ajiye, zama tayi akan sofa tare daɗan ƙaƙalo murmushi, cikin son daurewa yanayin da takejin kanta aciki tace. "Ummi sannu da gida."
Cikin kulawa Ummi tace. "Yauwa Ameena har kuntaso daga wajen aikin?."
Girgiza kai tayi tare da cewa.
"A'a wallahi, kawai dai naɗanji yunwa na damuna ne shine nace bari na gudo gida."
Murmushi Ummi tayi tare da faɗin.
"Ayya sannu to, Raliya na kitchine bara nace ta zubo miki abinci kici ko". Ummi taƙare maganar cikin kulawa.
Akunyace Ameenan ta miƙe tare da cewa.
"Bari naje na zubo da kaina kawai Ummi kada asata wahala."
Nan tamiƙe ta wuce kitchine ɗin.
Ummy kuwa cewa tayi.
"To inaga fa gwara Sule ya rinƙa kai miki abinci bana son wuni da yunwa da kikeyin nan."
Tana ƙoƙarin shiga kitchin ɗinne tace.
"Ba komai fa Ummy in naji yunwa ina sayan abu inci kinga wani Lokacin kuma inama tafiya da abinda zan ci."
Kai kawai Ummy ta jinjina, ita kuwa Ameena.
Raliya ta iske tsaye tana ta ƙoƙarin haɗawa Saifuddeen pepper chicken soup.
Cikin kulawa Ameena tace.
"Sannu agogo sarkin aiki."
Murmushi Raliya tayi tare da faɗin.
"Ke kuma likita bokan turai ba."
Dariya sukayi su dukansu, nan Ameena ta buɗe food flask ɗin da aka zuba haɗaɗɗiyar fried rice aciki, plate ta ɗauka inda ta ɗebi kaɗan, coslow ta zuba asaman shinkafan sannan ta buɗe wata ƴar kula wanda ke ɗauke da liver sauce, kaɗan ta zuba akan abincin, sannan ta sanya spoon tundaga cikin kitchine ɗin tasoma ci. Dubanta Raliya tayi tare da sakin murmushi, har acikin ranta tana ƙaunar Ameenan badan komai ba kuwa saidan ƙaunar Saifuddeen da Ameenan keyi.
Saifuddeen kuwa shigowarsa cikin falon kenan, yana riƙe da kwalin holandia milk inda yake sipping da kaɗan kaɗan.
Dai-dai lokacin Ameena ta fito daga cikin kitchine ɗin, hannunta riƙe da plate ɗin abinci.
Ɗan jim tayi tare da lumshe idanunta, lokaci guda taga wani duhu naneman mamaye ganinta, taku ɗaya zuwa biyu tayi, taji gaba ɗaya jikinta ya saki wani irin jiri mai ƙarfi ya kwasheta, nan tatafi luuuuu tafaɗa kan kujera, take kuwa plate ɗin hannunta ya faɗi, abincin ya tarwatse acikin falon.
Arazane su Ummi da Hayatuddeen sukayo kanta, cikin tsananin damuwa Ummi tace.
"Innalillahi wa'inna ilaihirraju'un, Ameena! Ameena lafiya kuwa?." aruɗe Ummi tayi maganan tana me jijjiga Ameena'n, Saifuddeen ne ya tuƙa wheelchair ɗinsa inda ya ƙaraso cikin sauri, hannunsa yakai yaɗan taɓa fuskar Ameena'n, tare da ɗan bubbuga kumatunta.
Ahankali taɗan buɗe idanunta wanda sukayi luhu-luhu dasu, dishi-dishi haka take ganinsu.
Hannunta ya kamo ya riƙe acikin nasa, cikin kulawa ya ɗaura hannunsa akan goshinta, jin zafi ajikinta yasa shi ɗago kansa ya kalli Ummi.
Jin jina kai Ummi tayi tare da cewa.
"Hayatuddeen miƙomin wayata naƙira Dr Adnan."
Cikin sauri kuwa Hayaruddeen yamiƙo mata wayan nata.
Dialing numbern Dr Adnan ɗin Ummi tayi, bugu biyu ya ɗauka, nan ta shaida masa abun dake faruwa, cikin sauri kuwa yace.
"To Ummy ganinan zuwa."
Anutse Saifuddeen ya gyarawa Ameenan kwanciyarta akan kujera, inda har yanzu yana riƙe da hannunta acikin nasa. Hakanne yasa Ummi taji wani irin sanyi acikin ranta, saboda dama burinta ne taga Saifuddeen ɗin na kulawa da Ameena.
Cikin mintuna ƙalilan Dr Adnan da ya iso, har zuwa lokacin kuwa Ameena dishi-dishin take gani a idanunta.
Jininta Dr Adnan ya ɗiba, sannan yace zaije yayi checking ɗin jinin nata, yana dawowa, amma kafunnan asama mata wani abu taci.
Ummi da kanta tahaɗawa Ameenan maltina da madara, nan ta ɗan ɗagota cikin kulawa ta bata tasha, tana gama sha kuwa ta koma ta kwanta, gefenta Saifuddeen ya koma, nan dai sukayi jigum suna jiran dawowan Dr Adnan.
Inda duk bayan minti ɗaya sai Ummi tayiwa Ameenan sannu.
Turo ƙofar falon Dr Adnan yayi ya shigo, fuskarsa ƙunshe take da zallan farinciki marar misaltuwa.
Zama yayi akan kujera tare da duban Ummi, murmushi yayi inda ya kuma duban Saifuddeen, cikin farin ciki ya tashi ya rungume Saifuddeen ɗin, abun daya basu mamaki kenan.
Ɗan janye jikinsa yayi tare da kamo hannun Saifuddeen ɗin ya riƙe, cikin yanayin farin ciki yace.
"Congratulation My brother, tabbas ƙarfin ikon Allah ya wuce misali Alhamdulillah yau dai ɗaya daga cikin tabbacin da Dr Acash ya bamu ya tabbata saura na biyu, domin da yardan Allah ka kusa zama Baba, dan kuwa Ameena na ɗauke da ciki har na tsawon wata biyu!!"
Cikin tsananin mamaki Saifuddeen dasu Ummi ke kallon Dr Adnan.
