iya taka ƙafafunta, dan sun kumbura sosai, saikace me haihuwa yau ko gobe, wannan daliline yasa ta ɗauki hutu awajen aikinsu, Ummi ne ke bata kulawa sosai.
Ɓangaren Adda Maryam ma kuwa yanzu cikinta nada wata shida itama, saidai girman cikin nata baikai na Ameena ba.
Yau tunsafe da ta tashi takejin wani irin matsanancin ciwon mara, haka takejin bayanta ya riƙe ƙam, gashi ƙafarta ta sake kumburi, da ƙyar dai take iya takawa, haka ta lallaɓa ta nufi ɓangaren Ummi tana zuwa kuwa ta iskesu zaune afalo, zama tayi itama tana cije laɓɓanta, ganin haka yasa Ummi da kanta ta haɗa mata emptyn shayi me zafi ta bata tace tasha.
Tana sha kuwa tariƙe bayanta da takejinsa kaman zai ɓalle, Ummi da Raliya ne sukayo kanta, abu kaman wasa fa saiga naƙuda ya tashiwa Ameena gadan gadan, nan Ummi ta ka mata, inda ita da Raliya suka sanyata amota,
hankalinsa Saifuddeen a tashe ya shiga motar yana tsoron abinda zai sami ɗanshi tunda yasan cikin bai kai haihuwa ba.
Ahmad ne yayi driving ɗinsu zuwa Medical center, suna zuwa kuwa abokan aikinta suka karɓeta hannu bibbiyu nan aka wuce da ita labour room.
Jigum-jigum haka su Ummi sukayi suna mejiran sakamako, hankalin Ummi atashe yake sosai, musamman da likitotin suka tabbatar musu da cewa haihuwace Ameenan zatayi, ma'ana ɗan abakwaini zaizo.
Da shigar da Ameena labour room ko 40 minute ba a rufa ba, wata nurse ta fito inda take sanar musu da cewa. "Ameenan ta haihu ta haifi ɗa namiji, kuma daga ita har yaron dukansu suna cikin ƙoshin lafiya."
Wannan magana ita tasanya dariya ya wanzu akan fuskokin su Ummi, Saifuddeen kuwa hamdala yayi tare da ɗaga hannunsa sama ya godewa Allah.
Nan Ummi tashiga ƙiran ƴan uwa da abokan arziki tana sanar musu, ana fito da Ameena zuwa ɗakin hutu kuwa, nurse ɗin tace zasu iya shiga.
Suna shiga ɗakin wata nurse ta miƙowa Ummi yaron, hawayene suka cika idanun Ummi abayyane tace.
"Alhamdulillah, masha Allah."
Saboda tsananin kaman Saifuddeen ɗinta da ta hango akan fuskar yaron, gashi yaron kamar ba bakwaini ba, dan yana da girmansa, tsabar fari kuwa har saida yayi wani jaja-jaja.
Miƙawa Saifuddeen tayi ya amshi yaron yana mejin tarin ƙaunarsa acikin ransa, rumgume yaron yayi aƙirjinsa yana murmushi, bayan yayi wa yaron huɗuba da ƙiran sallah acikin kunnensa.
Nan dai Su Adda Rahama da Raliya suka amshi yaron suma suna yabawa da irin kyautar da Allah yayi musu.
Kasancewar Ameena bata wani jigata ba, hakan yasa bayan ankimtsata aka basu sallama da ƙara bata shawarwarin yadda zata kula da ɗanta tunda ɗan bakwainine sun sallamesune sabida sanin ita ɗin sashin Doctors take, nan dai suka tattaro suka dawo gida.
Kusan kullum ƴan barka sai sunzo, Mamy da Adda Maryam ma sunzo barka, Inna matar Baba Bello ma tazo yi musu barka. Ana sauran kwana uku suna Raihana ta diro garin na Gombe, da Aliyun ta takwaran bappa Alinsu (Affan) ɗinta kenan sosai itama tayi murna da ganin ɗan Hamma'nta. Ranan washe garin suna ne dangin Ameena suka zo, Aunty's ɗinta dama Sister's ɗinta duk sunzo daga Abuja wasu daga Jada.
Ranan suna kuwa yaro yaci sunan MUHAMMAD BASHEER. wato takwaran Baba Malam kenan, inda za'ana ƙiran yaron sa sunan. (Adeel) wannan karamci da Saifuddeen yayiwa Baba Malam yasashi matuƙar jin daɗi, bama iya shi ba, harta ga ƴaƴansa sunji matuƙar daɗi, haka Baba Malam da Mamy suka cika akwati guda da kayan yaro masu kyau'n gaske.
Nan dai akasha shagalin suna wanda yasamu hallaran mutane da yawa, dan dayawan danginsu na Dukku ma sunzo, ga kuma dangin Ameena. Adda Maryam ma tazo, duk da cewa cikinta na sata laulayi gashi dai yanzu har ya kai wata shida amman har yanzu yana sata laulayi. amma hakan baihanata zuwa ba.
Sosai Saifuddeen yayi ɓarin naira ranan sunan, dan anci ansha, sannan an rarraba kyautuka gaduk wanda yazo.
Aranan kuwa ya damƙawa Ameena makullin sabuwar motar daya saya mata, saboda tsabar daɗi Ameena har ƙwalla saida tayi.
Shikuwa Saifuddeen yayi hakanne saboda sauƙe haƙƙinta, dan bai kyautuwa ace yasawa Zaleeha mota da kuɗinsa, amma ita Ameenan bai saya mata ba, duk da cewa Zaleehan tariga zuwa kafun ita, sannan kuma ma motar Amina tafi ta Zaleeha kyau da kuma tsada.
Anyi taron suna an watse, inda Ummi dasu Adda Rahama suka nunawa Ameena gata sosai, dan kaya suka mata baɗan kaɗan ba, Hayatuddeen ma ba a barsa abaya ba, dan rigunan yaro har kala 6 ya saya masu kyaun gaske, Ameenan kuwa turamen vlisco ya saya mata guda biyu masu tsada, asusun da yakeyi musamman ya fasa dan yin shagalin sunan.
