wata ƙila gobe idan kika koma Baba Malam zaiyi haƙuri ya yafe miki".
Kuka ta fashe dashi tare da faɗawa jikin Zakariyya'n, cikin kuka tace.
"Na cuci kaina Zakariyya, nadasawa ƴan uwana baƙin ciki da ɓacin rai, nayi nesa da ku gashi har Adda Maryam tarasu batare da mun sake ganawa ba, lokacin dana tafi taƙira wayana, yafi sau 20 amma ban taɓa ɗagawa ba, kowa yaƙini sai bayan nayi wata biyu a can na fara amsa kiranta Zakariyya kai kaɗaine kaji tausayina, ya zanyi Zakariyya idan Baba Malam be yafemin ba, ya zanyi?".
Kukane yaci ƙarfinta sosai.
Zakariyya ma kukan yake. Zamewa yayi ya zauna tare da ɗaura kanta akan cinyarsa, ganin haka yasa ta takure jikinta waje ɗaya, nan tashiga rera sabon kuka, ita tanayi Zakariyya nayi, an rasa me rarrashin wani acikinsu, tayi kuka kam bana wasa ba, ita kanta bazata iya faɗin yaushe ne kuma tayaya ne, bacci ya ɗauketa ba, haka tayi bacci kanta nakan cinyan Zakariyya, yin baccin nata kuwa bairasa nasaba da irin kukan da tasha ta ƙoshiba, saboda yawan kuka nasanya mutum bacci, batare daya shiryawa hakan ba.
Ganin tayi bacci yasa Zakariyya zame jikinsa, pillown kujera ya ɗauka ya ɗora mata kanta akai, dubanta yayi, bacci take amma kuma sheshsheƙan kuka take tayi, hawayen da suka zubo daga cikin idanunsa ya goge, sannan ya tashi ya fita daga falon, kaitsaye ya koma gida.

Ita kuwa Zaleeha ko mintuna 20 batayi tana baccin ba, azabure tatashi, ganin bataga Zakariyyan ba, yasata dasa wani sabon kukan.
Tayi kukan tayi kukan harsaida taji kamar ma ba aduniya ta ke ba, ciwon kai kuwa ba'a magana, domin saboda tsabar ciwon da kanta keyi mata, har wani dishi dishi take gani

Haka dai ta zauna agidan idan tayi shiru yanzu anjima kuwa tayi kuka, da ƙyar ma ta iya tashi tayi sallah.
Tana nan tana kuka har dare ya rufa, yanda taga rana kuwa haka taga dare, ko lumshewa idanunta batayi ba, balle bacci ya ɗauketa, batun ciwon kai kuwa sai abun da yayi gaba, dan kuwa zuwa yanzu harwani ji take kaman kannata ya kumbura, saboda tsabar ciwo da yakeyi mata.
Haka ta kwana azaune tana karatu qur'an da kuka har gari yayi haske.
Nan dai daga falon babu inda ta gusa, banda toilet da ta shiga ta ɗauro alwala, tana nan zaune Zakariyya ya buɗe kofar falon ya shigo, ganin yanda idanunta suka kumbura kana sukai jajur yasa shi ɗan zaro idanunsa, cikin sauri ya ƙaraso cikin falon, agabanta ya zauna tare da aje ƴar ƙaramar kulan dake hannunsa, hankalinsa amatuƙar tashe yace.
"Kwana kikayi kina kuka ko?."
Yafaɗa yana me sanya hannunsa ya share mata hawayen dake kan fuskarta, kulan da ya shigo dashi ya buɗe, soyayyen dankali da ƙwai ne, sai sauce ɗin egg, turo mata kulan gabanta yayi, cikin tausayawa yace.
"Waima rabonki da abinci tun yaushe ne Adda Zaleeha? kici wannan abincin kinji." Kanta ta girgiza masa, cikin da shashshiyar muryarta tace.
"Banajin zan iyacin wani abu Zakariyya, bana buƙatar komai yanzu a duniya sai yafiyan Baba Malam, tayaya kake tunanin zan iya sakawa cikina abinci a airin wannan halin da nake ciki? bazan iya ba, ka kaini kawai naje nasake bawa Baba Malam haƙuri, hakanne kaɗai zaisa naji sanyi araina."
