dama kallonta ya keyi, murmushi ta sakar masa, domin tuni haushin nasa da takeji ya gushe, ayanda take matsanancin sonsa batajin zata iya dogon fushi dashi bare ta ɓata rawanta da tsalle, shiɗin ma murmushi yayi mata tare da miƙa mata hannunsa, ganin Idanun su Ummi baya kansu yasa ta kama hannun nasa, gamamakinta sai gani tayi yajawota dab dashi, har jikinsu na gogan na juna, kasancewar jiyan ba'a ɗaki ɗaya suka kwana ba, hakan yasa bata gaishesa ba sai yanzun, ahankali tace.
"Ina kwana." Kansa ya jinjina mata alaman lafiya, sannan ya tallafo haɓarta, kiss ya ɗaura mata akan kumatunta da kuma bakinta, baruwansa da wani jin kunya wai dan su Ummi na falon bare yasan idon Ummi baya kansu.
Gaba ɗayansu sunga abun da Saifuddeen din yayiwa Ameena hakan ne yasa suka janye idanunsu gefe, Zaleeha ma da tsautsayi yasa ta ɗago, idanunta sun gane mata abun da ya faru, kawar da kanta gefe tayi, tare da ƙara manne Adeel ajikinta, ko ajikinta itakam, bata ma ji wani abu adangane dasu ba, saidai zuciyarta ta tsegunta mata cewa. "Halan Ameenan matarsa ce kenan." Ummi kuwa, tashi tayi gaba ɗaya ma tabar falon, dan ta gano cewa wannan sabuwar kulawan da Saifuddeen ɗin ya fara bawa Ameena agabansu wani salone, kawai yayi ne saboda wata manufarsa ta daban. Ameena kuwa da gangan ta kamo lips ɗinsa itama ta tsotsa, cikin sanyin murya tace. " I will miss you dear" sake manna masa wani kiss ɗin tayi, sannan ta ɗan janye daga jikinsa, Hayatuddeen kuwa baki ya sake yana kallon ikon Allah,
Zaleeha kuwa sam bata ƙara ɗago kanta bama sai wasa takeyiwa Adeel wanda da ka gani kasan tana jin son yaron har cikin ranta.
Ƙarasowa inda suke Ameenan tayi, tare da sanya hannu ta ɗauki Adeel, tana sakin murmushi me ɗauke da ma'anoni kala kala, haka ta saɓa Adeel akafaɗanta ta fice daga cikin falon, wani irin farinciki takeji acikin ranta, wannan kiss ɗin da Saifuddeen yayi mata agaban Zaleeha ji take kaman kyautar zuciyarsa ya bata a gaban Zaleeha ji takeyi ya gama mata komai dan ko ba komai ya nunawa Zaleeha itama matarsa ce kuma yana sonta murmushi kawai take tayi.

Tashi Zaleeha tayi ta wuce ɗakinta, kusan rabin cup tasha yoghurt ɗin sannan ta kwanta. Acan falo kuwa Raleeya ce ta gama shirya musu abinci akan dinning area, Ummi ne tace da Hayatuddeen yaje ya ƙira Zaleeha tazo suyi beak, koda yaje ɗakin nan ya isketa tana bacci. Dawowa yayi ya faɗawa Ummi'n, hakan yasa Ummi tasa Raleeya ta ɗeba mata nata break fast ɗin daban.