Hatta Zakariyya ma saida ya sayawa ɗan Hamma Saifuddeen ɗin riguna masu kyau.
Hakama Ya Ahmad da yaji labarin Baba malam akayiwa mai suna sosai ya goggojesu
Babu wani ɗaya daga cikin abokan Saifuddeen kuwa dabai kawo nasa kayan ba, sosai sukayi bajinta.
Abun saidai ace masha Allah.
Haka rayuwa tatafi har Ameena tayi wata biyu da haihuwa, wanda yanzu ta gama wanka, sannan tana bawa ɗanta kulawa sosai yanda ya dace, idan kaga yaron kuwa bazaka taɓa cewa bakwaini bane, saidai in anfaɗa maka, dan yana da girman jiki.
Sannan yarone me shiga rai sosai.
Kasancewar ta cika wata biyu da haihuwa hakan yasa ta shirya tsab inda su Ummi da Saifuddeen suka cikata da abubuwan al'khairi, nan ta tafi Abuja, kwananta uku acan ta dawo, tana dawowa kuwa ta koma bakin aikinta, don dama hutun 2 month kawai suka bata.
Acan Numan kuwa Abubuwa sunyiwa Zaleeha sauƙi sosai, inda ta kama addu'a sosai, ruwan addu'a kuwa kullum shi take sha, Alhamdulillah taji sauƙin abubuwa da yawa, dan yanzu begen gidane gaba ɗaya ya cika zuciyarta.
Yau tun da safe ta shirya tatafi gidan su Aisha nan ta samu Baffa agida dan bai fita gona ba bayan sun gaisa ya bata rubutun da ya mata tasha,
nanne yake tambayanta ko daga fara maganin nata zuwa yanzu ko taji sauyi ajikinta?
Sosai kuwa tagaya masa irin sauyin da taji,
Gyaran murya yayi tare da cewa.
"Tunda kika fara shan rubutun nan nece miki duk mafarkin da kikayi ki gaya min shin har yau bakiyi mafarkin komai ba?."
Da sauri ta kalleshi cikin al'ajabi tace.
"Baffa jiya nayi mafarkin daya bani mmki dan na taɓa yin makamancinsa".
Gyara zama yayi tare da fuskantarta da kyau yace.
"Mafarkin me kikayi?".
Gyara maya fita tayi tare cewa.
"Nayi mafarkin, da'a cikin mafarkin naga wani ƙaton maciji baƙiƙƙirin ya fito daga ƙarƙashin gadona na gidan Saifuddeen, wanda acikin mafarkin ne kuma naga Baba Malam yana cikin ɗakin ni kuma ina ta waje bakin ƙofar shiga ɗakin ta gefe, naji Baba Malam na cemin, in dawo gida in dawo ɗakinna in zauna, yanzu babu komai babu wani abu wanda zai cutar da ni a ɗakin.
Har yana ce min in matsa a baƙin ƙogar kada macicijin ya taɓa ni."
Cikin sauri da fargaba Baffa yace.
"Macijin yataɓaki?."
kai ta jujjuya tare da cewa.
"A a bai taɓani." ajiyan zuciya ya sauƙe tare da gyara zama.
Ita kuwa Zaleeha cikin sanyi tace.
"Na dai ga Macijin kuma na taɓa yin mafarkinshi, tun randa akaje akayi jeren kayana a gidan Saifuddeen nayi mafarkin wai ina kan gado sai macijin ya shigo ina ganinshi ƙato ya lume ƙarƙashi gadona.
To randa aka kaini gidanma na sake yin mafarkin."
Jinjina kai Baffa yayi bayan yagama jin kalaman nata cikin jin daɗi yace.
"Alhamdulillah. babu komai sai al'khairi kuma Insha Allah duk wani asirin dake jikinki yanzu ya karye, babushi a jikinki sannan yadda kikaga macijin nan ya shiga ƙasan gadonki haka sihiri yayi ta ratsaki, kuma yanzu yadda kikaga macin ya fita daga ƙasan gadonki to sihirin ya bar jikinki da ɗakinki, kuma zan baki maganin tsarin jiki tayanda insha Allah Allah zaikareki da dukkan wani sharri zakiyi amfani dashi sau uku."
Cikin wani irin begen gida da son komawa cikin ahlinta tace.
"Baffa ina son komawa yau in dai zan samu mota".
Cikin jin daɗi da gamsuwa da cewa ta samu waraka yace.
"Kiyi haƙuri sai gobe, tabbas kam tafiyar ta karato, dan haka kiyi haƙuri yanzu zan baki mgnin tsari kiyi wonka dashi sau uku yanzu in kin koma sai kuma da yamma, sai kuma gobe da asuba ki ƙarashi."
Don dole da kimar dottijon ta haƙura dan ji take tamkar ta zama tsunstsuwa tayi fiffige ta fire ta koma gida,ji yakeyi kamar ta rumtse idonta ta buɗe su ta ganta gaban Baba Malam ya mata duk hukuncin daya dace da ita ta nemi yafiyarshi da sanya al'barkanshi.
Ae kuwa bata bar gidan ba saida ya haɗa mata magungunan tsari, wanda duk addu'o'i ne, nan yake ce mata.
"Insha Allah takusa komawa gida."
Tajima agidan nasu Aisha kafun take komawa gida.
A ranar ne kuma Solomon da matarsa sukayi mata tambayar da ta bata mmki, suna tambayarta in mutun zai musulunta me da me zaiyi kuɗi kamar nawa zai kashe,
wannan abu ya sata jin karsashi ta zauna tayi musu bayanin komai na sauƙin musulunci, sai suke ce mata to suna son musulunta to amman sai sun gayawa sarkin majami'arsu. Tace su gaya mata da dole sai sun gaya mishi ,
sai sukace ta bari nanda sati ɗaya zasu gaya mata.
