kamkamni ya na sauke Numfashi.
Ni na samu barci ammh shi ya kasa sai Tunane Tunane ya ke yi.
Salama da natsuwa yake ji suna Shigarsa duk da farko shed'an ya so ya yi masa wasa da kyakyawan niyarsa.
Shed'an na fad'a masa ta yi aure aure wasu sun rigasa sanin inda ya ke son sani yanzu.
Ammh tunda ya kasance a wajen ya ji ya daina wani kokwanto Hasiya ta zama shi, shima kuma ya zama ita na Har Gaban Abada.
Itace mace ta farko da ta nemi Sauya rayuwarsa, kuma ta yi nasara sannan itace mscen da ta san sirrinsa a yadda ya Sameta shi dai dari bisa Dari ta yi masa bai san ko in ya sake wani auran zai ji makin da ya bata ya ragu ba.
Tun daga ranar Assadiq ya Bud'e anarcinsa ba kama hannun yaro.
Wata irin rayuwa muke gudawar ta soyayya da kauna mai Tsayawa a zuciyar Masoya.
Assadiq ya zama nawa nima na zama na shi ya maidani yar gata acikin mata kuma ya sa na fara Tunanin na yi ma Sauran mata zarra.
"Hasiya zan kula da ke, zan zama bangon ki mai kare ki da dukan wani abun da zai kawo miki kunci ko Damuwa."
Kalamansa kenan koda yaushe kuma na aminta da shi, Domin komai na Muradin ya'a mace Assadiq na yi min shi.
Na kara kiba kularwar Assadiq yasa na bude har raman wuyana ya fara cikewa haka Ramatu ta rika fad'i Lokacin da tazo wajena.
Adda Fati ta fi kowa farinciki ganin na samu kwanciyar Hankali Amma ma Dagachan bangaran ta na sanin Labarina Hankalinta ya kwanta.
Adda Rukayya ma da tazo ta ganni sai da ta yi mamaki, saboda ni kaina nasan na sauya kamar ba wanchan Hasiyar ba.
Yanzu ko su Ummi basa gabana Soyayyar Mijina ta isheni komai Tunda bai taba barina na yi kuka ba.
Suma sun kula da haka sai suka shiga Taitayinsu.
gwarama Maman Sulaihat muna shiri da ita tunda ita bata kyamaceni ba.
*Janafty*
*TMWBK2017*
*TMW is a paid Novel, Pay 500 for regular or VIP N1K, Via 0552179550 Jamila Umar Gt bank, 09069067488*
Haba Babyn Habiby ya zaki zauna kina ta fama cutar infection, ke ce rashin sha’awa, ke ce jin zafi yayin tarayya, ke xche d’aukewar ni’ima, ke ce kai’kayi ki fitar farin ruwa da sauransu, an yi maganin asibiti da na gargajiya amma duka dai, tau share hawayenki ‘karshen matsalarki ta zo, da Honeydrops infection flusher ko cleanser pro sai kin yi dariya da godiya don zai wanke miki duk wata cutar sanyi. Akwai original sabaya ta gyaran breast su cicciko kamar baki shayar ba, akwai ta hips da mazaunai ki yi ma sha Allah ki samu kaya kema su miki d’as ki bar yawo da doguwar riga.
Na ce ba a nan muka tsaya ba muna da hadaddun kaya irinsu sweeteners, tighteners and wetners na tashin kan oga, wanda zai miki tukwicin dole, ke ko kurma ne sai ya yi magana ranar, don sumbatu ki dai samu abun rufe mai baki gudun ma’kota. Muna nan a garin Sokoto muna aike kowani gari kowacce kasa cikin aminci da rahusa. Kuna iya danna link din nan domin yi mana magana Kai tsaye https://Wa.me/2348167888934 ko kuma a kira 08167888934. Sai mun ji daga gareku isassun mata.
*Bayan Shekara D'aya da Rabi.*
ALHAMDULILLAH kawai zan ce acikin Shud'ewar Shekara d'aya da Rabi, wanda ya yi daidai da shekaru Biyu da wasu wattani da aurena da Assadiq.
A zuwa wannan lokacin ni Hasiya Mamman kona na riga nasan Ubangiji ya gama yi mini dukkan wani gata anan Duniya.
Ya bani rai da lafiya sannan ya bani kwanciyar hankali natsuwa da cikar Zatin aure a tare dani, sannan ya Turomin Namiji tamkar da Dubu ASSADIQ wanda ya kasance wani Kafad'a da na kan saukar da kaina a samanta cikin kuka ko Dariya.
In Dariya ne shi zai tayani mu Dara in kuma abun kuka ne shi zai taimakamin ya Sharemin hawayena.
Zaman aure daman hausawa sun ce zo mu zauna ne sannan kuma sunce zo mu sab'a ne.
Bazan ce ina cikin Farinciki dari bisa Dari ba akwai kananun matsalolin da ba su kai ma a fad'e su ba.
Assadiq ya gama min koma a wannan Duniyan Tunda ya tsamo ni daga cikin kuntattaciyar Rayuwar da ni ke ciki ya raya zuciyata da abun kawa da Soyayya ya kuma nuna min nima kamar sauran mutane na ke wanda Ubangiji ya Hallice su tare da Tarin Ni'imominsa.