Kai ya gyaɗawa Ummy tare da ce mata,
"Eh Ummy matar Saifuddeen nada shigar ciki har na tsawon wata biyu."
Cikin wani irin matsanancin farin ciki Ummi tace.
"Alhamdulillah Allah abun godiya, Alhamdulillah, tsarki ya tabbata ga Allah maɗaukakin sarki, tabbas kaine me kowa me komai, me kumayi alokacin da yaso, sannan ya hana alokacin da yaso!".
Tuni har ƙwallan farin ciki sun cika idanun Ummi.
Shikuwa Saifuddeen lumshe idanunsa yayi yana murmushi mai ɗauke da zallan farin ciki.
Hayatuddeen kuwa wani irin tsalle ya buga, tare da faɗawa jikin Raliya cikim matsanancin farin ciki yace.
"Wayyo Allah na daɗi kasheni zanga ɗan Hammana nima."
Raliyanma da matsanancin farin ciki yasa hawaye suka gangaro daga cikin idanunta, ta rungume Hayatuddeen ɗin, duk da cewa ɗazu suka gama faɗa dashi, amma yanzu farin cikin da suke ciki ya goge wannna faɗan.
Ameena kuwa jin abun da Dr Adnan yafaɗa yasa ta ɓoye kanta cikin hijabi, dan wani irin kunyan Ummi ne ya kamata, cikin zuciyarta kuwa wani irin farin ciki ne wanda bata taɓajin irinsa ba ashe zatonta gsky ne cikine da ita.
Tashi Ummi tayi inda tazo ta rungume Ameena'n, cikin matsanancin farin ciki tace.
"Tabbas aurenki da Saifuddeen yazame mana al'khairi agremu Ameena, Allah yayi miki al'barka ya kuma sauƙeki lafiya."
Akunyace Ameena taɗanyi murmushi tare da sadda kanta ƙasa.
Raliya kuwa sakin Hayatuddeen tayi, tare da zagayowa ta rungume Ameena'n, cikin farin ciki tace.
"Allah ya sauƙeki lafiya Auntyna."
Asanyaye Ameena ta rungumeta tare da faɗin "Ameen."
Murmushi Dr Adnan ketayi, yayinda Ummi kuwa bakinta ya kasa rufuwa.
Ashe zataga jinin Saifuddeen ɗinta aduniya? Ta godewa Allah da cewar nakasan sa bata shafi lafiyarsa ba.
Saifuddeen ma murmushi yake ta saki, sosai yaji wani irin farin ciki aransa, ashe shima zai zamanto uba, cikin ransa yake ta yiwa Allah godiya, da wannan kyautar daya basa.
Nan Ahmad ya shigo ya iske labari me matuƙar daɗi, cikin farin ciki kuwa ya rungume Saifuddeen yana me tayasa murna.
Ummi ce tace da Raliya ta taimakawa Ameena'n ta yi wanka sannan ta kwanta ta huta.
Hakan kuwa akayi Raliya ne ta riƙeta suka je har part ɗinsu, sannan ita ta haɗa mata ruwan wanka, tananan har Ameenan ta fito daga wanka, nan ta kimtsa kanta, inda ta haye gado ta kwanta, sai alokacin Ameena tafita don bata waje ta huta.
Can ɓangaren Ummi kuwa Dr Adnan ne ya haɗa kayan aikinsa inda ya musu sallama ya koma office.
Nan Saifuddeen ma ya fice daga falon.
Ummi kuwa waya ta ciro inda ta dannawa numbern Adda Rahama ƙira, koda ta sanar da Adda Rahama maganan cikin Ameena'n, baƙaramin farin ciki tayi ba, har hawaye saida ta zubar.
Nan tace tananan zuwa da yamma.
Ummi na gama waya da Adda Rahama taƙirayi Bappa Ali ta faɗa masa, baƙaramin farin ciki kuwa Bappa Ali yayi ba, sosai yaji daɗin maganan.
Ahankali ya tura ƙofar ɗakinta ya shiga ɗakinda tun da tazo gidan bai taɓa shigaba sai yau kuma yanzu, kwance take akan gado, inda ta lumshe idanunta, dan bacci ne keson ɗaukarta.
Ƙarasowa cikin ɗakin yayi, inda ya nufo inda take.
Jin motsinsa yasa ahankali ta ɗan buɗe idanunta, ganinsa yasa ta sakin murmushi, kusa da ita ya ƙaraso, ahankali yakai hannunta inda ya shafi kanta, cikin kulawa fuska ɗauke da murmushi ya jinjina mata kai tare da buɗe mata hannunshi, alamun tazo yaji ɗumin Baby'nshi murmushi ta kuma sakar masa tare da tashi zaune ta faɗa jikinsa, yau yana cikin farin ciki hakan ne yasa yayi hugging ɗinta, haɗe fuskarsu waje ɗaya tayi nan ta haɗe bakinsu, yau kam biye mata yayi, inda ya soma sucking lips ɗinta tare dasa hannunshi yana ɗan shafa cikinta.
Daga nan kuma ta shiga gwada masa salon romance ɗinta.
Sosai yau ya biye mata, hakanne yasa daɗin da taji yau dabanne, sannan aɓangarensa shima babu laifi.
Da Yamma kuwa saiga Adda Rahama tazo, rungume Saifuddeen ɗin tayi tana mejin matsanamcin farin ciki, haka dai ta zauna har kusan magriba sannan ta-tafi.
Acikin dangi kuwa kowa yaji labarin samun cikin Ameena sai yayi murna sosai ƴan uwa da abokanshi kabsun cika da farin ciki.
Haka dai Ameena keta renon cikin jikinta kulawa take samu sosai da sosai daga wajen gaba ɗaya mutanen gidan, aɓangaren Saifuddeen ma yanzu kulawa na musamman yake bata, duk da cewa bawai yana wani damuwa da ita bane, amma yana kulawa da ita yanda ya kamata, sannan kuma cikin nata ma ba irin me laulayi ɗinnan bane, tana zuwa wajen aikinta, sannan kuma bata yarda ta gaza wa Saifuddeen takowani ɓangare ba, naci da jaraba kuwa sai abunda ya ƙaru, wani lokaci Saifuddeen idan yaga abun nata yayi yawa, guduwa yake sashin Ummi, bazai dawo ba kuwa sai ya tabbatar da cewa tayi bacci in gari ya waye taita fushinta yaita mata dariya yace zata lalata shi daga nan ta huce.