A safiyar ranar dai kuma A Gombe.
Saifuddeen ne zaune akan wheelchair ɗinsa, yana riƙe da Adeel ɗan wata uku ya shiga na uɗu wanda ya ƙara girma yakuma yi wayo yayi kuɓul-kuɓul, wasa yakeyiwa yaron yana me shafa lallausan gashin kansa, wanda yayi shige da nasa, sosai yakejin ƙauna da son yaron acikin ransa.
Ƙurawa yaron idanu yayi aransa.yana me cewa.
"Badan ƙaddara ta kawo Hajia Ameena rabo ba, da yanzu wannan yaron ajikinki zai fito Zaleeha, amman ba damuwa in sha Allah kema naki yana jikina in Allah ya yarda ni dake sai mun samar da abu ɗaya ina ji a jikina kin kusa dawowa gareni, kin gama naki zaki dawo ki tadda nawa. Wai toms in kin dawo me zakice? Ina kikaje? Meyasaki tafiya?".
Yayiwa kansa tambayar tare daɗan lumshe idanunsa, tabbas yayi kewar Zaleeha sosai musamman cikin kwanakin nan tana yawa faɗo mishi cikin rai, ya rasa dalili gashi yanzu sam ta daina hawa online kuma duk sabida yana mata mgna da number sa ta siirin nan dama tace mishi zata goge whatsapp gaba ɗaya kuma ta goge ɗin acewarta ita matar aurece.
Ameena ne tafito daga cikin ɗaki cikin shirinta na zuwa wajen aiki, ƙarasowa wajen su tayi cike da ƙaunarsu, ranƙwafowa tayi inda ta mannawa Saifuddeen din kiss akan laɓɓansa, sannan ta ɗaga yaron zuwa kafaɗanta, cikin kulawa ta ce da Saifuddeen ɗin.
"Saimun dawo" hannu ta ɗaga masa sannan ta fice, dan tayi late.
Shikuwa Saifuddeen laptop dinsa ya ɗauka, inda ya shiga cikin file ɗin da yake aje hotunan Zaleeha, view ɗin wani hoton Zaleehan yayi yana kallo, sosai tayi kyau acikin hoton dimple ɗinta ya zubawa ido, dan tana sanye ne da doguwar rigar da ta amshi jikinta, yajima yana kallon hoton kafun ya rufe laptop ɗin ya nufi ɗaki.
Ameena kuwa saida tabiya ta wajen Ummi tayi mata sallama kafun take wucewa wajen aikin.
Federal medical center.
Baba Malam ne da Ya Ameenu haɗe da Mamy, da kuma Ya Habu ke tsaye, sunyi jigum, matsanancin damuwane kwance biss fuskokinsu, sakamakon kawo Maryam haihuwa da sukayi, gashi kuma ance dole saidai ayi mata theatre.
Wasu nurses biyu ne suka turo wani ɗan dogon gado da Maryam ɗin ke kwance akai, ansanya mata kayan theatre, dai-dai sunzo wucewa ta wajen su Baba Malam ɗinne, Maryam ta sanya hannunta ta kamo na Baba Malam, tare da cewa.
"Baba Malam kazo mana kayi min addu'a kafin a shiga dani."
da sauri Baba Malam ya dubeta cikin tausayawa yace.
"To Maryam zan miki addu'a kinjiko ƴata mai sunan ƴar uwata insha Allah zaki haihu lafiya da yardan Allah."
ganin nos ɗin zasu shiga da itane yasa ta kallesu cikin sanyin murya tace.
"Dan Allah in mun shiga ku kirawo min Babana da mijina suzo akwa abinda zan ce musu kafin ayi aikin."
yanayin nitsuwarta ne yasa sukace.
"To". Suna shigar da ita ɗan falon da za'a ratsa a shiga ainhin ɗakin tiyatan.
Nan suka tsaida gadon kana ɗaya nos ɗin ta fito ta kira su Baba Malam da Ya Ameenu.
Suna shiga ta yunƙura ta tashi zaune cikin sanyi tasa hannunta da yayi sanyi ƙalau tamkar ƙanƙara ta riƙo hannun mahaifinta.
Kai ta girgiza take kuma saiga hawaye sun silalo daga cikin idanunta, cikin muryarta dake fita da sanyi tace.
"Baba Malam ka yafe mi ninaji ajikina cewa bazan tashi ba Baba, dan Allah kayafemin in akwai laifin da nayi maka."
Da sauri Baba malam ya riƙe hannunta tare da cewa.
"Ni kam bakiyi komai ba Maryam, koda ko kinyi min na yafe miki duniya da lahira, bare ni baki min komai ba face biyayya, ubangiji ya yassare miki rayuwar duniya data lahira."
Hannu tasa ta share hawayenta murya na rawa tace.
"Nagode Babana."
Da ƙarfi zuciyar Baba Malam ta buga jin yadda ta kirashi, kama hannunta yayi da kyau jin tana cewa.
"Sannan kuma ina neman wata al'farma a wurinka Babana".
Zuciya a tsinke yace.
"Wacce al'farmace Maryam gaya min".
Lumshe idanunta tayi wasu zafafan hawaye suka kwaranyo mota, cikin sanyin murya tace.
"Dan Allah ina son ka dawo da Mama dan Allah, ka kuma yafewa ƴar uwata Zaleeha, dan Allah Baba kayafe mana baki ɗayanmu Baba Malam ka yafewa Zaleeha dan kada rayuwa tayi mata muni bance kada kayi fushi ka nuna mata illar abinda tayiba, amman kada kuyi dogon fushi da ita, sannan in Mamana tazo kace mats na nemi yafiyarta, ta gafarta min".
Sai kuma ta fara kuka murya na rawa taci gaba da cewa.