Hawayen tausayinta ya share, sannan ya kamo hannunta, cikin sanyin murya yace.
"Taso muje." Nan ta miƙe yana riƙe da hannunta yazama kaman shine yayanta ita kuma ƙanwarsa, haka suka fita daga gidan, tafiya kaɗan sukayi suka samu napep.

Aƙofar gidan ta baya Zakariyya yace da me napep ɗin ya sauƙesu, duban Zaleehan Zakariyya yayi, cikin sanyi yace.
"Kije Baba Malam shida su Mamy suna falonsa, nikam zan shiga ta babban ƙofa kar agane tare muke dake, nasan fushin da Baba Malam keyi dake zai iya shafana."
Kanta ta jinjina tana me share hawayenta, nan ta nufi cikin gidan, shikuwa Zakariyya ya sallami me napep ɗin ya tafi. Jikinta amatuƙar sanyaye haka ta shiga cikin gidan nasu, dayawan familynsu na cikin gida, na zaune a compund ɗin gidan, ganinta yasa gaba ɗaya duk suka tsaya kallonta, kanta aƙasa tana me zubar da ƙwalla haka ta nufi sashin Baba Malam,
jikinta asanyaye ta kai hannunta jikin ƙofar falon ta buɗe, Baba Malam, Malam Adam, Ya Ameenu, Ya Habu, Mamy, Ya Ahmad, da kuma Mama sai Goggo Maryama, sune zaune afalon, sunyi jigum, gefe kuwa wani babban abokin Baba Malam ne wanda yazo tundaga Kaduna, dan yi musu ta'aziyya, Ganin Zaleehan yasa Baba Malam rumtse idanunsa, Itakuwa Zaleeha ƙarasowa tsakiyar falon tayi, nan ta zube akan guiwowinta, tare da sakin wani irin fitinannen kuka, cikin kukan ta soma rarrafawa, dan ƙarasawa wajen Baban nata, cikin sauri Baba Malam ya ɗaga mata hannu, ransa amatuƙar ɓace yace.
"Idan kika sake kika taɓani banyafe miki ba, banason ganinki kifitamin daga gida!" Yafaɗi maganar yana me yi mata nuni da ƙofar fita. Hankalinta ne yasake tashi, take taji komai ya dawo mata sabo, cikin wani irin matsanancin kuka, ta rarrafa zuwa gaban su Mamy, azauce take matuƙa, cikin matsanancin kuka ta kamo hannun Mamy dana Goggo Maryama, amatuƙar gigice cikin tsananin kuka murya na rawa tace.
"Dan Allah Mamy Goggo Maryama ku bawa Baba Malam haƙuri, wallahi aduniya bani da kowa sama daku, Mamy dan Allah kibasa haƙuri na tuba ku yafe min." Hawayene suka zubo daga idanun Mamy na tausayin Zaleehan to amma itama, bata da ikon buɗan baki tace da Baba Malam ɗin yayi haƙuri, Goggo Maryama kuwa ma ɗauke kanta tayi gaba ɗaya, ganin haka yasa Zaleeha rarrafawa ta nufi wajen Ya Ahmad, cikin sauri Ya Ahmad ɗin natama ya miƙe batare daya bari ta iso wajen ba, ya nufi can cikin ɗakin Baba Malam ɗin, Allah yasani shi zuciyarsa me rauni ce akan Zaleeha, ko a jiya kukanta daya ganine yaƙara masa nasa kukan, sannan kuma awannan karan shi kansa baida wani hurumin bawa Baba Malam haƙuri akan ya yafe mata, ganin Ya Ahmad ɗin ya tashi, yasa Zaleeha sakin firgitaccen kuka, Mama ma kukan take sosai, wanda gaba ɗaya zuciyarta nadama da dana sanine ne ya cinye, dan har kunyan haɗa idanu dasu Baba Malam ɗin takeyi.
Kallon Ya Habu Baba Malam yayi, cikin ɓacin rai yace.
"Habu fitarmin da ita daga falo na da gida na baki ɗaya."
