ya'yan dan'uwansu da ya rasu da yarinyar da akace ta na da Farar kafa sai ta manta Tunda dai ita bata kara jin Labarin su ba.
Abun na ranta ya na dawowa da Daddare bayan ta Shiga masa sannu da zuwa ta kai masa ruwa.
Ta na zaune gefensa ta ce"Maganar auran Murabak din yanzu ne?
Ya na gyad'a kai yace"In dai suka Fahinci juna me zamu jira?
Hajiya Murjanatu tace"Hakane to Allah ya tabbatar mana da alheri su waye zasu nemam auran?
Kai Tsaye yace"Alhaji Tanko da Saminu mana ina da wasu yan'uwan da suka fi su ne?
Mirmiahi ta yi kafin tace"Baka da shi kam tunda duk sun rasu, ya ma sunan wannan wanda ya taba rasuwa kace min Ya haifi wata yarinya mai Farar kafa sai da ta talauta shi kuma sannan ta yi Sanadiyar Mutuwarsa?
Sai da ya sha ruwa Sosai sannan ya mikamata kofin ya na fadin"Mamman kenan ki ke mgana."
Da Sauri tace"Yauwa shi, wai ina Labarin iyalansa da matarsa?
Alhaji Jibril ya tabe baki kafin yace"Ina zan sani? ni dai chan kwanaki naji Alhaji Tanko na mganar yarinyar ta sake wani aure kuma wai ko uwar tasu ta koma garin su."
Hajiya Murjanatu tace"Ina ne garin na su?
Cikin karamin tsaki yace"Bafullatanan Ruga ce na manta sunan garin, yaran kamar su hudu ne ina ji sauran biyun sun yi aure ita mai Farar kafar ce akace auranta uku duk wanda ta aura sai ta talauta shi wani ma an ce dakyar ya rayu."
Cikin Tsausayi tace"Allah Sarki ku ma da laifin ku ai hakkin ku ne ku Kula da su bayan kasa ta Rufe idanuwansa."
Cikin zaro ido ya kalleta kafin yace"Uban waye zai Daukan ma kansa masifa ? Ko Tanko da suke uwa da Ubansu bai Daukan ma kansa ba ballatana wani, ke ana gayamiki yarinyar sai a Hankali kina wata mganar ta Dabam"
Hajiya Murjanatu tace"ammh ai babu wata Farar kafa a addini Abban zahra Canfi ne da rashin Tauhidi."
Kallonta ya yi daga sama har kasa kafin ya tabe baki.
Zata kara mgana ya Daga mata hannu Lokaci d'aya ya na mikewa ya shige ciki ya barta nan zaune.
Da kallo ta bisa kafin ta Sauke Numfaahi.
A cikin ranta sai taji Tausayin wannan Yarinyar Allah kad'ai yasan Halin Tsaka mai wuyar da ta ke Fuskanta a wajen Mutane.
Abu kamar wasa sai ga shi ya Tabbata acikin watan waliyan Mubarak suka je har Gusau gidan Alhaji Sulaiman suka yi ma Mubarak Tambayan aure.
Su Baba Sammani suka ba su Salima a matsayim mata.
Sai dai ba'a tsaida Lokaci ba tunda Mubarak na gini sai aka saka nan da Shekara daya da Rabi kafin na Sultana da Sadiq kenan.
Alhaji Jibril ya fi kowa jin dadin wannan Labarin bakinsa har kunne ko Mubarak albarka.
Alhaji Tanko da suka Dawo nan kaduna gidan Alhaji Jibril fadi ya ke yi"Jibo ina ka had'u da wannan Ahalin ma su kudi haka?
Alhaji jibril ya yi dariya kawai bai ce komai ba. shi ko Saminu fad'i ya ke yi" ni dai ko akwai kanwarta sai Nasiru Shima ya nema."
Alhaji Jibril ya yi dariya kafin yace"Shege saminu har yanzu baka Daina son abun duniya ba ko?
Shima ya na dariya yace"Yaya kaima fa na sanka baka kwai sai da Zakara."
Dariya ya Bushe da shi kafin yace"Ka sanni sosai Saminu."
Suna wannan Hiran ne a falon Alhaji Jibril bayan sun dawo daga Gusai da labarin irin sha tara na arzikin da aka yi musu a chan.
Su ko sauran yan'uwan Salima mata yan Dakin Umma da suka ji Labari sai sukace meyasa ba'a hade da na Sadiq da Sultana ba? Umma tace itama sai da ta yi wannan tunanin ammh ganin kamar Mama ta fi son a fara yin na Salimar Shiyasa bata ce komai ba.
Suma tace su bi mganar da Fatan alheri kada su furta komai.
Innani ko sai shiri ta ke ta na Murna zata aurar da jikoki uku alokaci d'aya ba ta ga ta zama ba.
Duk abunda ta samu sai ta boye tace na Hidimar Bikin Magajin gida da Sultana ne, Sai kuma Salima tace masu kid'an kwarya har bakin get sai sun cika gida. su san ranta ya kai na ganin auran jikokinta.
Ba ma wanda ya zauna da ita ballatana ya sanar da ita ba Rana daya za'ayi auran ba.