"Baba malam Nasan duk inda Zaleeha take. Duk inda take a faɗin wannan duniyar in dai tana raye in taji rasuwata zata zo, dan Allah idan tazo kace mata na ajiye mata saƙo a cikin durowar gadona, kuma kada taje ita kaɗai in zata ɗauka taje ita da Mijinta Saifuddeen sannan kacewa. Ya Ahmad da Zakariyya kada suyi dogon fushi da Zaleeha su zame mata madadina."
taƙare maganar tana dhessheƙan kuka, kai Baba Malam ya jijjiga lokaci ɗaya hawaye suka cika idanunsa, hannunta ya kama ƙam cikin matsanancin ƙaunar ƴartasa yace.
"Insha Allah zaki tashi Maryam, za ayi miki aiki lafiya, kidaina faɗin irin waƴannan maganganun."
Murmushi tayi tare da kamo hannun Ya Ameenu wanda tuni hawaye sun wanke masa fuska, cikin matsanancin ƙaunar mijin nata tace.
"Inaji ajikina cewa zan barka Yayana, zantafi inda bazaka sake ganinka ba, kakulamin da Ayman ɗinmu kaji, sannan kayafemin duk wani abu danayi maka."
Kuka Ya Ameenu ya fashe dashi tare da durƙushewa awajen, don bayajin zai iya cewa komai.
Mamy ma kuka take, nan ita da Ya Habu suka kama hannun Maryam ɗin, murya asanyaye Mamy tace.
"Ki daina faɗin haka Maryam zaki tashi da yardan Allah."
Hannun Mamyn Maryam tasake riƙewa sosai, cikin muryan kuka tace.
"Ku yafemin Mamy, idan Zaleeha ta dawo kice mata nace tabi mijinta sauda ƙafa tayi masa biyayya, danni kam bazan samu daman faɗa mata hakan da bakina ba.
Ya Habu kaima kayafemin, sannan kada kuyi dogon fushi da Zaleeha."
Kukane ya ƙwace wa Mamy, da Ya Habu, Baba malam ma hawaye yake sosai.
Ganin haka yasa nurses ɗin suka tura keken sukayi ciki da Maryam ɗin, tana kallon Ya Ameenu shima yana kallonta haka aka shiga da ita ɗakin theatre'n, kuka sosai Ya Ameenu yasa kaman ƙaramin yaro, Baba Malam ne ya riƙesa yana rarrashinsa.
Ameena kuwa koda taje asibitin aje Adeel tayi awajen wata ƙawarta mesuna Umaima, nan ta nufi theatre room dan ansanar da ita cewa, babban Dr ɗinsu na nemanta acan ɗin.
Takusan kaiwa theatre room ɗinne tahango Baba Malam, Ya Ameenu, da kuma Ya Habu, sai Mamy suna tsaitsaye, cikin sauri taƙarasa garesu, ganin fuskokinsu ɗauke da matsanancin damuwa yasa jikinta yin sanyi asanyaye ta gaidasu, tare dayi musu tambayan halan ko wani suka kawo bashi da lafiya, dan taga idanunsu gaba ɗaya sunyi jajur.
Hankalim Mamy amatuƙar tashe yake faɗa mata cewa.
"Maryam ne suka kawota haihuwa, ankuma ce dole sai theatre za'ayi mata, yanzu haka ma anshiga da ita ɗakin theatre'n."
Hankalin Ameena ne ya tashi sosai, take cikin sauri ta nufi ɗakin theatre'n.
Littafina na ƙuɗine in kina buƙata turo katin mtn na ɗari uku ta wannan no ɗin 09097853257 ko kimin transfer ta asusuna 0005388578 jaiz bank Aisha Aliyu Garkuwa.
By
*GARKUWAN FULANI*
10/4/20, 7:04 PM - Mmn Khalid: *(heart touching)*
Sbpejy Su Baba Malam kuwa tsayuwa sukayi, gaba ɗaya jikinsu asanyaye y'ake, babu wanda yayi yunƙurin zama acikinsu, Mamy kuwa hawaye take ta sharewa, zuciyarta cike take da tausayin Maryam.
Can cikin theater room kuwa, alluran nan dake gusar da hankali, likitotin sukayiwa Adda Maryam, Doctors kusan guda huɗu ne suka duƙufa akanta, cikin ƙwarewa kuwa suka soma yi mata aiki.
Shiru ɗakin theater'n yayi bakajin motsin komai, sai na kayayyakin aikin da likitotin ke amfani dasu.
Sosai aikin nasu ya ɗauko nisa, gefe kuwa Ameena ne da wata nurse wanda sune ke taimakawa wajen miƙawa doctors ɗin kayan aiki.
Ahankali ƙwayar idanunta ke tsiyayar da wasu sassanyan hawaye, sosai kuma hawaye suka rinƙa kwaranyowa daga cikin idanunta, Ameena wanda gaba ɗaya hankalinta naga Maryam din ne, ganin idanun Maryam ɗin na zubda hawaye, yasa amatuƙar firgice ta matso kusa da ɗaya daga cikin doctors ɗin dake yi mata aiki'n, ɗan taɓasa tayi yana juyowa kuwa tayi masa nuni da fuskar Maryam, cikin yanayin tsoro haɗi da mamakin ikon Allah likitan yayiwa ƴan uwansa nuni da Maryam ɗin, wanda idanunta suke ta zubda hawaye, koda suma suka ga yanda Maryam ɗin take , sosai suka shiga shock, saboda sunsan sunyi mata alluran gusar da
Showing 81001 words to 84000 words out of 237945 words
Ɓangaren Adda Maryam ma kuwa yanzu cikinta nada wata shida itama, saidai girman cikin nata baikai na Ameena ba.
Yau tunsafe da ta tashi takejin wani irin matsanancin ciwon mara, haka takejin bayanta ya riƙe ƙam, gashi ƙafarta ta sake kumburi, da ƙyar dai take iya takawa, haka ta lallaɓa ta nufi ɓangaren Ummi tana zuwa kuwa ta iskesu zaune afalo, zama tayi itama tana cije laɓɓanta, ganin haka yasa Ummi da kanta ta haɗa mata emptyn shayi me zafi ta bata tace tasha.