Daga can gidansu Zaleeha kuwa suma murnan samun cikin Adda Maryam wanda yakeda wata ɗaya amman sabida yawan laulayinshi duk dangi sun gane,
inda Ya Ameenu ke cike da farin ciki yana kulada matarsa sanyin idanunshi tamkar ransa .
A hankali rayuwa ke juyawa watanni na tafiya tuni lokaci ya tafi.
Numan.
To zuwa yanzu dai Zaleeha tana jin zazamanta cikin garin Numan ɗin tamkar zama cikin kurku ne, domin hankalinta da nitsuwar kab basa jikinta,
Kullum da begen iyayenta da ƴan uwanta take kwana, musaman Adda Maryam da suna magana da ita.
Tana son komawa cikin ƴan uwanta tayiwa mahaifinta biyayya amman sai taji bazata iyaba.
Sauƙin ta ɗaya tana ɗan samun nitsuwa cikin musulmai ƴan uwanta na rugar fulanin nan,
do kuwa sosai sukayi sabo da Aisha, sannan kuma tana ɗebe mata kewa,
Damuwar da take ciki ya baiyana a jikinta domin ta rame fuskarsa tayi fiyau sai dai daga ɓangaren kyawunta kuwa sai abun da yaci gaba, dan wani irin fresh skin ɗinta yayi, komai nata yayi normal, fatarta takara haske da sheƙi sakamakon kayan fruits da take ci da kuma yanayin ni'imar wurin, ita kanta tanajin sauyi ajikinta sosai ramar da tayi sai yasa hancinta ya ƙara baiyana, daga gefe kuwa kullum Aisha saita kawo mata abinci daga gidansu, Man Liman kuwa sosai yake janta a jiki in tazo ta sameshi a gida har sun ɗan saba.
Yauma tana gidan su Aishan kasan cewar yau jumma'a ne bayan an sauƙo daga sallan jumma'an ne Man Liman ya iske su a tsakar gida ƙarƙashin bishiyar ceɗiya bisa dukkan alamu suma sallan sukayi.
Cikin girmamawa suka haɗa baki wurin ce mishi.
"Baffa sannu da dawowa."
Murmushi yayi tare da miƙa musu ledan cefen da ke hannunshi tare da ce musu.
"Yauwa sannunku tagwayen Baffa, kunyi sallanko?."
Murmushi sukayi tare da gyaɗa mishi kai alamun eh.
Man Liman dattijone me karamcin gaske,
Har ya wuce sai kuma ya juyo ya kalli Zaleeha cikin fullanci yace.
"Zaleehatu taho ki ɗan rubuta min wani abu, ke kuma Aisha wonke allon ƙarfen can ki miƙo min."
Da sauri sukace to tare da miƙewa.
A hankali Zaleeha ta shiga sashin baffa,
kan taburma ta sameshi bisa farin buzunshi, gefenshi ya nuna mata tare da cewa.
"Zauna nan wasiƙa zaki rubuta min zuwa ga sarkin numan, dan arnan garin sun samu a gaba."
Cikin ganin girman dottijon tace to.
Kana ya gaya mata duk abinda zata rubuta, ta rubuta mishi sannan ya kira wani ɗanshi ya kaiwa ɗan aikensu takardar.
Har ta yunƙura zata tashi sai kuma ta koma ta zauna jin yace.
"A a zauna Zaleehatu ban gama da keba."
Murmushi tayi tare da cewa.
"To". Gyara zamanshi yayi da kyau ya fuskanceta kana a hankali yace.
"Zaleeha."
jin yadda ya kirata yasa ta amsa a nitse, cikin kulawa yace.
"In na tambayeki wani abu zaki gaya min gaskiya, kuma. Sannan ban miki shisshigi bako?."
Da sauri ta jujjuya kanta tare da cewa.
"In sha Allah zan gaya maka iya gskyar da na sani. Kuma ka tambayeni duk abin da kakeso dan ka isa katambayenin."
Gyaran murya yayi tare da cewa.
"Ke ƴar wanne garine?."
Cikin nitsuwa tace.
"Baffa ni bagombiyace."
Kai ya gyaɗa cikin gamsuwa kana yace.
"Me sunan mahaifinki?."
a take idanunta suka cika da hawaye, murya na rawa tace.
"Sunan babana Malam Bashir Sulaiman Dukku."
Fuska cike da al'ajabi Man Liman yace.
"ikon Allah Malam Bashiru ne mahaifinki?".
cin mmki tace.
"Baffa ka sanshi ne?".
Kai ya jujjuya mata tare da cewa.
"Eh to ba a zahiri na sanshiba ina dai jin azuzzukan shi, a radio, shiyasa bai zama ɓoyeyyen mutunba".
Sai kuma ya gyara zama tare da zuba mata ido cikin kula yace.
"To amman meyasaki daga tambayar sunashi kika fara zubda hawaye?, kuma meya kawoki nan cikin arna kika zauna Zaleehatu gaya min meyasa?."
Hannunta tasa ta share hawayenta dake zuba tanajisa kamar matsayin Babanta mahaifi, cikin rawar murya ta bashi labarin duk abinda ya faru na sanadin gudowanta har kwana a gardin da takeyi bata ɓoye mishiba, ta ƙara da cewa.
"Ina so in koma in je in bawa Baba malam haƙuri inyi mishi biyayya kan zaɓin dayamin amman ji nake bazan iyaba gani nake kamar in na koma zan mutu, nasan babana da ƴan uwana duk sunyi fushi dani".
Nisawa yayi tare da gyara zama cikin kula yace.
"Ae bazaki komaba Zaleehatu sabida kafa akayi anan matuƙar ba'a karya sihirin dake jikinki ba, haka bazaki iya yiwa mahaifinki biyayya, kuma dolene yasa kikayi ta gudun ɗakinki kina kwana cikin ciyawayi, domin an miki turen sihiri a ƙarƙashin gadonki, muddin ba'a karya sihirinba ɗakin zaike miki duhu zaina baki tsoro, kuma sihirin da akayi miki kin maganshi a mafarki sai in kin manta ne koda yake an rufe bakinma bazaki iya faɗiwa ko abinda kikeji ba, nima kaina yau tsawon wata uku kenan ina miki tofi cikin abincin da ake mishi shiyasa kika samu damar min bayani da izinin Allah."