Saida suka kusa kammala break fast ɗin, Ummi ta ɗago kanta ta dubi Saifuddeen wanda yake tsakalan chips yana kaiwa bakinsa, ahankali yake tauna abincin, yanayin komai nasa cikin nutsuwa.
Gyara zama Ummi tayi tare da ɗan muskutawa ta kamo hannunsa, ɗago kansa yayi, tare da sakarwa Ummin nasa murmushi.
Itama Ummin murmushi tayi masa, cikin kulawa tace.
"Ka bani key ɗin side ɗin Zaleeha,"
Fuska ya ɗan kwaɓe tare da mata alamu.
Shiga baisan inda key ɗin yakeba".
Kwaffa tayi tare da cewa.
"Uhumm yayi kyau." Fuska ya ɗan kele,
tsareshi da ido Ummin tayi tana mai nazartanshi kana tace.
"To Inaso kashirya anjima ka raka Zaleeha ta bawa Baba Malam haƙuri, ko kuma shima car keys ɗin naka duk baka san inda sukeba."
take yanayin fuskarsa ya sanja, kansa ya girgiza, tare da aje spoon ɗin hannunsa. Idanu Ummi ta zuba masa ganin ya mata alamun dan Allah tayi haƙuri, sai kuma yaja wheelchair ɗinsa yayi baya, tare da juyawa yabar wajen baki ɗaya,
da idanu Ummi ta bisa har ya fice daga cikin falon.



Wasa farin girki sannu sannu dai bata hana zuwa sai dai a dadde ba'a jeba



Littafina na kuɗine. in kina buƙata ga number 09097853276 katin mtn zaki turo na ɗari 300 ko kimin transfer ta asusuna 0005388578 jaiz bank Aisha Aliyu Garkuwa.




By
*GARKUWAR FULANI*
10/4/20, 7:04 PM - Mmn Khalid: Sbpejtt Kai kawai Ummi ta girgiza tare da tashi kaitsaye ta wuce ɗakinta, Hayatuddeen ma dake zaune ji yayi gaba ɗaya jikinsa yayi sanyi, sam baiso hakan ba, yaso ace Hamman nasa ya amince, saboda shima ya gamsu cewa, da taimakon Hamman nashi ne kaɗai Baba Malam zai iya haƙura ya yafewa Adda Zaleeha'n.
Haka dai suka kammala cin abincin nasu duk jikinsu asanyaye, acan ɓangaren Saifuddeen kuwa yana barin falon nasa, kaitsaye ɓangarensa ya nufa, sauƙa daga kan wheelchair ɗinsa yayi, tare da haurawa saman ɗaya daga cikin haɗaɗɗun kujerun falon ya kwanta, idanunsa ya lumshe yana jin zuciyarsa nayi masa wani iri, maganganun Ummin ne ya dawo cikin tunaninsa, ahankali ya girgiza kansa, cikin zuciyarsa yace.
"Ada ni ba komai bane awajenta, bata ɗaukeni matsayin komai ba, kullum idan akwai wata magana da zai fito abakinta, wanda ta shafeni to baiwuce kalmar ƙiyayya ba, matsalar da ta faɗa ayanzu, shiyasa ta ɗaukeni wani me mahimmanci agareta, ta gudu ne saboda batason aurena, yanzu kuma gashi ta dawo tana zaune aƙarƙashin inuwata, ahaka kuwa shine har da wani neman alfarmarta."
wani murmushi me ciwo yayi tare da girgiza kansa, shiba sakarai bane, ita tayi amanta saboda haka ita kaɗai zata lashe.
Yana gama tunanin ya gyara kwanciyarsa, tare da sake lumshe idanunsa, yana sakin ajiyar zuciya.
Acan ɓangaren Part ɗin Ummi kuwa baccin Zaleeha baiyi wani nisa sosai ba ta farka, Hayatuddeen ne ya kawo mata abinci, haka ya sakata gaba dolen ta saida taci, tana kammalawa kuwa ya miƙo mata ruwa da magungunanta tasha, nan ƙasan carpet ya zauna, ita kuwa tana kwance akan gado, ganin cewa akwai damuwa atattare da itane yasa shi, soma bata labarai wanda yasan dole zasu ɗebe mata kewa, suna zaune ahaka Raleeya ta shigo, akusa da Zaleehan ta zauna, cikin kulawa tace "Aunty Zaleeha ya jikin naki?".
ɗan jinjina kanta tayi, asanyaye tace.
"Da sauƙi." Murmushi Raleeya tayi, tare da faɗin.
"Masha Allah, Allah Ya ƙarasa sauƙi."
Da "Ameen" Zaleehan ta amsa, haka dai suka ci gaba da hiransu, Ita dai Zaleeha idanu kawai ta zuba musu, sau dayawa dramer'n Hayatuddeen da Raleeyan na burgeta. Duk dama har yanzu akwai damuwa kwance aƙasan zuciyarta.
Suna ahaka Ummi tashigo cikin ɗakin, ganinsu atare ne yasata sakin murmushi, sake gaisheta Zaleehan tayi, ta amsa mata fuska asake, har cikin ranta kuwa taji daɗin ganin Zaleehan cikin ɗan yanayi me kyau, kallon kayan dake jikin Zaleehan tayi, take wani tunani yazo mata hakan yasa tace da Hayatuddeen yazo zata aikeshi.
Babu musu ko ya tashi yabi bayanta.
Kaitsaye ɗakinta suka wuce, nan kan gado ta zauna, tare da jawo jakarta ta zage zip ɗin, duban Hayatuddeen tayi, cikin kulawa tace. "Makay zan aike ka ne, ko San Hussain Super Market?".
ta tambayesa da yanayi na ɗan tunani, zama yayi akusa da ita, tare da cewa.
"Wani abu za a sayo miki ne?".
"Kaya nakeson kasayowa Zaleeha, kaga dai bata zo da kayanta ba, part ɗin ta kuma akulle yake, na kuma ce Hammanku ya bada key yayimin biris, dama daya ba da key ɗin sai nasa ko Raleeya ne ta ɗebo mata sauran kayanta." cikin zumuɗi Hayatuddeen yace. "Ummi Makay zanje, wallahi dama ina kwaɗayin strowberry cake, kinga kawai sai na shiga Makay shawarma na saya, nasan itama Adda Zaleehan idan na sayo mata zataci." Hararansa Ummi tayi tare da cewa.
"To sarkin kwaɗayi, an faɗa maka cewa dama kowa irinka ne, koko ance maka kowa kwaɗayi kawai yasa agaba?."
Murmushi yayi, cikin zaƙuwa yace.
"Hmm Ummi bakisan wacece Adda Zaleeha ba kenan, ai shan zaƙinta ko shazumami sai haka, yanzu kawo kuɗin naje na sayo mata kayan."