Tana sha kuwa tariƙe bayanta da takejinsa kaman zai ɓalle, Ummi da Raliya ne sukayo kanta, abu kaman wasa fa saiga naƙuda ya tashiwa Ameena gadan gadan, nan Ummi ta ka mata, inda ita da Raliya suka sanyata amota,
hankalinsa Saifuddeen a tashe ya shiga motar yana tsoron abinda zai sami ɗanshi tunda yasan cikin bai kai haihuwa ba.
Ahmad ne yayi driving ɗinsu zuwa Medical center, suna zuwa kuwa abokan aikinta suka karɓeta hannu bibbiyu nan aka wuce da ita labour room.
Jigum-jigum haka su Ummi sukayi suna mejiran sakamako, hankalin Ummi atashe yake sosai, musamman da likitotin suka tabbatar musu da cewa haihuwace Ameenan zatayi, ma'ana ɗan abakwaini zaizo.
Da shigar da Ameena labour room ko 40 minute ba a rufa ba, wata nurse ta fito inda take sanar musu da cewa. "Ameenan ta haihu ta haifi ɗa namiji, kuma daga ita har yaron dukansu suna cikin ƙoshin lafiya."
Wannan magana ita tasanya dariya ya wanzu akan fuskokin su Ummi, Saifuddeen kuwa hamdala yayi tare da ɗaga hannunsa sama ya godewa Allah.
Nan Ummi tashiga ƙiran ƴan uwa da abokan arziki tana sanar musu, ana fito da Ameena zuwa ɗakin hutu kuwa, nurse ɗin tace zasu iya shiga.
Suna shiga ɗakin wata nurse ta miƙowa Ummi yaron, hawayene suka cika idanun Ummi abayyane tace.
"Alhamdulillah, masha Allah."
Saboda tsananin kaman Saifuddeen ɗinta da ta hango akan fuskar yaron, gashi yaron kamar ba bakwaini ba, dan yana da girmansa, tsabar fari kuwa har saida yayi wani jaja-jaja.
Miƙawa Saifuddeen tayi ya amshi yaron yana mejin tarin ƙaunarsa acikin ransa, rumgume yaron yayi aƙirjinsa yana murmushi, bayan yayi wa yaron huɗuba da ƙiran sallah acikin kunnensa.
Nan dai Su Adda Rahama da Raliya suka amshi yaron suma suna yabawa da irin kyautar da Allah yayi musu.
Kasancewar Ameena bata wani jigata ba, hakan yasa bayan ankimtsata aka basu sallama da ƙara bata shawarwarin yadda zata kula da ɗanta tunda ɗan bakwainine sun sallamesune sabida sanin ita ɗin sashin Doctors take, nan dai suka tattaro suka dawo gida.
Kusan kullum ƴan barka sai sunzo, Mamy da Adda Maryam ma sunzo barka, Inna matar Baba Bello ma tazo yi musu barka. Ana sauran kwana uku suna Raihana ta diro garin na Gombe, da Aliyun ta takwaran bappa Alinsu (Affan) ɗinta kenan sosai itama tayi murna da ganin ɗan Hamma'nta. Ranan washe garin suna ne dangin Ameena suka zo, Aunty's ɗinta dama Sister's ɗinta duk sunzo daga Abuja wasu daga Jada.
Ranan suna kuwa yaro yaci sunan MUHAMMAD BASHEER. wato takwaran Baba Malam kenan, inda za'ana ƙiran yaron sa sunan. (Adeel) wannan karamci da Saifuddeen yayiwa Baba Malam yasashi matuƙar jin daɗi, bama iya shi ba, harta ga ƴaƴansa sunji matuƙar daɗi, haka Baba Malam da Mamy suka cika akwati guda da kayan yaro masu kyau'n gaske.
Nan dai akasha shagalin suna wanda yasamu hallaran mutane da yawa, dan dayawan danginsu na Dukku ma sunzo, ga kuma dangin Ameena. Adda Maryam ma tazo, duk da cewa cikinta na sata laulayi gashi dai yanzu har ya kai wata shida amman har yanzu yana sata laulayi. amma hakan baihanata zuwa ba.
Sosai Saifuddeen yayi ɓarin naira ranan sunan, dan anci ansha, sannan an rarraba kyautuka gaduk wanda yazo.
Aranan kuwa ya damƙawa Ameena makullin sabuwar motar daya saya mata, saboda tsabar daɗi Ameena har ƙwalla saida tayi.
Shikuwa Saifuddeen yayi hakanne saboda sauƙe haƙƙinta, dan bai kyautuwa ace yasawa Zaleeha mota da kuɗinsa, amma ita Ameenan bai saya mata ba, duk da cewa Zaleehan tariga zuwa kafun ita, sannan kuma ma motar Amina tafi ta Zaleeha kyau da kuma tsada.
Anyi taron suna an watse, inda Ummi dasu Adda Rahama suka nunawa Ameena gata sosai, dan kaya suka mata baɗan kaɗan ba, Hayatuddeen ma ba a barsa abaya ba, dan rigunan yaro har kala 6 ya saya masu kyaun gaske, Ameenan kuwa turamen vlisco ya saya mata guda biyu masu tsada, asusun da yakeyi musamman ya fasa dan yin shagalin sunan.
Hatta Zakariyya ma saida ya sayawa ɗan Hamma Saifuddeen ɗin riguna masu kyau.
Hakama Ya Ahmad da yaji labarin Baba malam akayiwa mai suna sosai ya goggojesu
Babu wani ɗaya daga cikin abokan Saifuddeen kuwa dabai kawo nasa kayan ba, sosai sukayi bajinta.
Abun saidai ace masha Allah.