*******

*Bayan wata biyu.*

Wata biyun da ya yi daidai da wajen wata hud'u da Tafiyar Sadiq Zariya.
Yaje dai Gusai sau daya ya kwana Biyu sannan a wannan zuwan sun yi tad'i da Sultana a bangaren Innani.
Duk saboda kauda Tunanin su Umma kan Boyayyiyar Rayuwarsa kuma ya yi nasaran haka.
A lokacin ita da Siyama suna jarabawar shiga SS2 ne.
Ko ba'a fada maka ba in ka ga Sultana zaka san ta kara girma da wayau.
Kuma ta na ji kanta ita watace Tunda ta na da Miji a hannunta irin Sadiq.
Salima kuma Tuni ban so ban so ya kare soyayya ta mika tsakaninta da Mubarak da ta ke kira Habibina.
A sannu sannu kuma suna ta shirin su Tunda har Mutanen shinkafi sun san da mganar auran.
Innani ta matsa sai da Abba ya Kira Mallan Shitu ya sanar da shi komai kan mganar auran Sultanan.
A cewarta kada ya je ya kwanta ya ki yin komai gwara dai yasan an yi masa kokari.
Zuwan da Sadiq zai yi Hasiya ta saka ayi masa awara tunda karya ya yi mata da cewa zai je gaida Matan ubangidansa da ya yi aiki a karkarshinsa sannan yace zai biya kauye ya gaishe da su.
Da tace masa zataje kai Tsaye yace mata ba yanzu ba.
Sai bata matsa masa ba sanin Halinsa baya son gaddama.
Ramatu ta kira tana gayamata zai je garinsu me zata ba shi ya kai ma kakarsa.?
Sai tace zata yi mata awara zata kira Habiba sai tazo ta karba ta kai mata.
Aiko ta yi awara mai kwai ta saka a wata Roba ta yi siling dinsa.
Habiba ta kira tazo ta Dauka ta kaima Hasiya.
Sannan ta kira tace ta had'o da Turare ta hada ma Kakar tashi da shi.
Shi dai ya tashi tafiya ne ta ba shi abu a leda tace kada ya Bude sai ya isa garin.
Kuma haka akayi sai da yazo ya Bude da takardan da ta Rubuta na Kaka ne.
Assadiq yaji matukar dad i kuma ya saka aransa zai kaima Innani.
Kuma haka akayi ita ya kai mawa yace daga wata yarinya ce mai kirki abokiyar aikinsa da ya ke yawan bata Labarinta.
Innani ta hau washe baki ta na ta saka albarka har ta na tambayansa matar aure ce? Ya na mirmishi yace"Eh sosai ma."
Nan Innani ta fara addu'a da Fatan zaman lafiya da zuru'a dayyiba.
Shi kuma ya amsa mata da Ameen.
To chan Shashen Umma yaga Roban wajen su Umma suna ta santi Innani kadan ta sam musu tace a saka mata a Firiza in kuma wata taci Allah ya isa.
Da zai koma d'an kunnen mai Tsada ya siyama Hasiya a matsayin tukwaici shima Dan kunnen wajen Anty Sa'ima  ya siya Tunda ta na saida su.
Sai ya siya biyu daya na Hasiya daya na Sultana.
Ammh sai ce musu dayar na abokiyar aikinsa ce data aiko ma da Innani da awara da Turare.
Har Umma na fadin hakan ya yi daidai, har ta had'a mata da Sabon Hijabi tace ya kai mata..
Bata san Surukarta ta aikamawa ba har Umma na tambayansa sunanta yace"ASIYA.!"
umma tace Allah ya yi mata albarka.
Da ya koma ya kaima Hasiya yace in ji kakarsa ta yi ta murna ta na Tsalle ya na yi mata Dariya.
Baisan addu'an Innani ta karb'u  na Allah ya ba su zuru'a Dayyiba bq sai da yaji matsuwar kasancewa da Hasiya.
Sannan kuma ya fahimci son Hasiya ya ke yi soyayyar da ta sa ya fara fad'a da Ahalinsa saboda ita.
Kuma ya Fahimci ya yi nisa da bayajin kiran kowa a wannan Lokaci shi dai Burinsa ya kasance tare da Hasiya.
Tunda ya Dawo ba shi da Sukuni gashi ya sabar mata in dai ya na gida ta na tare da shi.
Ya rasa mafita ya duba kuma ya Hango sai yaga ai cutar da kansa ya ke yi. Hasiya matarsa ce ba laifi in ya ji Dadi da ita ko ya samu natsuwa da ita.
Sai ya fara Romances da ni domin deb'e kewa akai akai ammh duk a banza kamar ma ya taso ma abun ne ko da yaushe da Ciwon mara ya ke kwana.
Sai kawai ya zauna ya yanke wani Tunani da shawara.
In dai zai yi Tunanin fara kasancewa Tare da Hasiya to ya zama Dole ya zama mai adalci a gareta.
Kuma in dai zai yi mata adalci sai dai ya zauna tare da ita har  na abada.
Kuma Faruwan hakan daidai ya ke da Fallasa abunda ya Boye.
Ammh kuma in zai iya yin haka ya na da wata mafita guda d'aya.
Duk da mafitan ta wani bangaren akwai Cutuwa ta bangaran Hasiya.
Ammh kuma ba shi da zabi ne.
Wannan mafitar ita kad'ai ce ta Rage masa kuma ya na Tunanin zai yi amfani da ita.
A fili ya Furta "Am sorry HASIYA bani da Sauran zabi ne."