Kai kawai Ummi ta girgiza tare da zaro Kuɗin da aƙalla zasu kai 70k, acikin jakanta ta miƙa masa, cikin kulawa tace.
"Kanutsu dan Allah Hayatuddeen, dogayen riguna nakeson kasayo mata masu kyau, ni hankalina ma kwata kwata bai kwanta da aikanka ka ba, dan tunda ka iya mota kuma shikenan ka zama ayawo, dan ma ana zaman makokin nan ne da da Zakariyya zakuje, saboda hankalina zaifi kwanciya, saboda ya fika nutsuwa wani lokaci'n."
Ɗan bakinsa ya turo gaba, cikin halin sakalcinsa yace. "Yanzu Ummi dan Allah Zakariyya'n ne ya fini nutsuwa." Murmushi Ummi tayi, tana me zuge zip ɗin jakarta tace.
"Ni maza yi sauri ka kawomin aikana, sannan kuma katabbatar kayi driving cikin nutsuwa."
Haka yafita daga ɗakin yanata wani shagwaɓa, da turo baki gaba, tuno da cewa zaije ya saya strowberry cake yasan yashi sakin murmushi, haka ya fice daga cikin falon, yana karkaɗa ɗan makullin motar dake hannunsa.

Zaleeha da Raleeya kuwa har yanzu suna tare, hira Raleeya ke tayiwa Zaleeha'n, ahaka har wani sabon bacci ya ɗauketa, ganin tayi bacci ne yasa Raleeya sakin murmushi, nan tatashi ta fice daga ɗakin dan zuwa kitchine ɗaura lunch.