Haka rayuwa tatafi har Ameena tayi wata biyu da haihuwa, wanda yanzu ta gama wanka, sannan tana bawa ɗanta kulawa sosai yanda ya dace, idan kaga yaron kuwa bazaka taɓa cewa bakwaini bane, saidai in anfaɗa maka, dan yana da girman jiki.
Sannan yarone me shiga rai sosai.
Kasancewar ta cika wata biyu da haihuwa hakan yasa ta shirya tsab inda su Ummi da Saifuddeen suka cikata da abubuwan al'khairi, nan ta tafi Abuja, kwananta uku acan ta dawo, tana dawowa kuwa ta koma bakin aikinta, don dama hutun 2 month kawai suka bata.
Acan Numan kuwa Abubuwa sunyiwa Zaleeha sauƙi sosai, inda ta kama addu'a sosai, ruwan addu'a kuwa kullum shi take sha, Alhamdulillah taji sauƙin abubuwa da yawa, dan yanzu begen gidane gaba ɗaya ya cika zuciyarta.
Yau tun da safe ta shirya tatafi gidan su Aisha nan ta samu Baffa agida dan bai fita gona ba bayan sun gaisa ya bata rubutun da ya mata tasha,
nanne yake tambayanta ko daga fara maganin nata zuwa yanzu ko taji sauyi ajikinta?
Sosai kuwa tagaya masa irin sauyin da taji,
Gyaran murya yayi tare da cewa.
"Tunda kika fara shan rubutun nan nece miki duk mafarkin da kikayi ki gaya min shin har yau bakiyi mafarkin komai ba?."
Da sauri ta kalleshi cikin al'ajabi tace.
"Baffa jiya nayi mafarkin daya bani mmki dan na taɓa yin makamancinsa".
Gyara zama yayi tare da fuskantarta da kyau yace.
"Mafarkin me kikayi?".
Gyara maya fita tayi tare cewa.
"Nayi mafarkin, da'a cikin mafarkin naga wani ƙaton maciji baƙiƙƙirin ya fito daga ƙarƙashin gadona na gidan Saifuddeen, wanda acikin mafarkin ne kuma naga Baba Malam yana cikin ɗakin ni kuma ina ta waje bakin ƙofar shiga ɗakin ta gefe, naji Baba Malam na cemin, in dawo gida in dawo ɗakinna in zauna, yanzu babu komai babu wani abu wanda zai cutar da ni a ɗakin.
Har yana ce min in matsa a baƙin ƙogar kada macicijin ya taɓa ni."
Cikin sauri da fargaba Baffa yace.
"Macijin yataɓaki?."
kai ta jujjuya tare da cewa.
"A a bai taɓani." ajiyan zuciya ya sauƙe tare da gyara zama.
Ita kuwa Zaleeha cikin sanyi tace.
"Na dai ga Macijin kuma na taɓa yin mafarkinshi, tun randa akaje akayi jeren kayana a gidan Saifuddeen nayi mafarkin wai ina kan gado sai macijin ya shigo ina ganinshi ƙato ya lume ƙarƙashi gadona.
To randa aka kaini gidanma na sake yin mafarkin."
Jinjina kai Baffa yayi bayan yagama jin kalaman nata cikin jin daɗi yace.
"Alhamdulillah. babu komai sai al'khairi kuma Insha Allah duk wani asirin dake jikinki yanzu ya karye, babushi a jikinki sannan yadda kikaga macijin nan ya shiga ƙasan gadonki haka sihiri yayi ta ratsaki, kuma yanzu yadda kikaga macin ya fita daga ƙasan gadonki to sihirin ya bar jikinki da ɗakinki, kuma zan baki maganin tsarin jiki tayanda insha Allah Allah zaikareki da dukkan wani sharri zakiyi amfani dashi sau uku."
Cikin wani irin begen gida da son komawa cikin ahlinta tace.
"Baffa ina son komawa yau in dai zan samu mota".
Cikin jin daɗi da gamsuwa da cewa ta samu waraka yace.
"Kiyi haƙuri sai gobe, tabbas kam tafiyar ta karato, dan haka kiyi haƙuri yanzu zan baki mgnin tsari kiyi wonka dashi sau uku yanzu in kin koma sai kuma da yamma, sai kuma gobe da asuba ki ƙarashi."
Don dole da kimar dottijon ta haƙura dan ji take tamkar ta zama tsunstsuwa tayi fiffige ta fire ta koma gida,ji yakeyi kamar ta rumtse idonta ta buɗe su ta ganta gaban Baba Malam ya mata duk hukuncin daya dace da ita ta nemi yafiyarshi da sanya al'barkanshi.
Ae kuwa bata bar gidan ba saida ya haɗa mata magungunan tsari, wanda duk addu'o'i ne, nan yake ce mata.
"Insha Allah takusa komawa gida."
Tajima agidan nasu Aisha kafun take komawa gida.
A ranar ne kuma Solomon da matarsa sukayi mata tambayar da ta bata mmki, suna tambayarta in mutun zai musulunta me da me zaiyi kuɗi kamar nawa zai kashe,
wannan abu ya sata jin karsashi ta zauna tayi musu bayanin komai na sauƙin musulunci, sai suke ce mata to suna son musulunta to amman sai sun gayawa sarkin majami'arsu. Tace su gaya mata da dole sai sun gaya mishi ,
sai sukace ta bari nanda sati ɗaya zasu gaya mata.
A safiyar ranar dai kuma A Gombe.
Saifuddeen ne zaune akan wheelchair ɗinsa, yana riƙe da Adeel ɗan wata uku ya shiga na uɗu wanda ya ƙara girma yakuma yi wayo yayi kuɓul-kuɓul, wasa yakeyiwa yaron yana me shafa lallausan gashin kansa, wanda yayi shige da nasa, sosai yakejin ƙauna da son yaron acikin ransa.
Ƙurawa yaron idanu yayi aransa.yana me cewa.