*Janafty*
*TMWBK2016*

*TMW is a paid Novel, Pay 500 for regular or VIP N1K, Via 0552179550 Jamila Umar Gt bank, 09069067488*

https://chat.whatsapp.com/CPRnRPcAD5K8vEY91Ziz8V

*LAME NIG!*

*KASAITATTUN MATA MUN GAISHE KU*.
*AISHA LAME TA KAWO MUKU DUKKAN NAU'IN KAYAN KWALLIYA*.
*KUNSAN GWANAACE WAJEN BAWA FATA HAKKIN TA*
*KUN TUNA KYUAN FATAR GUDUYO KO?*
*KUN TUNA DAI YADDA BULKACHUWA KE SIYAWA YABI KAYAN KWALLIYA NA ORIFLAME KO?*
*TO KEMA GARZAYO KI ZABI NA KI, KO TA ZABA MIKI WANDA ZAI FI DACEWA DA FATARKI*.
*BA IYA KAYAN ORIFLAME BA KAD'AI.*
*TANA DA PRODUCTS DABAN DABAN MASU KYAU, MASU MASTAKAITAN FARASHI*.
*KU TUNTUBE JIKAR DADAR MARINA A WANNAN LAMBAR 07036662633*.
*ADO DA KAMSHI NE SIRRIN GAYU*

Gabad'aya acikin satin nan sukuku ya ke, gani ya ke kamar abunda ya ke shirin aikatawa ba mai kyau ba ne. Kamar kuma ya so kansa da yawa.
Sai dai Kuma ba shi da wata mafita ne tunda shima ya shiga tsaka mai wuya ne, wanda fitarsa wani mawuyacin Hali ne ba shi da mafita ne ballatana zabi Shiyasa ya zabi abunda ya ke ganin shine daidai matukar ya na son kasancewa tare da Hasiya.
Sai ya so kamar ya yi mata mgana sai ya kasa gabadaya ba shi da sukuni Gulty din abunda zai aikata ya fara Damunsa Tun kafin ya aikata.
Da ya so ya Hakura ammh kuma sai ya ke jin hakan kamar daidai ya ke da Rabashi da Numfashinsa Ya fara Son Hasiya tun ranar da ya fara ganinta tana rokonsa ya taimakama mahaifiyarta bai sani ba sai yanzu ya Fahimci haka.
Matukar kuma ya na son kasancewa taee da ita sai ya bi hanyar da ya ke ganin ita ta dace, yasan ko a gaba Hasiya bazata Tsane shi ba Tunda komai zai aikata koma ya aikata Saboda Farincikinta ne.