Ummi kuwa ganin fitan Hayautuddeen yasa, ta ɗauki wayarta, text ta turawa Saifuddeen akan cewa tana son ganinsa, tana nan zaune kuwa ko mintuna 7 ba acika ba, sai gashi ya shigo cikin ɗakin.
Har gaban Ummin ya ƙaraso da kekensa, sai wani shagwaɓe fuska yake, saboda yasan bai wuce maganan Zaleeha Ummin zatayi masa. Ummi kuwa ɗago kai tayi ta dubesa, cikin nutsuwa tace.
"Wai Saifuddeen me kake nufi da Zaleeha ne? tunfa jiya nake binka da ka bani key ɗin ɗakinta amma kaƙi, ko anan kakeso ta zauna mana bayan gacan ɗakinta?" Ɗan kwaɓe fuska yayi, cikin body language ɗinsa yace.
"Nifa Ummi bansan inda key ɗin ɗakinta yake ba." gane abunda yake nufi yasa Ummi ɗan buɗe baki, da mamaki tace. "Bakasan inda key ɗin yake ba kuma.?"
Kansa ya jinjina alamar "Eh" kuma har ga Allah ya mance inda ya ake key ɗin. Kai Ummi ta jinjina tare da cewa.
"Sannu uban maƙaryata, Saifuddeen yaushe ka fara yimin ƙarya? wato ma sokake kace key ɗin ya ɓata ko? hmmm inace nan da Addarku Rahama ta amshi key ɗin tatafi dashi, ko wata ɗaya baicika ba kaje har gidan ta ka amso, ko kana tunanin banida labari ne? kaga tunkan raina ya ɓaci Saifuddeen ka buɗewa yarinyar nan ɗakinta ta koma tayi zamanta." bakinsa ya turo gaba, sam shi baisoma Ummi tanayi masa maganan Zaleeha'n, ai koma me yafaru itace ta jawo, hakanan saboda ta ɗaukesu sakarkaru saita gudu ta kuma dawo alokacin da take so. Kuma zancen gaskiya harga Allah ya mance in da ya ɓoye key ɗin side ɗinta, amman gashi Ummi gani take ƙarya yayimata abinda bai taɓata kwatanta yimataba.
Hararansa Ummi tayi tare da ɗanyin ƙwafa tace.
"Ayi mutum da taurin kai da riƙo sai kace mutanen farko, wallahi ka tabbatar ka kawomin key ɗinnan tunkan raina ya ɓaci, idan kaƙi kuwa zansa a ɓalla ƙofan da ƙarfi, ta koma ɗaƙinta ta zauna."
Idanunsa yaɗan zaro waje, jin cewa za'a ɓalla ƙofar, tuna cewa ma ƙofar bazata taɓa ɓalluwa bane ya sashi ɗan sakin ajiyar zuciya, hannuwansa ya haɗe waje ɗaya, alaman Ummin tayi haƙuri, kuma shi ya mance inda key ɗin yake ne.
Haranshi tayi sannan tace.
"To batun rakata gidansu ta bawa Babanta haƙurifa ko shima ka mance hanyar gidan ne?".
A hankali ya jujjuya mata kai alamun bai mance ba, sai kuma yayi ƙasa da kanshi.
Ganin cewa bazai biyu ta sauƙi ba yasa Ummi'n, cewa ya tashi yaje kawai.
Yana fita kuwa Ummi tayi ƙwafa tare da cewa. "Ɗan nema zan yi maganinka ne."
Daga haka ta-tashi ta wuce toilet dan ɗauro al'walan sallan azahar.