"Badan ƙaddara ta kawo Hajia Ameena rabo ba, da yanzu wannan yaron ajikinki zai fito Zaleeha, amman ba damuwa in sha Allah kema naki yana jikina in Allah ya yarda ni dake sai mun samar da abu ɗaya ina ji a jikina kin kusa dawowa gareni, kin gama naki zaki dawo ki tadda nawa. Wai toms in kin dawo me zakice? Ina kikaje? Meyasaki tafiya?".
Yayiwa kansa tambayar tare daɗan lumshe idanunsa, tabbas yayi kewar Zaleeha sosai musamman cikin kwanakin nan tana yawa faɗo mishi cikin rai, ya rasa dalili gashi yanzu sam ta daina hawa online kuma duk sabida yana mata mgna da number sa ta siirin nan dama tace mishi zata goge whatsapp gaba ɗaya kuma ta goge ɗin acewarta ita matar aurece.
Ameena ne tafito daga cikin ɗaki cikin shirinta na zuwa wajen aiki, ƙarasowa wajen su tayi cike da ƙaunarsu, ranƙwafowa tayi inda ta mannawa Saifuddeen din kiss akan laɓɓansa, sannan ta ɗaga yaron zuwa kafaɗanta, cikin kulawa ta ce da Saifuddeen ɗin.
"Saimun dawo" hannu ta ɗaga masa sannan ta fice, dan tayi late.
Shikuwa Saifuddeen laptop dinsa ya ɗauka, inda ya shiga cikin file ɗin da yake aje hotunan Zaleeha, view ɗin wani hoton Zaleehan yayi yana kallo, sosai tayi kyau acikin hoton dimple ɗinta ya zubawa ido, dan tana sanye ne da doguwar rigar da ta amshi jikinta, yajima yana kallon hoton kafun ya rufe laptop ɗin ya nufi ɗaki.
Ameena kuwa saida tabiya ta wajen Ummi tayi mata sallama kafun take wucewa wajen aikin.
Federal medical center.
Baba Malam ne da Ya Ameenu haɗe da Mamy, da kuma Ya Habu ke tsaye, sunyi jigum, matsanancin damuwane kwance biss fuskokinsu, sakamakon kawo Maryam haihuwa da sukayi, gashi kuma ance dole saidai ayi mata theatre.
Wasu nurses biyu ne suka turo wani ɗan dogon gado da Maryam ɗin ke kwance akai, ansanya mata kayan theatre, dai-dai sunzo wucewa ta wajen su Baba Malam ɗinne, Maryam ta sanya hannunta ta kamo na Baba Malam, tare da cewa.
"Baba Malam kazo mana kayi min addu'a kafin a shiga dani."
da sauri Baba Malam ya dubeta cikin tausayawa yace.
"To Maryam zan miki addu'a kinjiko ƴata mai sunan ƴar uwata insha Allah zaki haihu lafiya da yardan Allah."
ganin nos ɗin zasu shiga da itane yasa ta kallesu cikin sanyin murya tace.
"Dan Allah in mun shiga ku kirawo min Babana da mijina suzo akwa abinda zan ce musu kafin ayi aikin."
yanayin nitsuwarta ne yasa sukace.
"To". Suna shigar da ita ɗan falon da za'a ratsa a shiga ainhin ɗakin tiyatan.
Nan suka tsaida gadon kana ɗaya nos ɗin ta fito ta kira su Baba Malam da Ya Ameenu.
Suna shiga ta yunƙura ta tashi zaune cikin sanyi tasa hannunta da yayi sanyi ƙalau tamkar ƙanƙara ta riƙo hannun mahaifinta.
Kai ta girgiza take kuma saiga hawaye sun silalo daga cikin idanunta, cikin muryarta dake fita da sanyi tace.
"Baba Malam ka yafe mi ninaji ajikina cewa bazan tashi ba Baba, dan Allah kayafemin in akwai laifin da nayi maka."
Da sauri Baba malam ya riƙe hannunta tare da cewa.
"Ni kam bakiyi komai ba Maryam, koda ko kinyi min na yafe miki duniya da lahira, bare ni baki min komai ba face biyayya, ubangiji ya yassare miki rayuwar duniya data lahira."
Hannu tasa ta share hawayenta murya na rawa tace.
"Nagode Babana."
Da ƙarfi zuciyar Baba Malam ta buga jin yadda ta kirashi, kama hannunta yayi da kyau jin tana cewa.
"Sannan kuma ina neman wata al'farma a wurinka Babana".
Zuciya a tsinke yace.
"Wacce al'farmace Maryam gaya min".
Lumshe idanunta tayi wasu zafafan hawaye suka kwaranyo mota, cikin sanyin murya tace.
"Dan Allah ina son ka dawo da Mama dan Allah, ka kuma yafewa ƴar uwata Zaleeha, dan Allah Baba kayafe mana baki ɗayanmu Baba Malam ka yafewa Zaleeha dan kada rayuwa tayi mata muni bance kada kayi fushi ka nuna mata illar abinda tayiba, amman kada kuyi dogon fushi da ita, sannan in Mamana tazo kace mats na nemi yafiyarta, ta gafarta min".
Sai kuma ta fara kuka murya na rawa taci gaba da cewa.
"Baba malam Nasan duk inda Zaleeha take. Duk inda take a faɗin wannan duniyar in dai tana raye in taji rasuwata zata zo, dan Allah idan tazo kace mata na ajiye mata saƙo a cikin durowar gadona, kuma kada taje ita kaɗai in zata ɗauka taje ita da Mijinta Saifuddeen sannan kacewa. Ya Ahmad da Zakariyya kada suyi dogon fushi da Zaleeha su zame mata madadina."
taƙare maganar tana dhessheƙan kuka, kai Baba Malam ya jijjiga lokaci ɗaya hawaye suka cika idanunsa, hannunta ya kama ƙam cikin matsanancin ƙaunar ƴartasa yace.
"Insha Allah zaki tashi Maryam, za ayi miki aiki lafiya, kidaina faɗin irin waƴannan maganganun."