Tsam kuwa Ya Habu ya miƙe, hannunsa yakai ya damƙi hannun Zaleeha'n, haka ya jata yana ƙoƙarin fitar da ita daga falon, kuka take sosai har numfashinta na sarƙewa, sam Ya Habu baiji tausayinta acikin ransa ba, saboda har yanzu bai manta da irin baƙincikin da ta shayar dasu ba, asanadin ɓacin ranta, har Baba Malam saida ya kwanta jinya, shine yanzu zata zo da wani kuka tace a yafe mata.
Zakariyya kuwa ganin an fito da Zaleeha'n, kamar wata wanda ba ƴar gidan ba, yasashi fashewa da kuka, nan ya lallaɓa ya fita, dan zuwa ya sameta, Ya Habu kuwa ƙofa ya buɗe, ya turata waje, sannan ya jawo ƙofar gidan ya rufe, sulalewa tayi ajikin ƙofar tare da sakin wani irin marayan kuka, dai-dai lokacin Zakariyya ya ƙaraso, hannunta ya kamo, tare da jawota jikinsa ya rungumeta, ahankali yake ɗan bubbuga bayanta, shiɗin ma kuka yake sosai.
Cikin sheshsheƙan kuka tace.
"Bani da inda zanje Zakariyya, Baba Malam ya tsaneni, yasa Ya Habu ya koreni kamar karya, ko ganina bayason yi, wayyo Allah ni Zaleeha ina zansakana kai da rayuwata! Wa zan samu ya tayani bawa Baba Malam haƙuri,tunda kowa yaƙi ya saurareni"
Cikin kuka Zakariyya yace.
"Mafita ɗayace Adda Zaleeha,."
Cikin tsananin kuka murya a disashe tace.
"Menene mafitan me zanyi in samu Baba Malam ya yafe min ne
Zakariyya?".
Hawayenshi ya share tare da cewa.
"Mafitar kuwa itace baki da wajen zuwa wanda ya wuce gidan su Hayatuddeen, wallahi na tabbata mutum ɗayane zai roƙi Baba Malam akan ya yafe miki, kuma ya aminta ya yafe miki ɗin a sauƙaƙe."
Cikin disashewar murya tace.
"Waye ne?."
Gyara tsayuwanshi yayi tare da cewa.
"Bakowa bane kuwa wannan mutumin face HAMMA SAIFUDDEEN, na tabbata idan kikazo da Hamma SAIFUDDEEN to Baba Malam zai yarda ya yafe miki."
Cikin kukan ta shiga jinjina kanta.
Murya na rawa tace. "Nayarda zanje koma inane, matuƙar Baba Malam zai yafemin, zanje shima in bashi haƙuri dan Allah Zakariyya ka kaini gidan su Hamma Saif ɗin kaji."
Kai Zakariyya ya girgiza, cikin tausayinta yace.
"Bazan iya zuwa ba.
Sam bazan iya kaikiba Adda Zaleeha, saboda bansan da wani idon zan kallesu nace nadawo musu dake ba, ke kikayi amanki saboda haka ke zaki lashe abunki ke ɗayanki, ke kaɗanki kika gudu kuma ke kaɗanki zaki koma da ƙafarki zakije ki shiga gidan dai da kika gujewan ki kwashi kayan kunyanki".
Yana gama faɗin haka ya tara mata wani mai adai-dai-ta sahu, sam bata fahimci ma me yake cewa ba, ita dai burinta kawai shine ta samu me baiwa Baba Malam haƙuri.
Zakariyya ne ya faɗawa mai napep ɗin inda zai kaita, tare da zaro kuɗinsa ya basa.
Ko acikin napep ɗin kuka take sosai, batasan cewa girman fushin da ƴan uwan nata sukayi da ita har yakai haka ba.

Koda mai napep ɗin ya sauƙeta a bakin gate ɗin gidan Saifuddeen, ido ta zubawa gidan da data gujewa kusan shekara ɗaya kenan.
Toma me matsayinta a gidan? Me sunanta? Matar gidan ko baƙuwar gidan? Da waɗanne idanun zata kallesu? Me zata cewa Ummi dottijiyar mata mai tarin mutunci da kima a idonta, me zata ce mata meyasa ta gudu? tace mata bata son ɗanta na cikinta ne ko meye? Ina zata ce musu taje? Da izinin wa ta fita? Zasu saurareta ma kuwa? Gaba ɗaya tsoro da fargaba da kunya da ƙuncin zuciya da rayuwa da nadama da danasani sun rufeta, fuskar nan tayi tib-tib tayi jazir idanun duk sun ƙanƙance, a hankali take jan ƙafarta har ta isa baki ƙofa, hannu tasa ta ƙonƙosa,
Da sauri mai gadinsu yazo ya buɗe mata ƙofar, ganin matar mai gidan ne dan bai mancetaba, da sauri ya bata hanya tare da cewa.