*****

Na dad'e da Lura da Assadiq ba shi da walwala acikin kwanakin nan, Saboda ya rage hira da bani Labarai sannan wasu abubuwan da muke kafin mu kwanta da Daddare irin su kallo ko fita yawo duk ya daina sannan Rikenin da ya ke yi a jikinsa shima ya daina ballatana wasannin da ya sabar min kamar dai ya na jan baya dani ne.
Kuma na tambayesa ko wani abu na yi masa? sai yace bakomai gajiyan aiki ne kawai.
Yau jumma'a ne da La'asar ya ke dawowa daga wajen aikinsa, tun bayan da na idar da sallah na fito Falon ina Dakon jiransa kamar yadda na Saba na tuna da Safe kafin ya fita yace na shirya in ya dawo zamu fita ina ta Murna a zatona wajen cin abinci zamu je ko kuna wayon zaga garin da ya saba fita dani.
Sanye na ke da Atamfa Riga da sikat sai na Daura saukakken Dankwalina hoda na shafa da man baki, da wuri na gama abinci Farar Shinkafa da wake da Miya Tunda ina da kayan miya satin da ya wuce mun je kasuwa mun yo Cafane mai yawa.
Ina jin an fara knookig din kofata na Mike da Sauri Farinciki ya cika zuciyata sanin da na yi Assadiq ne sai dai ina zuwa na bude sai da na Rage Fara'ata ganin ba wanda na yi tunanin gani ba ne.
Maman Sulaihat ce matar da ta tare a falt din kusa da na Fadila.
Yake na yi mata bata ma jira mun gaisa ba ta tureni kad'an ta shigo Cikin Dakin ta na fadin"Ina ce dai megidan bai dawo ba ko?
Sai da na Rufe kofar sannan na biyo bayanta ina Fad'in"Bai dawo ba Mama."
Saboda Mama na ke kiranta Tunda ta Haifeni ya'ya gareta zaka zaka zaka mata da maza, biyu mata biyu sun yi aure, sannan ta na da budurwa yanzu a gabanta da balaggagen Namiji.
Ko da nazo har ta samu waje ta zauna ta yi rashe raahe ta na faman washemin Fararan hakoranta masu Dauke da hakorin makkanta ya na tashin kyalli.
Kujeran da ke fuskantarta na samu na zauna ina gaisheta ta amsa cikin Fara'arta, ni har mamaki na ke yi yadda ta ke son shigemin Alhalin nasan su Fadila sun gayamata komai game dani Tunda tun bayan tarewarta suna hulda da ita, ita ma d'in ta na Huld'a da su.
Abunda na lura da matar bata san ta girma ba, ba ruwanta da shigema yara sa'anin ya'yanta,  sannan ga surutu haka zata zo ta yi ta min surutu ta na dukan ruwan cikina kaza an yi kaza ni dai ban taba bata Fuska ba.
Sau d'aya na taba shiga Dakinta itama matsamin tayi sai na shiga na Duba kaya bayan ta je kano ta dawo, da yake babbar yar kasuwa ne babu abunda bata siyarwa kama daga Atamfa leshi, materila, Dogayen Riguna na Hajiya Maryam's Eygptian Abaya +201123302418
Saboda ingancin su yasa ta ke sara a wajenta, ga takalma, zannuwan gado komai da kuka sani ba abunda bata siyarwa.
Babbar yar kasuwa ce sosai to ta tab'amin matsamin na Shiga naga kayan na saka albarka Tundaga Lokacin ta cigaba da matsamin da cewa ban yi ma megidana tallah ba ne a yi mata ciniki.
Yanzu ma bayan shigowarta mganar ta faramin cikin mirmishi nace"na gaya masa yace ba shi da kudi ammh in ya samu zaki jimu."
Cikin yar dariyanta tace"Ai bakomai wlh waye baisan yadda Rayuwar nan ta yi Tsada ba yar nan? Ai mazaje na kokari wlh Allah dai ya saka musu da Hairan."
Na amsa mata da Ameen hankalina na kan agogon wayata naga har Biyar Saura Assadiq bai dawo ba.
Sama sama naji ta na fadin"Wai a ina mijin naki ya ke aiki ne? Naga da Sassafe ya kan fita?
Kallonta na yi cikin mamaki kafin nace"Bansani ba."
Cikin mamaki tace"Baki sani ba fa kika ce?
Cikin son kauda zencen nace"Eh mana Tunda ban taba zuwa ba, na dai san yana aiki da wani kamfani ne."