Assadiq ya yi sanadiyar da na manta da Rayuwata ta baya gabadaya, na Fuskanci Farincikin da ke tare da Rayuwata yanzu Assadiq na sona sannan yana son Farincikina kuma Bukatuna daidai misali in bai fi karfinsa ba yana cika mun su.
Ya maidani yar gata sannan yar lele wacce na zarce duka yayyena sa'ar miji da gidan aure.
A wanchan Shekaran ne ya sakani na Zana Jamb daman SSCE na ta yi kyau bani da matsala duk da ya lura karatun bai wani Dameni ba ammh bai Damu ba ya zaunar da ni ya nunamin Muhimmanci ilimin ya'ya mata a wannan Rayuwar.
Da taimakon kalaman karfin gwiwansa da Aljihunsa da kokarinsa na Fara karatu a Federal Collage of Education da ke zariya, da kuma Amincewarsa ko nace zabinsa na fara karatu a kolejin a shashen Biology Computer.
Da Farko ina ganin wahalan karatun ammh kuma Jajircewan Assadiq yasa na fara jin dad'in kasancewata cikin Daliban kalejin ta zariya mai Dauke da Dalibai mabambamta daga garuruwa a fad'in kasar nan.
Duk abunda ban gane ba shi ya ke zaunar dani ya koyamin har sai na gane, sannan bangaren Computer bani da matsala babu abunda bai sani ba na Computer.
Yanzu haka muna hutun karshen Shekara ne in mun koma zamu shiga NCE2.
In muna da karatun Safe tunda Regular na ke yi tare muke fita, ya sama min abun hawa sai na wuce shima ya ke tafiya wajen aikinsa in kuma aka tashi na samu abun hawan da zai kawoni har gida ya na bani ishasshen kudin kudin mota tare da kudin kashewa har ma wani Lokacin in ce masa kudin ya yi yawa hararata kawai ya ke baya cewa komai.
Duk abubuwan da suka faru na Farinciki ne a Rayuwata, Amma ta yi rashin lafiya mun je har gadan mallam Mamman tare da Assadiq ya gaida Amma da Adda, sai dai bai Kwana ba ya Dawo ya barni na kwana Biyu tare da Amma sai dai muka Dawo Tare da su Adda Fati.
Sannan Itama Amma tazo garin Zariya sau daya ta Dubamu kwananta uku a gidan Adda Fati ta sauka.
A zuwan ne ta taramu gabadaya ta yi mana Nasihan mu nemi Dangin Babanmu mu yi zumunci da su in muka ce zamu yanke zumunci Allah bazai kyalemu ba.
Sai muka nuna mata, cewa ai suma basa neman mu sai ta fashemana da kuka da cewa in Aka je Lahira Mahaifin mu ita zai ma kaico tunda bata nuna mana Muhimmancin Ahalinsa ba, ta Horemu da kada mu Damu su basu neme mu ba, mu sani suna da Hakkin zumunci a kan mu kamar yadda mu ma mu ke da shi a kansu Ruwanmu ne in mun ga Dama mu sauke wannan nauyin.
Da wannnan Nasihan nata yasa muka fara zuwa wasu sha'anin na su, ni saboda makaranta ma, ba kasafai na ke shiga ba, tunda Tun farko daman ina da wani bakin fenti da bakowa ke ina Rab'ana ba.
Kuma asabar da Lahadi Tare da Assadiq muke cinyesu a gida da Fita siyon kayan kwalama a kantina kantina Zariya da Suya spots har sun gaji da gane kammanin mu.
Restaurant kuwa sun samu bakin Aljihun Assadiq sai yadda suka yi da shi tunda na Lura shi Namiji ne mai son Fita irin wajejenan tare da matarsa.
A lokacin ya siyamin kayan alfarma kala kala a wajen maman Suhailat da Dogayen Riguna takalma da Hijabai ba na shigar banza sannan duk wanda ya gani yasan ina cikin jin dad'i da kwanciyar Hankali ballatana da duk ya siyamin Dogayen Rigunan na wajen Maryam's Eyptian Abaya masu kyau da yarari.
In na saka su sai na zama kamar balarabiyar kasar Saudiya Saboda Hasken Fata ta da ya karu tunda ina Samun ababen gina jiki, sannan abun mamaki na kara kiba na cika kamar bani bace wannan Hasiyar da kashi duk ya bayyana ajikina ba.
Mun taba zuwa bikin Yaron Baba Tanko wanda yan'uwa da Dama da suka ganni sun yi ta mamakin ganina da Irin sauyin rayuwar da na samu su azaton su ina chan cikin Wulakantciyar Rayuwa ne.
Har Baaba ta Lagos sai da ta yi maganar chanzatawata, Goggon kona kuwa ba kunya ta tambayeni wani miji na ke aure?
Mirmishi nayi ban bata amsa ba, Sai Adda Rukayya ce ta ba su amsa da cewa ma'aikaci ne kuma ya na karatu, nasan suna ta mamakin chanzata tare da mamakin ya aka yi na iya zaman aure kuma wani abu bai samu mijin ba? Tunda har suna tambayan shekara nawa da auran nawa ?
Adda Fati tace shekaru biyu da wani abu.
A fuskarsu sun kasa boye mamakin su, Baba Tanko da ya shigo ya ganni har na gaishesa bai iya gane ni ba sai da ya shiga ciki aka masa bayani sannan ya iya gane ni.
