zataje anguwa, in tayi kolliyar sai mun ɓata kolliyar forkon muyi wonka tare kafin tayi na biyu".
Cikin sanyi ta tace.
"To in da zaka kaini?".
Zip ɗin rigarta ya fara zugewa tare da cewa.
"In kin min duk abinda nayi mikiba".
Da haka ya shagalar da ita ya biya musu buƙatarsu sannan, suka sake wonka suka sake sabon shiri sannan ya kaita gidan Zaleeha,
yana sauƙeta ya juya ya fita
Ita kuwa a hankali ta nufi sashin Ummi tana tafe cikin nitsuwa.
A hankali ta murɗa ƙofar falon tare da yin sallama.
Da sauri Raliya tace.
"A a Ziyada maraba da zuwa."
Zaleeha dake kitchin ne ta fito da sauri jin an kira sunan ƴar uwarta.
Da sauri ta nufesu tare da cewa.
"Oyoyo my Ayman miss you so much".
ɗagoshi tayi tsam ta riƙeshi.
Kana ta kalli Ziyada dake ɗan murmushi cikin jin daɗi tace.
"Allah sarki Ziyada sai yau kika tunani?".
Murmushi Ziyada tayi kana ta juyo ta kalli Ummi da yanzu ta fito ɗakinta cikin kula tace.
"A a lale marhabin Ziyada sannu da zuwa".
A hankali tace.
"Yauwa Ummi sannu, ina kwana?".
"Lafiya lau ya mai gidanki?".
Ummi ta faɗi cikin kulawa ita kuwa Ziyada a sanyaye tace.
"Alhamdulillah Ummi yace in gaidaki ma, yace ince miki sai yazo ɗaukarmu zai shigo ku gaisa, yanzu yana sauri ne".
Cikin kula Ummi tace.
"Ayyah to mgd sosai".
Raliya ce ta kalli Ziyada tare da cewa.
"Ina kwana ya gida?".
Fuska a sake tace.
"Lfy lau Alhamdulillah, ya ayyuka?".
Alhamdulillah tace.
cikin girmamawa Ziyada ta kalli Zaleeha dake ta shafa kan Ayman tuni ida nunta sun cicciko da hawaye,
kanta ta kawar dan ganin hawayen Zaleeha zaisa nata hawayen fitowa a hankali tace.
"Inna kwana Adda Zaleeha".
Murya a sanyaya Zaleeha ta kalleta tare da cewa.
"Lfy Ziyada ya gida, ina ya Ameenu?".
"Alhamdulillah gida lfy Ya Ameenu yana lfy
Book Chapters
Chapter 1Chapter 2Chapter 3Chapter 4Chapter 5Chapter 6Chapter 7Chapter 8Chapter 9Chapter 10Chapter 11Chapter 12Chapter 13Chapter 14Chapter 15Chapter 16Chapter 17Chapter 18Chapter 19Chapter 20Chapter 21Chapter 22Chapter 23Chapter 24Chapter 25Chapter 26Chapter 27Chapter 28Chapter 29Chapter 30Chapter 31Chapter 32Chapter 33Chapter 34Chapter 35Chapter 36Chapter 37Chapter 38Chapter 39Chapter 40Chapter 41Chapter 42Chapter 43Chapter 44Chapter 45Chapter 46Chapter 47Chapter 48Chapter 49Chapter 50Chapter 51Chapter 52Chapter 53Chapter 54Chapter 55Chapter 56Chapter 57Chapter 58Chapter 59Chapter 60Chapter 61Chapter 62Chapter 63Chapter 64Chapter 65Chapter 66Chapter 67Chapter 68Chapter 69Chapter 70Chapter 71Chapter 72Chapter 73Chapter 74Chapter 75Chapter 76 Chapter 77Chapter 78Chapter 79Chapter 80