"Hajia barka da hanya. An dawo lfy?".
Kai kawai ta iya gyaɗa mishi a wani sashin na zuciyarta kuwa ta ɗanji sauƙin tsoronta na kada su Ummi su koreta, taku takeyi a hankali yayinda hawayenta ke kwaranya, jin muryar mai gadin nasu na cewa.
"Ya mukaji da haƙuri Allah ya jiƙanta da rahma".
a hankali tace.
"Amin Amin."
kana ta ci gaba da nufar sashin Ummi.


Acan cikin gidan Hamma Saifuddeen kuwa Gabaki ɗayansu suna tare a falon Ummi, banda Ameena wanda tun da sassafe data dawo ta ɗan huta so ta koma dan zasuyi wani taro da manyansu shiyasa tatafi wajen aiki, Saifuddeen, Ummi, Ahmad, Raliya, Hayatuddeen, sai kuma Adda Rahama, wanda dawowanta kenan daga gidan su Zaleehan, inda taje tayi musu ta'aziyya, yanzu ma zaune suke suna ƙara jajanta rasuwan Maryam ɗin, duban Ummi Adda Rahama tayi kana tace.
"Wallahi Ummi na tausayawa Ya Ameenun su Zaleeha ƙwarai, domin tabbas yayi rashin mace ta gari, kinga fa ko ranan nan nakaiwa Abban su Akih abinci, kasancewar yana sauri, hakan yasa ya fita batare da yayi break fast ba, nan asibitin nasu na haɗu da ita taje awu, ashe haɗuwan mu na ƙarshe kenan, Allah sarki Maryam, wallahi mace ce me hankali da nutsuwa, babu ruwanta, ta iya zama da mutane, kowa nata ne, gata da fara'a da kuma kyautata wa, insha Allah halinta na gari zai bita, Allah Ubangiji kuma ya jiƙanta da rahama." Nan suka amsa da Ameen su dukansu, Hayatuddeen kuwa, miƙewa yayi daga zaunen da yake, kaitsaye yafice daga falon, so yake yaɗanje shagon nan dake ƙarshen titin gidan nasu ya sayo rechard card.
Dai-dai ya kawo ƙofar fita daga falon, ita kuma Zaleeha ta kawo kai, hakan yasa sukayi karo da juna, da sauri yaja baya, idanunsa ya waro cike da mamakin ganin Zaleehan agidansu.
Ita Zaleeha kuwa idanu ta ƙura masa, hawaye na bin fuskarta, lokaci guda kuwa Hayatuddeen ya sanja fuska, tare da ɗauke kansa, yi yayi ma kamar baisanta ba, kana ya raɓa ta gefenta ya wuce, batare da yace da ita ƙala ba, hakan ne yasa jikin Zaleehan yayi wani irin mugun sanyi, take kuma hawayenta suka ƙaru fargaba da tsoro ya ƙara rufeta, haka dai da ƙyar take iya ɗaga ƙafafunta ta nufi cikin falon Ummi zuciyarta na duka tara-tara, koda ta ƙarasa bakin ƙofar shiga falon, hakanan taji ƙirjinta na wani irin bugu, kuka ne me ƙarfi keson ƙwace mata, cikin wata irin dashashshiyar murya wanda bata fita sosai tayi sallama, tare da shigowa cikin falon!.
Cikin mamaki su duka suka ɗago kansu suna kallonta kusan a tare sukace,
"Laaaaa."
Saifuddeen ne ya fara ganinta, kasancewar dama shi yana facing ɗin ƙofar shigowan falon ne shiyasa ya rigasu ganinta.
Taku ɗaya tayi tana ƙoƙarin shigowa cikin falon Saifuddeen yayi wani irin tsuke fuska cikin yanayin zafi ya ɗaga mata hannu, alaman dakatarwa.