Da ya dawo zai fita kai tsaye ya kalleni ya na fad'in"Hasiya ko ba ke ba ce Hasiya ba?
Ina mirmishi nace ni ce Baba, kai tsaye yace"To to ammh nace bazaki jima ba zaki tafi ba ko?
Nasan abunda ya ke tsoro shi yasa ban Damu ba na gyada masa kai.
Kamar yadda yace ban jima ba na tafi ammh na yi ta sharan hawaye acikin adaidaita.
Duk da haka ba kowa ya ke zama kusa da ni ba sai yan'uwana da suka zame min Dole, ban ga laifin Baba Tanko ba Tunda Har yau Mijin Adda Rukayya in dai ya na gida ban isa na shigar masa gida ba, in kuma na shiga sai dai in baya nan da na Fahimci zuwana na kawo ma yar'uwata matsala.
Rabona da gidan tun wani zuwa da nayi ya tare kofar gida yace bazan shigar masa gida ba, na yi kokarin kada na nuna naji zafi ammh sai da na nuna hakan da na koma gida kuka na fashema Assadiq, shi ya yi ta lallashina ya kara Tusamin yakana da Iklasi acikin zuciyata ya kuma kara Sanar da ni cewa jarabawa ce in na yi wasa da Tauhidi to zan gaza har a wajen Ubangiji.
Da nasihansa da shawarwarinsa yasa yanzu na daina damuwa da ire iren wad'anan kananun abubuwan.
na maida Hankalina wajen karatunaa, ban dauka bayan Ramatu zan kara yin wata kawa ba sai ga shi Shigata kwaleji na had'u da Wata Safiya Ahmad, group d'in mu daya da ita kamar wasa sai ga shi mun saba har mun zama kawaye.
Ita yar anguwan kaya ce sannan ita batayi aure ba, abunda yasa ma muka Saba ita ta fara muna ta na so na da kawa, sannan gata da Hankali da natuwa ga kokari, shiyasa sai na amimta da ita muke kawance da juna.
Tasan ina da aure ta kuma san inda na ke zaune ammh bata san wani Labari a kaina ba.
Assadiq kuma bai taba ganinta ba sai dai yakan ji sunanta a bakina, tunda baya zaman gidan sai weekend, saboda aiki da kuma karatunsa.
Ko matan gidanmu yanzu ba na bi ta kansu kwata kwata duk da yanzu Ummi ce kad'ai Fadila sun tashi ammh kafin ta shin su sai da suka yi Rabuwar uwaka da Ubanka da juna ita da Ummi fad'a har da shigar mazajensu cikin maganar.
Ranar da sukayi tsiyan ina gidan har da Dambe ina gefe ban ko rabasu ba, Maman Sulaihat ce ke raba su fad'an mganace ta tsegumi da kananun maganganu.
Da cewar ita Fadilan Ummi ce taje gari ta na yawo da cewa wai ta na jin ihunta ranar Daren farkonta sannan ta ce kuma ta na jin ihun mijnta in suna kwanciyar aure.
Wani Tudu wani ganganre Fadila taji Labari shine tazo ta tada bala'i daga gani dai ba gaskiya a lamarin Ummi Tunda tace itama Fadila tace mijinta ba shi da karfin mazantaka Tundaga yanayinsa wuyansa kamar marikin lema.
Abu kamar wasa kamar abun Dariya, Sai ga shi sun had'u suna ta Tona ma kansu asiri,da mazajensu kuma daga gani suna zama ne su yi hirar, Dambe suka yi kace kace kamar wasu yara Maman Suhailat na ta ce min nazo mu yi rabo na yi baya, ni ba ma a wannan gidan ba na riga nasan irin wannan abubuwan na gidan Haya Tun zaman mu a garin Samaru.
Su kansu kwanaki chan gidan da muka zauna da naje kwanaki gaisuwa Maman Salihi mahaifiyarta ta rasu Ramatu ta gayamin na biyamata muka ke gidan tare shine zuwa na Farko Tun bayan aurena.
Gidan duk ya watse kaltume ta tashi ita da Maman Boy suma ance fad'a ce ta had'a su kaca kaca abun dai ba dadin ji ballatana gani, shiyasa na kiyayi kaina da mutanen da ke zama a gidan haya sannan na san duka Tarin kalubalen da mata ke Fuskata a zaman gidan Haya.
Bayan Fadila ta tashi an saka wata wata ya'yanta Biyar, Sai Ummi ta koma kamar jaba saboda yadda ta ke Dari dari da mutane ba Halin kuma ni ta Dawomin bayan ta san abunda suka yi min duk da ta so hakan ammh kwata kwata ban bata Fuska ba.
Saboda Sau daya maciji ke saran Mumuni, bazan kara saken da wata zata shiga jikina daga baya kuma ta Tozartani da kaddarata ba.
Yanzu babbar waya ce ke hannuna ta kamfanin Infinix, sai dai har karamar wayar ta na Hannuna ita d'ayan layin ke ciki sai kuma ita ya siyamin Layin Airtel na ke amfani da shi Saboda makaranta sannan na ce masa ina son na Fara kasuwanci kuma ya bani goyon baya ammh yace na bari mu samu jari mai Tsoka Tukunnah.