Shiru tayi cikin sanyi tace.
"Baffa bana son mijin da aka haɗani dashi wanda nacema ya taimakenin nan shine nakeso."
Murmushi yayi tare da cewa.
"Kada ki damu, dukkan wani farin cikinki yana ƙarƙashin inuwar mijin da aka aura miki, na nemi al'farma kada ki sake cewa bakya son mijinki, kuma kada ki sake cewa akwai wanda kikeso bayanshi kisa a ranki shine ya taimakeki kuma dashi aka haɗaki, sai kici gaba da yiwa shi wancan ɗin addu'ar Allah ya azirtashi da mafificiyar al'janna Allah ya taimakeshi fiye da yadda ya taimakeki, Allah yasa soyayyarshi a zuciyar maƙiyanshi soyayya ta rinjaƴi ƙiyayyarsa a zuƙatan makusan tansa wlh in kin masa haka kin gama mishi komai sannan in kin yiwa mahaifinki biyayya zaki samu dukkan salama. Kiyi min wannan al'ƙawarin ni kuwa daga yawau zan fara baki addu'oi insha Allah zaki rabu da duk wani sihiri kuma zaki koma ɗakinki."
Cikin jin sanyin da tunda ta gudo bataji ba tace.
"To baffa in sha Allah zanyi ta mishi addu'a, ngd da taimako."
Murmushi yayi kana a hankali yace.
"Akwai wacce ke zuga mahaifiyarki, kuma ta asirce mahaifiyarki ne, da bata isa ta mata musuba,duk abinda tasata ko bata so sai tayi, amman ina karya abin jikinki itama abinda ke jikinta zai karye domin sunan ALLAH a duk inda take zaije ya sameta".
Ganin tayi shiru ne ya sashi ɗan sahir tawa tare da cewa.
"Ko Mamanki bata da yar uwa da suke tare".
A hankali ta gyaɗa mishi kai tare da.
"Tana dasu ɗaya musul mace ɗaya kuwa arniya ce".
Murmushi yayi tare da cewa.
"Ba Shatuba ai ita hasken addini na jikinta da zuciyarta, ita ɗayar dai domin ita burinta Mamanku daku yaranta duk kuyi ridda ku koma addininsu, to kuma ya rigada Allah ya tsareku kana mahaifinku a tsaye yake a kanku kun kuma samu cikakkiyar tarbiya."
Ajiyan zuciya ya sauƙe tare da cewa.
"Akwai kuma ƙawayenki cikinsu wacca kikafi so ɗin ita ke cin dunduniyarki, amman da zaran kin samu waraka da abinda akayi miki, keda kanki zakiji bakya son mu'amala da ita".
Cikin mutuwan jiki tace.
"Baffa ina son komawa gida".
Murmushi yayi tare da cewa.
"Zaki koma in sha Allah, yanzu zamu fara addu'oi tsawon sati biyu, daga randa zamu fara miki rubutu kina sha kuma duk mafarkin da kikayi ki sanarmin".
Kai ta gyaɗa alamar to.
Hahira sukayi sosai da Baffa'n, nan ta ƙara faiyace mishi irin yanayin da takejin kanta aciki, wanda sau da yawa tanajin son komawa gida aranta, amma saita najin kaman kafata agarin akayi, cikin son kwantar mata da hankali Baffa'n yace.
"Insha Allah zai taimaka mata da wasu addu'o'i wanda zatana sha, da kuma wanda zata nayi."
Nan dai tayi masa godiya sosai, dan ita kanta tanajin son komawa gida acikin ranta.
Bayan wasu ƴan kwanaki ne kuma Baffan yasa, Aisha tayi ƙiranta, nan yabata wani ruwan addu'a yace tana sha tana shafawa jikinta.
Sai kuma haɗin ayatushshifa da ganyen magarya guda bakwai, da kuma zam-zam, yace tana amfani dasu, ƙara jaddada mata yawan yin azkar da kuma zama da al'wala yayi, nan dai tayi masa godiya sosai.
Cikin ikon Allah kuwa yau kwananta biyu da fara amfani da maganin, sannan kuma tanajin sauƙin wasu abubuwan.
Gashi daren jiya ne Adda Maryam taƙirata awaya, sosai kuma tayi mata nasiha, mai ratsa jiki, wanda kalamanta suka ƙara sanyawa taji gaba ɗaya jikinta yayi sanyi.
A gefen Solomon da matarsa kuwa zaman Zaleeha a gidansu yasa hasken addinin musulunci yana ratsa zuƙatansu, suna ganin daraja da kimar addinin musulunci fiye da nasu addinin har an kai matin da yanzu sun fara watsi da addininsu dan sai ayi lahadi uku basuje majami'arsuba, zuwa yanzu Zaleeha kuwa tana tallata musu addinin dayi musu tayi su shiga domin shine hanyar tsira, kana tana ƙyautata musu sosai da kuɗin dake hannunta irin kyautatawar da musulunci ya umarci musulmi yayiwa ahlul kitab dan da kyautata zasu ƙaunaci addinin su san addinine mai sauƙi da tausayawa, to zuwa yanzu dai Zaleeha na zaton musuluntar su Solomon da elizabet a ko wanne lokoci.
Kwanci tashi babu wuya, inda yanzu cikin Ameena yakai wata bakwai, sosai kuma yayi girma, dan kuwa zuwa yanzu daƙyar ma take
Showing 78001 words to 81000 words out of 237945 words
Cikin kulawa Ummi tace. "Yauwa Ameena har kuntaso daga wajen aikin?."
Girgiza kai tayi tare da cewa.
"A'a wallahi, kawai dai naɗanji yunwa na damuna ne shine nace bari na gudo gida."
Murmushi Ummi tayi tare da faɗin.
"Ayya sannu to, Raliya na kitchine bara nace ta zubo miki abinci kici ko". Ummi taƙare maganar cikin kulawa.
Akunyace Ameenan ta miƙe tare da cewa.