Jin haka yasa sai ta yi shuru ganin yadda na Had'e fuskata.
Sai ta basar cikin tafa Hannu ta fara mgana da cewa"Ke yar nan na tab'a ki da Alheri sai naji wani Labari a bakin makotan zaman ki?
Cikin mamaki na kalleta kafin nace"Wani Labari?
Ai sai ta gyara zama kafin tace"Fadila da Ummi suka sameni har daki suna gayamin wai na kiyaye ki, kina da Farar kafa, kaza da kaza maganganu dai kala kala wai har suna fadin kin yi aure aure kina talauta mazan da kika aura har fa Wanchan yar fara ta na ce min na yi a sannu kada na Rabeki ki yi sanadiyar karayan arzikiina."
Har ta gama mgana ina kallonta Daman ai nasan za'a rina sai naji raina bai baci ba.
Cikin Sanyin Murya nace"Ai gaskiya suka fad'a miki"
Sai ta wani tabe baki kafin tace"Wani gaskiyan, tuni na warware su dukkansu nace ni ba'a haka dani, kin gani nan wlh nasan Allah kuma ina da Ikilasi na kuma san Tauhidi na kuma san Allah ke yi ba wani ba tuni na zagesu na Fattake su yi ni har za su nuna min wannan mganar? Ni da kanwar uwata ta haifi yarinya sak irin ki itama duk wanda ta aura sai bala'ai su rika fad'a musu auranta Biyar wannan na Shiddan bai dad'e ba shima hukumar Costume ta kame kayan mijin, kuma wajen cucukun Fitowa da kayan sai dai komai na shi ya kare karkenta dai kannensa suka mata Duka suka saka ya saketa da cewar itace sanadin Faruwar haka jama'a ina zamu kai kan mu a wannan Rayuwar sam ba Allah a ran mu?
Ta fad'a ta na wani rike Hab'a irin abun ya Dameta.
Sai na kasa mgana a raina ina fad'in daman akwai mata ma su ire iren kaddara na?
Kafin ma na tambayeta ta fara bani Labarin komai tundaga Tushe sai ga shi ina sharan kwallar Tausayin yarinyar nan sai naji ashe ni nawa mai Sauki ne, ta na fad'amin duk inda yarinyar nan ta zauna na Sati daya sai anga bala'i da Iftila'i.
Ni ina ganin kaina ashe akwai wasu wad'anda suke Fuskarta mummunar Rayuwar da ta fi nawa, ashe ashe ni yar aljanna ce.
Saboda yadda Hankalin mu ya tafi yasa bamu ji buga kofar ba sai da naji kiran wayata dake gefe.
Da Sauri na Duba sai naga Assadiq ne ina rawan jiki na Daga.
Cikin Dakushewar Murya yace"Ki na ina ne? Ina buga kofa baki nan ne?
Da Sauri na mike ina Fad'in"Ina nan mana ban ji ba ne."
Ganin na Nufi kofa yasa ta mike ta na fadin"Na shiga uku ba dai megidan ne ya dawo ba ko?
Kai Tsaye nace mata shine ya dawo.
Sai ta mike tana gyare gyaren mayafi ta na fad'in"An yi abun kunya ke kuma ba sai ki fad'amin ya na hanya ba."
Ni dai bam kara kulata ba na nufi kofa na Bude ya na tsaye rataye jakarsa sai Wata Leda dake hannunsa.
Ina kauce ma kallonsa na mika hannu zan karbi' ledan hannunsa ina Fadin"Sannu da zuwa."
Hanani Ledan ya yi ya maida ledan bayansa ya na kallon idanuwana.
Cikin mamaki yace"Me ya faru? Naga idanuwan ki sun sauya ne, ko kuka yi ne?
Kafin na samu zarafin mgana Sai ga Maman Sulaihat ta na yar dariya yace"Sannu da zuwa."
A dakune ya amsa mata ya na kallona cikin mamaki.
Da Sauri nace"Ta shigo mu gaisa ne." sai ya  matsa ya bata hanya ta fita ta na cemin sai an juma.
Sai da ta fita sannan shima ya shigo ni kuma na kulle kofar na bi bayansa.
Ya na Tsaye a tsakiyar falon ina Shigowa ya mikamin ledan hannunsa Lokaci d'aya ya na fadin"Fruit ne ki yanka min"
Da Toh na amsa kafin na karb'a, shi kuma sai kawai ya nufi hanyar cikin Dakin ya na kara fad'in"Zan yi wanka."
Sai na
Showing 69001 words to 72000 words out of 98628 words