Ina zaune ne a wani yammancin Alhamis tunda muna Hutun makaranta ina Tunanin wani irin kalubale na taba fuskata a zamana da Assadiq?, Na duba na hango na kasa hango ko d'aya sai wata matsala guda daya da ta fara cin mu tuwo a kwarya.
Abu na Farko shine da gaske ne na Fara Fahimtar Assadiq na Boye min wani abu, duk yadda muka zama Rufin asirin juna bai yarda a kirasa a waya ya yi ta a gabana ba, in dai ya na tare dani to wayarsa ta na kashe ne sai dai ko in ya fita daga gidan sannan yana yin wasu abubuwan marasa gaskiya..
Na fara Fahimtar bai gayama Yan'uwansa na kauye ya aureni ba, Tunda har yau bai taba had'ani da wani na shi ko a waya ba, Sannan na yi nayi har na gaji bai taba kaini garin su ba, daganan sai na fara Fahimtar akwai wani abu Tunda ai ya na zuwa ganinsu akai akai kuma yana kawomin Tsaraba yace Daga kakarsa.
Ammh ya ki amincewa da ya kaini na gansu, har na gaji da tambayoyin su Adda Fati na zauna na Sharara musu karyar cewa ai ya kaini naje na ga Ahalinsa.
In ma na Cigaba da matsamasa sai ya Sauya fuska kwata kwata ya nuna baya son mganar abun na Damuna, kada yazo mu fara tara zuru'a a samu matsala fa, tunda chan kwanaki na fara zargin ko ina da ciki ne ganin wattani uku ban yi batan wata ba ina Shirin yi masa mganar sai kuma naga Period dina daga kuma watan bai karamin Tsallake ba sai na watsar da Zargin cewa ina da Shigar ciki ne.
A yanzu haka ko wata Daya Assadiq bai cika da Samun wani aiki a garin Abuja ba, ya tafi Sati uku bai zo gida ba mun yi mgana da shi yace min sai yagama sanin kan wajen gabadaya ko zai fara zuwa min weekend sai da ya barmin komai na kayan abinci da Ishaahen kud'i a Hannuna ko da wata bukatar ta taso.
Sannan ya siya mota duk dai ba wata babba bace, Assadiq ya mallaki yar karamar motar hawa tun kafin ya samu wannan aikin na garin Abuja.
Yadda abun ke damuna a raina yasa na kasa sukuni ga shi na yi karya ba Halin na samu Ramatu ko Adda Fati mu Tattauna.
Ammh tabbas jikina ya bani akwai wani matsalan! Kuma ina da kyakyawan zato akan cewa yan'uwan Assadiq ba su san da ni a matsayin matarsa ba.
********
*GUSAU.*
Asabar, 12:10pm.
A gidan Alhaji Sulaiman Shinkafi a tsakiyar Falon Innani ne mata baje ana ta Bude wasu kayan alfarma acikin wasu Rantsatsun akwatina.
Masu kawo kayan auren Mubarak ne daga Kaduna Yan'uwan Hajiya Murjanatu sai wasu daga cikin Dangin Alhaji Jibril daga Zariya.
Innani na gefe da katon gilashinta sai faman washe baki ta ke yi ita da su Umma da Mama sai yan'uwan Mama da suma suna wajen.
Sai kuma yan'uwan Saliman duka matan masu aure a garin suna wajen yan nesa ne ba su riga sun zo ba sun ce sai ana biki saura Sati daya zasu Fara sauka a garin.
Yau ya rage saura sati Hudu Bikin Mubarak da Salima, shine suka kawo kayan aure akwatuna Shidda da ghana cike da kaya sai son barka.
An yi musu abinci jallop rice da Chicken sai lemuka na kwali da wanda su Surayya suka had'a musu na kayan Itatuwa.
Sauran kayan su Sanks kuma da za'a ba su su tashi da shi ya na chan gidan Surayya sun had'u da ita Amaryan tare da Siyama da Sultana sai Sajida da Saddiqa suka je suna kama musu sauran kuma suna gidan Abba da su aka tarbi maso kawo kayan auren.
An gama Bud'e kayan an saka albarka Gabadaya sun ba da kudin Dinki Dubu Dari, Umma kuma ta maida musu Dubu Hamsun na Tukwaicin su.
Nan suka Rantse ba za su karb'a ba Umma kuma tace sai sun karb'a suma kudin yabawa ce suka ba su.
Falon dai na Innani ya yi albarka sai Hira ake da Shewa su Sa'ima na ta Daukan Video kayan Suna Rangad'a guda.
Innani dai yau ba Masifa sai washe baki ta ke yi Allah ya kusa cika mata Burinta saura na Magajin gida da Sulsana Shikenan bayan ta gama ganin ya'yan su sai ta mutu daga baya.
Baki na shirin tafiya bayan sun ci abinci sun yi salloli sai suka fara Haraman Tafiya.
Umma taja Surraya gefe ta na fadin"Wai ina su Sultana ne? Shuru har yanzu basu kawo ba kada a yi aikin banza naga suna shirin tafiya ne."
Surayya ta Dauko wayarta Cikin Aljihun Doguwar rigar da ke
Showing 75001 words to 78000 words out of 98628 words
Ni na samu barci ammh shi ya kasa sai Tunane Tunane ya ke yi.
Salama da natsuwa yake ji suna Shigarsa duk da farko shed'an ya so ya yi masa wasa da kyakyawan niyarsa.