"Bari naje na zubo da kaina kawai Ummi kada asata wahala."
Nan tamiƙe ta wuce kitchine ɗin.
Ummy kuwa cewa tayi.
"To inaga fa gwara Sule ya rinƙa kai miki abinci bana son wuni da yunwa da kikeyin nan."
Tana ƙoƙarin shiga kitchin ɗinne tace.
"Ba komai fa Ummy in naji yunwa ina sayan abu inci kinga wani Lokacin kuma inama tafiya da abinda zan ci."
Kai kawai Ummy ta jinjina, ita kuwa Ameena.
Raliya ta iske tsaye tana ta ƙoƙarin haɗawa Saifuddeen pepper chicken soup.
Cikin kulawa Ameena tace.
"Sannu agogo sarkin aiki."
Murmushi Raliya tayi tare da faɗin.
"Ke kuma likita bokan turai ba."
Dariya sukayi su dukansu, nan Ameena ta buɗe food flask ɗin da aka zuba haɗaɗɗiyar fried rice aciki, plate ta ɗauka inda ta ɗebi kaɗan, coslow ta zuba asaman shinkafan sannan ta buɗe wata ƴar kula wanda ke ɗauke da liver sauce, kaɗan ta zuba akan abincin, sannan ta sanya spoon tundaga cikin kitchine ɗin tasoma ci. Dubanta Raliya tayi tare da sakin murmushi, har acikin ranta tana ƙaunar Ameenan badan komai ba kuwa saidan ƙaunar Saifuddeen da Ameenan keyi.
Saifuddeen kuwa shigowarsa cikin falon kenan, yana riƙe da kwalin holandia milk inda yake sipping da kaɗan kaɗan.
Dai-dai lokacin Ameena ta fito daga cikin kitchine ɗin, hannunta riƙe da plate ɗin abinci.
Ɗan jim tayi tare da lumshe idanunta, lokaci guda taga wani duhu naneman mamaye ganinta, taku ɗaya zuwa biyu tayi, taji gaba ɗaya jikinta ya saki wani irin jiri mai ƙarfi ya kwasheta, nan tatafi luuuuu tafaɗa kan kujera, take kuwa plate ɗin hannunta ya faɗi, abincin ya tarwatse acikin falon.
Arazane su Ummi da Hayatuddeen sukayo kanta, cikin tsananin damuwa Ummi tace.
"Innalillahi wa'inna ilaihirraju'un, Ameena! Ameena lafiya kuwa?." aruɗe Ummi tayi maganan tana me jijjiga Ameena'n, Saifuddeen ne ya tuƙa wheelchair ɗinsa inda ya ƙaraso cikin sauri, hannunsa yakai yaɗan taɓa fuskar Ameena'n, tare da ɗan bubbuga kumatunta.
Ahankali taɗan buɗe idanunta wanda sukayi luhu-luhu dasu, dishi-dishi haka take ganinsu.
Hannunta ya kamo ya riƙe acikin nasa, cikin kulawa ya ɗaura hannunsa akan goshinta, jin zafi ajikinta yasa shi ɗago kansa ya kalli Ummi.
Jin jina kai Ummi tayi tare da cewa.
"Hayatuddeen miƙomin wayata naƙira Dr Adnan."
Cikin sauri kuwa Hayaruddeen yamiƙo mata wayan nata.
Dialing numbern Dr Adnan ɗin Ummi tayi, bugu biyu ya ɗauka, nan ta shaida masa abun dake faruwa, cikin sauri kuwa yace.
"To Ummy ganinan zuwa."
Anutse Saifuddeen ya gyarawa Ameenan kwanciyarta akan kujera, inda har yanzu yana riƙe da hannunta acikin nasa. Hakanne yasa Ummi taji wani irin sanyi acikin ranta, saboda dama burinta ne taga Saifuddeen ɗin na kulawa da Ameena.
Cikin mintuna ƙalilan Dr Adnan da ya iso, har zuwa lokacin kuwa Ameena dishi-dishin take gani a idanunta.
Jininta Dr Adnan ya ɗiba, sannan yace zaije yayi checking ɗin jinin nata, yana dawowa, amma kafunnan asama mata wani abu taci.
Ummi da kanta tahaɗawa Ameenan maltina da madara, nan ta ɗan ɗagota cikin kulawa ta bata tasha, tana gama sha kuwa ta koma ta kwanta, gefenta Saifuddeen ya koma, nan dai sukayi jigum suna jiran dawowan Dr Adnan.
Inda duk bayan minti ɗaya sai Ummi tayiwa Ameenan sannu.
Turo ƙofar falon Dr Adnan yayi ya shigo, fuskarsa ƙunshe take da zallan farinciki marar misaltuwa.
Zama yayi akan kujera tare da duban Ummi, murmushi yayi inda ya kuma duban Saifuddeen, cikin farin ciki ya tashi ya rungume Saifuddeen ɗin, abun daya basu mamaki kenan.
Ɗan janye jikinsa yayi tare da kamo hannun Saifuddeen ɗin ya riƙe, cikin yanayin farin ciki yace.
"Congratulation My brother, tabbas ƙarfin ikon Allah ya wuce misali Alhamdulillah yau dai ɗaya daga cikin tabbacin da Dr Acash ya bamu ya tabbata saura na biyu, domin da yardan Allah ka kusa zama Baba, dan kuwa Ameena na ɗauke da ciki har na tsawon wata biyu!!"
Cikin tsananin mamaki Saifuddeen dasu Ummi ke kallon Dr Adnan.
Kai ya gyaɗawa Ummy tare da ce mata,
"Eh Ummy matar Saifuddeen nada shigar ciki har na tsawon wata biyu."
Cikin wani irin matsanancin farin ciki Ummi tace.
"Alhamdulillah Allah abun godiya, Alhamdulillah, tsarki ya tabbata ga Allah maɗaukakin sarki, tabbas kaine me kowa me komai, me kumayi alokacin da yaso, sannan ya hana alokacin da yaso!".
Tuni har ƙwallan farin ciki sun cika idanun Ummi.
Shikuwa Saifuddeen lumshe idanunsa yayi yana murmushi mai ɗauke da zallan farin ciki.