Can ɓangaren Hayatuddeen kuwa saboda tsabar kwaɗayi yaci ransa saida ya fara zuwa makay shawarma ya sayi strowberry cake ɗinsa, ya kuma haɗa da roasted fish, saboda yasan Adda Zaleehan naso kuma idan ya kai mata zata ci.
Saida ya gama ƙwalamarsa kafun yafito daga Makay Shawarma ɗin, kaitsaye ya nufi cikin Makay Super Market, ɓangaren da dogayen rigunan mata suke ya nufa, sosai ya darje wajen zaɓawa Adda Zaleehan nasa dogin riguna masu kyau, bai tsaya anan ba kuwa harda wasu riga da sket ƴan kanti masu kyau kusan kala uku ya zaɓa mata, haka dai ya gama sayayyyan cikin nutsuwa, sannan ya ƙarasa wajen biyan kuɗi, koda akayi lissafin kayan kuɗin sun haura wanda Ummi ta basa, dan 70k Ummi ta basa, kayan da ya saya kuwa sun haurawa haka, dan kuɗinsu 77k ne, baiwani damu ba, haka ya zaro ATM card ɗinsa dake cikin aljihunsa ya basu, kasancewar dama yana aje ƴan kuɗaɗensa anan cikin asusun banki, dan sau dayawa kuɗin da Hammansa ke basa ba kashewa yake ba, yakan tarasu ne idan sun ɗanyi yawa sai yakai ƙaramin account ɗinsa na bank ba asalin babba da ake sa mishi kason dukiyarsa ba a ƙaramin yake ɗan gutun ajiyarsa, haka dai suka zare 7k ɗinsu suka basa ATM card ɗinsa, daganan kuma suka zuba masa kayan acikin leda.
Har mota kuwa sukasa aka kai masa kayan, haka ya ɗauki hanyar gida, sai ciye ciye yake acikin motar.
Koda ya ƙarasa gida kuwa, Ummi ya bawa kayan, dan har zuwa lokacin Zaleeha bata tashi abacci ba, babu laifi kuma Ummi ta yaba da rigunan dan sunyi kyau sosai.

Saifuddeen kuwa tunda yabar part ɗin Ummi ɓangarensa ya koma, al'wala yayi sannan ya nufi masallaci, tunda yayi sallan azahar kuwa bai dawo gidan ba, Sule driver yaƙira suka ɗan fita, saboda wani aikin daya taso masa, dole saida yaje office ɗinsu, saida aka kusa sallan la'asar sannan ya dawo, anan masallacin ƙofar gidansu yayi sallan la'asar, sannan ya shigo cikin gidan, ɓangaren Ummin nasa ya sake nufa, dan kuwa ɗazu koda yana zaune a office saida yaga text message ɗinta, kancewa
"Lallai ya kawo mata key ɗin ɗakin Zaleeha, sannan kuma ya tabbatar yazo yakai Zaleehan gida ta bawa Baba Malam haƙuri."
Shidai kam yama rasa yanda zaiyi.
Yana shiga falon kuwa ya iske Ummi da Ahmad, sai kuma Hayatuddeen dake zaune ƙasan turkish carpet yana ta faman lodawa cikinsa abinci. Ganin yanda fuskar Ummi take babu wani walwala asamanta yasa yaji jikinsa yayi sanyi, ƙarasowa cikin falon yayi tare da bawa Ahmad hannu suka gaisa, saboda yau duk basu haɗuba. duban Ummin nasa yayi, asanyaye cikin body language ɗinsa yayi mata sannu da gida.
Kai kawai ta jinjina masa, ko kallonsa batayi ba, hakanne yasa jikinsa ƙarayin sanyi, sam baisom fushin Ummin nasa. Ummi kuwa da gangan ta nuna cewar tana fushi dashi, saboda tasan idan ba haka tayi masa ba bazai taɓa yin abun da ta sakashi ba.
Raleeya wanda shigowarta falon kenan, ganin Hamman nata yasa ta wuce kitchine, abinci da drinks ta zubo masa, saboda yau ɗin favorite food ɗinsa ta dafa. nan gabansa ta ƙaraso tare da ɗan durƙusawa, ƙoƙarin aje plate ɗin abincin agabansa take, cikin sauri yaɗan riƙe hannunta tare da girgiza mata kai, alaman ya ƙoshi, kallon sa tayi fuskarta ɗauke da ɗan damuwa, kansa ya jinjina mata alaman cewa. "Tayi haƙuri bayajin yunwa."
Asanyaye ta ɗaga kanta ta kalli Ummi, gani tayi fuskar Ummin atsuke, hakanne yasa ta juyawa ta maida abincin kitchine.
Cikin sanyin jiki ya danna madannin wheelchair ɗinsa tare da ƙarasawa gaban Ummin nasa, hannunta ya kamo tare da ɗan
Showing 111001 words to 114000 words out of 237945 words