Shed'an na fad'a masa ta yi aure aure wasu sun rigasa sanin inda ya ke son sani yanzu.
Ammh tunda ya kasance a wajen ya ji ya daina wani kokwanto Hasiya ta zama shi, shima kuma ya zama ita na Har Gaban Abada.
Itace mace ta farko da ta nemi Sauya rayuwarsa, kuma ta yi nasara sannan itace mscen da ta san sirrinsa a yadda ya Sameta shi dai dari bisa Dari ta yi masa bai san ko in ya sake wani auran zai ji makin da ya bata ya ragu ba.
Tun daga ranar Assadiq ya Bud'e anarcinsa ba kama hannun yaro.
Wata irin rayuwa muke gudawar ta soyayya da kauna mai Tsayawa a zuciyar Masoya.
Assadiq ya zama nawa nima na zama na shi ya maidani yar gata acikin mata kuma ya sa na fara Tunanin na yi ma Sauran mata zarra.
"Hasiya zan kula da ke, zan zama bangon ki mai kare ki da dukan wani abun da zai kawo miki kunci ko Damuwa."
Kalamansa kenan koda yaushe kuma na aminta da shi, Domin komai na Muradin ya'a mace Assadiq na yi min shi.
Na kara kiba kularwar Assadiq yasa na bude har raman wuyana ya fara cikewa haka Ramatu ta rika fad'i Lokacin da tazo wajena.
Adda Fati ta fi kowa farinciki ganin na samu kwanciyar Hankali Amma ma Dagachan bangaran ta na sanin Labarina Hankalinta ya kwanta.
Adda Rukayya ma da tazo ta ganni sai da ta yi mamaki, saboda ni kaina nasan na sauya kamar ba wanchan Hasiyar ba.
Yanzu ko su Ummi basa gabana Soyayyar Mijina ta isheni komai Tunda bai taba barina na yi kuka ba.
Suma sun kula da haka sai suka shiga Taitayinsu.
gwarama Maman Sulaihat muna shiri da ita tunda ita bata kyamaceni ba.
*Janafty*
*TMWBK2017*
*TMW is a paid Novel, Pay 500 for regular or VIP N1K, Via 0552179550 Jamila Umar Gt bank, 09069067488*
Haba Babyn Habiby ya zaki zauna kina ta fama cutar infection, ke ce rashin sha’awa, ke ce jin zafi yayin tarayya, ke xche d’aukewar ni’ima, ke ce kai’kayi ki fitar farin ruwa da sauransu, an yi maganin asibiti da na gargajiya amma duka dai, tau share hawayenki ‘karshen matsalarki ta zo, da Honeydrops infection flusher ko cleanser pro sai kin yi dariya da godiya don zai wanke miki duk wata cutar sanyi. Akwai original sabaya ta gyaran breast su cicciko kamar baki shayar ba, akwai ta hips da mazaunai ki yi ma sha Allah ki samu kaya kema su miki d’as ki bar yawo da doguwar riga.
Na ce ba a nan muka tsaya ba muna da hadaddun kaya irinsu sweeteners, tighteners and wetners na tashin kan oga, wanda zai miki tukwicin dole, ke ko kurma ne sai ya yi magana ranar, don sumbatu ki dai samu abun rufe mai baki gudun ma’kota. Muna nan a garin Sokoto muna aike kowani gari kowacce kasa cikin aminci da rahusa. Kuna iya danna link din nan domin yi mana magana Kai tsaye https://Wa.me/2348167888934 ko kuma a kira 08167888934. Sai mun ji daga gareku isassun mata.
*Bayan Shekara D'aya da Rabi.*
ALHAMDULILLAH kawai zan ce acikin Shud'ewar Shekara d'aya da Rabi, wanda ya yi daidai da shekaru Biyu da wasu wattani da aurena da Assadiq.
A zuwa wannan lokacin ni Hasiya Mamman kona na riga nasan Ubangiji ya gama yi mini dukkan wani gata anan Duniya.
Ya bani rai da lafiya sannan ya bani kwanciyar hankali natsuwa da cikar Zatin aure a tare dani, sannan ya Turomin Namiji tamkar da Dubu ASSADIQ wanda ya kasance wani Kafad'a da na kan saukar da kaina a samanta cikin kuka ko Dariya.
In Dariya ne shi zai tayani mu Dara in kuma abun kuka ne shi zai taimakamin ya Sharemin hawayena.
Zaman aure daman hausawa sun ce zo mu zauna ne sannan kuma sunce zo mu sab'a ne.
Bazan ce ina cikin Farinciki dari bisa Dari ba akwai kananun matsalolin da ba su kai ma a fad'e su ba.
Assadiq ya gama min koma a wannan Duniyan Tunda ya tsamo ni daga cikin kuntattaciyar Rayuwar da ni ke ciki ya raya zuciyata da abun kawa da Soyayya ya kuma nuna min nima kamar sauran mutane na ke wanda Ubangiji ya Hallice su tare da Tarin Ni'imominsa.
Assadiq ya yi sanadiyar da na manta da Rayuwata ta baya gabadaya, na Fuskanci Farincikin da ke tare da Rayuwata yanzu Assadiq na sona sannan yana son Farincikina kuma Bukatuna daidai misali in bai fi karfinsa ba yana cika mun su.