Hayatuddeen kuwa wani irin tsalle ya buga, tare da faɗawa jikin Raliya cikim matsanancin farin ciki yace.
"Wayyo Allah na daɗi kasheni zanga ɗan Hammana nima."
Raliyanma da matsanancin farin ciki yasa hawaye suka gangaro daga cikin idanunta, ta rungume Hayatuddeen ɗin, duk da cewa ɗazu suka gama faɗa dashi, amma yanzu farin cikin da suke ciki ya goge wannna faɗan.
Ameena kuwa jin abun da Dr Adnan yafaɗa yasa ta ɓoye kanta cikin hijabi, dan wani irin kunyan Ummi ne ya kamata, cikin zuciyarta kuwa wani irin farin ciki ne wanda bata taɓajin irinsa ba ashe zatonta gsky ne cikine da ita.
Tashi Ummi tayi inda tazo ta rungume Ameena'n, cikin matsanancin farin ciki tace.
"Tabbas aurenki da Saifuddeen yazame mana al'khairi agremu Ameena, Allah yayi miki al'barka ya kuma sauƙeki lafiya."
Akunyace Ameena taɗanyi murmushi tare da sadda kanta ƙasa.
Raliya kuwa sakin Hayatuddeen tayi, tare da zagayowa ta rungume Ameena'n, cikin farin ciki tace.
"Allah ya sauƙeki lafiya Auntyna."
Asanyaye Ameena ta rungumeta tare da faɗin "Ameen."
Murmushi Dr Adnan ketayi, yayinda Ummi kuwa bakinta ya kasa rufuwa.
Ashe zataga jinin Saifuddeen ɗinta aduniya? Ta godewa Allah da cewar nakasan sa bata shafi lafiyarsa ba.
Saifuddeen ma murmushi yake ta saki, sosai yaji wani irin farin ciki aransa, ashe shima zai zamanto uba, cikin ransa yake ta yiwa Allah godiya, da wannan kyautar daya basa.
Nan Ahmad ya shigo ya iske labari me matuƙar daɗi, cikin farin ciki kuwa ya rungume Saifuddeen yana me tayasa murna.
Ummi ce tace da Raliya ta taimakawa Ameena'n ta yi wanka sannan ta kwanta ta huta.
Hakan kuwa akayi Raliya ne ta riƙeta suka je har part ɗinsu, sannan ita ta haɗa mata ruwan wanka, tananan har Ameenan ta fito daga wanka, nan ta kimtsa kanta, inda ta haye gado ta kwanta, sai alokacin Ameena tafita don bata waje ta huta.
Can ɓangaren Ummi kuwa Dr Adnan ne ya haɗa kayan aikinsa inda ya musu sallama ya koma office.
Nan Saifuddeen ma ya fice daga falon.
Ummi kuwa waya ta ciro inda ta dannawa numbern Adda Rahama ƙira, koda ta sanar da Adda Rahama maganan cikin Ameena'n, baƙaramin farin ciki tayi ba, har hawaye saida ta zubar.
Nan tace tananan zuwa da yamma.
Ummi na gama waya da Adda Rahama taƙirayi Bappa Ali ta faɗa masa, baƙaramin farin ciki kuwa Bappa Ali yayi ba, sosai yaji daɗin maganan.
Ahankali ya tura ƙofar ɗakinta ya shiga ɗakinda tun da tazo gidan bai taɓa shigaba sai yau kuma yanzu, kwance take akan gado, inda ta lumshe idanunta, dan bacci ne keson ɗaukarta.
Ƙarasowa cikin ɗakin yayi, inda ya nufo inda take.
Jin motsinsa yasa ahankali ta ɗan buɗe idanunta, ganinsa yasa ta sakin murmushi, kusa da ita ya ƙaraso, ahankali yakai hannunta inda ya shafi kanta, cikin kulawa fuska ɗauke da murmushi ya jinjina mata kai tare da buɗe mata hannunshi, alamun tazo yaji ɗumin Baby'nshi murmushi ta kuma sakar masa tare da tashi zaune ta faɗa jikinsa, yau yana cikin farin ciki hakan ne yasa yayi hugging ɗinta, haɗe fuskarsu waje ɗaya tayi nan ta haɗe bakinsu, yau kam biye mata yayi, inda ya soma sucking lips ɗinta tare dasa hannunshi yana ɗan shafa cikinta.
Daga nan kuma ta shiga gwada masa salon romance ɗinta.
Sosai yau ya biye mata, hakanne yasa daɗin da taji yau dabanne, sannan aɓangarensa shima babu laifi.
Da Yamma kuwa saiga Adda Rahama tazo, rungume Saifuddeen ɗin tayi tana mejin matsanamcin farin ciki, haka dai ta zauna har kusan magriba sannan ta-tafi.
Acikin dangi kuwa kowa yaji labarin samun cikin Ameena sai yayi murna sosai ƴan uwa da abokanshi kabsun cika da farin ciki.
Haka dai Ameena keta renon cikin jikinta kulawa take samu sosai da sosai daga wajen gaba ɗaya mutanen gidan, aɓangaren Saifuddeen ma yanzu kulawa na musamman yake bata, duk da cewa bawai yana wani damuwa da ita bane, amma yana kulawa da ita yanda ya kamata, sannan kuma cikin nata ma ba irin me laulayi ɗinnan bane, tana zuwa wajen aikinta, sannan kuma bata yarda ta gaza wa Saifuddeen takowani ɓangare ba, naci da jaraba kuwa sai abunda ya ƙaru, wani lokaci Saifuddeen idan yaga abun nata yayi yawa, guduwa yake sashin Ummi, bazai dawo ba kuwa sai ya tabbatar da cewa tayi bacci in gari ya waye taita fushinta yaita mata dariya yace zata lalata shi daga nan ta huce.
Daga can gidansu Zaleeha kuwa suma murnan samun cikin Adda Maryam wanda yakeda wata ɗaya amman sabida yawan laulayinshi duk dangi sun gane,
inda Ya Ameenu ke cike da farin ciki yana kulada matarsa sanyin idanunshi tamkar ransa .
A hankali rayuwa ke juyawa watanni na tafiya tuni lokaci ya tafi.
Numan.