Murmushi tayi tare da kamo hannun Ya Ameenu wanda tuni hawaye sun wanke masa fuska, cikin matsanancin ƙaunar mijin nata tace.
"Inaji ajikina cewa zan barka Yayana, zantafi inda bazaka sake ganinka ba, kakulamin da Ayman ɗinmu kaji, sannan kayafemin duk wani abu danayi maka."
Kuka Ya Ameenu ya fashe dashi tare da durƙushewa awajen, don bayajin zai iya cewa komai.
Mamy ma kuka take, nan ita da Ya Habu suka kama hannun Maryam ɗin, murya asanyaye Mamy tace.
"Ki daina faɗin haka Maryam zaki tashi da yardan Allah."
Hannun Mamyn Maryam tasake riƙewa sosai, cikin muryan kuka tace.
"Ku yafemin Mamy, idan Zaleeha ta dawo kice mata nace tabi mijinta sauda ƙafa tayi masa biyayya, danni kam bazan samu daman faɗa mata hakan da bakina ba.
Ya Habu kaima kayafemin, sannan kada kuyi dogon fushi da Zaleeha."
Kukane ya ƙwace wa Mamy, da Ya Habu, Baba malam ma hawaye yake sosai.
Ganin haka yasa nurses ɗin suka tura keken sukayi ciki da Maryam ɗin, tana kallon Ya Ameenu shima yana kallonta haka aka shiga da ita ɗakin theatre'n, kuka sosai Ya Ameenu yasa kaman ƙaramin yaro, Baba Malam ne ya riƙesa yana rarrashinsa.
Ameena kuwa koda taje asibitin aje Adeel tayi awajen wata ƙawarta mesuna Umaima, nan ta nufi theatre room dan ansanar da ita cewa, babban Dr ɗinsu na nemanta acan ɗin.
Takusan kaiwa theatre room ɗinne tahango Baba Malam, Ya Ameenu, da kuma Ya Habu, sai Mamy suna tsaitsaye, cikin sauri taƙarasa garesu, ganin fuskokinsu ɗauke da matsanancin damuwa yasa jikinta yin sanyi asanyaye ta gaidasu, tare dayi musu tambayan halan ko wani suka kawo bashi da lafiya, dan taga idanunsu gaba ɗaya sunyi jajur.
Hankalim Mamy amatuƙar tashe yake faɗa mata cewa.
"Maryam ne suka kawota haihuwa, ankuma ce dole sai theatre za'ayi mata, yanzu haka ma anshiga da ita ɗakin theatre'n."
Hankalin Ameena ne ya tashi sosai, take cikin sauri ta nufi ɗakin theatre'n.
Littafina na ƙuɗine in kina buƙata turo katin mtn na ɗari uku ta wannan no ɗin 09097853257 ko kimin transfer ta asusuna 0005388578 jaiz bank Aisha Aliyu Garkuwa.
By
*GARKUWAN FULANI*
10/4/20, 7:04 PM - Mmn Khalid: *(heart touching)*
Sbpejy Su Baba Malam kuwa tsayuwa sukayi, gaba ɗaya jikinsu asanyaye y'ake, babu wanda yayi yunƙurin zama acikinsu, Mamy kuwa hawaye take ta sharewa, zuciyarta cike take da tausayin Maryam.
Can cikin theater room kuwa, alluran nan dake gusar da hankali, likitotin sukayiwa Adda Maryam, Doctors kusan guda huɗu ne suka duƙufa akanta, cikin ƙwarewa kuwa suka soma yi mata aiki.
Shiru ɗakin theater'n yayi bakajin motsin komai, sai na kayayyakin aikin da likitotin ke amfani dasu.
Sosai aikin nasu ya ɗauko nisa, gefe kuwa Ameena ne da wata nurse wanda sune ke taimakawa wajen miƙawa doctors ɗin kayan aiki.
Ahankali ƙwayar idanunta ke tsiyayar da wasu sassanyan hawaye, sosai kuma hawaye suka rinƙa kwaranyowa daga cikin idanunta, Ameena wanda gaba ɗaya hankalinta naga Maryam din ne, ganin idanun Maryam ɗin na zubda hawaye, yasa amatuƙar firgice ta matso kusa da ɗaya daga cikin doctors ɗin dake yi mata aiki'n, ɗan taɓasa tayi yana juyowa kuwa tayi masa nuni da fuskar Maryam, cikin yanayin tsoro haɗi da mamakin ikon Allah likitan yayiwa ƴan uwansa nuni da Maryam ɗin, wanda idanunta suke ta zubda hawaye, koda suma suka ga yanda Maryam ɗin take , sosai suka shiga shock, saboda sunsan sunyi mata alluran gusar da
Book Chapters
Chapter 1Chapter 2Chapter 3Chapter 4Chapter 5Chapter 6Chapter 7Chapter 8Chapter 9Chapter 10Chapter 11Chapter 12Chapter 13Chapter 14Chapter 15Chapter 16Chapter 17Chapter 18Chapter 19Chapter 20Chapter 21Chapter 22Chapter 23Chapter 24Chapter 25Chapter 26Chapter 27Chapter 28 Chapter 29Chapter 30Chapter 31Chapter 32Chapter 33Chapter 34Chapter 35Chapter 36Chapter 37Chapter 38Chapter 39Chapter 40Chapter 41Chapter 42Chapter 43Chapter 44Chapter 45Chapter 46Chapter 47Chapter 48Chapter 49Chapter 50Chapter 51Chapter 52Chapter 53Chapter 54Chapter 55Chapter 56Chapter 57Chapter 58Chapter 59Chapter 60Chapter 61Chapter 62Chapter 63Chapter 64Chapter 65Chapter 66Chapter 67Chapter 68Chapter 69Chapter 70Chapter 71Chapter 72Chapter 73Chapter 74Chapter 75Chapter 76Chapter 77Chapter 78Chapter 79Chapter 80