Ya maidani yar gata sannan yar lele wacce na zarce duka yayyena sa'ar miji da gidan aure.
A wanchan Shekaran ne ya sakani na Zana Jamb daman SSCE na ta yi kyau bani da matsala duk da ya lura karatun bai wani Dameni ba ammh bai Damu ba ya zaunar da ni ya nunamin Muhimmanci ilimin ya'ya mata a wannan Rayuwar.
Da taimakon kalaman karfin gwiwansa da Aljihunsa da kokarinsa na Fara karatu a Federal Collage of Education da ke zariya, da kuma Amincewarsa ko nace zabinsa na fara karatu a kolejin a shashen Biology Computer.
Da Farko ina ganin wahalan karatun ammh kuma Jajircewan Assadiq yasa na fara jin dad'in kasancewata cikin Daliban kalejin ta zariya mai Dauke da Dalibai mabambamta daga garuruwa a fad'in kasar nan.
Duk abunda ban gane ba shi ya ke zaunar dani ya koyamin har sai na gane, sannan bangaren Computer bani da matsala babu abunda bai sani ba na Computer.
Yanzu haka muna hutun karshen Shekara ne in mun koma zamu shiga NCE2.
In muna da karatun Safe tunda Regular na ke yi tare muke fita, ya sama min abun hawa sai na wuce shima ya ke tafiya wajen aikinsa in kuma aka tashi na samu abun hawan da zai kawoni har gida ya na bani ishasshen kudin kudin mota tare da kudin kashewa har ma wani Lokacin in ce masa kudin ya yi yawa hararata kawai ya ke baya cewa komai.
Duk abubuwan da suka faru na Farinciki ne a Rayuwata, Amma ta yi rashin lafiya mun je har gadan mallam Mamman tare da Assadiq ya gaida Amma da Adda, sai dai bai Kwana ba ya Dawo ya barni na kwana Biyu tare da Amma sai dai muka Dawo Tare da su Adda Fati.
Sannan Itama Amma tazo garin Zariya sau daya ta Dubamu kwananta uku a gidan Adda Fati ta sauka.
A zuwan ne ta taramu gabadaya ta yi mana Nasihan mu nemi Dangin Babanmu mu yi zumunci da su in muka ce zamu yanke zumunci Allah bazai kyalemu ba.
Sai muka nuna mata, cewa ai suma basa neman mu sai ta fashemana da kuka da cewa in Aka je Lahira Mahaifin mu ita zai ma kaico tunda bata nuna mana Muhimmancin Ahalinsa ba, ta Horemu da kada mu Damu su basu neme mu ba, mu sani suna da Hakkin zumunci a kan mu kamar yadda mu ma mu ke da shi a kansu Ruwanmu ne in mun ga Dama mu sauke wannan nauyin.
Da wannnan Nasihan nata yasa muka fara zuwa wasu sha'anin na su, ni saboda makaranta ma, ba kasafai na ke shiga ba, tunda Tun farko daman ina da wani bakin fenti da bakowa ke ina Rab'ana ba.
Kuma asabar da Lahadi Tare da Assadiq muke cinyesu a gida da Fita siyon kayan kwalama a kantina kantina Zariya da Suya spots har sun gaji da gane kammanin mu.
Restaurant kuwa sun samu bakin Aljihun Assadiq sai yadda suka yi da shi tunda na Lura shi Namiji ne mai son Fita irin wajejenan tare da matarsa.
A lokacin ya siyamin kayan alfarma kala kala a wajen maman Suhailat da Dogayen Riguna takalma da Hijabai ba na shigar banza sannan duk wanda ya gani yasan ina cikin jin dad'i da kwanciyar Hankali ballatana da duk ya siyamin Dogayen Rigunan na wajen Maryam's Eyptian Abaya masu kyau da yarari.
In na saka su sai na zama kamar balarabiyar kasar Saudiya Saboda Hasken Fata ta da ya karu tunda ina Samun ababen gina jiki, sannan abun mamaki na kara kiba na cika kamar bani bace wannan Hasiyar da kashi duk ya bayyana ajikina ba.
Mun taba zuwa bikin Yaron Baba Tanko wanda yan'uwa da Dama da suka ganni sun yi ta mamakin ganina da Irin sauyin rayuwar da na samu su azaton su ina chan cikin Wulakantciyar Rayuwa ne.
Har Baaba ta Lagos sai da ta yi maganar chanzatawata, Goggon kona kuwa ba kunya ta tambayeni wani miji na ke aure?
Mirmishi nayi ban bata amsa ba, Sai Adda Rukayya ce ta ba su amsa da cewa ma'aikaci ne kuma ya na karatu, nasan suna ta mamakin chanzata tare da mamakin ya aka yi na iya zaman aure kuma wani abu bai samu mijin ba? Tunda har suna tambayan shekara nawa da auran nawa ?
Adda Fati tace shekaru biyu da wani abu.
A fuskarsu sun kasa boye mamakin su, Baba Tanko da ya shigo ya ganni har na gaishesa bai iya gane ni ba sai da ya shiga ciki aka masa bayani sannan ya iya gane ni.
Da ya dawo zai fita kai tsaye ya kalleni ya na fad'in"Hasiya ko ba ke ba ce Hasiya ba?
Ina mirmishi nace ni ce Baba, kai tsaye yace"To to ammh nace bazaki jima ba zaki tafi ba ko?