To zuwa yanzu dai Zaleeha tana jin zazamanta cikin garin Numan ɗin tamkar zama cikin kurku ne, domin hankalinta da nitsuwar kab basa jikinta,
Kullum da begen iyayenta da ƴan uwanta take kwana, musaman Adda Maryam da suna magana da ita.
Tana son komawa cikin ƴan uwanta tayiwa mahaifinta biyayya amman sai taji bazata iyaba.
Sauƙin ta ɗaya tana ɗan samun nitsuwa cikin musulmai ƴan uwanta na rugar fulanin nan,
do kuwa sosai sukayi sabo da Aisha, sannan kuma tana ɗebe mata kewa,
Damuwar da take ciki ya baiyana a jikinta domin ta rame fuskarsa tayi fiyau sai dai daga ɓangaren kyawunta kuwa sai abun da yaci gaba, dan wani irin fresh skin ɗinta yayi, komai nata yayi normal, fatarta takara haske da sheƙi sakamakon kayan fruits da take ci da kuma yanayin ni'imar wurin, ita kanta tanajin sauyi ajikinta sosai ramar da tayi sai yasa hancinta ya ƙara baiyana, daga gefe kuwa kullum Aisha saita kawo mata abinci daga gidansu, Man Liman kuwa sosai yake janta a jiki in tazo ta sameshi a gida har sun ɗan saba.
Yauma tana gidan su Aishan kasan cewar yau jumma'a ne bayan an sauƙo daga sallan jumma'an ne Man Liman ya iske su a tsakar gida ƙarƙashin bishiyar ceɗiya bisa dukkan alamu suma sallan sukayi.
Cikin girmamawa suka haɗa baki wurin ce mishi.
"Baffa sannu da dawowa."
Murmushi yayi tare da miƙa musu ledan cefen da ke hannunshi tare da ce musu.
"Yauwa sannunku tagwayen Baffa, kunyi sallanko?."
Murmushi sukayi tare da gyaɗa mishi kai alamun eh.
Man Liman dattijone me karamcin gaske,
Har ya wuce sai kuma ya juyo ya kalli Zaleeha cikin fullanci yace.
"Zaleehatu taho ki ɗan rubuta min wani abu, ke kuma Aisha wonke allon ƙarfen can ki miƙo min."
Da sauri sukace to tare da miƙewa.
A hankali Zaleeha ta shiga sashin baffa,
kan taburma ta sameshi bisa farin buzunshi, gefenshi ya nuna mata tare da cewa.
"Zauna nan wasiƙa zaki rubuta min zuwa ga sarkin numan, dan arnan garin sun samu a gaba."
Cikin ganin girman dottijon tace to.
Kana ya gaya mata duk abinda zata rubuta, ta rubuta mishi sannan ya kira wani ɗanshi ya kaiwa ɗan aikensu takardar.
Har ta yunƙura zata tashi sai kuma ta koma ta zauna jin yace.
"A a zauna Zaleehatu ban gama da keba."
Murmushi tayi tare da cewa.
"To". Gyara zamanshi yayi da kyau ya fuskanceta kana a hankali yace.
"Zaleeha."
jin yadda ya kirata yasa ta amsa a nitse, cikin kulawa yace.
"In na tambayeki wani abu zaki gaya min gaskiya, kuma. Sannan ban miki shisshigi bako?."
Da sauri ta jujjuya kanta tare da cewa.
"In sha Allah zan gaya maka iya gskyar da na sani. Kuma ka tambayeni duk abin da kakeso dan ka isa katambayenin."
Gyaran murya yayi tare da cewa.
"Ke ƴar wanne garine?."
Cikin nitsuwa tace.
"Baffa ni bagombiyace."
Kai ya gyaɗa cikin gamsuwa kana yace.
"Me sunan mahaifinki?."
a take idanunta suka cika da hawaye, murya na rawa tace.
"Sunan babana Malam Bashir Sulaiman Dukku."
Fuska cike da al'ajabi Man Liman yace.
"ikon Allah Malam Bashiru ne mahaifinki?".
cin mmki tace.
"Baffa ka sanshi ne?".
Kai ya jujjuya mata tare da cewa.
"Eh to ba a zahiri na sanshiba ina dai jin azuzzukan shi, a radio, shiyasa bai zama ɓoyeyyen mutunba".
Sai kuma ya gyara zama tare da zuba mata ido cikin kula yace.
"To amman meyasaki daga tambayar sunashi kika fara zubda hawaye?, kuma meya kawoki nan cikin arna kika zauna Zaleehatu gaya min meyasa?."
Hannunta tasa ta share hawayenta dake zuba tanajisa kamar matsayin Babanta mahaifi, cikin rawar murya ta bashi labarin duk abinda ya faru na sanadin gudowanta har kwana a gardin da takeyi bata ɓoye mishiba, ta ƙara da cewa.
"Ina so in koma in je in bawa Baba malam haƙuri inyi mishi biyayya kan zaɓin dayamin amman ji nake bazan iyaba gani nake kamar in na koma zan mutu, nasan babana da ƴan uwana duk sunyi fushi dani".
Nisawa yayi tare da gyara zama cikin kula yace.
"Ae bazaki komaba Zaleehatu sabida kafa akayi anan matuƙar ba'a karya sihirin dake jikinki ba, haka bazaki iya yiwa mahaifinki biyayya, kuma dolene yasa kikayi ta gudun ɗakinki kina kwana cikin ciyawayi, domin an miki turen sihiri a ƙarƙashin gadonki, muddin ba'a karya sihirinba ɗakin zaike miki duhu zaina baki tsoro, kuma sihirin da akayi miki kin maganshi a mafarki sai in kin manta ne koda yake an rufe bakinma bazaki iya faɗiwa ko abinda kikeji ba, nima kaina yau tsawon wata uku kenan ina miki tofi cikin abincin da ake mishi shiyasa kika samu damar min bayani da izinin Allah."
Shiru tayi cikin sanyi tace.
"Baffa bana son mijin da aka haɗani dashi wanda nacema ya taimakenin nan shine nakeso."
Murmushi yayi tare da cewa.