Hawayen dake cikin idanunta ne suka kuma gangarowa har zuwa kan ƙirjinta kai ta fara jujjuyawa cikin kiɗima ganin ya ɗago, Hannunsa ya yana me yi mata alama akan cewa kada tayi kuskuren shigowa cikin falon, ta koma inda ta fito.
Wani marayan kuka ta saki tare yayyarfa hannu alamun bata cikin haiyacintama bisa alamu duk a gigice take.

Dubansa Ummi tayi tare da cewa.
"Lafiyanka kuwa Saifuddeen, akan me zaka koreta?"
Rumtse idanunsa yayi tare da girgizawa Ummin nasa kai, alaman cewa bayason ganin Zaleehan. Kukan daya zo mata ne takasa dannewa, hakan yasa ta sakeshi da tsananin ƙarfi a hankali jiki na rawa ta shiga takowa, tana ƙarasowa gaban Ummi.
Ganin halin da take cikine yasa Ummi miƙo mata hannu alamun tazo.
ai kuwa ganin haka yasa da sassarfa ta ƙaraso gaban Ummi cikin kuka ta zube akan guiwowinta, tare da ɗaura kanta akan cinyar Ummin, nan ta saki wani irin gigitaccen kuka, mai ratsa zuciya, da kuma ban tausayi, Shiru sukayi gaba ɗayansu falon sai sautin kukan Zaleeha'n ne kawai ke tashi, wanda hakanne ya sanya gaba ɗaya jikin su Adda Rahama Ahmad Raliya yayi sanyi, Kuka take kamar ranta zai fita, cikin kukan tare da sarƙaƙƙiyar muryarta wanda bata fita sosai tace.
"Na shiga uku Ummi Baba Malam yayi fushi dani, naje gidansa ya koreni, yace baya ko son ganina, Ummi kowa baya sona, kowa guduna yake, Ummi ya zanyi, yazanyi da rayuwata, Ƴar uwata tatafi ta barni, Babana kuma yana fushi dani, duka ƴan uwana suna fushi dani, ina zansa rayuwata, Ina ma da ace mutuwa ni ta ɗauka ba Adda Maryam ba, ina ma ace mutuwa zata ɗaukeni!!!." ta ƙare maganar tana sakin wani irin gigitaccen kuka, harda shiɗewa.
Jin abun da Zaleeha'n ke faɗa ne yasa Ummi taji idanunta sun kawo ƙwalla, wani irin tausayin Zaleehan ne ya kamata,
Cikin wani irin yanayi Numfashin Zaleehan ya sarƙe aƙirjinta,
Ummi ne tasanya hannu ta ɗan ɗagota, hakan kuwa yayi dai-dai da ɗaukewar numfashinta, take ta tafi luuuu ta faɗi ƙasa summamiya.
Hankalin Ummi da su Adda Rahama ne yayi wani irin masifaffen tashi, da sauri sukayo kanta.
Ganin Haka yasa Saifuddeen rumtse idanunsa, wanda lokaci guda sukayi ja, bayajin zai iya cigaba da zama acikin falon baya jin zuciyarshi nada ƙarfi da taurin da zata juri ganin halin da Zaleeha ke cikiba, hakan yasa ya danna madannin kekensa, batare dasu Ummi sun farga ba ya fice daga cikin falon.




Littafin nan na ƙuɗine


By
*GARKUWAN FULANI*
10/4/20, 7:04 PM - Mmn Khalid: Sbpejddwl Cikin tsananin ruɗani da firgici Ummi ta ɗago kanta, ta kalli Raliya, cikin sauri tace.
"Raliya bani ruwa na yayyafa mata maza-maza bani da sauri-sauri, kiyi sauri mana."
Cikin sauri jiki na rawa Raliya ta nufi, fridge ɗin dake cikin falon, goran ruwa ta ɗauko, saboda tsabar sauri kuwa har tana haɗawa da tuntuɓe. Ummi ne ta karɓi goran ruwan, jiki na rawa ta ɓalle murfin tare da zuba ruwan ahannunta, ta watsa a fuskar Zaleeha, ko motsi batayi ba bare su saka ran farfaɗowanta, ganin haka yasa Ummi sake watsa mata
Showing 99001 words to 102000 words out of 237945 words