Nasan abunda ya ke tsoro shi yasa ban Damu ba na gyada masa kai.
Kamar yadda yace ban jima ba na tafi ammh na yi ta sharan hawaye acikin adaidaita.
Duk da haka ba kowa ya ke zama kusa da ni ba sai yan'uwana da suka zame min Dole, ban ga laifin Baba Tanko ba Tunda Har yau Mijin Adda Rukayya in dai ya na gida ban isa na shigar masa gida ba, in kuma na shiga sai dai in baya nan da na Fahimci zuwana na kawo ma yar'uwata matsala.
Rabona da gidan tun wani zuwa da nayi ya tare kofar gida yace bazan shigar masa gida ba, na yi kokarin kada na nuna naji zafi ammh sai da na nuna hakan da na koma gida kuka na fashema Assadiq, shi ya yi ta lallashina ya kara Tusamin yakana da Iklasi acikin zuciyata ya kuma kara Sanar da ni cewa jarabawa ce in na yi wasa da Tauhidi to zan gaza har a wajen Ubangiji.
Da nasihansa da shawarwarinsa yasa yanzu na daina damuwa da ire iren wad'anan kananun abubuwan.
na maida Hankalina wajen karatunaa, ban dauka bayan Ramatu zan kara yin wata kawa ba sai ga shi Shigata kwaleji na had'u da Wata Safiya Ahmad, group d'in mu daya da ita kamar wasa sai ga shi mun saba har mun zama kawaye.
Ita yar anguwan kaya ce sannan ita batayi aure ba, abunda yasa ma muka Saba ita ta fara muna ta na so na da kawa, sannan gata da Hankali da natuwa ga kokari, shiyasa sai na amimta da ita muke kawance da juna.
Tasan ina da aure ta kuma san inda na ke zaune ammh bata san wani Labari a kaina ba.
Assadiq kuma bai taba ganinta ba sai dai yakan ji sunanta a bakina, tunda baya zaman gidan sai weekend, saboda aiki da kuma karatunsa.
Ko matan gidanmu yanzu ba na bi ta kansu kwata kwata duk da yanzu Ummi ce kad'ai Fadila sun tashi ammh kafin ta shin su sai da suka yi Rabuwar uwaka da Ubanka da juna ita da Ummi fad'a har da shigar mazajensu cikin maganar.
Ranar da sukayi tsiyan ina gidan har da Dambe ina gefe ban ko rabasu ba, Maman Sulaihat ce ke raba su fad'an mganace ta tsegumi da kananun maganganu.
Da cewar ita Fadilan Ummi ce taje gari ta na yawo da cewa wai ta na jin ihunta ranar Daren farkonta sannan ta ce kuma ta na jin ihun mijnta in suna kwanciyar aure.
Wani Tudu wani ganganre Fadila taji Labari shine tazo ta tada bala'i daga gani dai ba gaskiya a lamarin Ummi Tunda tace itama Fadila tace mijinta ba shi da karfin mazantaka Tundaga yanayinsa wuyansa kamar marikin lema.
Abu kamar wasa kamar abun Dariya, Sai ga shi sun had'u suna ta Tona ma kansu asiri,da mazajensu kuma daga gani suna zama ne su yi hirar, Dambe suka yi kace kace kamar wasu yara Maman Suhailat na ta ce min nazo mu yi rabo na yi baya, ni ba ma a wannan gidan ba na riga nasan irin wannan abubuwan na gidan Haya Tun zaman mu a garin Samaru.
Su kansu kwanaki chan gidan da muka zauna da naje kwanaki gaisuwa Maman Salihi mahaifiyarta ta rasu Ramatu ta gayamin na biyamata muka ke gidan tare shine zuwa na Farko Tun bayan aurena.
Gidan duk ya watse kaltume ta tashi ita da Maman Boy suma ance fad'a ce ta had'a su kaca kaca abun dai ba dadin ji ballatana gani, shiyasa na kiyayi kaina da mutanen da ke zama a gidan haya sannan na san duka Tarin kalubalen da mata ke Fuskata a zaman gidan Haya.
Bayan Fadila ta tashi an saka wata wata ya'yanta Biyar, Sai Ummi ta koma kamar jaba saboda yadda ta ke Dari dari da mutane ba Halin kuma ni ta Dawomin bayan ta san abunda suka yi min duk da ta so hakan ammh kwata kwata ban bata Fuska ba.
Saboda Sau daya maciji ke saran Mumuni, bazan kara saken da wata zata shiga jikina daga baya kuma ta Tozartani da kaddarata ba.
Yanzu babbar waya ce ke hannuna ta kamfanin Infinix, sai dai har karamar wayar ta na Hannuna ita d'ayan layin ke ciki sai kuma ita ya siyamin Layin Airtel na ke amfani da shi Saboda makaranta sannan na ce masa ina son na Fara kasuwanci kuma ya bani goyon baya ammh yace na bari mu samu jari mai Tsoka Tukunnah.
Ina zaune ne a wani yammancin Alhamis tunda muna Hutun makaranta ina Tunanin wani irin kalubale na taba fuskata a zamana da Assadiq?, Na duba na hango na kasa hango ko d'aya sai wata matsala guda daya da ta fara cin mu tuwo a kwarya.