"Kada ki damu, dukkan wani farin cikinki yana ƙarƙashin inuwar mijin da aka aura miki, na nemi al'farma kada ki sake cewa bakya son mijinki, kuma kada ki sake cewa akwai wanda kikeso bayanshi kisa a ranki shine ya taimakeki kuma dashi aka haɗaki, sai kici gaba da yiwa shi wancan ɗin addu'ar Allah ya azirtashi da mafificiyar al'janna Allah ya taimakeshi fiye da yadda ya taimakeki, Allah yasa soyayyarshi a zuciyar maƙiyanshi soyayya ta rinjaƴi ƙiyayyarsa a zuƙatan makusan tansa wlh in kin masa haka kin gama mishi komai sannan in kin yiwa mahaifinki biyayya zaki samu dukkan salama. Kiyi min wannan al'ƙawarin ni kuwa daga yawau zan fara baki addu'oi insha Allah zaki rabu da duk wani sihiri kuma zaki koma ɗakinki."
Cikin jin sanyin da tunda ta gudo bataji ba tace.
"To baffa in sha Allah zanyi ta mishi addu'a, ngd da taimako."
Murmushi yayi kana a hankali yace.
"Akwai wacce ke zuga mahaifiyarki, kuma ta asirce mahaifiyarki ne, da bata isa ta mata musuba,duk abinda tasata ko bata so sai tayi, amman ina karya abin jikinki itama abinda ke jikinta zai karye domin sunan ALLAH a duk inda take zaije ya sameta".
Ganin tayi shiru ne ya sashi ɗan sahir tawa tare da cewa.
"Ko Mamanki bata da yar uwa da suke tare".
A hankali ta gyaɗa mishi kai tare da.
"Tana dasu ɗaya musul mace ɗaya kuwa arniya ce".
Murmushi yayi tare da cewa.
"Ba Shatuba ai ita hasken addini na jikinta da zuciyarta, ita ɗayar dai domin ita burinta Mamanku daku yaranta duk kuyi ridda ku koma addininsu, to kuma ya rigada Allah ya tsareku kana mahaifinku a tsaye yake a kanku kun kuma samu cikakkiyar tarbiya."
Ajiyan zuciya ya sauƙe tare da cewa.
"Akwai kuma ƙawayenki cikinsu wacca kikafi so ɗin ita ke cin dunduniyarki, amman da zaran kin samu waraka da abinda akayi miki, keda kanki zakiji bakya son mu'amala da ita".
Cikin mutuwan jiki tace.
"Baffa ina son komawa gida".
Murmushi yayi tare da cewa.
"Zaki koma in sha Allah, yanzu zamu fara addu'oi tsawon sati biyu, daga randa zamu fara miki rubutu kina sha kuma duk mafarkin da kikayi ki sanarmin".
Kai ta gyaɗa alamar to.
Hahira sukayi sosai da Baffa'n, nan ta ƙara faiyace mishi irin yanayin da takejin kanta aciki, wanda sau da yawa tanajin son komawa gida aranta, amma saita najin kaman kafata agarin akayi, cikin son kwantar mata da hankali Baffa'n yace.
"Insha Allah zai taimaka mata da wasu addu'o'i wanda zatana sha, da kuma wanda zata nayi."
Nan dai tayi masa godiya sosai, dan ita kanta tanajin son komawa gida acikin ranta.
Bayan wasu ƴan kwanaki ne kuma Baffan yasa, Aisha tayi ƙiranta, nan yabata wani ruwan addu'a yace tana sha tana shafawa jikinta.
Sai kuma haɗin ayatushshifa da ganyen magarya guda bakwai, da kuma zam-zam, yace tana amfani dasu, ƙara jaddada mata yawan yin azkar da kuma zama da al'wala yayi, nan dai tayi masa godiya sosai.
Cikin ikon Allah kuwa yau kwananta biyu da fara amfani da maganin, sannan kuma tanajin sauƙin wasu abubuwan.
Gashi daren jiya ne Adda Maryam taƙirata awaya, sosai kuma tayi mata nasiha, mai ratsa jiki, wanda kalamanta suka ƙara sanyawa taji gaba ɗaya jikinta yayi sanyi.
A gefen Solomon da matarsa kuwa zaman Zaleeha a gidansu yasa hasken addinin musulunci yana ratsa zuƙatansu, suna ganin daraja da kimar addinin musulunci fiye da nasu addinin har an kai matin da yanzu sun fara watsi da addininsu dan sai ayi lahadi uku basuje majami'arsuba, zuwa yanzu Zaleeha kuwa tana tallata musu addinin dayi musu tayi su shiga domin shine hanyar tsira, kana tana ƙyautata musu sosai da kuɗin dake hannunta irin kyautatawar da musulunci ya umarci musulmi yayiwa ahlul kitab dan da kyautata zasu ƙaunaci addinin su san addinine mai sauƙi da tausayawa, to zuwa yanzu dai Zaleeha na zaton musuluntar su Solomon da elizabet a ko wanne lokoci.
Kwanci tashi babu wuya, inda yanzu cikin Ameena yakai wata bakwai, sosai kuma yayi girma, dan kuwa zuwa yanzu daƙyar ma take
Book Chapters
Chapter 1Chapter 2Chapter 3Chapter 4Chapter 5Chapter 6Chapter 7Chapter 8Chapter 9Chapter 10Chapter 11Chapter 12Chapter 13Chapter 14Chapter 15Chapter 16Chapter 17Chapter 18Chapter 19Chapter 20Chapter 21Chapter 22Chapter 23Chapter 24Chapter 25Chapter 26Chapter 27 Chapter 28Chapter 29Chapter 30Chapter 31Chapter 32Chapter 33Chapter 34Chapter 35Chapter 36Chapter 37Chapter 38Chapter 39Chapter 40Chapter 41Chapter 42Chapter 43Chapter 44Chapter 45Chapter 46Chapter 47Chapter 48Chapter 49Chapter 50Chapter 51Chapter 52Chapter 53Chapter 54Chapter 55Chapter 56Chapter 57Chapter 58Chapter 59Chapter 60Chapter 61Chapter 62Chapter 63Chapter 64Chapter 65Chapter 66Chapter 67Chapter 68Chapter 69Chapter 70Chapter 71Chapter 72Chapter 73Chapter 74Chapter 75Chapter 76Chapter 77Chapter 78Chapter 79Chapter 80