Abu na Farko shine da gaske ne na Fara Fahimtar Assadiq na Boye min wani abu, duk yadda muka zama Rufin asirin juna bai yarda a kirasa a waya ya yi ta a gabana ba, in dai ya na tare dani to wayarsa ta na kashe ne sai dai ko in ya fita daga gidan sannan yana yin wasu abubuwan marasa gaskiya..
Na fara Fahimtar bai gayama Yan'uwansa na kauye ya aureni ba, Tunda har yau bai taba had'ani da wani na shi ko a waya ba, Sannan na yi nayi har na gaji bai taba kaini garin su ba, daganan sai na fara Fahimtar akwai wani abu Tunda ai ya na zuwa ganinsu akai akai kuma yana kawomin Tsaraba yace Daga kakarsa.
Ammh ya ki amincewa da ya kaini na gansu, har na gaji da tambayoyin su Adda Fati na zauna na Sharara musu karyar cewa ai ya kaini naje na ga Ahalinsa.
In ma na Cigaba da matsamasa sai ya Sauya fuska kwata kwata ya nuna baya son mganar abun na Damuna, kada yazo mu fara tara zuru'a a samu matsala fa, tunda chan kwanaki na fara zargin ko ina da ciki ne ganin wattani uku ban yi batan wata ba ina Shirin yi masa mganar sai kuma naga Period dina daga kuma watan bai karamin Tsallake ba sai na watsar da Zargin cewa ina da Shigar ciki ne.
A yanzu haka ko wata Daya Assadiq bai cika da Samun wani aiki a garin Abuja ba, ya tafi Sati uku bai zo gida ba mun yi mgana da shi yace min sai yagama sanin kan wajen gabadaya ko zai fara zuwa min weekend sai da ya barmin komai na kayan abinci da Ishaahen kud'i a Hannuna ko da wata bukatar ta taso.
Sannan ya siya mota duk dai ba wata babba bace, Assadiq ya mallaki yar karamar motar hawa tun kafin ya samu wannan aikin na garin Abuja.
Yadda abun ke damuna a raina yasa na kasa sukuni ga shi na yi karya ba Halin na samu Ramatu ko Adda Fati mu Tattauna.
Ammh tabbas jikina ya bani akwai wani matsalan! Kuma ina da kyakyawan zato akan cewa yan'uwan Assadiq ba su san da ni a matsayin matarsa ba.
********
*GUSAU.*
Asabar, 12:10pm.
A gidan Alhaji Sulaiman Shinkafi a tsakiyar Falon Innani ne mata baje ana ta Bude wasu kayan alfarma acikin wasu Rantsatsun akwatina.
Masu kawo kayan auren Mubarak ne daga Kaduna Yan'uwan Hajiya Murjanatu sai wasu daga cikin Dangin Alhaji Jibril daga Zariya.
Innani na gefe da katon gilashinta sai faman washe baki ta ke yi ita da su Umma da Mama sai yan'uwan Mama da suma suna wajen.
Sai kuma yan'uwan Saliman duka matan masu aure a garin suna wajen yan nesa ne ba su riga sun zo ba sun ce sai ana biki saura Sati daya zasu Fara sauka a garin.
Yau ya rage saura sati Hudu Bikin Mubarak da Salima, shine suka kawo kayan aure akwatuna Shidda da ghana cike da kaya sai son barka.
An yi musu abinci jallop rice da Chicken sai lemuka na kwali da wanda su Surayya suka had'a musu na kayan Itatuwa.
Sauran kayan su Sanks kuma da za'a ba su su tashi da shi ya na chan gidan Surayya sun had'u da ita Amaryan tare da Siyama da Sultana sai Sajida da Saddiqa suka je suna kama musu sauran kuma suna gidan Abba da su aka tarbi maso kawo kayan auren.
An gama Bud'e kayan an saka albarka Gabadaya sun ba da kudin Dinki Dubu Dari, Umma kuma ta maida musu Dubu Hamsun na Tukwaicin su.
Nan suka Rantse ba za su karb'a ba Umma kuma tace sai sun karb'a suma kudin yabawa ce suka ba su.
Falon dai na Innani ya yi albarka sai Hira ake da Shewa su Sa'ima na ta Daukan Video kayan Suna Rangad'a guda.
Innani dai yau ba Masifa sai washe baki ta ke yi Allah ya kusa cika mata Burinta saura na Magajin gida da Sulsana Shikenan bayan ta gama ganin ya'yan su sai ta mutu daga baya.
Baki na shirin tafiya bayan sun ci abinci sun yi salloli sai suka fara Haraman Tafiya.
Umma taja Surraya gefe ta na fadin"Wai ina su Sultana ne? Shuru har yanzu basu kawo ba kada a yi aikin banza naga suna shirin tafiya ne."
Surayya ta Dauko wayarta Cikin Aljihun Doguwar rigar da ke
Book Chapters
Chapter 1Chapter 2Chapter 3Chapter 4Chapter 5Chapter 6Chapter 7Chapter 8Chapter 9Chapter 10Chapter 11Chapter 12Chapter 13Chapter 14Chapter 15Chapter 16Chapter 17Chapter 18Chapter 19Chapter 20Chapter 21Chapter 22Chapter 23Chapter 24Chapter 25Chapter 26 Chapter 27Chapter 28Chapter 29Chapter 30Chapter 31Chapter 32Chapter 33